Back to Languages

    Hausa - Chapter 23

    Translation by Abubakar Mahmood Jummi

    Verse 1

    Lalle ne, Muminai* sun sami babban rabo

    Verse 2

    Waɗanda suke a cikin sallarsu masu tawali'u ne

    Verse 3

    Kuma waɗanda suke, sudaga barin yasassar magana, masu kau da kai ne

    Verse 4

    Kuma waɗanda suke ga zakka masu aikatawa ne

    Verse 5

    Kuma waɗanda suke ga farjojinsu masu tsarewa ne

    Verse 6

    Face a kan matan aurensu, ko kuwa abin da hannayen damansu suka mallaka to lalle su ba waɗanda ake zargi, ba, ne

    Verse 7

    Saboda haka wanda ya nemi abin da ke bayan wancan, to, waɗancan su ne masu ƙetarewar haddi

    Verse 8

    Kuma waɗanda suke, suga amanoninsu da alkawarinsu masu tsarewa ne

    Verse 9

    Kuma da waɗanda suke, su a kan sallolinsu suna tsarewa

    Verse 10

    Waɗannan, su ne magada

    Verse 11

    Waɗanda suke gadon (Aljannar) Firdausi,* su a cikinta madawwama ne

    Verse 12

    Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga laka

    Verse 13

    Sa'an nan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya

    Verse 14

    Sa'an nan kuma Muka halitta shi gudan jini, sa'an nan Muka halitta gudan jinin tsoka, sa'an nan Muka halitta tsokar ta zama ƙasusuwa, sa'an nan Muka tufatar da ƙasusuwan da wani nama sa'an nan kuma Muka ƙaga shi wata halitta dabam. Saboda haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyawun masu halittawa

    Verse 15

    Sa'an nan kuma ku, bayan wannan, lalle ne masu mutuwa ne

    Verse 16

    Sa'an nan kuma lalle ne ku a Ranar alkiyama, za a iayar da ku

    Verse 17

    Kuma lalle ne haƙiƙa Mun halitta, a samanku, hanyoyi bakwai, kuma ba Mu kasance, daga barin halittar, Masu shagala ba

    Verse 18

    Muka saukar da ruwa daga sama bisa gwargwado, sa'an nan Muka zaunar da shi a cikin ƙasa alhali, lalle ne Mu, a kan tafiyar da shi, Masu iyawa ne

    Verse 19

    Sai Muka ƙaga muku, game da shi (ruwan), gonaki daga dainai da inabobi, kuna da, a cikinsu, 'ya'yan itacen marmari masu yawa, kuma daga gare su kuke ci

    Verse 20

    Da wata itaciya,* tana fita daga dutsin Saina'a, tana tsira da man shafawa, da man miya domin masu ci

    Verse 21

    Kuma lalle ne kuna da abin lura a cikin dabbobin ni'imomi Muna shayar da ku daga abin da yake a cikinsu, kuma kuna da a cikinsu abubuwan amfani* masu yawa, kuma daga gare su kuke ci

    Verse 22

    Kuma a kansu da a kan jirgin ruwa ake ɗaukar ku

    Verse 23

    Kuma lalle ne haƙiƙa Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautawa waninsa. Shin, to, ba za ku yi taƙawa ba

    Verse 24

    Sai mashawarta waɗanda suka kafirta daga mutanensa, suka ce: "Wannan ba kowa ba ne, face mutum misalinku, yana nufin ya ɗaukaka a kanku. Da Allah Ya so, lalle ne da Ya saukar da Mala'iku, Ba muji (kome) ba, game da wannan, a cikin ubanninmu na farko

    Verse 25

    Shi bai zamo kowa ba face wani namiji ne, a gare shi akwai hauka, sai ku yi jinkiri da shi har wani lokaci

    Verse 26

    Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka taimakeni Saboda mutanena sun ƙaryata ni

    Verse 27

    Sai Muka yi wahayi zuwa gare shi. "Ka sana'anta jirgin bisa ga idon Mu, da wahayinMu. To, idan umuminMu ya je, kuma tanda ta ɓuɓɓuga da ruwa, to, ka shigar a cikinta daga kome, ma'aura biyu, da iyalanka, sai wanda Magana ta gabata a kansa, daga gare su, kuma kada ka roƙe Ni (saboda wani) a cikin waɗanda suka yi zalunci, lalle ne su waɗanda ake nutsarwa ne

    Verse 28

    Sa'an nan idan ka daidaitu kai da waɗanda ke tare da kai a kan jirgin, sai ka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya tsirar damu daga mutane azzalumai

    Verse 29

    Kuma ka ce: 'Ya Ubangijina! Ka saukar da ni, saukarwa mai albarka. Kuma Kai ne Mafi alherin masu saukarwa

    Verse 30

    Lalle ne a cikin wancan akwai ayoyi, ko da yake Mun kasance, haƙiƙa' Masu jarrabawa

    Verse 31

    Sa'an nan kuma Muka ƙaga wani ƙarni na waɗansu dabam daga bayansu

    Verse 32

    Sai Muka aika a cikinsu Manzo daga gare su. "Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautawa, sai Shi. Shin to, ba za ku yi taƙawa ba

    Verse 33

    Mashawarta daga mutanensa, waɗanda suka kafirta kuma suka ƙaryata game da haɗuwa da Lahira, kuma Muka ni'imtar da su a cikin rayuwar duniya, suka ce: "Wannan ba kowa ba face wani mutum ne kamarku, yana ci daga abin da kuke ci daga gare shi, kuma yana sha daga abin da kuke sha

    Verse 34

    Kuma lalle ne idan kun yi ɗa' a ga mutum misalinku, lalle ne, a lokacin nan, haƙiƙa, ku masu hasara ne

    Verse 35

    Shin, yana yi muku wa'adin (cewa) lalle ku, idan kun mutu kuma kuka kasance turɓaya da kasusuwa lalle ne ku waɗanda ake fitarwa ne

    Verse 36

    Faufau faufau ga abin da ake yi muku wa'adi da shi

    Verse 37

    Rayuwa ba ta zama ba face rayuwarmu ta duniya, muna mutuwa kuma muna rayuwa,* kuma ba mu zama waɗanda ake tayarwa ba

    Verse 38

    Bai zama kowa ba face namiji, ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma ba mu zama, saboda shi, masu imani ba

    Verse 39

    Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka taimake ni saboda sun ƙaryata ni

    Verse 40

    Ya ce: "Daga abu kaɗan, lalle ne za su wayi gari suna masu nadama

    Verse 41

    Sai tsawa ta kama su da gaskiya, sai Muka sanya su tunkuɓa. Saboda haka nisa ya tabbataga mutane azzalumai

    Verse 42

    Sa'an kuma Muka ƙaga halittar wasu ƙarnoni dabam daga bayansu

    Verse 43

    Wata al'umma ba ta gabatar ajalinta, kuma ba za su jinkirta ba

    Verse 44

    Sa'an nan kuma Muka aika da ManzanninMu jere a koda yaushe Manzon wata al'umma ya je mata, sai su ƙaryata shi, saboda haka Muka biyar da sashensu ga sashe, kuma Muka sanya su labarun hira. To, nisa ya tabbata ga mutane (waɗanda) ba su yin imani

    Verse 45

    Sa'an nan kuma Muka aika Musa da ɗan'uwansa Haruna, game da ayoyin Mu da, dalili bayyananne

    Verse 46

    Zuwa ga Fir'auna da majalisarsa, sai suka kangara, alhali sun kasance mutane ne marinjaya

    Verse 47

    Sai suka ce: "Shin, za Mu yi imani saboda wasu mutane biyu misalinmu, alhali kuwa mutanensu a gare mu, masu bauta ne

    Verse 48

    Sai suka ƙaryata su saboda haka suka kasance halakakku

    Verse 49

    Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun bai wa Musa littafi tsammaninsu* za su shiryu

    Verse 50

    Kuma Mun sanya ¦an Maryama, shi da uwarsa wata aya* Kuma Muka tattara su zuwa ga wani tsauni ma'abucin natsuwa da maremari

    Verse 51

    Ya ku Manzanni! Ku ci daga abubuwa masu daɗi* kuma ku aikata aikin ƙwarai. Lalle Niga abin da kuke aikatawa, Masani ne

    Verse 52

    Kuma lalle ne, wannan al'ummarku ce, al'umma guda, kuma Ni, Ubangijinku ne, sai ku bi Ni da taƙawa

    Verse 53

    Sai (al'ummar) suka yanyanke al'amarinsu a tsakaninsu guntu-guntu,* kowace ƙungiya suna masu farin ciki da abin da yake a gare su

    Verse 54

    To, ka bar su a cikin ɓatarsu har a wani lokaci

    Verse 55

    Shin, suna zaton cewa abin da Muke taimakon su da shi daga dukiya da ɗiya

    Verse 56

    Muna yi musu gaggawa ne a cikin alherori

    Verse 57

    Lalle ne waɗanda suke masu sauna sabo da tsoron Ubangijinsu

    Verse 58

    Da waɗanda suke, game da ayoyin Ubangijinsu suna imani

    Verse 59

    Da waɗanda suke game da Ubangijinsu ba su yin shirki

    Verse 60

    Da waɗanda ke bayar da abin da suka bayar, alhali kuwa zukatansu suna tsorace domin suna komawa zuwa ga Ubangijinsu

    Verse 61

    Waɗancan suna gaggawar tsere a cikin ayyukan alheri, alhali kuwa suna masu tserewa zuwa gare su (ayyukan alheri)

    Verse 62

    Kuma ba Mu kallafa wa rai face abin iyawarsa, kuma a wurinMu akwai wani Littafi wanda yake magana da gakiya, kuma su ba a zaluntar su

    Verse 63

    A'a, zukatansu suna cikin jahilci daga wannan (magana), kuma suna da waɗansu ayyuka, baicin wancan, su a gare su, masu aikatawa ne

    Verse 64

    Har idan Mun kama mani'imtansu da azaba, sai ga su suna hargowa

    Verse 65

    Kada ku yi hargowa a yau, lalle ne ku, daga gare Mu ba a taimakon ku

    Verse 66

    Lalle ne, ayoyiNa sun kasance ana karatun su a kanku, sai kuka kasance, a kan dugaduganku, kuna komawa baya

    Verse 67

    Kuna masu girman kai gare shi (Annabi), da hira kuna alfasha

    Verse 68

    Shin fa, ba su yi ta'ammalin maganar (Alƙur'ani) ba, ko abin da bai je wa ubanninsu na farko ba ne ya je musu

    Verse 69

    Ko ba su san Manzonsu ba ne domin haka suke masu musu a gare shi

    Verse 70

    Ko suna cewa, "Akwai hauka gare shi?" A'a, ya zo musu da gaskiya, alhali kuwa mafi yawansu, ga gaskiya, masu ƙi ne

    Verse 71

    Kuma da gaskiya (Alƙur'ani) ya bi son zuciyoyinsu, haƙiƙa da sammai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sun ɓaci. A'a, Mun tafo musu da ambaton* (darajar) su, sa'an nan su daga barin ambaton su masu bijirewa ne, bijirewa

    Verse 72

    Ko kana tambayar su wani haraji ne (a kan iyar da Manzanci a gare su)? To, harajin Ubangijinka ne mafi alheri kuma Shi ne Mafi alherin masu ciyarwa

    Verse 73

    Kuma lalle ne kai haƙiƙa kana kiran su zuwa ga hanya madaidaiciya

    Verse 74

    Kuma lalle waɗanda ba su yi imani da Lahira ba masu karkacewa daga hanya ne

    Verse 75

    Kuma da Mun ji tausayinsu, kuma Muka kuranye musu abin da yake tare da su na cuta, lalle ne da sun yi zurfi a cikin ɓatarsu, suna ɗimuwa

    Verse 76

    Kuma lalle ne haƙiƙa Muna kama su da azaba* sai dai ba su saukar da kai ba, ga Ubangijinsu, kama ba su yin tawali'u

    Verse 77

    Har idan Mun buɗe, akansu, wata ƙofa mai azaba mai tsanani sai ga su a cikinta suna masu mugi

    Verse 78

    Kuma Shi ne Wanda Ya ƙaga halittar ji da gani da zukata dominku. Kaɗan ƙwarai kuke godewa

    Verse 79

    Kuma Shi ne Ya halitta ku a cikin ƙasa, kuma zuwa gare Shi ake tayar da ku

    Verse 80

    Kuma Shi ne Wanda Yake rayarwa, kuma Yana matarwa, kuma a gare Shi ne saɓawar dare da yini take. Shin, to, ba za ku hankalta ba

    Verse 81

    A'a, sun faɗi misalin abin da na farko suka faɗa

    Verse 82

    Suka ce: "Shin idan mun mutu kuma muka kasance turɓaya da ƙasusuwa shin lale ne mu haƙiƙa waɗanda ake tayarwa ne

    Verse 83

    Lalle ne, haƙiƙa, an yi mana wa'adi, mu da ubanninmu ga wannan a gabani, wannan abu bai zama kome ba, face tatsuniyoyin na farko

    Verse 84

    Ka ce: "Wane ne da mulkin ƙasa da wanda ke a cikinta, idan kun kasance kuna sani

    Verse 85

    Za su ce: "Ta Allah ne." Ka ce, "Shin, to, ba za ku yi tunani ba

    Verse 86

    Ka ce: "Wane ne Ubangijin sammai bakwai kuma Ubangijin Al'arshi mai girma

    Verse 87

    Za su ce: "Na Allah ne." Ka ce, "Shin, to, ba za ku bi Shi da taƙawa ba

    Verse 88

    Ka ce: "Wane ne ga hannunsa mallakar kowane abu take alhali kuwa shi yana tsarewar wani, kuma ba a tsare kowa daga gare shi, idan kun kasance kuna sani

    Verse 89

    Za su ce: "Ga Allah yake." Ka ce: "To, yaya ake sihirce ku

    Verse 90

    A'a, Mun zo musu da gaskiya, kuma lalle ne su, haƙiƙa, maƙaryata ne

    Verse 91

    Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma babu wani abin bautawa tare da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne da kowane abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, da waɗansu sun rinjaya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantawa

    Verse 92

    Masanin ɓoye da bayyane. sa'an nan Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka

    Verse 93

    Ka ce: "Ya Ubangijina! Ko dai Ka nuna mini abin da ake yi musu wa'adi da shi

    Verse 94

    Ya Ubangijina, to, kada Ka sanya ni a cikin mutane azzalumai

    Verse 95

    Kuma lalle ne Mu haƙiƙa Masu iyawa ne a kan Mu nuna maka abin da Muke yi musu wa'adi da shi

    Verse 96

    Ka tunkuɗe cuta da wadda take ita ce mafi kyau. Mu ne Mafi sani game da abin da suke siffantawa

    Verse 97

    Ka ce: "Ya Ubangijina, ina neman tsari da Kai daga fizge-fizgen Shaiɗanu

    Verse 98

    Kuma ina neman tsari da Kai, ya Ubangijina! Domin kada su halarto ni

    Verse 99

    Har idan mutuwa ta je wa ɗayansu, sai ya ce: "Ya Ubangijina, Ku mayar da ni (duniya)

    Verse 100

    Tsammanina in aikata aiki na ƙwarai cikin abin da na bari." Kayya! Lalle ne ita kalma ce, shi ne mafaɗinta, alhali kuwa a baya gare su akwai wani shamaki har ranar da za a tayar da su

    Verse 101

    Sa'an nan idan an yi busa a cikin ƙaho, to, babu dangantakoki a tsakaninsu a ranar nan kuma ba za su tambayi junansu ba

    Verse 102

    To, wadanda sikelinsu ya yi nauyi, to, waɗannan su ne masu babban rabo

    Verse 103

    Kuma waɗanda sikelinsu ya yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu suna madawwama a cikin Jahannama

    Verse 104

    Fuskokinsu suna balbalar wuta, kuma su a cikinta masu yagaggun leɓɓa daga haƙora ne

    Verse 105

    Shin, ayoyiNa ba su kasance ana karanta su a kanku ba sai kuka kasance game da su kuna ƙaryatawa

    Verse 106

    Suka ce: "Ya Ubangijinmu, shaƙawace ta rinjaya a kanmu, kuma mun kasance mutane ɓatattu

    Verse 107

    Ya Ubangjinmu! Ka fitar da mu daga gare ta, sa'an nan idan mun koma, to, lalle ne, mu ne masu zalunci

    Verse 108

    Ya ce: "Ku tafi (da wulakanci) a cikinta. Kada ku yi Mini magana

    Verse 109

    Lalle ne waɗansu ƙungiyoyi daga bayiNa sun kasance suna cewa, "Ya Ubangijinmu! Mun yi imani, sai Ka gafarta mana, kuma Ka yi mana rahama, kuma Kai ne Mafi alherin masu tausayi

    Verse 110

    Sai kuka riƙe su leburori har suka mantar da ku ambato Na kuma kun kasance, daga gare su kuke yin dariya

    Verse 111

    Lalle ne Ni Ina saka musu a yau, saboda abin da suka yi wa haƙuri. Domin lalle ne su su ne masu samun babban rabo

    Verse 112

    Ya ce: "Nawa kuka zauna a cikin ƙasa na ƙidayar shekaru

    Verse 113

    Suka ce: "Mun zauna a yini ɗaya ko rabin yini, sai ka tambayi masu ƙidayawa

    Verse 114

    Ya ce: "Ba ku zauna ba face kaɗan, da dai kun kasance kuna sani

    Verse 115

    Shin, to, kun yi zaton cewa Mun halitta ku ne da wasa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, ba za ku komo ba

    Verse 116

    Allah Mamallaki gaskiya, Ya ɗaukaka. Babu abin bautawa, face Shi. Shi ne Ubangijin Al'arshi, mai daraja

    Verse 117

    Kuma wanda ya kira, tare da Allah, waɗansu abubuwan bautawa na dabam, ba yana da wani dalili game da shi (kiran) ba, to hisabinsa yana wurin Ubangijinsa kawai. Lalle ne, kafirai ba su cin nasara

    Verse 118

    Kuma ka ce: "Ya Ubangijina! Ka yi gafara, Ka yi rahama, kuma Kai ne Mafi alherin masu rahama