Back to Languages

    Hausa - Chapter 53

    Translation by Abubakar Mahmood Jummi

    Verse 1

    Ina rantsuwa da tauraron, a lokacin da ya faku

    Verse 2

    Ma'abucinku bai ɓata ba, kuma bai ƙetare haddi ba

    Verse 3

    Kuma ba ya yin magana daga son zuciyarsa

    Verse 4

    (Maganarsa) ba ta zamo ba, face wahayi ne da ake aikowa

    Verse 5

    (Mala'ika) mai tsananin ƙarfi *ya sanar da shi

    Verse 6

    Ma'abucin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita

    Verse 7

    Alhali kuwa yana a sararin sama mafi daukaka

    Verse 8

    Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurowa

    Verse 9

    Har ya kasance gwargwadon zira'i biyu, ko kuma abin da ya fi kusa

    Verse 10

    Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bawan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa)

    Verse 11

    Zuciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba

    Verse 12

    Shin, za ku yi masa musu a kan abin da yake gani

    Verse 13

    Kuma lalle ya gan shi, haƙiƙatan, a wani lokacin saukarsa

    Verse 14

    A wurin da magaryar tuƙewa take

    Verse 15

    A inda taken, nan Aljannar makoma take

    Verse 16

    Lokacin da abin da yake rufe magaryar tuƙewa ya rufe ta

    Verse 17

    Ganinsa* bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba

    Verse 18

    Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma* daga ayoyin Ubangijinsa

    Verse 19

    Shin, kun ga Lata da uzza

    Verse 20

    Da (wani gunki wai shi) Manata, na ukunsu

    Verse 21

    Ashe, ku ne da ɗa namiji Shi (Allah) kuma da ɗiya mace

    Verse 22

    Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe

    Verse 23

    Waɗannan ba kome ba ne face sunaye, waɗanda kuka ambace su da su, ku da uwayenku. Allah bai saukar da wani dalili game da su ba. (Kafirai) ba su biyar kome face zato da abin da rayukansu ke so, Alhali kuwa shiriyar* ta daga wajen Ubangijinsu, ta je musu (sai suka bar ta suka koma wa zaton)

    Verse 24

    Ko (an fai cewa) mutum zai sami abin da yake guri

    Verse 25

    To, Lahira da duniya na Allah kawai ne (wanda ya neme su daga wani, ya yi kuskure)

    Verse 26

    Akwai mala'iku da yawa a cikin sammai cetonsu ba ya wadatar da kome face bayan Allah Ya yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda

    Verse 27

    Lalle waɗannan da ba su yin imani da Lahira, haƙiƙa suna kiran mala'iku da sunan mace

    Verse 28

    Kuma ba su da wani ilmi game da shi, ba su bin kome face zato alhali kuwa lalle zato ba ya amfanar da kome daga gaskiya

    Verse 29

    Saboda haka sai ka kau da kai daga wanda ya juya baya daga ambaton Mu kuma bai yi nufin kome ba face rayuwar kusa (duniya)

    Verse 30

    Wannan ita ce iyakar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyar Sa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nemi shiriya

    Verse 31

    Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa na Allah kawai ne, domin Ya saka wa waɗanda suka munana da abin da suka aikata, kuma Ya saka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau

    Verse 32

    Waɗanda ke nisantar manyan zunubai da abubuwan alfasha, face ƙananan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gafara ne, Shi ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lokacin da Ya ƙaga halittarku daga ƙasa, kuma a lokacin da kuke tayuna a cikin cikannan uwayenku. Saboda haka, kada ku tsarkake* kanku, Shi ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa

    Verse 33

    Shin, ka ga wannan da ya juya baya

    Verse 34

    Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa

    Verse 35

    Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Saboda haka yana ganin gaibin

    Verse 36

    Ko kuwa ba a ba shi labari ba ga abin da yake a cikin Littafan Musa

    Verse 37

    Da Ibrahim wanda ya cika alkawari

    Verse 38

    Cewa wani rai mai kayan laifi ba ya ɗaukar kayan laifin wani

    Verse 39

    Kuma mutum ba shi da kome face abin da ya aikata

    Verse 40

    Kuma lalle, aikinsa za a gan shi

    Verse 41

    Sa'an nan a saka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni

    Verse 42

    Kuma lalle, makomar zuwa Ubangijinka kawai take

    Verse 43

    Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kuka

    Verse 44

    Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya kashe, kuma Ya rayar

    Verse 45

    Kuma lalle Shi ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace

    Verse 46

    Daga wani ɗigon ruwa guda a lokacin da ake jefa shi a cikin mahaifa

    Verse 47

    Kuma a kansa ne ƙaga halitta ta biyu take

    Verse 48

    Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya azurta, kuma Ya wadatar

    Verse 49

    Kuma lalle, Shi, Shi ne Ubangijin Shi'ira

    Verse 50

    Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya halaka Adawa na farko

    Verse 51

    Da Samudawa, sa'an nan bai rage su ba

    Verse 52

    Da mutanen Nuhu a gabanin haka, lalle su sun kasance mafi zalunci kuma mafi girman kai

    Verse 53

    Da waɗanda aka birkice *ƙasarsu, Ya kayar da su

    Verse 54

    Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su

    Verse 55

    To, da wace daga ni'imomin Ubangijinka kake *yin shakka

    Verse 56

    wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin masu gargaɗi na farko

    Verse 57

    Makusanciya* fa, ta yi kusa

    Verse 58

    Babu wani rai, banda Allah, mai iya bayani gare ta

    Verse 59

    Shin, kuma daga wannan *labari kuke mamaki

    Verse 60

    Kuma kuna yin dariya, kuma ba ku yin kuka

    Verse 61

    Alhali kuna masu wasa

    Verse 62

    To, ku yi tawali'u *ga Allah, kuma ku bauta (masa)