Back to Languages
Hausa - Chapter 88
Translation by Abubakar Mahmood Jummi
Verse 1
Lalle ne labarin (¡iyama) mai rufe mutane da tsoronta ya zo maka
Verse 2
Wasu huskoki a ranar nan ƙasƙantattu ne
Verse 3
Masu aikin wahala ne, masu gajiya
Verse 4
Za su shiga wata wuta mai zafi
Verse 5
Ana shayar da su daga wani marmaro mai zafin ruwa
Verse 6
Ba su da wani abinci face dai daga danyi
Verse 7
Ba ya sanya ƙiba, kuma ba zai wadatar daga yunwa ba
Verse 8
Wasu huskoki a ranar nan masu ni'ima ne
Verse 9
Game da aikinsu, masu yarda ne
Verse 10
(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya
Verse 11
Ba za su ji yasassar magana ba, a cikinta
Verse 12
A cikinta akwai marmaro mai gudana
Verse 13
A cikinta akwai gadaje maɗaukaka
Verse 14
Da kofuna ar'aje
Verse 15
Da filoli* jere
Verse 16
Da katifu shimfiɗe
Verse 17
Ashe to ba za su dubawa ba ga raƙuma yadda aka halitta su
Verse 18
Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta
Verse 19
Da zuwa ga duwatsu yadda aka kafa su
Verse 20
Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗa ta
Verse 21
saboda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai
Verse 22
Ba ka zama mai ikon tanƙwasawa a kansu ba
Verse 23
Face dai duk wanda ya juya baya, kuma ya kafirta
Verse 24
To, Allah zai yi masa azaba, azabar nan da take mafi girma
Verse 25
Lalle ne, zuwa gare Mu komowarsu take
Verse 26
Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisabi