Back to Languages

    Hausa - Chapter 96

    Translation by Abubakar Mahmood Jummi

    Verse 1

    Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta

    Verse 2

    Ya hahitta mutum daga gudan jini

    Verse 3

    Ka yi karatu, kuma Ubangijinka shi ne Mafi karimci

    Verse 4

    Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami

    Verse 5

    Ya sanar da mutum abin da bai sani ba

    Verse 6

    A'aha! Lalle, ne mutum haƙiƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu)

    Verse 7

    Domin ya ga kansa, ya wadata

    Verse 8

    Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take

    Verse 9

    Shin, ka ga wanda ke hana

    Verse 10

    Bawa idan ya yi salla

    Verse 11

    Ashe, ka gani, idan (shi bawan) ya kasance a kan shiriya

    Verse 12

    Ko ya yi umurni da taƙawa

    Verse 13

    Ashe, ka gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya juya baya

    Verse 14

    Ashe, bai sani ba cewa Allah Yana gani

    Verse 15

    A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne za Mu ja gashin makwarkwaɗa

    Verse 16

    Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi

    Verse 17

    Sai ya kirayi ƙungiyarsa

    Verse 18

    Za Mu kirayi zabaniyawa (mala'iku masu girma)

    Verse 19

    A'aha kada ka bi shi. Kuma ka yi tawali'u,* kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka)