Back to Languages

Hausa - Chapter 18

Translation by Abubakar Mahmood Jummi

Verse 1

Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya saukar da Littafi a kan bawansa kuma bai sanya karkata ba a gare shi

Verse 2

Madaidaici, domin Ya yi gargaɗi da azaba mai tsanani daga gare shi, kuma Ya yi bushara ga muminai, waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai da (cewa) suna da wata lada mai kyau

Verse 3

Suna masu zama a cikinta har abada

Verse 4

Kuma Ya yi gargaɗi ga waɗanda* suka ce: "Allah yana da ɗa

Verse 5

Ba su da wani ilmi game da wannan magana, kuma iyayensu ba su da shi, abin da ke fita daga bakunansu ya girma ga ya zama kalmar faɗa! Ba su faɗan kome face ƙarya

Verse 6

To, ka yi kusa ka halaka ranka a gurabbansu, wai domin ba su yi imani da wannan labari ba saboda baƙin ciki

Verse 7

Lalle ne Mu, Mun sanya abin da ke kan ƙasa wata ƙawa* ce gare ta, domin Mu jarraba su; wanne daga cikinsu zai zama mafi kyau ga aiki

Verse 8

Kuma lalle Mu, Masu sanya abin da ke a kanta (ya zama) turɓaya ƙeƙasasshiya ne

Verse 9

Ko kuwa ka yi zaton cewa ma'abuta kogo* da allo sun kasance abin mamaki daga ayoyin Allah

Verse 10

A lokacin da samarin suka tattara zuwa ga kogon, sai suka ce: "Ya Ubangijinmu*! Ka ba mu wata rahama daga gare Ka, kuma Ka sauƙaƙe mana (samun) shiriya daga al'amarinmu

Verse 11

Sai Muka yi duka a kan kunnunwansu,* a cikin kogon, shekaru masu yawa

Verse 12

Sa'an nan Muka tayar da su, domin Mu san wane ɗayan ƙungiyoyin biyu suka fi lissafi ga abin da suka zauna na lokacin

Verse 13

Mu ne ke jeranta maka labarinsu da gaskiya. Lalle ne su, waɗansu samari ne. Sun yi imani da Ubangijinsu, kuma Muka ƙara musu wata shiriya

Verse 14

Kuma Muka ɗaure a kan zukatansu, a lokacin da suka tsayu, sa'an nan suka ce: "Ubangijinmu Shi ne Ubangijin sammai daƙasa. Ba za mu kirayi wanin Sa abin bautawa ba. (Idan mun yi haka) lalle ne, haƙiƙa, mun faɗi abin da ya ƙetare haddi a sa'an nan

Verse 15

Ga waɗannan mutanenmu sun riƙi waninSa abin bautawa! Don me ba su zuwa da wata hujja bayyananna a kansu (waɗanda ake bautawar)? To, wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙaga ƙarya ga Allah

Verse 16

Kuma idan kun nisance su su da abin da suke bautawa, face Allah, to, ku tattara zuwa ga kogon sai Ubangijinku Ya watsa muku daga rahamar Sa kuma Ya sauƙaƙe muku madogara daga al'amarinku

Verse 17

Kuma kana ganin rana idan ta fito tana karkata daga kogonsu wajen dama kuma idan ta faɗi tana gurgura su wajen hagu, kuma su, suna a cikin wani fili daga gare shi. Wannan abu yana daga ayoyin Allah. Wanda Allah Ya shiryar, to shi ne mai shiryuwa, kuma wanda Allah Ya ɓatar to ba za ka samar masa wani majiɓinci mai shiryarwa ba

Verse 18

Kuma kana zaton su farkakku ne, alhali kuwa su masu barci ne. Muna juya su wajen dama da wajen hagu, kuma karensu yana shimfiɗe da zira'o'in ƙafafuwansa ga farfajiya (ta kogon). Da ka leka (a kan) su (da) lalle ne, ka juya daga gare su a guje kuma (da) lalle ne ka cika da tsoro daga gare su

Verse 19

Kuma kamar wannan ne Muka tayar da su, domin* su tambayi juna a tsakaninsu. Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Mene ne lokacin da kuka zauna?" suka ce: "Mun zauna yini ɗaya ko sashen yini." Suka ce: "Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da kuka zauna. To, ku aika da ɗayanku, game da azurfarku wannan, zuwa ga birnin**. Sai ya duba wanne ne mafi tsarki ga abin dafawa, sai ya zo muku da abinci daga gare shi. Kuma sai ya yi da hankali, kada ya sanar da ku ga wani mutum

Verse 20

Lalle ne su idan sun kama ku, za su jefe ku, ko kuwa su mayar da ku a cikin addininsu kuma ba za ku sami babban rabo, ba, a sa'an nan har abada

Verse 21

Kuma kamar wancan ne, Muka nuna su (gare su) domin su san lalle wa'adin Allah gaskiya ne, kuma lalle ne Sa'a babu shakka a cikinta. A lokacin da suke jayayyar al'amarinsu a tsakaninsu* sai suka ce: "Ku gina wani gini a kansu, Ubangijinsu ne Mafi sani game da su." Waɗanda suka rinjaya a kan al'amarinsu suka ce: "Lalle mu riƙi masallaci a kansu

Verse 22

Za su ce: "Uku ne da na huɗunsu karensu."Kuma suna cewa, "Biyar ne da na shidansu karensu," a kan jifa a cikin duhu. Kuma suna cewa, "Bakwaine da na takwas ɗinsu karensu."Ka ce: "Ubangijina* ne Mafi saniga ƙidayarsu, babu wanda ya san su face kaɗan."Kada ka yi jayayya bayyananna. Kuma kada ka yi fatawa** ga kowa daga gare su a cikin al'amarinsu

Verse 23

Kuma kada lalle ka ce ga wani abu, "Lalle ni, mai aikatawa ne ga wancan a gobe

Verse 24

Face idan Allah Ya so. Kuma ka ambaci Ubangijinka idan ka manta, kuma ka ce: "¦ammani ga Ubangijina, Ya shiryar da ni ga abin da yake shi ne mafi kusa ga wannan na shiriya

Verse 25

Kuma suka zauna a cikin kogonsu shekaru ɗari uku kuma suka daɗa tara

Verse 26

Ka ce: "Allah ne Mafi sani ga abin da suka zauna. Shi ne da (sanin) gaibin sammai da ƙasa. Mune ne ya yi ganin Sa da jin Sa! Ba su da wani majiɓinci baicin Sa kuma ba Ya tarayya da kowa a cikin hukuncinsa

Verse 27

Ka karanta abin da aka yi wahayi zuwa gare ka, na littafin Ubangijinka. Babu mai musanyawa ga kalmominSa kuma ba za ka sami wata madogara ba daga waninsa

Verse 28

Ka haƙurtar da ranka tare da waɗanda ke kiran Ubangijinsu, safe da maraice, suna nufin yardar Sa. Kuma kada idanunka su juya daga barinsu, kana nufin ƙawar rayuwar duniya.* Kuma kada ka biwanda Muka shagaltar da zuciyarsa daga hukuncin Mu, kuma ya bi son zuciyarsa, alhali kuwa al'amarinsa ya kasance yin ɓarna

Verse 29

Kuma ka ce: "Gaskiya daga Ubangijinku take." Saboda haka wanda ya so, to, ya yi imani, kuma wanda ya so, to, ya kafirta. Lalle ne Mu, Mun yi tattali domin azzalumai wata wuta wadda shamakunta, sun ƙewaye da su. Kuma idan sun nemi taimako sai a taimake su da wani ruwa kamar dabzar mai, yana soye fuskoki. Tir da abin shansu, kuma wutar ta yi munin zama mahutarsu

Verse 30

Lalle ne waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai lalle ne Mu ba Mu tozartar da ladar wanda ya kyautata aiki

Verse 31

Waɗannan suna da gidajen Aljannar zama, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu, ana sanya musu ƙawa, a cikinsu, daga mundaye na zinariya, kuma suna tufantar waɗansu tufafi kore, na alharini raƙiƙi da alharini mai kauri suna kishingiɗe a cikinsu, a kan, karagu. Madalla da sakamakonsu. Kuma Aljanna ta kyautatu da zama wurin hutawa

Verse 32

Kuma ka buga musu misali* da waɗansu maza biyu. Mun sanya wa ɗayansu gonaki biyu na inabobi, kuma Muka kewayesu da itacen dabinai, kuma Muka sanya shuka a tsakaninsu (su gonakin)

Verse 33

Kowace gona daga biyun, ta bayar da amfaninta, kuma ba ta yi zaluncin kome ba daga gare shi. Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙoramu a tsakaninsu

Verse 34

Kuma ɗan itace ya kasance gare shi. Sai ya ce wa abokinsa, alhali kuwa yana muhawara da shi, "Ni ne mafifici daga gare ka a wajen dukiya, kuma mafi izza a wajen jama'a

Verse 35

Kuma ya shiga gonarsa, alhali yana mai zalunci ga kansa, ya ce: "Ba ni zaton wannan za ta halaka har abada

Verse 36

Kuma ba ni zaton sa'a mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan an mayar da ni zuwa ga Ubangijiina, to, lalle ne, zan sami abin da yake mafi alheri daga gare ta ya zama makoma

Verse 37

Abokinsa ya ce masa, alhali kuwa yana muhawara da shi, "Ashe ka kafirta da wanda Ya halitta ka daga turɓaya, sa'an nan daga ɗigon maniyi, sa, an nan Ya daidaita ka, ka zama mutum

Verse 38

Amma ni, shi ne Allah Ubangijina, kuma ba zan tara kowa da Ubangijina ba

Verse 39

Kuma don me, a lokacin da ka shiga gonarka, ka, ce, 'Abin da Allah ya so (shi ke tabbata) babu wani ƙarfi face game da Allah.' Idan ka gan ni, ni ne mafi ƙaranci daga gare ka a wajen dukiya da ɗiya

Verse 40

To, akwai fatan Ubangijina Ya ba ni abin da yake mafi alheri daga gonarka, kuma ya aika azaba a kanta (ita gonarka) daga sama, sai ta wayi gari turɓaya mai santsi

Verse 41

Ko kuma ruwanta ya wayi gari faƙaƙƙe, saboda haka, ba za ka iya nemo shi ba dominta

Verse 42

Kuma aka halaka dukan 'ya'yan itacensa, sai ya wayi gari yana juyar da tafunansa biyu, saboda abin da ya kashe a cikinta, alhali kuwa ita tana kwance a kan rassanta, kuma yana cewa, "Kaitona, da dai ban tara* wani da Ubangijina ba

Verse 43

Kuma wata jama'a ba ta kasance a gare shi ba, waɗanda ke taimakon sa, baicin Allah, kuma bai kasance mai taimakon kansa ba

Verse 44

A can taimako da jiɓinta ga Allah yake. Shi ne kawai Gaskiya, shi ne Mafifici ga lada kuma Mafi fici ga aƙiba

Verse 45

Ka buga musu misalin rayuwar duniya, kamar ruwane wanda Muka saukar da shi daga sama sa'an nan tsirin ƙasa ya garwaya da shi, sa'an nan ya wayi gari dudduga, iska tana shiƙar sa. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan ikon yi ne a kan dukan kome

Verse 46

Dukiya da ɗiya,* su ne ƙawar rayuwar duniya, kuma ayyuka masu wanzuwa na ƙwarai sun fi zama alheri a wurin Ubangijinka ga lada kuma sun fi alheri ga buri

Verse 47

Kuma a ranar da Muke tafiyar da duwatsu, kuma ka ga ƙasa bayyane, kuma Mu tara su har ba Mu bar kowa ba daga gare su

Verse 48

Kuma a gitta* su ga Ubangijinka suna sahu guda, (Mu ce musu), "Lalle ne haƙiƙa kun zo Mana, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lokaci. A'a, kun riya cewa ba za Mu sanya mukuwani lokacin haɗuwa ba

Verse 49

Kuma aka aza littafin ayyuka, sai ka ga masu laifi suna masu jin tsoro daga abin da ke cikinsa, kuma suna cewa "Kaitonmu! Mene ne ga wannan littafi, ba ya barin ƙarama, kuma ba ya barin babba, face ya ƙididdige ta?" Kuma suka sami abin da suka aikata halarce. Kuma Ubangijinka ba Ya zaluntar kowa

Verse 50

Kuma a lokacin da Muka ce wa malaiku, "Ku yi sujada ga Adamu." Sai suka yi sujada face Iblisa, ya kasance daga aljannu sai ya yi fasiƙanci ga barin umurnin Ubangijinsa, To fa, ashe, kuna riƙon sa, shi da zuriyarsa, su zama majiɓinta baicin Ni, alhali kuwa su maƙiya ne a gare ku? Tir da ya zama musanya ga azzalumai

Verse 51

Ban shaida musu halittar sammai da ƙasa ba, kuma ban (shaida musu) halittar rayukansu ba kuma ban kasance mai riƙon masu ɓatarwa (da wani) su zama mataimaka ba

Verse 52

Kuma da ranar da Allah Yake cewa, "Ku kirayi abokan tarayyaTa, waɗanda kuka riya." Sai su kiraye su, sai ba za su karɓa musu ba, kuma Mu sanya Maubiƙa* (Mahalaka) a tsakaninsu

Verse 53

Kuma masu laifi suka ga wuta suka tabbata lalle ne, su masu, auka mata ne, kuma ba su sami majuya ba daga gare ta

Verse 54

Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun jujjuya, a cikin wannan Alƙur'ani, daga kowane irin misali ga mutane (domin su gane, su bi shari'a), kuma mutum ya kasance mafi yawan abu ga jidali

Verse 55

Kuma babu abin da ya hana mutane su yi imani a lokacinda shiriya ta zo musu, kuma su nemi gafara daga Ubangijinsu, face hanyar farko* ta je musu ko kuma azaba ta je musu nau'i-nau'i

Verse 56

Kuma ba Mu aika Manzanni ba face suna masu bayar da bushara kuma masu gargaɗi, kuma waɗanda suka kafirta suna jidali da ƙarya domin su ɓata gaskiya da ita, kuma suka riƙi ayoyi Na da abin da aka yi musu gargaɗi da shi abin izgili

Verse 57

Kuma wane ne mafi zalunci daga wanda aka tunatar game da ayoyin Ubangijinsa, sai ya bijire daga barinsu, kuma ya manta abin da hannayensa suka gabatar? Lalle ne Mu, Mun sanya abubuwan rufi a kan zukatansu domin kada su fahimce shi, kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi, kuma idan ka kiraye su zuwa ga shiriya, to, ba za su shiryu ba, a sa'an nan, har abada

Verse 58

Kuma Ubangijinka Mai gafara ne, Ma'abucin rahama. Da Yana kama su saboda abin da suka sana'anta, lalle ne, da Ya gaggauta azaba a gare su. A'a, suna da lokacin alkawari, (wanda) ba za su sami wata makoma ba, baicinSa

Verse 59

Kuma waɗancan alƙaryu* Mun halaka su, a lokacin da suka yi zalunci, kuma Muka sanya lokacin alkawarin, ga halaka** su

Verse 60

Kuma a lokacin da Musa* ya ce wa yaronsa, "Ba zan gushe ba sai na isa mahaɗar teku biyu, ko in shuɗe da tafiya shekara da shekaru

Verse 61

To, a lokacin da suka isa mahaɗar tsakaninsu sai suka manta kifinsu, sai ya kama tafarkinsa a cikin teku kamar biga

Verse 62

To, a lokacin da suka wuce ya ce wa yaronsa, "Ka kawo mana kalacinmu. Lalle ne haƙiƙa mun haɗu da wahala daga tafiyarmu wannan

Verse 63

(Yaron) ya ce: "Ka gani! A lokacin da muka tattara zuwa ga falalen nan to, lalle ni, na manta kifin, kuma babu abin da yamantar da ni shi, face Shaiɗan, domin kada in tuna shi, sai ya kama tafarkinsa a cikin teku, da mamaki

Verse 64

Ya ce: "Wancan ne abin da muka kasance muna biɗa." Sai suka koma a kan gurabunsu, suna bibiya

Verse 65

Sai suka sami wani bawa daga bayin Mu, Mun ba shi wata rahama* daga wurin Mu, kuma Mun sanar da shi wani ilmi daga gun Mu

Verse 66

Musa ya ce masa, "Ko in bi ka a kan ka sanar da ni daga abin da aka sanar da kai na shiriya

Verse 67

Ya ce: "Lalle ne kai ba za ka iya yin haƙuri tare da ni, ba

Verse 68

Kuma yaya za ka yi haƙuri a kan abin da ba ka kewayeda shi ba ga jarrabawa

Verse 69

Ya ce: "Za ka same ni, in Allah Ya so mai haƙuri kuma ba zan saɓa maka ba ga wani umurni

Verse 70

Ya ce: "To idan ka bi ni to kada ka tambaye ni daga kome sai na labarta maka ambato* daga gare shi

Verse 71

Sai suka tafi har a lokacin da suka hau a cikin jirgi, ya huje shi, ya ce, "Ka huje shi domin ya nutsar da mutanensa? Lalle ne, haƙiƙa, ka zo da wani babban abu

Verse 72

Ya ce: "Ashe ban ce, lalle kai, ba za ka iya yin haƙuri tare da ni ba

Verse 73

Ya ce: "Kada ka kama ni da abin da na manta kuma kada ka kallafa mini tsanani ga al'amarina

Verse 74

Sai suka tafi, har suka haɗu da wani yaro, sai ya kashe shi. Ya ce: "Ashe ka kashe rai tsarkakakke, ba da wani rai ba? Lalle ne haƙiƙa ka zo da wani abu na ƙyama

Verse 75

Ya ce: "Shin, ban ce maka ba, lalle ne kai ba za ka iya yin haƙuri tare da ni ba

Verse 76

Ya ce: "Idan na tambaye* ka daga wani abu a bayanta, to, kada ka abuce ni. Lalle ne, ka isa ga iyakar uzuri daga gare ni

Verse 77

Sai suka tafi, har a lokacin da suka je wa mutanen wata alƙarya, suka nemi mutanenta da su ba su abinci, sai suka ƙi su yi musu liyafa. Sai suka sami wani bango a cikinta yana nufin ya karye, sai (Halliru) ya tayar da shi miƙe. (Musa) ya ce: "Da ka so, lalle ne da ka karɓi ijara a kansa

Verse 78

Ya ce: "Wannan shi ne rabuwar tsakanina da tsakaninka. Za ni gaya maka fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa

Verse 79

Amma Jirgin, to, ya zama na waɗansu matalauta ne suna aiki* a cikin teku, sai na yi niyyar in aibanta shi, alhali kuwa wani sarki ya kasance a gaba gare su, yana karɓewar kowane jirgi (lafiyayye) da ƙwace

Verse 80

Kuma amma yaron, to, uwayensa sun kasance muminai, to, sai muka ji tsoron ya kallafa musu kangara da kafirci

Verse 81

Sai muka yi nufin Ubangijinsu Ya musanya musu mafi alheri daga gare shi ga tsarkakuwa, kuma mafi kusantar tausayi

Verse 82

Kuma amma bangon, to, ya kasance na waɗansu yara biyu ne, marayu a cikin birnin, kuma akwai wata taska tasu a ƙarƙashinsa, kuma ubansu ya kasance sahihin mutum* ne, domin haka Ubangijinka Ya yi nufin su isa iyakar ƙarfinsu, kuma su, su fitar da taskarsu, saboda rahama ne daga Ubangijinka. Kuma ban yi shi ba daga umurnina. Wancan shi ne fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa

Verse 83

Kuma suna tambayar ka daga zulƙarnaini*, ka ce: "Zan karanta muku ambato daga gare shi

Verse 84

Lalle ne Mu Mun ba shi mulki a cikin ƙasa kuma Muka ba shi daga kowane abu, hanya (zuwa ga muradinsa)

Verse 85

Sai ya bi hanya

Verse 86

Har a lokacin da ya isa ga mafaɗar rana, kuma ya same ta tana ɓacewa a cikin wani ruwa mai baƙar laka, kuma ya sami waɗansu mutane a wurinta. Muka ce: "Ya Zulƙarnaini imma dai ka azabtar kuma imma ka riƙi kyautatawa a cikinsu

Verse 87

Ya ce: "Amma wanda ya yi zalunci, to za mu azabta shi, sa'an nan a mayar da shi zuwa ga Ubangijinsa, sai kuma Ya yi masa azaba, azaba abar ƙyama

Verse 88

Kuma amma wanda ya yi imani kuma ya aikata aikin ƙwarai to, za mu yi sakamako a gare shi (watau kyauta) mai kyau*, kuma za mu gaya masa sauƙi daga umurninmu

Verse 89

Sa'an nan kuma ya bi hanya

Verse 90

Har a lokacin da ya isa ga mafitar rana, ya same ta tana fita a kan waɗansu mutane (waɗanda) ba Mu sanya musu wata kariya ba daga barinta

Verse 91

Kamar wancan alhali kuwa haƙiƙa, Mun kewaye da jarrabawa ga abin da ke gunsa

Verse 92

Sa'an nan kuma ya bi hanya

Verse 93

Har a lokacin da ya isa a tsakanin duwatsu biyu, ya sami waɗansu mutane daga gabaninsu. Ba su yi kusa su fahimci magana ba

Verse 94

Suka ce: "Ya Zulƙarnaini! Lalle ne Yajuja da Majuja masu ɓarna ne a cikin ƙasa. To, ko za mu Sanya haraji saboda kai, a kan ka sanya wani danni a tsakaninmu da tsakaninsu

Verse 95

Ya ce: "Abin da Ubangijina Ya mallaka mini, a cikinsa ya fi zama alheri. Sai ku taimakeni da ƙarfi, in sanya babbar katanga a tsakaninku da tsakaninsu

Verse 96

Ku kawo mini guntayen baƙin ƙarfe". (Suka kai masa) har a lokacin da ya daidaita a tsakanin duwatsun biyu (ya sanya wuta a cikin ƙarfen) ya ce: "Ku hura (da zugazugai)." Har a lokacin da ya mayar da shi wuta, ya ce: "Ku kawo mini gaci (narkakke) in zuba a kansa

Verse 97

Domin haka ba za su iya hawansa ba, kuma ba za su iya hujewa gare shi ba

Verse 98

Ya ce: "Wannan wata rahama ce daga Ubangijina. Sai idan wa'adin* Ubangijina ya zo, ya mayar da shi niƙaƙƙe. Kuma wa'adin Ubangijina ya kasance tabbatacce

Verse 99

Kuma Muka bar sashensu a ranar nan, yana garwaya a cikin sashe, kuma aka busa a cikin ƙaho sai muka tara su, tarawa

Verse 100

Kuma Muka gitta Jahannama, a ranar nan ga kafirai gittawa

Verse 101

Waɗanda idanunsu suka kasance a cikin rufi daga tuna* Ni, kuma sun kasance ba su iya saurarawa

Verse 102

Shin fa, waɗanda suka kafirta sun yi zaton (daidai ne) su riƙi waɗansu bayiNa*, majiɓinta baic iNa? Lalle ne, Mun yi tattalin Jahannama ta zama liyafa ga kafirai

Verse 103

Ka ce: "Ko mu gaya muku game da mafifita hasara ga ayyuka

Verse 104

Waɗanda aikinsu ya ɓace a cikin rayuwar duniya, alhali kuwa suna zaton lalle ne su, suna kyautata, (abin da suke gani) aikin ƙwarai

Verse 105

Waɗancan ne waɗanda suka kafirta da ayoyin Ubangijinsu, da kuma haɗuwa da Shi, sai ayyukansu suka ɓaci. Saboda haka ba za Mu tsayar musu da awo* ba a Ranar ¡iyama

Verse 106

Wancan ne sakamakonsu shi ne Jahannama, saboda kafircinsu, kuma suka riƙi ayoyi Na da Manzanni Na abin izgili

Verse 107

Lalle ne, waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Aljannar Firdausi ta kasance ita ce liyafa a gare su

Verse 108

Suna madawwama a cikinta, ba su neman makarkata daga barinta

Verse 109

Ka ce: "Da teku* ta kasance tawada ga (rubutun) kalmomin Ubangijina, lalle ne da tekun ta ƙare a gabanin kalmomin Ubangijina su ƙare, kuma koda mun je da misalinsa domin ƙari

Verse 110

Ka ce: "Ni, mutum ne kawai kamarku, ana yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, saboda haka wanda ya kasance yana fatan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kowa ga bauta wa Ubangijinsa