Back to Languages
Hausa - Chapter 55
Translation by Abubakar Mahmood Jummi
Verse 1
(Allah) Mai rahama
Verse 2
Ya sanar da Alƙur'ani
Verse 3
Ya halitta mutum
Verse 4
Ya sanar da shi bayani (magana)
Verse 5
Rana da wata a kan lissafi suke
Verse 6
Kuma tsirrai masu yaɗo da itace suna tawalu'i
Verse 7
Kuma sama Ya ɗaukaka ta, Kuma Ya aza sikeli
Verse 8
Domin kada ku karkatar da sikelin
Verse 9
Kuma ku daidaita awo da adalci, kuma kada ku rage sikelin
Verse 10
Kuma ƙasa Ya aza ta domin talikai
Verse 11
A cikinta akwai 'ya'yan itacen marmari da dabino mai kwasfa
Verse 12
Da ƙwaya mai soshiya da ƙamshi
Verse 13
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangjinku *kuke ƙaryatawa
Verse 14
Ya halitta mutum daga ƙekasasshen yumɓu kumar kasko
Verse 15
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wuta
Verse 16
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 17
Ubangjin mafita biyu na rana, kuma Ubangijin mafaɗa biyu na rana
Verse 18
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 19
Ya garwaya teku biyu (ruwan daɗi da na zartsi) suna haɗuwa
Verse 20
A tsakaninsu akwai shamaki, ba za su ƙetare haddi ba
Verse 21
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 22
Lu'ulu'u da murjani na fita daga gare su
Verse 23
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 24
Kuma Yana da manyan jirage, waɗanda ake ƙagawa a cikin teku kamar manyan duwatsu
Verse 25
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 26
Dukkan wanda ke kanta* mai ƙarewa ne
Verse 27
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa
Verse 28
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 29
wanda ke a cikin sammai da ƙasa yana roƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani
Verse 30
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 31
Za mu ɗauki lokaci saboda ku, ya ku *masu nauyin halitta biyu
Verse 32
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 33
Ya jama'ar aljannu da mutane! Idan kuna iya zarcewa daga sasannin sammai da ƙasa to ku zarce. Ba za ku iya zarcewaba face da wani dalili
Verse 34
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 35
Ana sako wani harshe daga wata wuta a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, ba za ku nemi taimako ba
Verse 36
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 37
Sa'an nan idan sama ta tsage kuma ta zama ja kamar jar fata
Verse 38
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 39
To, a ran nan ba za a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani
Verse 40
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 41
za a iya sanin masu laifi da alamarsu, saboda haka sai a kama kwarkaɗarsu da sawayensu
Verse 42
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 43
Wannan Jahannama ce wadda masu laifi ke ƙaryatawa game da ita
Verse 44
Suna kewaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa
Verse 45
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 46
Kuma wanda ya ji tsoron tsayawa a gaba ga Ubangijinsa yana da Aljanna biyu
Verse 47
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 48
Masu rassan itace
Verse 49
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 50
A cikinsu akwai maremari biyu suna gudana
Verse 51
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 52
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kowane 'ya'yan itacen marmari
Verse 53
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 54
Suna gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufafin alharini mai kauri ne kuma nunannun 'ya'yan itacen Aljannar biyu kusakusa suke
Verse 55
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 56
A cikinsu akwai mata masu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani
Verse 57
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 58
Kamar dai su yaƙutu ne da murjani
Verse 59
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 60
Shin, kyautatawa na da wani sakamako? (A'aha) face kyautatawa
Verse 61
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 62
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidajen Aljanna biyu
Verse 63
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 64
Masu duhun inuwa
Verse 65
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 66
A cikinsu akwai maremari biyu masu kwararar ruwa
Verse 67
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 68
A cikinsu akwai 'ya'yan itacen marmari da dabino darummani
Verse 69
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 70
A cikinsu, akwai wasu mata masu kyawun halaye, masu kyaun halitta
Verse 71
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 72
Masu farin idanu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimomi
Verse 73
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 74
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani
Verse 75
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 76
Suna gincire a kan wasu matasai masu koren launi da katifun Abkara kyawawa
Verse 77
To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa
Verse 78
Sunan Ubangjinka, Mai girman Jalala da Karimci, ya tsarkaka