Back to Languages

    Hausa - Chapter 73

    Translation by Abubakar Mahmood Jummi

    Verse 1

    Ya wanda ya lulluɓe

    Verse 2

    Ka tsayu domin yin salla a cikin dare (duka) face kaɗan

    Verse 3

    Rabinsa, ko ka rage abu kaɗan daga gare shi

    Verse 4

    Ko ka ƙara kansa kuma ka kyautata karanta Alƙu'ani, daki daki

    Verse 5

    Lalle ne, Mu, za Mu jefa maka magana mai nauyi

    Verse 6

    Lalle ne, tashin dare shi ne mafi tsananin natsuwa, kuma mafi daidaituwa ga magana

    Verse 7

    Lalle ne, kana da, a cikin yini, wani tasihi mai tsawo

    Verse 8

    Kuma ka ambaci sunan Ubangijinka, kuma ka yanke (ƙauna daga kowa ka koma) zuwa gare Shi, yankewa

    Verse 9

    Shi ne Ubangijin mafitar rana da mafaɗarta, babu abin bautawa face Shi. Saboda haka ka riƙe Shi wakili

    Verse 10

    Kuma ka yi haƙuri ga abin da suke faɗa, kuma ka ƙaurace musu, ƙauracewa mai kyawo

    Verse 11

    Kuma ka bar Ni da masu ƙaryatawa, mawadata, kuma ka jinkirta musu kaɗan

    Verse 12

    Lalle ne, a wurin Mu, akwai wasu maruruwa masu nauyi da Jahim

    Verse 13

    Da wani abinci mai maƙara da azaba mai raɗaɗi

    Verse 14

    Ranar da ƙasa ke raurawa, da duwatsu kuma duwatsu su kasance tudun rairayi mai malala

    Verse 15

    Lalle ne, Mu. Mun aika zuwa gare ku, wani Manzo* mai shaida a kanku, kamar yadda Muka aika wani Manzo** zuwaga Fir'auna

    Verse 16

    Sai Fir'auna ya saɓa wa Manzon, saboda haka Muka kama shi kamu mai tsanani

    Verse 17

    To, yaya, idan kun kafirta, za ku kare (azabar) wani yini mai mayar da yara (tsofaffi) masu hurhura

    Verse 18

    Sama za ta tsage a cikinsa, wa'adinsa ya kasance mai aukuwa

    Verse 19

    Lalle ne, wannan wata tunatarwa ce, sai dai wanda ya so, ya kama hanyar ƙwarai zuwa ga Ubangijinsa

    Verse 20

    Lalle ne, Ubangijinka Ya sani cewa, kai kana tsayuwa a kusan kashi biyu daga uku na dare, da rabinsa, da sulusinsa, tare da wani ɓangare na waɗanda ke tare da kai. Allah Yake iya ƙaddara dare da yini, Ya san ba za ku iya lissafa shi ba, saboda haka Ya karɓi tubarku sai, ku karanta abin da ya sauƙaƙa na Alƙur'ani. Ya san wasu daga cikinku, za su yi ciwo, kuma wasu za su yi tafiya cikin ƙasa suna neman falalar Allah da fatauci, kuma wasu za su yi yaƙi a cikin banyar Allah. Saboda haka ku karanta abin da ya sauƙaƙa daga gare shi, kuma ku tsai da salla kuma ku bayar da zakka, kumaa ku bai wa Allah rance, rance mai kyawo. Kuma abin da kuka gabatar domin kanku, na alheri, za ku same shi a wurin Allah zai kasance mafifici (daga wanda kuka ajiye) kuma zai fi girma ga sakamako, kuma ku roƙi Allah gafara; lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai