Back to Languages
Hausa - Chapter 67
Translation by Abubakar Mahmood Jummi
Verse 1
(Allah), Wanda gudanar da mulki yake ga hannun Sa, Ya tsarkaka, kuma Shi Mai iko ne a kan kome
Verse 2
Shi ne Wanda Ya halitta mutuwa da rayuwa domin Ya jarraba ku, Ya nuna waye daga cikinku ya fi kyawon aiki, Shi ne Mabuwayi, Mai gafara
Verse 3
Shi ne wanda Ya halitta sammai bakawi, ɗabaƙoƙi a kan juna, ba za ka ga goggociya ba a cikin halittar (Allah) Mai rahama. Ka sake dubawa, ko za ka ga wata ɓaraka
Verse 4
Sa'an nan ka sake maimaita, dubawa, ganinka zai komo maka, gajiyayye, ba da ganin wata naƙasa ba
Verse 5
Kuma lalle Mun ƙawata samar farko da fitillu, kuma Muka sanya su abin jifa ga shaiɗanu, kuma Muka yi musu tattalin azabar Sa'ir
Verse 6
Kuma waɗanda suka kafirce wa Ubangjinsu na da azabar Jahannama, ta munana ga zamanta makomarsu
Verse 7
Idan an jefa su a cikinta, sai su ji daga gare ta wata ƙara, tana tafasa
Verse 8
Tana kusa ta tsage domin hushi, ko da yaushe aka jefa wani ɓangaren jama'a a cikinta, matsaranta na tambayar su da cewa, "Wani mai gargaɗi bai je muku ba
Verse 9
Sai su ce: "I, lalle wani mai gargaɗi ya je mana, sai muka ƙaryata shi, muka ce, 'Allah bai saukar da kome ba, ba ku cikin kome sai ɓata babba
Verse 10
Kuma suka ce: "Da mun zamo muna saurare, ko muna da hankali, da ba mu kasance a cikin 'yan sa'ir ba
Verse 11
Wato su yi iƙrari da laifinsu. Allah Ya la'ani'yan sa'ir
Verse 12
Lalle waɗanda ke tsoron Ubangjinsu, a ɓoye, suna da wata gafara da wani sakamako mai girma
Verse 13
Kuma ku asirta maganarku ko ku bayyana ta, lalle shi, (Allah), Masani ne ga abin da ke cikin ƙiraza
Verse 14
Ashe, wanda Ya yi halitta ba zai iya saninta ba, alhali kuwa shi Mai tausasawa ne, kuma Mai labartawa
Verse 15
Shi, (Allah), Ya sanya muku ƙasa horarriya, sai ku tafi cikin sasanninta, kuma ku ci daga arzikin Sa, kuma zuwa gare shi ne tashin yake
Verse 16
Shin ko kun amince cewa wanda ke cikin sama, ba zai iya shafe ƙasa tare da ku ba, sai ga ta tana mai girgiza
Verse 17
Ko kun amince cewa wanda ke cikin sama ba zai iya sako muku iskar guguwa ba? To, za ku san yadda (aƙibar) gargaɗi Na take
Verse 18
Lalle, waɗanda ke gabansu sun ƙaryata (manzanni). To, yaya (aƙibar) gargaɗi Na ta kasance
Verse 19
Ba za su yi dubi ba zuwa ga tsuntsaye a kansu, masu sanwa, kuma suna fiffikawa, babu mai riƙe da su sai (Allah), Mairahama? Lalle shi Mai gani ne ga dukan kome
Verse 20
Wane ne wanda zai zame muku mayaƙin da zai taimake ku, wanda ba (Allah) ba, Mai rahama? Kafirai ba su a cikin kome face ruɗu
Verse 21
Wane ne wanda zai ciyar da ku, idan (Allah) Ya riƙe arzikin Sa? A'aha, sun yi zurfi cikin girman kai da tashin hankali
Verse 22
Shin, wanda ke tafiya a kife a kan fuskarsa ya fi zama a kan shiryuwa, ko kuwa wanda ke tafiya miƙe a kan hanya madaidaiciya
Verse 23
Ka ce: "(Allah) Shine Wanda Ya ƙaga halittarku, Ya sanya muku ji da gani da tunani, amman kaɗan ce ƙwarai godiyarku
Verse 24
Kuma kace "Shi ne Ya halitta ku daga ƙasa, kuma zuwa gare Shi ne ake tashin ku
Verse 25
Kuma suna cewa, "Yaushe ne wannan alkawarin zai tabbata in dai kun kasance masu gaskiya ne ku
Verse 26
Ka ce: "Ilmin a wurin Allah kawai yake, kuma ni mai gargaɗi kawai ne, mai bayyana (gargaɗin)
Verse 27
To, lokacin da suka gan ta (azabar) a kusa, fuskokin waɗanda suka kafirta suka munana, kuma aka ce (musu) wannan shi ne abin da kuka zamo kuna ƙaryatawa
Verse 28
Ka ce musu "Idan Allah Ya halaka ni ni da wanda ke tare da ni, ko kuma, Ya yi mana rahama, to, wane ne zai tserar da kafirai daga wata azaba mai raɗaɗi
Verse 29
Ka ce: "Shi ne Mai rahama mun yi imani da Shi, gare Shi muka dogara, saboda haka za ku san wanda yake a cikin ɓata bayyananniya
Verse 30
Ka ce: "Ko kun gani, idan ruwanku ya wayi gari faƙaƙƙe, to, wane ne zai zo muku da ruwa wani mai ɓuɓɓuga