Hausa

    Translation: hau-abubakarmahmoud-la

    Author: Abubakar Mahmoud Gumi

    Mai Bude Littafi

    Surah 1

    [1] Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai

    [2] Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu

    [3] Mai rahama, Mai jin ƙai

    [4] Mai nuna Mulkin Ranar Sakamako

    [5] Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa

    [6] Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya

    [7] Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba

    Saniya

    Surah 2

    [1] L. M

    [2] Wancan ne Littafi, babu shakka a cikinsa, shiriya ne ga masu taƙawa

    [3] Waɗanda suke yin imani game da gaibi, kuma suna tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azurta su suna ciyarwa

    [4] Kuma waɗanda suke yin imani da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabaninka, kuma game da Lahira suna yin yaƙini

    [5] Waɗannan suna kan shiriya, daga Ubangjinsu, kuma waɗannan su ne masu cin nasara

    [6] Lalle ne waɗanda suka kafirta daidai ne a kansu, shin ka yi musu gargaɗi ko ba ka yi musu gargaɗi ba, ba za su yi imani ba

    [7] Allah Ya sa hatimi a kan zukatansu, da a kan jinsu, kuma a Kan ganin su akwai wata yana; kuma suna da wata azaba mai girma

    [8] Kuma akwai daga mutane wanda yake cewa: "Mun yi imani da Allah kuma da Yinin Lahira." Alhali kuwa su ba muminai ba ne

    [9] Suna yaudarayya da Allah da waɗanda suka yi imani, alhali ba su yaudarar kowa face kansu, kuma ba su sakankancewa

    [10] A cikin zukatansu akwai wata cuta. Sai Allah Ya ƙaramusu wata cuta, kuma suna da azaba mai raɗaɗi saboda abin da suka kasance suna yi na ƙarya

    [11] Kuma idan aka ce musu: "Kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa," sukan ce: "Mu masu kyautatawa kawai ne

    [12] To, lalle ne su, sune masu ɓarna, kuma amma ba su sansancewa

    [13] Kuma idan aka ce musu: "ku yi imani kamar yadda mutane suka yi imani," sukan ce: "Za mu yi imani ne kamar yadda wawaye suka yi imani?" To, lalle ne su, su ne wawaye, kuma amma ba su sani

    [14] Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi imani, sukan ce: "Mun yi imani. "Kuma idan sun wofinta zuwa ga shaiɗanunsu, sukan ce: "Lalle ne muna tare da ku: Mu masu izgili, kawai ne

    [15] Allah Yana yin izgili gare su kuma Yana taimakon su a cikin ɓatarsu, suna ɗimuwa

    [16] Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, sai fataucinsu bai yi riba ba, kuma ba su kasance masu shiryuwa ba

    [17] Misalinsu shi ne kamar misalin wanda ya hura wuta, to, a lokacin da ta haskake abin da yake gefensa (na abin tsoro), Allah Ya tafi da haskensu, kuma Ya bar su a cikin duffai, ba su gani

    [18] Kurame, bebaye, makafi, saboda haka ba su komowa

    [19] Ko kuwa kamar girgije mai zuba daga sama, a cikinsa akwai duffai da tsawa da walƙiya: suna sanyawar yatsunsu a cikin kunnuwansu daga tsawarwakin, domin tsoron mutuwa. Kuma Allah Mai kewayewane ga kafirai

    [20] Walƙiyar tana yin kusa ta fizge gannansu, ko da yaushe ta haskaka musu, sai su yi tafiya a cikinta, kuma idan ta yi duhu a kansu, sai su yi tsaye. Kuma da Allah Ya so, sai Ya tafi da jinsu da gannansu. Lalle ne Allah a kan dukan kome Mai ikon yi ne

    [21] Ya ku mutane! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, ku da waɗanda suke daga gabaninku, tsammaninku ku kare kanku

    [22] Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma sama gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya fitar da abinci daga 'ya'yan itace game da shi, saboda ku. Saboda haka kada ku sanya wa Allah wasu kishiyoyi, alhali kuwa kuna sane

    [23] Kuma idan kun kasance a cikin shakka daga abin da Muka sassaukar ga Bawanmu, to, ku zo da sura guda daga misalinsa (Alƙur'ani). Kuma ku kirawo shaidunku baicin Allah, idan kun kasance masu gaskiya

    [24] To, idan ba ku aikata (kawo sura) ba, to, ba za ku aikataba, saboda haka, ku ji tsoron wuta, wadda makamashinta mutane da duwatsu ne, an yi tattalinta domin kafurai

    [25] Kuma ka bayar da bishara ga waɗanda suka yi imani. kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, cewa lallene, suna da gidajen Aljanna, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu. Ko da yaushe aka azurta su da abinci daga wasu 'ya'yan itace daga gare su, sai su ce: "Wannan shi ne aka azurta mu da shi daga gabanin haka," Kuma a je musu da shi yana mai kama da juna, Kuma suna da, a cikin su, matan aure masu tsarki, kuma su, cikin su madawwama ne

    [26] Lalle ne, Allah ba Ya jin kunyar Ya bayyana wani misali, kowane iri ne, sauro da abin da yake bisa gare shi. To, amma waɗanda suka yi imani, sai su san cewa lalle shi ne gaskiya daga Ubangijin su, kuma amma waɗanda suka kafirta, sai su ce: "Mene ne Allah Ya yi nufi da wannan ya zama misali?" na ɓatar da wasu masu yawa da shi, kuma Yana shiryar da wasu masu yawada shi, kuma ba Ya ɓatarwa da shi face fasiƙai

    [27] Waɗanda suke warware alƙawarin Allah daga bayan ƙulla shi, kuma su yanke abin da Allah Ya yi umurni da shi a sadar, kuma suna ɓarna a cikin ƙasa, waɗannan su ne masu hasara

    [28] Yaya kuke kafirta da Allah, alhali kuwa kun kasance matattu sa'an nan Ya rayar da ku, sa'nnan kuma Ya matar da ku, sa'an nan kuma Ya raya ku, sa'an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [29] Shi ne Wanda Ya halitta muku abin da ke a cikin ƙasa gaba ɗaya, sa'an nan kuma Ya daidaita zuwa sama, sa'an nan Y a aikata su sammai bakwai. Kuma Shi ga dukan komai Masani ne

    [30] Kuma a lokacin da Ubangijinka Ya ce ga mala'iku: "Lalle ne, Ni Mai sanya wani halifa ne a cikin ƙasa," suka ce: "Ashe, za Ka sanya a cikinta, wanda zai yi ɓarna a cikinta, kuma mu, muna yi maka tasbihi tare da gode maka, kuma muna tsarkakewa gareka" Ya ce: "Lalle ne, Ni Na san abin da ba ku sani ba

    [31] Kuma Ya sanar da Adam sunaye dukansu, sa'an nan kuma ya gitta su a kan mala'iku, sa'n nan Ya ce: "Ku gaya mini sunayen waɗannan, idan kun nasance masu gaskiya

    [32] Suka ce: "Tsarki ya tabbata a gare Ka! Babu sani a gare mu, lalle ne Kai, Kai ne Masani, Mai hikima

    [33] Ya ce: "Ya Adam! Ka gaya musu sunayensu." To, a lokacin da ya gaya musu sunayensu, (Allah) Ya ce: "Ashe, ban ce muku ba, lalle Ni, Ina sane da gaibin sammai da ƙasa, kuma (Ina sane da) abin da kuke bayyanawa da abin da kuka kasance kuna ɓoyewa

    [34] Kuma a lokacin da Muka ce ga mala'iku: "Ku yi sujada ga Adam," Sai suka yi sujada, face Ibilisa ya ƙi, kuma ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kafirai

    [35] Kuma muka ce: "Ya Adam! Ka zauna kai da matarka a gidan Aljanna, kuma ku ci daga gare ta, bisa wadata, inda kuke so, kuma kada ku kusanci wannan itaciyar, har ku kasance daga azzalumai

    [36] Sai Shaiɗan ya talalaɓantar da su ga barinta, sai ya fitar da su daga abin da suka kasance a cikinsa. Kuma muka ce: "Sashenku na maƙiyi ga sashe, kuma kuna da a cikin ƙasa matabbata da jin daɗi zuwa ga wani lokaci

    [37] Sai Adam ya karɓi wasu kalmomi daga Ubangjjinsa, saboda haka ya karɓi tuba a kansa. Lalle ne Shi, Shi ne Mai karɓar tuba, Mai jin ƙai

    [38] Muka ce: "Ku ku sauka daga gare ta gaba ɗaya. To, imma lalle shiriya ta je muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiriya ta to, babu tsoro a kansu, kuma ba su yin baƙin ciki

    [39] Kuma waɗanda suka kafirta, kuma suka ƙaryata game da ayoyinMu, waɗannan su ne abokan Wuta; su a cikinta madawwama ne

    [40] Ya Bani Isra'Ila! Ku tuna ni'imaTa a kanku, kuma ku cika alƙawariNa, In cika muku da alƙawarinku. kuma Ni, ku ji tsoro Na

    [41] Kuma, ku yi imani da abin da na saukar, mai gaskatawa ga abin da yake tare da ku, kuma kada ku kasance farkon kafiri game da shi, Kuma kada ku sayi 'yan kuɗi kaɗan da ayoyiNa. Kuma ku ji tsoroNa, Ni kaɗai

    [42] Kuma kada ku lulluɓe gaskiya da ƙarya, kuma ku ɓoye gaskiya, alhali kuwa kuna sane

    [43] Kuma ku tsayar da salla; kuma ku bayar da zakka; kuma ku yi ruku'i tare da masu yin ruku'i

    [44] Shin, kuna umurnin mutane da alheri, kuma ku manta da kanku alhali kuwa kuna karatun littafi? Shin, baza ku hankalta ba

    [45] Kuma ku nemi taimako da yin haƙuri, da salla. Kuma lalle ne ita, haƙiƙa, mai girma ce face fa a kan masu tsoron Allah

    [46] Waɗanda suka tabbata cewa lalle ne su masu haɗuwa da Ubangijinsu, kuma lalle ne su a gareshi masu komawa ne

    [47] Ya bani Isra'ila! Ku tuna ni'imaTa, wadda Na ni'imta a kanku, kuma lalle ne Ni, na fifita ku a kan talikai

    [48] Kuma ku ji tsron wani yini, (a cikinsa) rai ba ya Wadatar da wani rai da kome, kuma ba a karɓar ceto daga gareshi, kuma ba a karɓar fansa daga gare shi, kuma ba su zama ana taimakon su ba

    [49] Kuma a lokacin da muka tsirar da ku daga mutanen Fir'auna, su na taya muku muguntar azaba, su na yayyanke ɗiyanku maza su na rayar da matanku. Kuma a cikin wancan akwai jarabawa mai girma daga Ubangijinku

    [50] Kuma a lokacin da Muka raba teku saboda ku, sai Muka tsirar da ku kuma Muka nutsar da mutanen Fir'auna, alhali kuwa ku kuna kallo

    [51] Kuma a lokacin da muka yi wa'adi ga Musa, dare arba'in, sa'an nan kuma kuka riƙi maraƙi daga bayansa, alhali ku, kuna masu zalunci (da bauta masa)

    [52] Sa'an nan kuma muka yafe muku daga bayan wancan, tsammaninku, kuna godewa

    [53] Kuma a lokacin da Muka baiwa Musa Littafi da rarrabewa, tsammaninku, kuna shiryuwa

    [54] Kuma a lokacin da Musa ya ce ga mutanensa: "Ya mutanena! Lalle ne ku, kun zalunci kanku game da riƙonku maraƙin, sai ku tuba zuwa ga Mahaliccinku, sai ku kashe kawunanku. Wancan ne mafii alheri a wajen mahaliccinku. Sa'an nan Ya karɓi tuba a kanku. lalle ne Shi, Shi ne Mai karɓar tuba, Mai jin ƙai

    [55] Kuma a lokacin da kuka ce: "Ya Musa! Ba za mu yi imani ba dominka, sai munga Allah bayyane," sabada haka tsawar nan ta kamaku, alhali kuwa kuna kallo

    [56] Sa'an nan kuma Muka tayar da ku daga bayan mutuwarku, tsammaninku, kuna godewa

    [57] Kuma Muka sanya girgije ya yi inuwa a kanku, kuma Muka saukar da darɓa da tantabaru a kanku; "Ku ci daga masu daɗin abin da Muka azurta ku." kuma ba su zalunce Mu ba, kuma amma kansu suka kasance suna zalunta

    [58] Kuma a lokacin da Muka ce: "Ku shiga wannan alƙarya. San nan ku ci daga gareta, idan kuka so, bisa wadata, kuma ku shiga ƙofa kuna masu tawalu'i, kuma ku ce; "kayar da zunubai" Mu gafarta muku laifukanku, kuma za mu ƙara wa masu kyautatawa

    [59] Sai waɗanda suka yi zalunci suka sake magana watar wannan da aka ce musu, saboda haka muka saukar a kan waɗanda suka yi zalunci da azaba daga sama saboda abin da suka kasance suna yi na fasiƙanci

    [60] Kuma a lokacin da Musa ya nemi shayarwa domin mutanensa, Muka ce; "Ka doki dutsen da sandarka." Sai marmaro goma sha biyu suka ɓuɓɓugo, haƙiƙa, kowaɗanne mutane sun san wurin shansu. "Ku ci kuma ku sha daga arziƙin Ubangijinku, kuma kada ku yi fasadi, a cikin ƙasa, kuna masu ɓarna

    [61] Kuma a lokacin da kuka ce: "Ya Musa! Ba za mu yi haƙuri ba a kan abinci guda. Sai ka roƙa mana Ubangijinka Ya fitar mana daga abin da ƙasa take tsirarwa daga ganyenta, dumanta, da alkamarta da albasarta. Ya ce: "Kuna neman musanya abin da yake mafi ƙasƙanci da wanda yake mafi alheri? Ku sauka wani birni (daga cikin birane), lalle ne, kuna da abin da kuka roƙa. "Kuma Muka doka musu walaƙanci da talauci. Kuma suka koma da wani fushi daga Allah. Wancan saboda lalle su, sun kasance suna kafirta da ayoyin Allah, kuma suna kashe Aannabawa, bada hakki ba. Wancan, saboda saɓawarsu ne, kuma sun kasance suna ƙetarewar haddi

    [62] Lalle ne waɗanda suka yi imani, da waɗanda suka tuba, da Nasara da Makarkata, wana ya yi imani da Allah da Yinin Lahira, kuma ya aikata aikin ƙwarai, to, suna da ijararsu a wurin Ubangijinsu, kuma babu tsoro a kansu, kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba

    [63] Kuma a lokacin da Muka riƙi alƙawarinku, kuma Muka ɗaukaka dutse a bisa gareku: "Ku kama abin da Muka baku da ƙarfi. Kuma ku ambaci abin da yake a cikin sa, tsammaninku ku karekanku

    [64] Sa'an nan kuma kuka juya daga bayan wancan, to, ba domin falalar Allah ba da rahamarSa a kanku, haƙiƙa, da kun kasance daga masu hasara

    [65] Kuma lalle ne, haƙiƙa, kun san waɗanda suka ƙetare haddi daga gare ku a cikin Asabar, sai muka ce musu: "ku kasance birai ƙasƙantattu

    [66] Muka sanya ta (mas'alar) azaba, domin abin da yake gaba gareta, da yake a bayanta, kuma wa'azi ga masu taƙawa

    [67] Kuma a lokacin da Musa yace ga mutanensa: "Lalle ne, Allah Yana umurtar ku da ku yanka wata saniya." Suka ce: "Shin kana riƙon mu ne da izgili?" Ya ce: "Ina neman tsari daga Allah da in kasance daga jahilai

    [68] Suka ce: "Ka roƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana, mece ce ita?" Ya ce: "Lalle ne, Shi, Yana cewa: "Lalle ne ita saniya ce; ba tsofuwa ba, ba kuma budurwa ba, tsakatsaki ce a tsakanin wancan,' sai ku aikata abin da ake umurninku

    [69] Suka ce: "Ka roƙa mana Ubangijinka Ya bayyana mana abin da yake launinta." Ya ce: "Lalle ne, Shi Yana cewa: "Ita wata saniya ce fatsa-fatsa, mai tsan-tsan launi, tana faranta ran mausu kallonta

    [70] Suka ce: "Ka roƙa mana Ubangijinka, Ya bayyana mana abin da yake ita, lalle ne shanu suna yi mana kama da juna, kuma mu, idan Allah Ya so, haƙiƙa, shiryuwa ne

    [71] Ya ce: "Lalle ne Shi, Yana cewa: "Ita wata saniya ce; ba horarra ba tana noman ƙasa, kuma ba ta shayar da shuka, lafiyayya ce: babu wani sofane a cikinta." Suka ce: "Yanzu ka zo da gaskiya. Sai suka yanka ta, kamar ba za su aikata ba

    [72] Kuma a lokacin da kuka yi kisan kai, kuka dinga tunkuɗa wa juna laifi a cikinsa, kuma Allah Mai fitar da abin da kuka kasance kuna ɓoyewa ne

    [73] Sai Muka ce: "Ku doke shi da wani sashenta." Kamar wancan ne Allah Yake rayar da matattu, kuma Ya nuna muku ayoyinSa, tsammaninku kuna hankalta

    [74] San'nan kuma zukatanku, suka ƙeƙashe daga bayan wancan. Saboda haka suka zamanto kamar duwatsu. Ko mafi tsananin ƙeƙashewa. kuma lalle ne daga duwatsu, haƙika, akwai abin da maremari suke ɓuɓɓuga daga gare shi, kuma lalle ne daga gare su, haƙiƙa, akwai abin da yake tsatstsagewa har ruwa ya fita daga gare shi, kuma lalle ne, haƙiƙa, daga gare su, haƙiƙa, akwai da yake faɗowa domin tsoron Allah, kuma Allah bai zama gafili ba daga barin abin da kuke aikatawa

    [75] Shin fa kuna tsammanin za su yi imani saboda ku, alhali kuwa, haƙiƙa, wata ƙungiya daga gare su sun kasance suna jin maganar Allah, sa'an nan kuma su karkatar da ita daga bayan sun gane ta, alhali su, suna sane

    [76] Kuma idan sun haɗu da waɗanda suka yi imani sukan ce: "Mun yi imani," kuma idan sashensu ya wofinta zuwa ga sashe, sukan ce: "Shin, kuna yi musu magana da abin da Allah Ya buɗa muku ne domin su yi muku hujja da shi a wurin Ubangijinku?" Shin fa, ba ku hankalta

    [77] Shin, kuma ba su sanin cewa lalle ne Allah Yana sanin abin da suke ɓoyewa da abin da suke bayyanawa

    [78] Kuma daga cikinsu akwai ummiyyai, ba su da sanin Littafi, face tatsuniyoyi, kuma su ba kome suke yi ba face suna yin zato

    [79] To, bone ya tabbata ga waɗanda suke rubuta littafi da hannuwansu sa'an nan kuma su ce wannan daga wurin Allah yake, domin su sayi kuɗi kaɗan da shi, san nan bone ya tabbata a gare su daga abin da hannayensu ke rubutawa, kuma bone ya tabbata a gare su daga abin da suke sana'antawa

    [80] Kuma suka ce: "Wuta ba za ta shafe mu ba, face, 'yan kwanuka ƙidayayyu."Ka ce: "Ashe kun riƙi wani alkawari a wurin Allah, sa'an nan Allah ba zai saɓa wa alkawarinSa ba ko kuwa kuna faɗin abin da ba ku sani ba bisa ga Allah

    [81] Na'am! Wanda ya yi tsiwur-wurin mugun abu, kuma laifinsa ya kewaye shi, to, waɗannan su ne 'yan Wuta, su a cikinta madawwama ne

    [82] Kuma waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, waɗannan, 'yan Aljanna ne, su a cikinta madawwama ne

    [83] Kuma a lokacin da Muka karɓi alkawarin Bani-Isra'ila: "Kada ku bauta wa kowa face Allah, kuma ga mahaifa ku kyautata, da mai zumunta da marayu da matalauta, kuma ku faɗi magana mai kyau zuwa ga mutane, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bayar da zakka, sa'an nan kuka juya baya, face kaɗan daga gare ku, alhali kuwa kuna masu bijirewa

    [84] Lokacin da Muka riƙi alkawarinku; ba za ku zubar da jininku ba, kuma ba za ku fitar da kanku daga gidajenku ba; sa'an nan kuka tabbatar alhali kuwa kuna bayar da shaida (a kanku)

    [85] Sa'an nan kuma, ga ku, ya waɗannan! Kuna kashe kanku, kuma kuna fitar da wani ɓangare daga gare ku daga gidajensu, kuna taimakon juna a kansu da zunubi da zalunci kuma idan kamammu suka je muku kuna fansarsu alhali kuwa shi fitar da su abin da aka haramta muku ne. Shin fa, kuna imani da sashen Littafin ne, kuma ku kafirta da sashe? To, mene ne sakamakon wanda ke aikata wancan daga gare ku face wulakanci a cikin rayuwar duniya? Kuma a Ranar ¡iyama ana mayar da su zuwa ga mafi tsananin azaba. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga barin abin da kuke aikatawa

    [86] Waɗannan su ne waɗanda suka sayi rayuwar duniya da Lahira, domin haka ba za a sauƙaƙa azaba ba daga kansu, kuma su, ba ataimakonsu

    [87] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Munbai wa Musa Littafi, kuma Mun biyar daga bayansa da wasu Manzanni, kuma Muka bai wa Isa ɗan Maryama hujjoji bayyanannu, kuma Muka ƙarfafa shi da Ruhi mai tsarki. Shinfa, ko da yaushe wani manzo ya je muku tare da abin da rayukanku ba su so, sai ku kangara, wani ɓangare kun ƙaryata, kuma wani ɓangare kuna kashewa

    [88] Kuma suka ce: "Zukatanmu suna cikin rufi." A'a, Allah Ya la'ane su, domin kafircinsu kadan kwarai suke yin imani

    [89] Kuma a lokacin da wani Littafi daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatawa ga abin da yake tare da su, alhali kuwa sun kasance daga gabanin haka suna fatar taimako da shi a kan waɗanda suka kafirta. To, a lokacin da abin da suka sani ya je musu, sai suka kafirta da shi. Saboda haka la'anar Allah ta tabbata a kan kafirai

    [90] Tir, da abin da suka sayi rayukansu da shi; watau su kafirta da abin da Allah Ya saukar saboda zalunci; kada Allah Ya saukar da falalarsa a kan wanda Yake so daga bayinsa. Sai suka komo da fushi game da wani fushi. Kuma ga kafirai akwai azaba mai wulaƙantarwa

    [91] Kuma idan aka ce musu: "Ku yi imani da abin da Allah Ya saukar." Sai su ce: "Muna imani da abin da aka saukar a gare mu," kuma suna kafircewa da abin da ke bayansa, alhali kuwa, shi ne gaskiyar (da suka sani) mai gaskatawa ga abin da yake tare da su (na Attaura) Ka ce: "To, don me kuke kashe annabawan Allah gabanin wannan, idan kun kasance masu bayar da gaskiya

    [92] Kuma lalle ne haƙiƙa Musa ya zo muku da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuka riƙi maraƙi (daga bayansa, alhali kuwa kuna masu zalunci)

    [93] Kuma a lokacin da Muka riƙi alkawarinku kuma Muka ɗaukaka dutse a bisa gare ku, (Muka ce:) "Ku riƙi abin da Muka kawo muku da ƙarfi kuma ku ji" Suka ce: "Mun ji kuma mun ƙi." Kuma aka zuba son maraƙin a cikin zukatansu saboda kafircinsu. Ka ce: "Tir da abin da imaninku yake umurnin ku da shi, har idan kun kasance masu imani

    [94] Ka ce: "Idan Gidan Lahira ya kasance saboda ku, a wurin Allah keɓe ba da sauran mutane ba, to, ku yi gurin mutuwa, idan kun kasance masu gaskiya

    [95] Kuma ba za su yi gurinta bahar abada saboda abin da hannayensu, suka gabatar. Kuma Allah Masani ne ga azzalumai

    [96] Kuma lalle ne, za ka same su mafiya kwaɗayin mutane a kan rayuwa, kuma su ne mafiya kwaɗayin rayuwa daga waɗanda suka yi shirka. ¦ayansu yana son da za a rayar da shi shekara dubu, kuma ba ya zama mai nisantar da shi daga azaba domin an rayar da shi. Kuma Allah, Mai gani ne ga abin da suke aikatawa

    [97] Ka ce: Wanda ya kasance maƙiyi ga Jibirilu, to, lalle ne shi ya saukar da shi a kan zuciyarka da izinin Allah, yana mai gaskatawa ga abin da yake gaba gare shi, kuma da shiriya da bishara ga muminai

    [98] Wanda ya kasance maƙiyi ga Allah da mala'ikunSa da manzanninSa da Jibirila da Mika'ila to, lalle ne, Allah Maƙiyi ne ga kafirai

    [99] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun saukar, zuwa gare ka, ayoyi bayyanannu, kuma ba wanda yake kafirta da su face fasikai

    [100] Shin, kuma a ko da yaushe suka ƙulla wani alkawari sai wani ɓangare daga gare su ya, yi jifa da shi? A'a, mafi yawansu ba su yin imani

    [101] Kuma a lokacin da wani manzo (Muhammadu) daga wurin Allah ya je musu, mai gaskatawa ga abin da yake tare da su, sai wani ɓangare daga waɗanda aka bai wa Littafi, suka yar da Littafin (Alƙur'anin) Allah a bayan bayansu, kamar dai su ba su sani ba

    [102] Kuma suka bi abin da shaiɗanu ke karantawa a kan mulkin Sulaimanu, kuma Sulaimanu bai yi kafirci ba, kuma Shaidanun, su ne suka yi kafirci, suna karantar da mutane sihiri. Kuma ba a saukar da shi ba a kan mala'iku biyu a Babila, Haruta da Maruta. Kuma ba su sanar da kowa ba balle su ce: "Mu fitina kawai ne, saboda haka kada ka kafirta," balle har su yi ta neman ilmin abin da suke rarrabewa tsakanin mutum da matarsa da shi daga gare su. Kuma su (masu yin sihirin) ba su zama masu cutar da kowa da shi ba, face da iznin Allah. Kuma suna neman ilmin abin da yake cutar da su, kuma ba ya amfaninsu. Kuma lalle ne, haƙiƙa, sun sani, tabbas, wanda ya saye shi, ba ya da wani rabo a cikin Lahira. Kuma tir da abin da suka sayar da rayukansu da shi, da sun kasance suna sani

    [103] Kuma da lalle ne su, sun yi imani, kuma sun yi taƙawa, haƙiƙa, da sakamako daga wurin Allah shi ne mafi alheri, da sun kasance suna sani

    [104] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku ce: 'Ra'ina' kuma ku ce: 'Jinkirta mana', kuma ku saurara. Kuma kafirai suna da azaba mai raɗaɗi

    [105] Waɗanda suka kafirta daga Ma'abuta Littafi, ba su son a saukar da wani alheri a kanku daga Ubangijinku, kuma mushirikai ma ba su so. Kuma Allah Yana keɓance da wanda Yake so da rahamarSa. Kuma Allah Ma'abucin falala mai girma ne

    [106] Abin da Muka shafe daga aya, ko kuwa Muka jinkirtar da ita, za Mu zo da mafi alheri daga gare ta ko kuwa misalinta. Ashe, ba ka sani ba, cewa lalle ne, Allah a kan dukkan kome Mai ikon yi ne

    [107] Shin ba ka sani ba, cewa lalle ne Allah, Shi ne da mulkin sammai da ƙasa kuma ba ku da, baicin Allah, wani majiɓinci, kuma ba ku da wani mataimaki

    [108] Ko kuna nufin ku tambayi Manzonku, kamar yadda aka tambayi Musa a gabanin haka? Kuma wanda ya musanya kafirci da imani, to, lalle ne ya ɓace tsakar hanya

    [109] Masu yawa daga Ma'abuta Littafi suna gurin da sun mayar da ku, daga bayan imaninku, kafirai, saboda hasada daga wurin rayukansu, daga bayan gaskiya ta bayyana a gare su. To, ku yafe, kuma ku kau da kai, sai Allah Ya zo da umurninSa. Lalle ne Allah a kan dukkan kome Mai ikon yi ne

    [110] Kuma ku tsayar da salla, kuma ku bayar da zakka. Kuma abin da kuka gabatar domin kanku daga alheri, za ku same shi a wurin Allah. Lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatawa Mai gani ne

    [111] Kuma suka ce: "Babu mai shiga Aljanna face waɗanda suka zama Yahudu ko Nasara." Waɗancan tatsuniyoyinsu ne. Ka ce: "Ku kawo dalilinku idan kun kasance masu gaskiya

    [112] Na'am! Wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhali kuwa yana mai kyautatawa, to, yana da ijararsa, a wurin Ubangijinsa, kuma babu tsoro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba

    [113] Kuma Yahudawa suka ce: "Nasara ba su zamana a kan kome ba," kuma Nasara suka ce: "Yahudawa ba su zamana a kan komeba," alhali kuwa su, suna karatun Littafi. Kamar wancan ne waɗanda ba su sani ba suka faɗa, kamar maganarsu saboda haka Allah ne ke yin hukunci a tsakaninsu a Ranar ¡iyama, a cikin abin da suka kasance suna saɓawa juna a cikinsa

    [114] Kuma wane ne mafi zalunci daga wanda ya hana masallatan Allah, domin kada a ambaci sunanSa a cikinsu, sai kuma ya yi aiki ga rushe su? Waɗannan ba ya kasancewa a gare su su shige su face suna masu tsoro. Suna da, a cikin duniya wani wulakanci, kuma suna da, a cikin Lahira, azaba mai girma

    [115] Kuma Allah ɗai yake da gabas da yamma saboda haka, inda duk aka juyar da ku, to, a can fuskar Allah take. Lalle ne, Allah Mawadaci ne, Mai ilmi

    [116] Kuma suka ce: "Allah Ya riƙi ɗa." Tsarki ya tabbata a gare Shi! A'a, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, dukansu, a gare Shi, masu ƙanƙan da kai ne

    [117] Mai kyautata halittar sammai da ƙasa, kuma idan Ya hukunta wani al'amari, sai kawai Ya ce masa: "Kasance." Sai ya yi ta kasancewa

    [118] Kuma waɗanda ba su da sani suka ce: "Don me Allah ba Ya yi mana magana, ko wata aya ta zo mana?" Kamar wancan ne waɗanda suke a gabaninsu suka faɗa, kamar maganarsu. zukatansu sun yi kama da juna. Lalle ne, Mun bayyana ayoyi ga mutane masu sakankancewa

    [119] Lalle ne Mun aike ka da gaskiya, kana mai bayar da bishara, kuma mai gargaɗi, kuma ba za a tambaye ka ba, game da abokan Wuta

    [120] Kuma Yahudu ba za su yarda da kome daga gare ka ba, kuma Nasara ba za su yarda ba, sai ka bi irin aƙidarsu. Ka ce: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya." Kuma lalle ne idan ka bi son zuciyoyinsu a bayan abin da ya zo maka na ilmi, ba ka da, daga Allah, wani majiɓinci, kuma babu wani mataimaki

    [121] Waɗanda Muka bai wa Littafi suna karatunsa a kan haƙƙin karatunsa, waɗannan suna imani da shi (Alƙur'ani). Kuma wanda ya kafirta da shi, to, waɗannan su ne masu hasara

    [122] Ya Bani Isra'ila! Ku tuna ni'imaTa wadda Na ni'imtar da ita a kanku, kuma lalle ne Ni, Na fifita ku a kan talikai

    [123] Ku ji tsoron wani yini, (a cikinsa) wani rai ba ya tunkuɗe wa wani rai kome kuma ba a karɓar fansa daga gare shi, kuma wani ceto ba ya amfanin sa, kuma ba su zama ana taimakon su ba

    [124] Kuma a lokacin da Ubangijin Ibrahim Ya jarrabe shi da wasu kalmomi, sai ya cika su. Ya ce: "Lalle ne Ni, Mai sanya ka shugaba domin mutane ne." Ya ce: "Kuma daga zuriyata." Ya ce: "AlkawariNa ba zai samu azzalumai ba

    [125] Kuma a lokacin da Muka sanya ¦akin ya zama makoma ga mutane, da aminci, kuma ku riƙi wurin salla daga Maƙami Ibrahim, kuma Muka yi alƙawari zuwa ga Ibrahim, da Isma'ila da cewa: "Ku tsarkake ¦akiNa domin masu ɗawafi da masu lizimta da masu ruku'i, masu sujada

    [126] Kuma a lokacin da lbrahim ya ce: "Ya Ubangijina! Ka sanya wannan gari amintacce, Ka azurta mutanensa, daga 'ya'yan itacen, wanda ya yi imani, daga gare su, da Allah da Ranar Lahira." Allah Ya ce: "Wanda ya kafirta ma Ina jiyar da shi daɗi kaɗan, sa'an nan kuma Ina tilasta shi zuwa ga azabar Wuta. Kuma makomar, ta munana

    [127] Kuma a lokacin da Ibrahim yake ɗaukaka harsashin gini ga ¦akin, da Isma'ila (suna cewa:) "Ya Ubangijnmu! Ka karɓa daga gare mu, lalle ne Kai, Kai ne Mai ji, Mai sani

    [128] Ya Ubangijnmu! Ka sanya mu, mu biyu, waɗanda suka sallama (al'amari) gare Ka, kuma daga zuriyarmu (Ka sanya) al'umma mai sallamawa zuwa gare Ka, Kuma Ka nuna mana wuraren ibadar hajjinmu, kuma Ka karɓi tuba a kanmu. Lalle ne Kai, Kai ne Mai karɓar tuba, Mai rahama

    [129] Ya Ubangijinmu! Ka aiko, a cikinsu, wani manzo daga gare su, yana karanta musu ayoyinKa, kuma yana karantar da su Littafin da hikimar, kuma yana tsarkake su. Lalle ne Kai, Kai ne Mabuwayi Mai hikima

    [130] Kuma wane ne yake gudu daga aƙidar Ibrahim, face wanda ya jahilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun zaɓe shi, a cikin duniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lahira, haƙiƙa, yana daga salihai

    [131] A lokacin da Ubangijinsa Ya ce masa: "Ka miƙa wuya," ya ce: "Na miƙa wuya ga Ubangijin talikai

    [132] Kuma lbrahim ya yi wasiyya da ita ga ɗiyansa, kuma Ya'aƙubu (ya yi wasiyya, suka ce:) "Ya ɗiyana! Lalle ne, Allah Ya zaɓa muku addini don haka kada ku mutu, lalle, face kuna Musulmi

    [133] Ko kun kasance halarce a lokacin da mutuwa ta halarci Ya'aƙubu, a lokacin da ya ce wa ɗiyansa: "Mene ne za ku bauta wa daga bayana?" Suka ce: "Muna bauta wa Abin bautawarka kuma Abin bautawar ubanninka lbrahim da lsma'ila da Is'haƙa, Ubangiji Guda, kuma mu a gare Shi masu miƙa wuya ne

    [134] Waccan, wata al'umma ce, ta riga ta shige, tana da abin da ta sana'anta kuma kuna da abin da kuka sana'anta, Kuma ba za a tambaye ku ba daga abin da suka kasance suna aikatawa

    [135] Kuma suka ce: "Ku kasance Yahudawa ko Nasara, kwa shiryu."Ka ce: "A'a aƙidar Ibrahim dai, maikarkata, zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga masu shirki ba

    [136] Ku ce: "Mun yi imani da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu, da abin da aka saukar zuwa ga Ibrahim da Isma'ila da Is'haka da Ya'aƙubu da jikoki, da abin da aka bai wa Musa da Isa, da abin da aka bai wa annabawa daga Ubangijinsu, ba mu rarrabewa a tsakanin kowa daga gare su, kuma mu, a gare Shi, masu miƙa wuya ne

    [137] To, idan sun yi imani da misalin abin da kuka yi imani da shi, to, lalle ne sun shiryu, kuma idan sun juya baya, to, suna a cikin saɓani kawai saboda haka Allah zai isar maka a gare su, kuma Shi ne Mai ji, Masani

    [138] Rinin Allah! Kuma wane ne mafi kyau ga rini daga Allah? Kuma mu, a gare Shi, masu bautawa ne

    [139] Ka ce: Shin kuna jayayyar hujia ne da mu a cikin al'amarin Allah, alhali kuwa Shi ne Ubangijinmu kuma Ubangijinku, kuma muna da ayyukanmu, kuma kuna da ayyukanku, kuma mu, a gare Shi, masu tsarkakewane

    [140] Ko kuna cewa: Lalle ne, Ibrahim da Isma'ila da Is'haƙa da Ya'aƙubu da Jikoki, sun kasance Yahudawa ko kuwa Nasara? Ka ce: Shin ku ne kuke mafi sani koAllah? Kuma wane ne ya zama mafi zalunci daga wanda ya boye shaida a wurinsa daga Allah? Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatawa

    [141] Waccan, wata al'umma ce, ta riga ta shige, suna da abin da suka sana'anta kuma kuna da abin da kuka sana'anta kuma ba a tambayar ku daga abin da suka kasance suna aikatawa

    [142] Wawaye daga mutane za su ce: Mene ne ya juyar da su daga alƙiblarsu wadda suka kasance a kanta? Ka ce: "Allah ¦ai ne Yake da gabas da yamma, Yana shiryar da wanda Yake so zuwa ga hanya madaidaiciya

    [143] Kuma kamar wancan, Muka sanya ku al'umma matsakaiciya domin ku kasance masu bayar da shaida a kan mutane. Kuma Manzo ya kasance mai shaida a kanku. Kuma ba Mu sanya Alƙibla wadda ka kasance a kanta ba, face domin Mu san wanda yake biyar Manzo daga wanda yake juyawa a kan duga-dugansa. Kuma lalle ne, ta kasance haƙiƙa, mai girma, sai a kan waɗanda Allah Ya shiryar. Kuma ba ya yiwuwa ga Allah Ya tozartar da imaninku. Lalle ne, Allah, ga mutane, haƙiƙa, Mai tausayi ne, Mai jin ƙai

    [144] Lalle ne, Muna ganin jujjuyawar fuskarka a cikin sama. To, lalle ne, Mu juyar da kai ga Alƙibla wadda kake yarda da ita. Sai ka juyar da fuskarka wajen Masallaci Tsararre, kuma inda duk kuka kasance, to, ku juyar da fuskokinku jiharsa. Kuma lalle ne waɗanda aka bai wa Littafi, haƙiƙa su, suna sanin lalle ne, shi ne gaskiya, daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da suke aikatawa

    [145] Kuma hakika, idan ka je wawaɗanda aka bai wa Littafi da dukan aya, ba za su bi Alƙiblarka ba, kuma kai ba ka zama mai bin Alƙiblarsu ba, kuma sashensu ba mai bin Alƙiblar sashe ba ne. Kuma haƙiƙa, idan ka bi son zuciyoyinsu daga bayan abin da ya zo maka daga ilmi, lalle ne kai, sa'an nan, haƙiƙa, azzalumi kake

    [146] Waɗanda Muka ba su Littafi, suna saninsa kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Kuma lalle ne wani ɓangare daga gare su, haƙiƙa, suna ɓoyewar gaskiya alhali kuwa su, suna sane

    [147] Gaskiya daga Ubangijinka take saboda haka, lalle kada ka kasance daga masu shakka

    [148] Kuma kowane ɓangare yana da alƙibla wadda yake shi mai fuskantar ta ne. Sai ku yi tsere zuwa ga ayyukan alheri, inda kuka kasance duka Allah zai zo da ku gaba ɗaya. Lalle ne Allah, a kan kome, Mai ikon yi ne

    [149] Kuma daga inda ka fita, to, sai ka juyar da fuskarka a wajen Masallaci Tsararre kuma lalle tabbas, shi ne gaskiya daga Ubangijinka. Kuma Allah bai zama Mai gafala ba daga abin da kuke aikatawa ba

    [150] Kuma daga inda ka fita, to, ka juyar da fuskarka a wajen Masallaci Tsararre kuma inda kuke duka, to, ku juyar da fuskokinku a wajensa, domin kada wata hujja ta kasance ga mutane a kanku, face waɗanda suka yi zalunci daga gare su. Saboda haka kada ku ji tsoronsu kuma ku ji tsoroNa kuma domin In cika ni'imaTa a kanku, kuma tsammaninku za ku shiryu

    [151] Kamar yadda Muka aika Manzo a cikinku, daga gare ku, yana karanta ayoyinMu a gare ku kuma yana tsarkake ku, kuma yana sanar da ku Littafi da hikima, kuma yana sanar da ku abin da ba ku kasance kuna sani ba

    [152] Saboda haka, ku tuna Ni, In tuna ku, kuma ku yi godiya gare Ni, kuma kada ku butulce Mini

    [153] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku nemi taimako da haƙuri game da salla. Lalle ne, Allah na tare da masu haƙuri

    [154] Kada ku ce ga waɗanda ake kashewa a cikin hanyar Allah: "Matattu ne." A'a, rayayyu ne, kuma amma ba ku sansancewa

    [155] Kuma lalle ne, Muna jarrabar ku da wani abu daga tsoro da yunwa da naƙasa daga dukiya da rayuka da 'ya'yan itace. Kuma ka yi bishara ga masu haƙuri

    [156] Waɗanda suke idan wata masifa ta same su, sai su ce: "Lalle ne mu ga Allah muke, kuma lalle ne mu, zuwa gare Shi, muke komawa

    [157] Waɗannan akwai albarku a kansu daga Ubangijinsu da wata rahama. Kuma waɗannan su ne shiryayyu

    [158] Lalle ne Safa da Marwa suna daga wuraren ibadar Allah, to, wanda ya yi hajin ¦aki ko kuwa ya yi Umra, to, babu laifi a kansa ga ya yi ɗawafi gare su, su biyu. Kuma wanda ya ƙara yin wani aikin alheri to, lalle ne Allah Mai godiya ne, Masani

    [159] Lalle ne waɗanda suke ɓoyewar abin da Allah Ya saukar da ga hujjoji bayyanannu, da shiriya, daga bayan Mun bayyana shi ga mutane, a cikin Littafi (Alƙur'ani), waɗannan Allah Yana la'anar su, kuma masu la'ana suna la'anar su

    [160] Sai waɗanda suka tuba, kuma suka gyara, kuma suka bayyana, to waɗannan Ina karɓar tuba a kansu kuma Ni ne Mai karɓar tuba, Mai jin ƙai

    [161] Lalle ne, waɗanda suka kafirta kuma suka mutu alhali kuwa suna kafirai, waɗannan akwai, a kansu, la'anar Allah da Mala'iku da mutane gaba ɗaya

    [162] Suna madawwama a cikinta, ba a sauƙaƙa azaba daga barinsu, kuma ba su zama ana jinkirta musu ba

    [163] Kuma Ubangijinku Ubangiji Guda ne. Babu wani Ubangiji face Shi, Mai rahama, Mai jin ƙai

    [164] Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa, da saɓawar dare da yini, da jirage wadaɗnda suke gudana a cikin teku (ɗauke) da abin da yake amfanin mutane, da abin da Allah Ya saukar daga sama daga ruwa, sai Ya rayar da ƙasa da shi a bayan mutuwarta, kuma Ya watsa, a cikinta, daga dukan dabba, kuma da juyawar iskoki da girgije horarre a tsakanin sama da ƙasa; haƙiƙa, akwaiayoyi ga mutane masu yin hankali

    [165] Kuma akwai daga mutane wanda yake riƙon kinaye, baicin Allah, suna son su, kamar son Allah, kuma waɗanda suka yi imani ne mafiya tsananin so ga Allah. Kuma da waɗanda suka yi zalunci, suna ganin lokacin da za su ga azaba, da cewa lalle ne ƙarfi ga Allah yake duka, da cewa lalle neAllah Mai tsananin azaba ne

    [166] A lokacin da waɗanda aka bi suka barranta daga waɗanda suka bi, kuma suka ga azaba, kuma sabubba suka yanke da su

    [167] Kuma waɗanda suka bi, suka ce: "Da lalle ne muna da wata komawa (duniya) sai mu barranta dagagare su kamar yadda suka barranta daga gare mu (da ba su riƙi kinayen ba)." Kamar wancan ne Allah ke nuna musu ayyukansu, suna da nadamomi a kansu, kuma ba su zama masu fita daga wutar ba

    [168] Ya ku mutane! Ku ci daga abin da yake a cikin ƙasa, wanda yake halal, mai daɗi. Kuma kada ku bi zambiyoyin Shaiɗan. Lalle ne shi, gare ku, maƙiyi ne bayyananne

    [169] Yana umurnin ku ne kawai da mugun aiki da alfasha, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba ga Allah

    [170] Kuma idan aka ce musu: "Ku bi abin da Allah Ya saukar," sai su ce: A'a, muna bin abin da muka iske ubanninmu a kansa." Shin, kuma ko da ubanninsu ba su hankaltar kome, kuma ba su shiryuwa

    [171] Kuma misalin (mai kiran) waɗanda suka kafirta kamar misalin wanda ke yin me! me! ga abin da ba ya ji ne, face kira da ƙara, kurame, bebaye, makafi, saboda haka ba su hankalta

    [172] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ci ku sha daga masu daɗin abin da Muka azurta ku. Kuma ku gode wa Allah, idan kun kasance Shi kuke bauta wa

    [173] Kawai abin da Ya haramta a kanku, mushe da Jini da naman alade da abin da aka kururuta game da shi ga wanin Allah. To, wanda aka matsa, wanin ɗan tawaye, kuma banda mai zalunci, to babu laifi a kansa. Lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [174] Lalle ne waɗannan da suke ɓoye abin da Allah Ya saukar daga Littafi, kuma suna sayen kuɗi kaɗan da shi; waɗannan ba su cin kome a cikin cikkunansu face wuta, kuma Allah ba zai yi musu magana ba a Ranar ¡iyama, kuma ba zai tsarkake su ba, kuma suna da azaba mai raɗaɗi

    [175] Waɗannan su ne waɗanda suka sayi ɓata da shiriya, kuma azaba da gafara. To, me ya yi haƙurinsu a kan Wuta

    [176] Wancan domin lalle ne Allah Ya saukar da Littafi da gaskiya, kuma lalle ne waɗanda suka saɓa a cikin Littafin, haƙiƙa, suna a cikin saɓani mai nisa

    [177] Bai zama addini ba domin kun juyar da fuskokinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi imani da Allah da Ranar Lahira da mala'iku da Littattafan sama da Annabawa, kuma ya bayar da dukiya, akan yana son ta, ga mai zumunta da marayu da matalauta da ɗan hanya da masu roƙo, kuma a cikin fansar wuya, kuma ya tsayar da salla, kuma ya bayar da zakka, da masu cika alkawari idan sun ƙulla alkawarin da masu haƙuri a cikin tsanani da cuta da lokacin yaƙi. Waɗannan su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne masu taƙawa

    [178] Ya ku waɗanda suka yi imani! An wajabta, a kanku, yin ƙisasi a cikin kasassu. ɗa da ɗa kuma bawa da bawa, kuma mace da mace, to, wanda aka yi rangwamen wani abu gare shi daga ɗan'uwansa to a bi da alheri da biya zuwa gare, shi da kyautatawa. Wancan sauƙaƙewa ne daga Ubangijinku, kuma rahama ce. To, wanda ya yi zalunci a bayan wancan, to, yana da azaba mai raɗaɗi

    [179] Kuma kuna da rayuwa a cikin ƙisasi, ya ma'abuta hankula; tsammaninku, za ku yi taƙawa

    [180] Kuma an wajabta, a kanku idan mutuwa ta halarci ɗayanku, idan ya bar wata dukiya, wasiyya domin mahaifa da dangi bisa ga abin da aka sani; wajabce a kan masu taƙawa

    [181] To, wanda ya musanya masa a bayan ya ji shi, to, kawai laifinsa yana a kan waɗanda suke musanya shi. Lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani

    [182] To, wanda ya ji tsoron karkata ko kuwa wani zunubi daga mai wasiyyar, sai ya yi sulhi a tsakaninsu to babu laifi a kansa. Lalle ne Allah, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [183] Ya ku waɗanda suka yi imani! An wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke daga gabaninku, tsammaninku, za ku yi taƙawa

    [184] Kwanuka ƙidayayyu. To, wanda ya kasance daga gare ku majinyaci ko kuwa yana a kan tafiya, sai (ya biya) adadi daga wasu kwanuka na dabam. Kuma a kan waɗanda suke yin sa da wahala akwai fansa; ciyar da matalauci, sai dai wanda ya ƙara alheri to, shi ne mafi alheri a gare shi. Kuma ku yi azumi (da wahalar) ne mafi alheri a gare ku idan kun kasance kuna sani

    [185] Watan Ramalana ne wanda aka saukar da Alƙur'ani a cikinsa yana shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu daga shiriya da rarrabewa. To, wanda ya halarta daga gare ku a watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya kasance majinyaci ko kuwa a kan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na dabam. Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare ku, kuma domin ku cika adadin, kuma domin ku girmama Allah a kan Ya shiryar da ku, kuma tsammaninku, za ku gode

    [186] Kuma idan bayiNa suka tambaye ka daga gare Ni, to, lalle Ni Makusanci ne. Ina karɓa kiran mai kira idan ya kira Ni. Saboda haka su nemi karɓawaTa, kuma su yi imani da Ni: tsammaninsu, su shiryu

    [187] An halatta a gare ku, a daren azumi, yin jima'i zuwa ga matanku su tufa ne a gare ku, kuma ku tufa ne a gare su, Allah Ya sani lalle ne ku kun kasance kuna yaudarar kanku. Saboda haka Ya karɓi tubarku, kuma Ya yafe muku. To, yanzu ku rungume su kuma ku nemi abin da Allah ya rubuta muku. Kuma ku ci kuma ku sha har silili fari ya bayyana a gare ku daga silili baƙi daga alfijiri, sa'an nan kuma ku cika azumi zuwa ga dare. Kuma kada ku rungume su alhali kuna masu itikafi a cikin masallatai. Waɗancan iyakokin Allah ne: don haka kada ku kusancesu kamar haka ne Allah Yake bayyana ayoyinSa ga mutane: tsammaninsu, za su yi taƙawa

    [188] Kada ku ci dukiyoyinku a tsakaninku da ƙarya, kuma ku sadu da ita zuwa ga mahukunta domin ku ci wani yanki daga dukiyoyin mutane da zunubi alhali kuwa ku, kuna sane

    [189] Kuma suna tambayar ka daga jirajiran wata. Ka ce: "Su lokatai ne domin mutane da haji, kuma ba addini ba ne ku je wa gidaje daga bayansu: kuma amma abin da yake addini shi ne wanda ya yi taƙawa. Kuma ku je wa gidaje daga ƙofofinsu, kuma ku bi Allah da taƙawa: tsammaninku, ku ci nasara

    [190] Kuma ku yaƙi waɗanda suke yaƙinku, a cikin hanyar Allah, kuma kada ku yi tsokana, lalle ne Allah ba Ya son masu tsokana

    [191] Kuma ku yaƙe su inda kuka same su, kuma ku fitar da su daga inda suka fitar da ku. Kuma fitina ita ce mafi tsanani daga kisa. Kuma kada ku yaƙe su a wurin Masallaci Tsararre (Hurumin Makka) face fa idan sun yaƙe ku a cikinsa. To, idan sun yaƙe ku, sai ku yaƙe su. Kamar wancan ne sakamakon kafirai yake

    [192] Sa'an nan idan sun hanu, to, lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [193] Kuma ku yaƙe su har ya zama wata fitina ba za ta kasance ba, kuma addini ya zama na Allah. Sa'an nan idan sun hanu to babu tsokana face a kan azzalumai

    [194] Watan alfarma da wani watan alfarma alfarmomi masu dukar juna ne. Saboda haka wanda ya yi tsokana a kanku, sai ku yi tsokana a kansa da misalin abin da ya yi tsokana a kanku. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cewa lalle ne, Allah Yana tare da masu taƙawa

    [195] Kuma ku ciyar a cikin hanyar Allah. Kuma kada ku jefa kanku da hannayenku, zuwa ga halaka. Kuma ku kyautata; lalle ne, Allah Yana son masu kyautatawa

    [196] Kuma ku cika hajji da umra domin Allah. To idan an kange ku, to, ku bayar da abin da ya sauƙaƙa na hadaya. Kuma kada ku aske kanunku, sai hadaya ta kai wurinta. To, wanda ya kasance majinyaci daga cikinku, ko kuwa akwai wata cuta daga kansa (ya yi aski) sai fansa (fidiya) daga azumi ko kuwa sadaka ko kuwa yanka. To, idan kuna cikin aminci to, wanda ya ji dadi da umra zuwa haji, sai ya biya abin da ya sauƙaƙa daga hadaya, sa'an nan wanda bai samu ba, sai azumin yini uku a cikin haji da bakwai idan kun koma, waɗancan goma ne cikakku. Wancan yana ga wanda iyalinsa ba su kasance mazaunan Masallaci Tsararre ba. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cewa Allah Mai tsananin uƙuba ne

    [197] Hajji watanni ne sanannu. To, wanda ya yi niyyar hajji a cikinsu to babu jima'i kuma babu fasiƙanci, kuma babu jayayya a cikin hajji. Kuma abin da kuka aikata daga alheri, Allah Ya san shi. Kuma ku yi guzuri. To, mafi alherin guzuri yin taƙawa. Kuma ku bi Ni da taƙawa, ya ma'abuta hankula

    [198] Babu laifi a kanku ga ku nemi falala daga Ubangijinku. Sa'an nan idan kun malalo daga Arafat, sai ku yi ta ambatar Allah a wurin Mash'aril Harami kuma ku tuna Shi kamar shiriyar da Ya yi muku kuma lalle ne kun kasance a gabaninsa, haƙiƙa, daga ɓatattu

    [199] Sa'an nan kuma ku malalo daga inda mutane suke malalowa. Kuma ku nemi gafara ga Allah. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [200] To, idan kun ƙare ayyukan hajji, sai ku ambaci Allah kamar ambatarku ga ubanninku, ko kuwa mafi tsanani ga ambato. To, daga cikin mutane akwai wanda yake cewa: "Ya Ubangjinmu! Ka ba mu a cikin duniya! Kuma ba ya da wanirabo a cikin Lahira

    [201] Kuma daga gare su akwai wanda yake cewa: "Ya Ubangijinmu! Ka ba mu mai kyau a cikin duniya da mai kyau a cikin Lahira, kuma Ka tsare mana azabar Wuta

    [202] Waɗannan suna da rabo daga abin da suka sana'anta; kuma Allah Mai gaggawar sakamako da yawa ne

    [203] Kuma ku ambaci Allah a cikin kwanuka ƙidayayyu. To, wanda ya yi gaggawa a cikin kwana biyu, to, babu laifi a kansa, kuma wanda ya jinkirta, to, babu laifi a kansa, ga wanda ya yi taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma ku sani cewa lalle ne ku, zuwa gare Shi ake tara ku

    [204] Kuma akwai daga mutane wanda maganarsa tana ba ka sha'awa a cikin rayuwar duniya, alhali yana shaidar da Allah a kan abin da yake cikin zuciyarsa, kuma shi mai tsananin husuma ne

    [205] Kuma idan ya juya sai ya yi gaggawa a cikin ƙasa domin ya yi ɓarna a cikinta, kuma ya halaka shuka da 'ya'yan dabbobi. Kuma Allah ba Ya son ɓarna

    [206] Kuma idan an ce masa: "Ka ji tsoron Allah," sai girman kai da yin zunubi ya ɗauke shi To abin da yake mai isarsa Jahannama ce. Kuma haƙiƙa, shimfiɗa ta munana

    [207] Kuma akwai daga mutane wanda yake sayar da ransa, domin neman yardar Allah: KumaAllah Mai tausayi ga bayi ne

    [208] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku shiga cikin Musulunci gaba ɗaya; kuma kada ku bi zambiyoyin Shaiɗan; lalle ne shi a gare ku maƙiyine, bayyananne

    [209] To, idan kun karkace daga bayan hujjoji bayyanannu sun zo muku to ku sani cewa lalle ne Allah, Mabuwayi ne, Mai hikima

    [210] Shin suna jira, face dai Allah Ya je musu a cikin wasu inuwoyi na girgije, da mala'iku, kuma an hukunta al'amarin? Kuma zuwa ga Allah al'amurra ake mayar da su

    [211] Ka tambayi Bani Isra'ila, da yawa Muka ba su daga ayoyi bayyanannu. Kuma wanda ya musanya ni'imar Allah daga bayan ta je masa, to, lalle ne Allah Mai tsananin uƙuba ne

    [212] An ƙawata rayuwar duniya ga waɗanda suka kafirta, kuma suna izgili daga waɗanda suka yi imani, alhali waɗanda suka yi taƙawa suna bisa gare su, a Ranar ¡iyama. Kuma Allah Yana azurta wanda Yake so, ba da lissafi ba

    [213] Mutane sun kasance al'umma guda. Sai Allah Ya aiki annabawa suna masu bayar da bishara kuma masu gargaɗi; kuma Ya saukar da Littafi da gaskiya tare da su domin (Littafin) ya yi hukunci a tsakanin mutanen a cikin abin da suka saɓa wa juna a cikinsa. kuma babu wanda ya saɓa, a cikinsa, face waɗanda aka bai wa shi daga bayan hujjoji bayyanannu sun je musu domin zalunci a tsakaninsu. Sai Allah Ya shiryar da waɗanda suka yi imani ga abin da suka saɓa a cikinsa daga gaskiya da izninSa. Kuma Allah Yana shiryar da wanda Yake so, zuwa ga hanya madaidaiciya

    [214] Ko kuna zaton ku shiga Aljanna kuma tun misalin waɗanda suka shige daga gabaninku bai zo muku ba? Wahaloli da cuta sun shafe su, kuma aka tsoratar da su har manzonsu da waɗanda suka yi imani tare da shi su ce: "Yaushe taimakon Allah zai zo?" To! Lalle ne, taimakon Allah yana kusa

    [215] Suna tambayar ka mene neza su ciyar. Ka ce: Abin da kuka ciyar daga alheri sai ga mahaifa da mafi kusantar dangantaka da marayu da matalauta da ɗan hanya. Kuma abin da kuka aikata daga alheri, to, lalle ne, Allah gare shi Masani ne

    [216] An wajabta yaƙi a kanku, alhali kuwa shi abin ƙi ne a gare ku, akwai fatar cewa ku ƙi wani abu, alhali shi ne mafi alheri a gare ku, kumaakwai fatar cewa kuna son wani abu alhali kuwa shi ne mafi sharri a gare ku. Kuma Allah ne Yake sani, kuma ku ba ku sani ba

    [217] Suna tambayar ka game da Watan Alfarma: yin yaki a cikinsa. Ka ce: "Yin yaƙi a cikinsa babban zunubi ne, kuma hani daga hanyar Allah, da kuma kafirci da Shi, da kuma da Masallaci Tsararre, da Kuma fitar da mutanensa daga gare shi, shi ne mafi girman zunubi a wurin Allah." Kuma fitina ita ce mafi girma daga kisa. Kuma ba su gushewa suna yaƙinku har su mayar da ku daga barin addininku idan za su iya. Kuma wanda ya yi ridda daga gare ku ga barin addininsa har ya mutu alhali kuwa yana kafiri, to, waɗannan ayyukansu sun ɓaci a cikin duniya da Lahira. Kuma waɗannan abokan Wuta ne, su a cikinta madawwama ne

    [218] Lalle ne waɗanda suka yi imani, da waɗanda suka yi hijira kuma suka yi jihadi a cikin hanyar Allah waɗannan suna fatar (samun) rahamar Allah kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [219] Suna tambayar ka game da giya da caca. Ka ce: "A cikinsu akwai zunubi mai girma da wasu amfanoni ga mutane, kuma zunubinsu ne mafi girma daga amfaninsu." Kuma suna tambayar ka mene ne za su ciyar; ka ce: "Abin da ya rage." Kamar wancan ne Allah Yake bayyanawar ayoyi a gare ku; tsammaninku, kuna tunani

    [220] A cikin duniya da Lahira. Kuma suna tambayar ka game da marayu. Ka ce: "Kyautatawa gare su ne mafi alheri, kuma idan kun haɗa da su (wajen abinci), to, 'yan'uwanku ne; kuma Allah Yana sanin mai ɓatawa daga mai kyautatawa. Kuma da Allah Ya so, da Ya tsananta muku. Lalle ne Allah Mabuwayi ne, Mai hikima

    [221] Kuma kada ku auri mata mushirikai sai sun yi imani: Kuma lalle ne baiwa muminaita ce mafi alheri daga ɗiya kafira, kuma ko da ta ba ku sha'awa. Kuma kada ku aurar wa maza mushirikai sai sun yi imani, kuma lalle ne bawa mumini shi ne mafi alheri daga da mushiriki, kuma ko da ya ba ku sha'awa, waɗannan suna kira ne zuwa ga wuta kuma Allah Yana kira zuwa ga Aljanna da gafara da izninsa. Kuma Yana bayyana ayoyinsa ga mutane; tsammaninsu suna tunawa

    [222] Kuma suna tambayar ka game da haila Ka ce: Shi cuta ne. Saboda haka ku nisanci mata a cikin wurin haila kuma kada ku kusance su sai sun yi tsarki. To, idan sun yi wanka sai ku je musu daga inda Allah Ya umurce ku. Lalle ne Allah Yana son masu tuba kuma Yana son masu tsarkakewa

    [223] Matanku gonaki ne a gare ku, saboda haka ku je wa gonakinku yadda kuka so. Kuma ku gabatar (da alheri) saboda kanku, ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cewa lalle neku masu haɗuwa da Shi ne. Kuma ka bayar da bishara ga muminai

    [224] Kuma kada ku sanya Allah kambu ga rantsuwoyinku domin kada ku yi wani alheri, kuma ku yi taƙawa, kuma ku yi wani gyara tsakanin mutane, kuma Allah Mai ji ne, Masani

    [225] Allah ba Ya kama ku da laifi saboda yasasshiya a cikin rantsuwoyinku. Kuma amma Yana kama ku saboda abin da zukatanku suka sana'anta. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai haƙuri

    [226] Ga waɗanda suke yin rantsuwa daga matansu akwai jinkirin wata huɗu. To, idan sun koma, to, lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [227] Kuma idan sun yi niyyar saki, to, lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani

    [228] Kuma mata waɗanda aka saki aurensu, suna jinkiri da kansu tsarki uku. Kuma ba ya halatta a gare su, su ɓoye abin da Allah Ya halitta a cikin mahaifunsu, idan sun kasance suna yin imani da Allah da Ranar Lahira. Kuma mazan aurensu su ne mafiya haƙƙi ga mayar da su a cikin wancan, idan sun yi nufin gyarawa. Kuma su matan suna da kamar abin da yake a kansu, yadda aka sani. Kuma maza suna da wata daraja a kansu (su matan). Kuma Allah Mabuwayi ne, Mai hikima

    [229] Saki sau biyu yake, sai a riƙa da alh eri, ko kuwa a sallama bisa kyautatawa. Kuma ba ya halatta a gare ku (maza) ku karɓe wani abu daga abin da kuka ba su, face fa idan su (ma'auran) na tsoron ba za su tsayar da iyakokin Allah ba, Idan kun (danginsu) ji tsoron ba za su tsayar da iyakokin Allah ba, to, babu laifi a kansu a cikin abin da ta yi fansa da shi. Waɗancan iyakokin Allah ne saboda haka kada ku ketare su. Kuma wanda ya ƙetare iyakokin Allah, to waɗannan su ne azzalumai

    [230] Sa'an nan idan ya sake ta (na uku), to, ba ta halatta a gare shi, daga baya, sai ta yi jima'i da wani miji waninsa. Sa'an nan idan (sabon mijin, watau na biyu) ya sake ta, to, babu laifi a kansu ga su koma wa (auren) juna, idan sun (mijin farko da matar) yi zaton cewa za su tsayar da iyakokin Allah, kuma waɗancan dokokin Allah ne Yana bayyana su ga mutane waɗanda suke sani

    [231] Kuma idan kun saki mata, sa'an nan suka isa ga ajalinsu (iddarsu), sai ku riƙe su da alheri ko ku sallame su da alheri, kuma kada ku riƙe su a kan cutarwa domin ta tsawaita idda. Kuma wanda ya aikata wancan, to, haƙiƙa, ya zalunci kansa. Kuma kada ku riƙi ayoyin Allah da izgili. Kuma ku tuna ni'imar Allah da abin da Ya saukar a kanku na Littafi da hikima. Yana yi muku wa'azi da shi. Kuma ku bi Allah da takawa kuma ku sani cewa lalle ne Allah ga dukan kome Masani ne

    [232] Kuma idan kuka saki mata, har suka isa ga ajalinsu (iddarsu), to, kada ku (waliyyansu) hana su, su auri mazansu (da suka sake su) idan sun yarda da juna a tsakaninsu (tsohon miji da tsohuwar mata) da alheri. Wancan ana yin wa'azi da shi ga wanda ya kasance daga gare ku yana imani da Allah da Ranar Lahira. Wancan ne mafi mutunci a gare ku, kuma mafi tsarki. Kuma Allah Yana sani, kuma ku ba ku sani ba

    [233] Kuma masu haifuwa (sakakku) suna shayar da abin haifuwarsu shekara biyu cikakku ga wanda ya yi nufin ya cika shayarwa. Kuma ciyar da su da tufatar da su yana a kan wanda aka haifar masa da alheri. Ba a kallafa wa rai face iyawarsa. Ba a cutar da uwa game da ɗanta, kuma ba a cutar da uba game da ɗansa, kuma a kan magaji akwai misalin wancan. To, idan suka yi nufin yaye, a kan yardatayya daga gare su, da shawartar juna, to babu laifi a kansu. Kuma idan, kun yi nufin ku bayar da ɗiyanku shayarwa, to, babu laifi a kanku idan kun miƙa abin da kukazo da shi bisa al'ada. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma ku sani cewa lalle ne Allah, ga abin da kuke aikatawa, Mai gani ne

    [234] Kuma waɗanda suke mutuwa daga gare ku suna barin matan aure, matan suna jinkiri da kansu wata huɗu da kwana goma. To, idan sun isa ga ajalinsu, to, babu laifi a kanku a cikin abin da suka aikata game da kansu ga al'ada. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne

    [235] Kuma babu laifi a kanku a cikin abin da kuka gitta da shi daga neman auren matako kuwa kuka ɓoye a cikin zukatanku. Allah Ya san cewa lalle ne ku za ku ambata musu (shi). Kuma amma kada ku yi wa juna alkawari da shia ɓoye, face dai ku faɗi magana sananniya. Kuma kada ku ƙulla niyyar daurin auren sai littafin (idda) ya kai ga ajalinsa. Kuma ku sani cewa lalle ne Allah Yana sanin abin da yake cikin zukatanku, saboda haka ku ji tsoronsa. Kuma ku sani cewa Allah Mai gafara ne, Mai haƙuri

    [236] Kuma babu laifi a kanku idan kun saki mata matuƙar ba ku shafe su ba, kuma ba ku yanka musu sadaki ba. Kuma ku ba su kyautar daɗaɗawa, a kan mawadaci gwargwadonsa, kuma a kan maƙuntaci gwargwadonsa; domin daɗaɗrwa, da alheri, wajibi ne a kan masu kyautatawa

    [237] Kuma idan kuka sake su daga gabanin ku shafe su, alhali kuwa kun yanka musu sadaki, to, rabin abin da kuka yanka face idan sun yafe, ko wanda ɗaurin auren yake ga hannunsa ya yafe. Kuma ku yafe ɗin ne mafi kusa da taƙawa. Kuma kada ku manta da falala a tsakaninku. Lalle ne Allah ga abin da kuke aikatawa Mai gani ne

    [238] Ku tsare lokatai a kan salloli da salla mafificiya. Kuma ku tsayu kuna masu ƙanƙan da kai ga Allah

    [239] To, idan kun ji tsoro, to (ku dai yi salla gwargwadon hali) da tafiya ƙasa ko kuwa a kan dabbobi. Sa'an nan idan kun amince sai ku ambaci Allah, kamar yadda Ya nuna muku abin da ba ku kasance kuna sani ba

    [240] Kuma waɗanda suke mutuwa daga gare ku, alhali suna barin matan aure, wasiyya ga matan aurensu da daɗaɗawa zuwa ga shekara guda babu fitarwa, to, idan sun fita to babu laifi a kanku a cikin abin da suka aikata game da kansu daga abin da aka sani, kuma Allah Mabuwayi ne, Mai hikima

    [241] Kuma waɗanda aka saki suna da daɗaɗawa gwargwadon hali, wajabce a kan masu taƙawa

    [242] Kamar wancan ne Allah Yake bayyana muku ayoyinSa; tsammaninku, kuna hankalta

    [243] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suka fita daga gidajensu, alhali kuwa su dubbai ne, domin tsoron mutuwa? Sai Allah Ya ce musu: "Ku mutu." Sa'an nan kuma Ya rayar da su, lalle ne Allah, haƙiƙa Ma'abucin falala a kan mutane ne, kuma amma mafi yawan mutane ba su godewa

    [244] Kuma ku yi yaƙi a cikin hanyar Allah, kuma ku sani cewa lalle ne, Allah Mai ji ne, Masani

    [245] Wane ne wanda zai bai wa Allah rance, rance mai kyau, domin Ya riɓanya masa, riɓanyawa mai yawa? Kuma Allah Shi ne ke damƙewa, kuma yana shimfiɗawa, kuma zuwa a gare Shi ake mayar da ku

    [246] Shin, ba ka gani ba zuwa ga wasu mashawarta daga Bani Isra'ila daga bayan Musa, a lokacinda suka ce ga wani annabi nasu: "Naɗa mana sarki, mu yi yaƙi a cikin hanyar Allah." Ya ce: "Ashe, akwai tsammaninku idan an wajabta yaƙi a kanku cewa ba za ku yi yaƙin ba?" Suka ce: "Kuma mene ne a gare mu, ba za mu yi yaƙi ba, a cikin hanyar Allah, alhali kuwa, haƙiƙa, an fitar da mu daga gidajenmu da ɗiyanmu?" To, a lokacin da aka wajabta yaƙin a kansu, suka juya, sai kaɗan daga gare su. Kuma Allah Masani ne ga azzalumai

    [247] Kuma annabinsu ya ce musu: "Lalle ne, Allah ya naɗa muku ¦aluta ya zama sarki." Suka ce: "Yaya ne sarauta za ta kasance a gare shi, a kanmu, alhali kuwa mu ne mafi cancanta da sarauta daga gare shi, kuma ba a ba shi wata wadata ba daga dukiya?" Ya ce: "Lalle ne, Allah Ya zaɓe shi a kanku, kuma Ya ƙara masa yalwa a cikin ilmi da jiki. Kuma Allah Yana bayar da mulkinSa ga wanda Yake so, kuma Allah Mawadaci ne, Masani

    [248] Kuma annabinsu ya ce musu: "Lalle ne alamar mulkinSa ita ce akwatin nan ya zo muku, a cikinsa akwai natsuwa daga Ubangijinku da sauran kaya daga abin da Gidan Musa da Gidan Haruna suka bari mala'iku suna ɗaukarsa. Lalle ne a cikin wancan akwai alama a gare ku (ta naɗin ¦aluta daga Allah ne) idan kun kasance masu imani

    [249] A lokacin da ¦aluta ya fita da rundunonin, ya ce: "Lalle ne Allah Mai jarrabarku ne da wani kogi. To, wanda ya sha daga gare shi, to, ba shi daga gare ni, kuma wanda bai ɗanɗane shi ba to lalle ne shi, yana daga gare ni, face, wanda ya kamfata, kamfata guda da hannunsa." Sai suka sha daga gare shi, face kaɗan daga gare su. To, a lokacin da (¦aluta) ya ƙetare shi, shi da waɗanda suka yi imani tare da shi, (sai waɗanda suka sha) suka ce: "Babu iko a gare mu yau game da Jaluta da rundunoninsa."Waɗanda suka tabbata cewa lalle su masu gamuwa ne da Allah, suka ce: "Da yawa ƙungiya kaɗan ta rinjayi wata ƙungiya mai yawa da iznin Allah, kuma Allah Yana tare da masu haƙuri

    [250] Kuma a lokacin da suka bayyana ga Jaluta da rundunoninsa, suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka zuba haƙuri a kanmu kuma Ka tabbatar da sawayenmu, kuma Ka taimake mu a kan mutanen nan kafirai

    [251] Sai suka karya su da iznin Allah. Kuma Dawudu ya kashe Jaluta, kuma Allah Ya ba shi mulki da hikima kuma Ya sanar da shi daga abin da Yake so. Kuma ba domin tunkuɗewar Allah ga mutane sashensu da sashe ba lalle ne da ƙasa ta ɓaci; kuma amma Allah Ma'abucin falala ne a kan talikai

    [252] Waɗancan ayoyin Allah ne: Muna karanta su a kanka da gaskiya: Kuma lalle ne kai, hakika, kana daga manzanni

    [253] Waɗancan manzannin Mun fifita sashensu a kan sashe: Daga cikinsu akwai wanda Allah Ya yi masa magana; kuma Ya ɗaukaka sashensu da darajoji; kuma Muka bai wa Isa dan Maryama hujjoji bayyanannu, kuma Muka ƙarfafa shi da Ruhi mai tsarki. Kuma da Allah Ya so da waɗanda suke daga bayansu, ba za su yi yaƙi ba, daga bayan hujjoji bayyanannu sun je musu. Kuma amma sun saɓa wa juna, saboda haka daga cikinsu akwai wanda ya yi imani, kuma daga cikin su akwai wanda ya kafirta. Kuma da Allah Ya so da ba za su yaƙi juna ba, kuma amma Allah Yana aikata abin da Yake nufi

    [254] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ciyar daga abin da Muka azurta ku daga gabanin wani yini ya zo babu ciniki a cikinsa kuma babu abuta, kuma babu ceto, kuma kafirai su ne azzalumai

    [255] Allah, babu wani Ubangiji face Shi, Rayayye, Mai tsayuwa da kome, gyangyaɗi ba ya kama Shi, kuma barci ba ya kama Shi, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa. Wane ne wanda yake yin ceto a wurinSa, face da izninSa? Yana sanin abin da yake a gaba gare su da abin da yake a bayansu. Kuma ba su kewayewa da kome daga ilminSa, face da abin da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa. Kuma tsare su ba ya nauyayarSa. Kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma

    [256] Babu tilastawa a cikin addini, haƙiƙa shiriya ta bayyana daga ɓata; Saboda haka wanda ya kafirta da ¦aguta kuma ya yi imani da Allah, to, haƙiƙa, ya yi riƙo ga igiya amintacciya, babu yankewa agare ta. Kuma Allah Mai ji ne, Masani

    [257] Allah Shi ne Masoyin waɗanda suka yi imani; Yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske, kuma waɗanda suka kafirta, masoyansu ¦agutu ne; suna fitar da su daga haske zuwa ga duffai. Waɗannan abokan Wuta ne, su a cikinta madawwama ne

    [258] Shin, ba ka gani ba zuwa ga wanda ya yi hujjatayya da Ibrahim a cikin (al'amarin) Ubangijinsa domin Allah Ya ba shi mulki, a lokacin da Ibrahim ya ce: "Ubangijina Shi ne Wanda Yake rayawa kuma Yana matarwa." Ya ce: "Ni ina rayarwa kuma ina matarwa." Ibrahim ya ce: "To, lalle ne Allah Yana zuwa da rana daga gabas: To, ka zo da ita daga yamma." Sai aka ɗimautar da wanda yakafirta. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [259] Ko kuwa wanda ya shuɗe a kan wata alƙarya, alhali kuwa tana wofintacciya a kan gadajen resunanta. Ya ce: "Yaya Allah zai rayar da wannan a bayan mutuwarta." Sai Allah Ya matar da shi, shekara ɗari; sa'an nankuma ya tayar da shi. Ya ce: "Nawa ka zauna?" Ya ce: "Na zauna yini ɗaya ko kuwa rabin yini." Ya ce: "A'a ka zauna shekara ɗari." To, ka duba zuwa ga abincinka, da abin shanka, (kowanensu) bai sake ba, kuma ka duba zuwa ga jakinka, kuma domin Mu sanya ka wata aya ga mutane. Kuma ka duba zuwa ga ƙasusuwa yadda Muke motsarda su sa'an nan kuma Mu tufatar da su, da nama", To, a lokacin da (abin) ya bayyana a gare shi, ya ce: "Ina sanin cewa lalle Allah a kan dukan kome Mai ikon yi ne

    [260] Kuma a lokacin da Ibrahim ya ce: "Ya Ubangijina! Ka nuna mini yadda Kake rayar da matattu." Ya ce: "Shin, kuma ba ka yi imani ba?" Ya ce: "Na'am! Kuma amma domin zuciyata, ta natsu." Ya ce: "To ka riƙi huɗu daga tsuntsaye, ka karkatar da su zuwa gare ka, ka yanka su, sa'an nan kuma ka sanya juzu'i daga gare su a kan kowane dutse, sa'an nan kuma ka kira su za su zo maka gudane. Kuma ka sani cewa lalle Allah Mabuwayi ne, Masani

    [261] Sifar waɗanda suke ciyar da dukiyoyinsu a cikin hanyar Allah, kamar sifar ƙwaya ce wadda ta tsirar da zangarniya bakwai, a cikin kowace zangarniya akwai ƙwaya ɗari. Kuma Allah Yana riɓinyawa ga wanda Ya so. Kuma Allah Mawadaci ne, Masani

    [262] Waɗanda suke ciyar da dukiyoyinsu a cikin hanyar Allah, sa'an nan kuma ba su biyar wa abin da suka ciyar ɗin da gori, ko cuta, suna da sakamakonsu a wurin ubangijinsu, kuma babu tsoro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba

    [263] Magana mai kyau da gafartawa su ne mafi alheri daga sadaka wadda wata cutarwa take biyar ta. Kuma Allah Wadatacce ne, Mai haƙuri

    [264] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku ɓata sadakokinku da gori da cutarwa, kamar wanda yake ciyar da dukiyarsa domin nuna wa mutane, kuma ba ya yin imani da Allah da Ranar Lahira. To, abin da yake misalinsa, kamar falalen dutse ne, a kansa akwai turɓaya, sai wabilin hadari ya same shi, sai ya bar shi ƙanƙara. Ba su iya amfani da kome daga abin da suka sana'anta. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai

    [265] Kuma sifar waɗanda suke ciyar da dukiyarsu domin neman yardojin Allah, kuma da tabbatarwa daga kansu, kamar misalin lambu ne a jigawa wadda wabilin hadari ya samu, sai ta bayar da amfaninta ninki biyu To, idan wabili bai same ta ba, sai yayyafi (ya ishe ta). Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Mai gani ne

    [266] Shin ɗayanku na son cewa wani lambu ya kasance a gare shi daga dabinai da inabobi' maremari suna gudana daga ƙarƙashinsa, yana da, a cikinsa daga kowane 'ya'yan itace, kuma tsufa ya same shi, alhali kuwa yana da zuriyya masu rauni sai guguwa wadda take a cikinta akwai wuta, ta same shi, har ta ƙone? Kamar wancan ne Allah Yana bayyanawar ayoyi a gare ku, tsammaninku kuna tunani

    [267] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ciyar daga mai kyaun abin da kuka sana'anta, kuma daga abin da Muka fitar saboda ku daga ƙasa, kuma kada ku yi nufin mummuna ya zama daga gare shi ne kuke ciyarwa, alhali kuwa ba ku zama masu karɓarsa ba face kun runtse ido a cikinsa. Kuma ku sani cewa lalle ne, Allah Mawadaci ne, Godadde

    [268] Shaiɗan yana yi muku alƙawarin talauci, kuma yana umurnin ku da alfasha, kuma Allah Yana yi muku alƙawarin gafara daga gare shi da ƙari, kuma Allah Mawadaci ne, Masani

    [269] Yana bayar da hikima (ga fahimtar gaskiyar abubuwa) ga wanda Yake so. Kuma wanda aka bai wa hikima to lalle ne an ba shi alheri mai yawa. Kuma babu mai tunani face ma'abuta hankula

    [270] Kuma abin da kuka ciyar daga ciyarwa, ko kuka cika alwashi daga wani bakance, to, lalle ne, Allah Yana sanin sa. Kuma azzalumai ba su da wasu mataimaka

    [271] Idan kun nuna sadakoki to, yana da kyau ƙwarai kuma idan kuka ɓoye su kuma kuka je da su ga matalauta, to shi ne mafi alheri a gareku, kuma Yana kankarewa, daga barinku, daga miyagun ayyukanku. Kuma Allah ga abin da kuke aikatawa Masani ne

    [272] Shiryar da su ba ya a kanka, kuma amma Allah Shi ne Yake shiryar da wanda Yake so, kuma abin da kuka ciyar daga alheri, to, domin kanku ne, kuma ba ku ciyarwa, face domin neman yardar Allah, kuma abin da kuke ciyarwa daga alheri za a cika ladarsa zuwa gare ku, alhali kuwa ku ba a zaluntarku

    [273] (Ciyarwar a yi ta) ga matalautan nan waɗanda aka tsare a cikin hanyar Allah, ba su iya tafiyar fatauci a cikin ƙasa, jahilin halinsu yana zaton su wadatattu saboda kamun kai kana sanin su da alamarsu, ba su roƙon mutane da nacewa. Kuma abin da kuka ciyar daga alheri, to, lalle Allah gare shi Masani ne

    [274] Waɗanda suke ciyar da dukiyoyinsu, a dare da yini, ɓoye da bayyane, to suna da sakamakonsu a wurin Ubangijinsu. Kuma babu tsoro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba

    [275] Wadanda suke cin riba ba su tashi, face kamar yadda wanda da Shaiɗan yake ɗimautarwa daga shafa yake tashi. Wancan, domin lalle ne sun ce: "Ciniki kamar riba yake."Kuma Allah Ya halatta ciniki kuma Ya haramta riba. To, wanda wa'azi daga Ubangijinsa, ya je masa, sa'an nan ya hanu, to yana da abin da ya shige, kuma al'amarinsa (ana wakkala shi) zuwa ga Allah. Kuma wanda ya koma, to, waɗannan su ne abokan Wuta, su a cikinta madawwama ne

    [276] Allah Yana shafe albarkar riba, kuma Yana ƙara sadakoki. Kuma Allah ba Ya son dukan mai yawan kafirci, mai zunubi

    [277] Lalle ne, waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka tsayar da salla, kuma suka bayar da zakka, suna da sakamakonsu a wurin Ubangijinsu, kuma babu tsoro a kansu, kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba

    [278] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku bar abin da ya rage daga riba, idan kun kasance masu imani

    [279] To, idan ba ku aikata ba to, ku sani fa da akwai yaƙi daga Allah da ManzonSa. Kuma idan kun tuba to kuna da asalin dukiyoyinku, ba ku zalunta, kuma ba a zaluntar ku

    [280] Kuma idan ma'abucin wahala ya kasance (mawahalci) to, jinkirtawa ake yi zuwa ga sauƙin al'amarinsa, kuma da kun yi sadaka, shi ne mafi alheri a gare ku, idan kun kasance kuna sani

    [281] Kuma ku ji tsoron wani yini wanda ake mayar da ku a cikinsa zuwa ga Allah, sa'an nan kuma a cika wa kowane rai abin da ya sana'anta, kuma su ba a zaluntar su

    [282] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun yi mu'amalar bayar da bashi zuwa ga wani ajali ambatacce, sai ku rubuta shi. Kuma wani marubuci ya yi rubutu a tsakaninku da adalci. Kuma kada marubuci ya ki rubutawa, kamar yadda Allah Ya sanar da shi, sai ya rubuta. Kuma wanda bashin yake a kansa sai ya yi shibta, kuma ya ji tsoron Allah, Ubangijinsa, da taƙawa, kuma kada ya rage wani abu daga gare shi. To, idan wanda bashin yake a kansa ya kasance wawa ne ko kuwa rarrauna, ko kuwa shi ba ya iya shibta, to, sai waliyyinsa ya yi shibtar da adalci. Kuma ku shaidar da shaidu biyu daga mazanku, to, idan ba su zama maza biyu ba, to, namiji guda da mata biyu, daga waɗanda kuke yarda da su daga shaidun domin mantuwar ɗayansu, sai gudarsu ta mazakutar da ɗayar. Kuma kada shaidun su ƙi, idan an kira su. Kuma kada ku ƙosa ga rubuta shi, ƙarami ya kasance ko babba, zuwa ajalinsa. Wancan ne mafi adalci a wurin Allah kuma mafi tsayuwa ga shaida, kuma mafi kusa ga rashin shakkarku. Sai idan ya kasance fatauci ne halartacce wanda kuke gewayarwa da shi hannu da hannu a tsakaninku to babu laifi a kanku, ya zama ba ku rubuta shi ba. Kuma ku shaidar idan kun yi sayayya. Kuma kada a wahalarda marubuci, kuma kada a wahalar da shaidu kuma idan kun aikata to, lalle ne, shi fasiƙanci ne game da ku. Kumaku bi Allah da takƙawa, kuma Allah Ya sanar da ku. Kuma Allah ga dukan kome Masani ne

    [283] Kuma idan kun kasance a kan tafiya, kuma ba ku sami marubuci ba, to, a bayar da jingina karɓaɓɓiya (ga hannu). To, idan sashenku ya amince wa sashe, to, wanda aka amince wannan sai ya bayar da amanarsa, kuma ya bi Allah, Ubangijinsa, da taƙawa. Kuma kada ku ɓoye shaida, kuma wanda ya ɓoye ta, to, shi mai zunubin zuciyarsa ne. KumaAllah ga abin da kuke aikatawa Masani ne

    [284] Allah ne, da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, kuma idan kun bayyana abin da yake a cikin zukatanku (na shaida), ko kuka ɓoye shi, Allah zai bincike ku da shi, sa'an nan Ya yi gafara ga wanda Yake so, kuma Ya azabta wanda Yake so. Kuma Allah a kan dukan kome Mai ikon yi ne

    [285] Manzon Allah ya yi imani da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da muminai. Kowanensu ya yi imani da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Ba mu rarrabewa a tsakanin daya daga manzanninSa. Kuma (muminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi da'a; (Muna neman) gafararKa, ya Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makoma take

    [286] Allah ba Ya kallafa wa rai face ikon yinsa, yana da ladar abin da ya tsirfanta, kuma a kansa akwai zunubin abin da ya yi ta aikatawa: "Ya Ubangijinmu! Kada Ka kama mu, idan mun yi mantuwa, ko kuma mun yi kuskure. Ya Ubangijinmu! Kuma kada Ka aza nauyi a kanmu, kamar yadda Ka aza shi a kan waɗanda suke a gabaninmu. Ya Ubangijinmu! Kada Ka sanya mu ɗaukar abin da babu iko gare mu da shi. Kuma Ka yafe daga gare mu, kuma Ka gafarta mana, kuma Ka yi jin ƙai gare mu. Kai ne Majibincinmu, saboda haka Ka taimake mu a kan mutanen nan kafirai

    Iyalan Imrana

    Surah 3

    [1] L. M

    [2] Allah, babu wani abin bautawa face Shi, Rayayye Mai tsayuwa da kome

    [3] Ya sassaukar da Littafi a gare ka da gaskiya, yana mai gaskatawa ga abin da ke gaba gare shi, kuma Allah Ya saukar da Attaura da Linjila

    [4] A gabani, suna shiryar da mutane, kuma Ya saukar da littattafai masu rarrabewa. Lalle ne waɗanda suka kafirta da ayoyin Allah, suna da azaba mai tsanani. Kuma Allah Mabuwayi ne, Ma'abucin azabar ramuwa

    [5] Lalle ne, Allah babu wani abin da ke ɓoyuwa gare Shi a cikin ƙasa, kuma babu a cikin sama

    [6] Shi ne wanda Yake suranta ku a cikin mahaifu yadda Yake so. Babu abin bautawa face Shi Mabuwayi, Mai hikima

    [7] Shi ne wanda ya saukar da Littafi a gare ka, daga cikinsa akwai ayoyi bayyanannu, su ne mafi yawan Littafin, da wasu masu kama da juna. To, amma waɗanda yake a cikin zukatansu akwai karkata sai suna bin abin da yake da kama da juna daga gare shi, domin neman yin fitina da tawilinsa. Kuma babu wanda ya san tawilinsaface Allah. Kuma matabbata a cikin ilmi suna cewa: "Mun yi imani da Shi; dukkansa daga wurin Ubangijinmu yake." Kuma babu mai tunani face ma'abuta hankula

    [8] Ya Ubangijinmu! Kada Ka karkatar da zukatanmu bayan har Ka shiryar da mu, kuma Ka ba mu rahama daga gunKa. Lalle ne, Kai, Kai ne Mai yawan kyauta

    [9] Ya Ubangijimu! Lalle ne Kai, Mai tara mutane ne domin wani yini wanda babu shakka a gare shi, Lalle ne Allah ba Ya saɓawar lokacin alkawari

    [10] Lalle ne waɗanda suka kafirta, dukiyoyinsu ba su tunkuɗe musu kome daga Allah, kuma 'ya'yansu ba su tunkuɗewa, kuma waɗannan, su ne makamashin wuta

    [11] Kamar ɗabi'ar mutanen Fir'auna da waɗanda ke a gabaninsu, sun ƙaryata ayoyinMu, sai Allah Ya kama su saboda zunubansu, kuma Allah Mai tsananin uƙuba ne

    [12] Ka ce wa waɗanda suka kafirta: "Za a rinjaye ku, kuma a taraku zuwa Jahannama, kuma shimfiɗar ta munana

    [13] Lalle ne wata aya ta kasance a gare ku a cikin ƙungiyoyi biyu da suka haɗu; ƙungiya guda tana yaƙi a cikin hanyar Allah, da wata kafira, suna ganin su ninki biyu nasu, a ganin ido. Kuma Allah Yana ƙarfafa wanda Yake so da taimakonSa. Lalle ne a cikin wannan, hakiƙa, akwai abin kula ga maabuta basira

    [14] An ƙawata wa mutane son sha'awoyi daga mata da ɗiya da dukiyoyi abubuwan tarawa daga zinariya da azurfa, da dawaki kiwatattu da dabbobin ci da hatsi. Wannan shi ne daɗin rayuwar duniya. Kuma Allah a wurinsa kyakkyawar makoma take

    [15] Ka ce: Shin kuma, in gaya muku mafi alheri daga wannan? Akwai gidajen Aljanna a wurin Ubangiji saboda waɗanda suka bi Shi da taƙawa, koguna suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, da matan aure tsarkakakku, da yarda daga Allah. Kuma Allah Mai gani ne ga bayinSa

    [16] Waɗanda suke cewa: "Ya Ubangijinmu! Lalle ne mu, mun yi imani, sai Ka gafarta mana zunubanmu kuma Ka tsare mu daga azabar wuta

    [17] Masu haƙuri, da masu gaskiya, da masu ƙanƙan da kai, da masu ciyarwa da masu istingifari a lokutan asuba

    [18] Allah Ya shaida cewa: Lalle ne babu abin bautawa face Shi kuma malaiku da ma'abuta ilmi sun shaida, yana tsaye da adalci, babu abin bautawa face Shi, Mabuwayi, Mai hikima

    [19] Lalle ne, addini a wurin Allah, Shi ne Musulunci. Kuma waɗanda aka bai wa Littafi ba su saɓa ba, face a bayan ilmi ya je musu, bisa zalunci a tsakaninsu. Kuma wanda ya kafirta da ayoyin Allah, to, lalle ne Allah Mai gaugawar sakamako ne

    [20] To, idan sun yi musu da kai, sai ka ce: "Na sallama fuskata ga Allah, kuma wanda ya bi ni (haka)." Kuma ka ce wa waɗanda aka bai wa littafi da Ummiyyai: "Shin kun sallama?" To, idan sun sallama, haƙiƙa, sun shiryu kuma idan sun juya, to, kawai abinda ke kanka, shi ne iyarwa. Kuma Allah Mai gani ne ga bayinSa

    [21] Lalle ne waɗanda suke kafirta da ayoyin Allah, kuma suna kashe Annabawa ba da wani hakki ba, kuma suna kashe waɗanda ke umurni da yin adalci daga mutane, to, ka yi musu bushara da azaba mai raɗaɗi

    [22] Waɗannan ne waɗanda ayyukansu suka ɓaci a cikin duniya da Lahira, kuma ba su da wasu mataimaka

    [23] Shin, ba ka ga waɗanda aka bai wa rabo daga littafi ba ana kiran su zuwa ga Littafin Allah domin ya yi hukunci a tsakaninsu sa'an nan wata ƙungiya daga cikinsu ta juya baya, kuma suna masu bijirewa

    [24] Wannan kuwa, domin lalle ne su sun ce: "Wuta ba za ta shafe mu ba, face a 'yan kwanaki ƙidayayyu." Kuma abin da suka kasance suna ƙirƙirawa na ƙarya ya ruɗe su a cikin addininsu

    [25] To, yaya idan Mun tara su a yini wanda babu shakka a cikinsa, kuma aka cika wa kowane rai sakamakon abin da ya tsirfanta, alhali kuwa, su ba za a zalunce su ba

    [26] Ka ce: "Ya Allah Mamallakin mulki, Kana bayar da mulki ga wanda Kake so, Kana zare mulki daga wanda Kake so, kuma Kana buwayar da wanda Kake so, kuma Kana ƙasƙantar da wanda Kake so, ga hannunKa alheri yake. Lalle ne Kai, a kan kowane abu, Mai ikon yi ne

    [27] Kana shigar da dare a cikin yini, kuma Kana shigar da yini a cikin dare, kuma Kana fitar da mai rai daga mamaci, kuma Kana fitar da mamaci daga mai rai, kuma Kana azurta wanda Kake so ba da lissafi ba

    [28] Kada muminai su riƙi kafirai masoya, baicin muminai. Kuma wanda ya yi wannan, to, bai zama a cikin kome ba daga Allah, face fa domin ku yi tsaro daga gare su da 'yar kariya. Kuma Allah yana tsoratar da ku kanSa. Kuma zuwa ga Allah makoma take

    [29] Ka ce: "Idan kun ɓoye abin da ke a cikin ƙirazanku, ko kuwa kun bayyana shi, Allah Yana sanin sa. Kuma Yana sanin abin da ke a cikin sammai da ƙasa. Kuma Allah a kan kowane abu Mai ikon yi ne

    [30] A Ranar da kowane rai yake samun abin da ya aikata daga alheri, a halarce, da kuma abin da ya aikata daga sharri, alhali yana gurin, da dai lalle a ce akwai fage mai nisa a tsakaninsa da abin daya aikata na sharrin! Kuma Allah Yana tsoratar da ku kanSa. Kuma Allah Mai tausayi ne ga bayinSa

    [31] Ka ce: "Idan kun kasance kuna son Allah to, ku bi ni, Allah Ya so ku, kuma Ya gafarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [32] Ka ce: "Ku yi ɗa'a ga Allah da Manzo." To, amma idan sun juya baya, to, lalle ne Allah ba Ya son kafirai

    [33] Lalle ne Allah Ya zaɓi Adama da Nuhu da Gidan Ibrahima da Gidan Imrana a kan talikai

    [34] Zuriyya ce sashensu daga sashe, kuma Allah Mai ji ne, Masani

    [35] A lokacin da matar Imrana ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle ni, na yi bakancen abin da ke cikin cikina gare Ka; ya zama 'yantacce, sai Ka karɓa daga gare ni. Lalle ne Kai, Kai ne Mai ji, Masani

    [36] To, a lokacin da ta haife ta sai ta ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne ni, na haife ta mace!"KumaAllah ne Mafi sanin abin da ta haifa." Kuma namiji bai zama kamar mace ba. Kuma ni na yi mata suna Maryamu kuma lalle ne ni, ina nema mata tsari gare Ka, ita da zuriyarta daga Shaiɗan jefaffe

    [37] Sai Ubangijinta Ya karɓe ta karɓa mai kyau. Kuma Ya yabanyartar da ita yabanyartarwa mai kyau, kuma Ya sanya renonta ga Zakariyya. Ko da yaushe Zakariyya ya shiga masallaci, a gare ta, sai ya sami abinci a wurinta. (Sai kuwa) ya ce: "Ya Maryamu! Daga ina wannan yake gare ki?" (Sai) ta ce: "Daga wurin Allah yake. Lalle ne Allah yana azurta wanda Ya so ba da lissafi ba

    [38] A can ne Zakariyya ya roki Ubangijinsa, ya ce: "Ya Ubangijina! Ka ba ni zuriyya mai kyau daga gunKa. Lalle ne Kai Mai jin addu'a Kake

    [39] Sai mala'iku suka kiraye shi, alhali kuwa shi yana tsaye yana salla a cikin masallaci. (Suka ce), "Lalle ne Allah yana ba ka bushara da Yahaya, alhali yana mai gaskatawar wata kalma daga Allah, kuma shugaba, kuma tsarkakke kuma annabi daga salihai

    [40] Ya ce: "Ya Ubangijina! Yaya yaro zai samu a gare ni, alhali kuwa, lalle tsufa ya same ni, kuma matata bakarariya ce?" Allah ya ce, "Kamar hakan ne, Allah yana aikata abin da Yake so

    [41] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka sanya mini wata alama!" (Allah) Ya ce "Alamarka ita ce ba za ka iya yi wa mutane magana ba har yini uku face da ishara. Sai ka ambaci Ubangijinka da yawa. Kuma ka yi tasbihi da marece da safe

    [42] Kuma a lokacin da mala'iku suka ce: "Ya Maryamu! Lalle ne, Allah Ya zaɓe ki, kuma Ya tsarkake ki, kuma Ya zaɓe ki a kan matan talikai

    [43] Ya Maryamu! Ki yi ƙanƙan da kai ga Ubangijinki, kuma ki yi sujada, kuma ki yi ruku'i tare da masu ruku'i

    [44] Wannan yana daga labarun gaibi, Muna yin wahayinsa zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka kasance ba a wurinsu a lokacin da suke jefa alƙalumansu (domin ƙuri'a) wane ne zai yi renon Maryam. Kuma ba ka kasance a wurinsu ba a lokacin da suke ta yin husuma

    [45] A lokacin da mala'iku suka ce "Ya Maryamu! Lalle ne Allah Yana ba ki bushara da wata kalma daga gare Shi; sunansa Masihu isa ɗan Maryama, yana mai daraja a duniya da Lahira kuma daga Makusanta

    [46] Kuma yana yi wa mutane magana a cikin shimfiɗar jariri, da kuma lokacin da yana dattijo, kuma yana daga salihai

    [47] Ta ce: "Ya Ubangijina! Yaya yaro zai kasance a gare ni, alhali kuwa wani mutum bai shafe ni ba?" (Allah) Ya ce: "Kamar wannan ne, Allah yana halittar abin da Yake so. Idan Ya hukunta wani al'amari, sai ya ce masa, "Ka kasance!, Sai yana kasancewa

    [48] Kuma Ya sanar da shi rubutu da hikima da Taurata da injila

    [49] Kuma (Ya sanya shi) manzo zuwa ga Bani Israila'ila (da sako, cewa), Lalle ne, ni haƙiƙa na zo muku, da wata aya daga Ubangijinku. Lalle ne ni ina halitta muku daga laka, kamar siffar tsuntsu sa'an nan in hura a cikinsa, sai ya kasance tsuntsu, da izinin Allah. Kuma ina warkar da wanda aka haifa makaho da kuturu, kuma ina rayar da matottu, da izibin Allah. Kuma ina gaya muku abin da kuke ci da abin da kuke ajiyewa acikin gidajenku. Lalle ne, a cikin wannan akwai aya a gare ku, idan kun kasance masu yin imani

    [50] Kuma ina mai gaskatawa ga abin da yake a gabanina daga Taurata. Kuma (nazo) domin in halatta muku sashen abin da aka haramta muku. Kuma na tafo muku da wata aya daga Ubangijinku. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [51] Lalle Allah shi ne Ubangijina, kuma Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Wannan ce hanya madaidaiciya

    [52] To, a lokacin da Isa ya gane kafirci daga gare su, sai ya ce: "Su wane ne mataimakana zuwa ga Allah?" Hawariyawa suka ce: "Mu ne mataimakan Allah. Mun yi imani da Allah. Kuma ka shaida cewa lalle ne mu, masu sallamawa ne

    [53] Ya Ubangijinmu! Mun yi imani da abin da Ka saukar, kuma mun bi ManzonKa, sai Ka rubuta mu tare da masu shaida

    [54] Kuma (Kafirai) suka yi makirci, Allah kuma Ya yi musu (sakamakon) makircin, kuma Allah ne Mafi alherin masu saka wamakirci

    [55] A lokacin da Ubangiji Ya ce: "Ya Isa! Lalle NI Mai karɓar ranka ne, kuma Mai ɗauke ka ne zuwa gare Ni, kuma Mai tsarkake ka daga waɗanda suka kafirta, kuma Mai sanya waɗanda suka bi ka a bisa waɗanda suka kafirta har Ranar ¡iyama. Sa'an nan kuma zuwa gare Ni makomarku take, sa'an nan in yi hukunci a tsakaninku, a cikin abin da kuka kasance kuna saɓa wa juna

    [56] To, amma waɗanda suka kafirta sai In azabta su da azaba mai tsanani, a cikin duniya da Lahira, kuma ba su da wasu masu taimako

    [57] Kuma amma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sai (Allah) Ya cika musu ijarorinsu. Kuma Allah ba Ya son azzalumai

    [58] Wannan Muna karanta shi a gare ka (Muhammad) daga ayoyi, da Tunatarwa mai hikima (Alƙur'ani)

    [59] Lalle ne misalin Isa a wurin Allah kamar misalin Adama ne, (Allah) Ya halitta shi daga turɓaya, sa'an nan kuma Ya ce masa: "Ka kasance: "Sai yana kasancewa

    [60] Gaskiya daga Ubangijinka take saboda haka kada ka kasance daga masu shakka

    [61] To, wanda ya yi musu da kai a cikinsa, a bayan abin da ya zo maka daga ilmi, to ka ce: "Ku zo mu kirayi, 'ya'yanmu da 'ya'yanku da matanmu da matanku da kanmu da kanku sa'an nan kuma mu ƙanƙantar da kai sa'an nan kuma mu sanya la'anar, Allah a kan maƙaryata

    [62] Lalle ne wannan, haƙiƙa, shi ne labari tabbatacce, kuma babu wani abin bautawa face Allah, kuma lalle ne, Allah, haƙiƙa, Shi ne Mabuwayi Mai hikima

    [63] To, idan sun juya baya, to, lalle Allah Masani ne ga maɓannata

    [64] Ka ce: "Ya ku Mutanen Littafi! Ku tafo zuwa ga kalma mai daidaitawa a tsaka ninmu da ku; kada mu bauta wa kowa fa ce Allah. Kuma kada mu haɗa kome da Shi, kuma kada sashenmu ya riƙi sashe Ubangiji, baicin Allah." To, idan sun juya ba ya sai ku ce: "ku yi shaida cewa, lalle ne mu masu sallama wa ne

    [65] Ya Mutanen Littafi! Don me kuke hujjacewa a cikin sha'anin lbrahima, alhali kuwa ba a saukar da Attaura da injila ba face daga bayansa? Shin ba ku hankalta

    [66] Ga ku ya waɗannan! Kun yi hujjacewa a cikin abin da yake kuna da wani ilmi game da shi, to, don me kuma kuke yin hujjacewa a cikin abin da ba ku da wani ilmi game da shi? Allah yana sani, kuma ku, ba ku sani ba

    [67] Ibrahima bai kasance Bayahude ba, kuma bai kasance Banasare ba, amma ya kasance mai karkata zuwa ga gaskiya, mai sallamawa, kuma bai kasance daga masu shirki ba

    [68] Lalle ne mafi hakkin mutane da Ibrahima haƙiƙa, su ne waɗanda suka bi shi a (zamaninsa) da wannan Annabi (Muhammadu) da waɗanda suka yi imani. Kuma Allah ne Majiɓincin muminai

    [69] Wata ƙungiya daga Mutanen Littafi sun yi gurin su ɓatar da ku, to, ba su ɓatar da kowa ba face kansu, kuma ba su sansancewa

    [70] Ya Mutanen Littafi! Don me kuka kafirta da ayoyin Allah, alhali kuwa ku, kuna shaida (cewa su gaskiya ne)

    [71] Ya Mutanen Littafi! Don me kuke lulluɓe gaskiya da ƙarya, kuma kuke ɓoye gaskiya, alhali kuwa kuna sane

    [72] Kuma wata ƙungiya daga Mutanen Littafi ta ce: "Ku yi imani da abin da aka saukar a kan waɗanda suka yi imani (da Muhammadu) a farkon yini, kuma ku kafirta a ƙarshensa; tsammaninsu, za su komo

    [73] Kada ku yi imani face da wanda ya bi addininku." Ka ce: "Lalle ne, shiriya ita ce shiriyar Allah. (Kuma kada ku yi imani) cewa an bai wa wani irin abin da aka ba ku, ko kuwa su yi musu da ku a wurin Ubangijinku." Ka ce: "Lalle ne falala ga hannun Allah take, yana bayar da ita ga wanda Yake so, kuma Allah Mawadaci ne, Masani

    [74] Yana keɓance wanda Ya so da rahamarSa, kuma Allah Ma'abucin falala ne, Mai girma

    [75] Kuma daga Mutanen Littafi akwai wanda yake idan ka ba shi amanar kinɗari, zai bayar da shi gare ka, kuma daga gare su akwai wanda idan ka ba shi amanar dinari, ba zai bayar da shi gare ka ba, face idan ka dawwama a kansa kana tsaye. Wannan kuwa, domin lalle ne su sun ce, "Babu laifi a kanmu a cikin Ummiyyai." Suna faɗar ƙarya ga Allah, alhali kuwa suna sane

    [76] Na'am! Wanda ya cika alkawarinsa, kuma ya yi taƙawa, to, lalle ne Allah yana son masu taƙawa

    [77] Lalle ne waɗanda suke sayen 'yan tamani kaɗan da alkawarin Allah da rantsuwoyinsu, waɗannan babu wani rabo a gare su a Lahira, Kuma Allah ba Ya yin magana da su, kuma ba Ya dubi zuwa gare su, a Ranar ¡iyama, kuma ba Ya tsarkake su, kuma suna da azaba mai raɗaɗi

    [78] Kuma lalle ne, daga gare su akwai wata ƙungiya suna karkatar da harsunansu da Littafi domin ku yi zaton sa daga Littafin, alhali kuwa ba shi daga Littafin. Kuma suna cewa: "Shi daga wurinAllah yake." Alhali kuwa shi, ba daga wurin Allah yake ba. Suna faɗar ƙarya ga Allah, alhali kuwa suna sane

    [79] Ba ya yiwuwa ga wani mutum, Allah Ya ba shi Littafi da hukunci da Annabci, sa'an nan kuma ya ce wa mutane: "Ku kasance bayi gare ni, baicin Allah." Amma (zai ce): "Ku kasance masu aikin ibada da abin da kuka kasance kuna karantar da Littafin, kuma da abin da kuka kasance kuna karantawa

    [80] Kuma ba ya umurnin ku da ku riƙi mala'iku da annabawa lyayengiji. Shin, zai umurce ku da kafirci ne a bayan kun riga kun zama masu sallamawa (Musulmi)

    [81] Kuma a lokacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabawa: "Lalle ne ban ba ku wani abu ba daga Littafi da hikima, sa'an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatawa ga abin da yake tare da ku; lalle ne za ku gaskata Shi, kuma lalle ne za ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawariNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Ni a tare da ku Ina daga masu shaida

    [82] To, waɗanda kuma suka juya baya a bayan wannan, to, waɗannan su ne fasiƙai

    [83] Shin wanin Addinin Allah suke nema, alhali kuwa a gare Shi ne waɗanda ke cikin sama da ƙasa suka sallama wa, a kan so da ƙi, kuma zuwa gare Shi ake mayar da su

    [84] Ka ce: "Mun yi imani da Allah kuma da abin da aka saukar mana da abin da aka saukar wa Ibrahima da Isma'ila da Is'haƙa da Yaƙuba da jikoki, da abin da aka bai wa Musa da isa da annabawa daga Ubangijinsu, ba mu bambantawa a tsakanin kowa daga gare su. Kuma mu, zuwa gare Shi masu sallamawa ne

    [85] Kuma wanda ya nemi wanin Musulunci ya zama addini, to, ba za a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lahira yana daga cikin masu hasara

    [86] Yaya Allah zai shiryar da mutane waɗanda suka kafirta a bayan imaninsu, kuma sun yi shaidar cewa, lalle Manzo gaskiya ne, kuma hujjoji bayyanannu sun je musu? Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [87] Waɗannan, sakamakonsu shi ne, lalle a kansu akwai la'anar Allah da mala'iku da mutane gaba ɗaya

    [88] Suna masu dawwama a cikinta, ba a sauƙaƙa azabar gare su, kuma ba su zama ana yi musu jinkiri ba

    [89] Face waɗanda suka tuba daga bayan wannan, kuma suka yi gyara, to, lalle ne Allah Mai gafara ne Mai jin ƙai

    [90] Lalle ne waɗanda suka kafirta a bayan imaninsu, sa'an nan kuma suka ƙara kafirci ba za a karɓi tubarsu ba. Kuma waɗannan su ne ɓatattu

    [91] Lalle ne wanɗanda suka kafirta, kuma suka mutu alhali kuwa suna kafirai to ba za a karɓi cike da ƙasa na zinari daga ɗayansu ba, ko da ya yi fansa da shi, waɗannan suna da azaba mai raɗaɗi, kuma ba su da wasu mataimaka

    [92] Ba za ku sami kyautatawa ba, sai kun ciyar daga abin da kuke so. Kuma abin da kuka ciyar, ko mene ne, to, lalle ne Allah, gare shi, Masani ne

    [93] Dukan abinci ya kasance halal ne ga Bani lsra'ila, face abinda Isra'ila ya haramta wa kansadaga gabanin saukar da Attaura. Ka ce: "To, ku zo da Attaura sa'an nan ku karanta ta, idan kun kasance masu gaskiya ne

    [94] To, wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah daga bayan wannan, to, waɗannan su ne azzalumai

    [95] Ka ce: "Allah Ya yi gaskiya, saboda haka ku bi aƙidar Ibrahima mai karkata zuwa ga gaskiya; kuma bai kasance daga masu shirki ba

    [96] Kuma lalle ne, ¦aki na farko da aka aza domin mutane, haƙiƙa, shi ne wanda ke Bakka mai albarka kuma shiriya ga talikai

    [97] A cikinsa akwai ayoyi bayyanannu; (ga misali) matsayin Ibrahima. Kuma wanda ya shige shi ya kasance amintacce. Kuma akwai hajjin ¦akin domin Allah a kan mutane, ga wanda ya sami ikon zuwa gare shi, kuma wanda ya kafirta to lalle Allah Mawadaci ne daga barin talikai

    [98] Ka ce: "Ya ku Mutanen Littafi! Don me kuke kafirta da ayoyin Allah, alhali kuwa Allah Mai shaida ne a kan abin da kuke aikatawa

    [99] Ka ce: "Ya ku Mutanen Littafi! Don me kuke taushe wanda ya yi imani, daga hanyar Allah, kuma kuna neman ta zama karkatacciya, alhali kuwa kuna masu shaida? Kuma Allah bai gushe daga abin da kuke aikatawa ba yana Masani

    [100] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun yi ɗa'aga wani ɓangare daga waɗanda aka bai wa Littafi, za su mayar da ku kafirai a bayan imaninku

    [101] Kuma yaya kuke kafircewa alhali kuwa ana karanta ayoyin Allah a gare ku, kuma a cikinku akwai manzonSa? Kuma wanda ya nemi tsari da Allah, to, an shiryar da shi zuwa ga hanya miƙaƙƙiya

    [102] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku bi Allah da taƙawa, a kan hakkin binsa da taƙawa, kuma kada ku mutu face kuna masu sallamawa (Musulmi)

    [103] Kuma ku yi daidami da igiyar Allah gaba ɗaya, kuma kada ku rarraba. Kuma ku tuna ni'imar Allah a kanku a lokacin da kuka kasance maƙiya sai Ya sanya soyayya a tsakanin zukatanku saboda haka kuka wayi gari, da ni'imarSa, 'yan'uwa. Kuma kun kasance a kan gaɓar rami na wuta sai Ya tsamar da ku daga gare ta, Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ayoyinSa, tsammaninku, za ku shiryu

    [104] Kuma wata jama'a daga cikinku, su kasance suna kira zuwa ga alheri, kuma suna umurnida alheri, kuma suna hani dagaabin da ake ƙi. Kuma waɗannan, su ne masu cin nasara

    [105] Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka rarrabu kuma suka saɓa wa juna, bayan hujjoji bayyanannu sun je musu kuma waɗannan suna da azaba mai girma

    [106] A ranar da wasu fuskoki suke yin fari kuma wasu fuskoki suke yin baƙi (za a ce wa waɗanda fuskokinsu suke yin baƙin): "Shin kun kafirta a bayan imaninku? Don haka sai ku ɗanɗani azaba saboda abin da kuka kasance kuna yi na kafirci

    [107] Kuma amma waɗanda fuskokinsu suka yi fari, to su suna cikin rahamar Allah kuma, su a cikinta, madawwama, ne

    [108] Waɗannan ayoyin Allah ne, muna karanta su a gare ka da gaskiya, kuma Allah ba Ya nufin wani zalunci ga talikai

    [109] Kuma abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa na Allah ne, kuma zuwa gare Shi ake mayar da al'amurra

    [110] Kun kasance mafi alherin al'umma wadda aka fitar ga mutane kuna umurni da alheri kuma kuna hani daga abin da ake ƙi, kuma kuna imani da Allah. Kuma da Mutanen Littafi sun yi imani, lalle ne, da (haka) ya kasance mafi alheri a gare su. Daga cikinsu akwai muminai, kuma mafi yawansufasiƙai ne

    [111] Ba za su cuce ku ba, face dai tsangwama. Kuma idan sun yaƙe ku za su juya muku baya, sa'an nan kuma ba za a taimake su ba

    [112] An doka ƙasƙanci a kansu a inda duk aka same su face da wani alkawari daga Allah, da alkawari daga mutane. Kuma sun koma da fushi daga Allah, kuma aka doka talauci a kansu. Wannan kuwa domin su, lalle sun kasance suna kafirta da ayoyin Allah, kuma suna kashe annabawa, ba da wani haƙƙi ba. Wannan kuwa domin saɓawar da suka yi ne, kuma sun kasance suna yin ta'adi

    [113] Ba su zama daidai ba; daga Mutanen Littafi akwai wata al'umma wadda take tsaye, suna karatun ayoyin Allah a cikin sa'o'in dare, alhali kuwa suna yin sujada

    [114] Suna imani da Allah da Yinin Lahira, kuma suna umurui da abin da aka sani kuma suna hani daga abin da ba a sani ba, kuma suna gaugawa a cikin alherai. Kuma waɗannan suna cikin salihai

    [115] Kuma abin da suka aikata daga alheri, to, ba za a yi musu musunsa ba. Kuma Allah Masani ne ga masu taƙawa

    [116] Lalle ne waɗanda suka kafirta, dukiyoyinsu ko ɗiyansu ba za su wadatar musu da kome ba daga Allah kuma waɗannan abokan wuta ne, su, acikinta, madawwama ne

    [117] Misalin abin da suke ciyarwa, a cikin wannan rayuwar duniya, kamar misalin iska ce (wadda) a cikinta akwai tsananin sanyi, ta sami shukar wasu mutane waɗanda suka zalunci kansu, sai ta halakar da ita. Allah bai zalunce su ba, amma kansu suka kasance suna zalunta

    [118] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku riƙi abokan asiri daga waninku, ba su taƙaita muku ɓarna. Kuma sun yi gurin abin da za ku cutu da shi. Haƙika, ƙiyayya ta bayyana daga bakunansu, kuma abin da zukatansu ke ɓoyewane mafi girma. Kuma lalle ne, Mun bayyana muku ayoyi, idan kun kasance kuna hankalta

    [119] Ga ku ya waɗannan! Kuna son su ba su son ku, kuma kuna imani da Littafi dukansa. Kuma idan sun haɗu da ku sukan ce "Mun yi imani". Kuma idan sun kaɗaita sai su ciji yatsu a kanku don takaici. Ka ce "Ku mutu da takaicinku. Lalle ne, Allah Masani ne ga abin da ke cikin ƙiraza

    [120] Idan wani alheri ya shafe ku sai ya baƙanta musu rai, kuma idan wata cutar ta shafe ku sai su yi farin ciki da ita. Kuma idan kun yi haƙuri kuma kuka yi taƙawa, ƙullinsu ba ya cutar ku da kome. Lalle ne, Allah ga abin da suke aikatawa Mai kewayewa ne

    [121] Kuma a lokacin da ka yi sauko daga iyalanka kana zaunar da muminai a wuraren zamadomin yaƙi, kuma Allah Mai ji ne, Masani

    [122] A lokacin da ƙungiyoyi biyu daga gare ku suka yi niyyar su karye, kuma Allah ne Majiɓincinsu, don haka, ga Allah muminai sai su dogara

    [123] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Allah Ya taimake ku a Badar, alhali kuwa kuna mafiya rauni, saboda haka ku bi Allah da taƙawa tsammaninku, kuna godewa

    [124] A lokacin da kake cewa ga muminai, "Shin bai ishe ku ba, Ubangijinku Ya taimake ku da dubu uku daga mala'iku saukakku

    [125] Na'am! Idan kuka yi haƙuri, kuma kuka yi taƙawa, kuma suka zo muku da gaugawarsu, irin wannan, Ubangijinku zai ƙare ku da dubu biyar daga malaiku masu alama

    [126] Kuma Allah bai sanya shi ba, face domin bushara a gare ku, kuma domin zukatanku su natsu da shi. Taimako bai kasance ba face daga wurin Allah, Mabuwayi, Mai hikima

    [127] Domin Ya katse wani gefe daga waɗanda suka kafirta ko kuma Ya ƙasƙanta su, har su juya, suna masu ruɓushi

    [128] Babu kome a gare ka game da al'amarin (shiryar da su banda iyar da manzanci). Ko Allah Ya karɓi tubarsu, ko kuwa Ya yimusu azaba, to lalle ne su, masu zalunci ne

    [129] Allah ne da mulkin abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, yana gafarta wa wanda Yake so, kuma yana azabta wanda Yake so, kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [130] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku ci riba ninkininki, riɓanye, kuma ku bi Allah da taƙawa, tsammaninku za ku ci nasara

    [131] Kuma ku ji tsoron wuta wadda aka yi tattali domin kafirai

    [132] Kuma ku yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, tsammaninku a yi muku rahama

    [133] Kuma ku yi gaugawa zuwa ga neman gafara daga Ubangijinku da wata Aljanna wadda faɗinta (dai dai da) sammai da ƙasa ne, an yi tattalinta domin masu taƙawa

    [134] Waɗanda suke ciyarwa a cikin sauƙi da tsanani kuma suke masu haɗiyewar fushi, kuma masu yafe wa mutane laifi. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa

    [135] Kuma waɗanda suke idan suka aikata wata alfasha ko suka zalunci kansu sai su tuna da Allah, saboda su nemi gafarar zunubansu ga Allah. Kuma wane ne ke gafara ga zunubai, face Allah? Kuma ba su doge a kan abin da suka aikata ba, alhali kuwa suna sane

    [136] Waɗannan sakamakonsu gafara ce daga Ubangijinsu, daga Gidajen Aljanna (waɗanda) ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu. Kuma madalla da ijarar masu aiki

    [137] Lalle ne misalai sun shuɗe a gabaninku, sai ku yi tafiya a cikin ƙasa sa'an nan ku duba, yaya aƙibar masu ƙaryatawa ta kasance

    [138] Wannan bayani ne ga mutane, kuma shiryuwa ce da wa'azi ga masu taƙawa

    [139] Kuma kada ku yi rauni, kuma kada ku yi baƙin ciki, alhali kuwa ku ne mafiya ɗaukaka, idan kun kasance masu imani

    [140] Idan wani miki ya shafe ku, to, lalle ne, wani miki kamarsa ya shafi mutanen, kuma waɗancan kwanaki Muna sarrafa su a tsakanin mutane domin Allah Ya san waɗanda suka yi imani kuma Ya sami masu shahada daga gare ku. Kuma Allah ba Ya son azzalumai

    [141] Kuma domin Allah Ya ɗauraye waɗanda suka yi imani, kuma Ya ƙoƙe kafirai

    [142] Ko kun yi zaton ku shiga Aljanna alhali kuwa Allah bai bada sanin waɗanda suka yi jihadi daga gare ku ba, kuma Ya san masu haƙuri

    [143] Kuma lalle ne, haƙiƙa kun kasance kuna gurin mutuwa tun a gabanin ku haɗu da ita, to lalle ne kun gan ta, alhali kuwa kuna kallo

    [144] Kuma Muhammadu bai zama ba face manzo lalle ne manzanni sun shuɗe a gabaninsa. Ashe idan ya mutu ko kuwa aka kashe shi, za kujuya a kan dugaduganku? To, wanda ya juya a kan dugadugansa, ba zai cuci Allah da kome ba. Kuma Allah zai saka wa masu godiya

    [145] Kuma ba ya yiwuwa ga wani rai ya mutu face da iznin Allah, wa'adi ne mai ƙayyadadden ajali. Kuma wanda yake nufin sakamakon duniya Muna ba shi daga gare ta. Kuma wanda ke nufin samakon Lahira Muna ba shi daga gare ta. Kuma za Mu saka wa masu godiya

    [146] Kuma da yawa wani Annabi wanda ya yi yaƙi, akwai jama'a masu yawa tare da shi, sa'an nan ba su yi laushi ba ga abin da ya same su a cikin hanyar Allah, kuma ba su yi rauni ba kuma ba su sad da kai ba. Kuma Allah yana son masu haƙuri

    [147] Kuma babu abin da ya kasance maganarsu face faɗarsu cewa: "Ya Ubangijinmu! Ka gafarta mana zunubanmu da ɓarnarmu a cikin al'amarinmu, kuma Ka tabbatar da dugaduganmu, kuma Ka taimake mu a kan mutanen nan kafirai

    [148] Allah Ya saka musu da sakamakon duniya da kuma kyakkyawan sakamakon Lahira. Kuma Allah yana son masu kyautatawa

    [149] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun yi ɗa'aga waɗanda suka kafirta za su mayar da ku a kan dugaduganku, har ku juya kuna masu hasara

    [150] A'a, Allah ne Majiɓincinku kuma ShI ne Mafi alherin matai maka

    [151] Za Mu jefa tsoro a cikin zukatan waɗanda suka kafirta saboda shirkin da suka yi da Allah game da abin da bai saukar da wani dalili ba game da shi. Kuma makomarsu wuta ce, kuma tir da mazaunin azzalumai

    [152] Kuma lalle ne haƙiƙa Allah Ya yi muku gaskiya ga wa'adinSa, a lokacin da kuke kashe su da izninSa har zuwa lokacin da kuka kasa, kuma kuka yi jayayya a cikin al'amarin, kuma kuka saɓa a bayan (Allah) Ya nuna muku abin da kuke so. Daga cikinku akwai wanda yake nufin duniya kuma daga cikinku akwai wanda ke nufin Lahira. Sa'an nan kuma Ya juyar da ku daga gare su, domin Ya jarrabe ku. Kuma lalle ne, haƙiƙa, Ya yafe muku laifinku. Kuma Allah Ma'abucin falala ne ga muminai

    [153] A lokacin da kuke hawan dutse, gudane. Kuma ba ku karkata a kan kowa ba, alhali kuwa Manzon Allah na kiran ku a cikin na ƙarshenku. Sa'an nan (Allah) Ya saka muku da baƙin ciki a tare da wani baƙin ciki. Domin kada ku yi baƙin ciki a kan abin da ya kuɓuce muku, kuma kada ku yi baƙin cikin a kan abin da ya same ku. Kuma Allah Masani ne ga abin da kuke aikatawa

    [154] Sa'an nan kuma (Allah) Ya saukar da wani aminci a gare ku daga bayan baƙin cikin; gyangyaɗi yana rufe wata ƙungiya daga gare ku, kuma wata ƙungiya, lalle ne, rayukansu sun shagaltar da su, suna zaton abin da ba shi ne gaskiya ba, a game da Allah, irin zaton jahiliyya, suna cewa: "Ko akwai waniabu a gare mu dai daga al'amarin?" Ka ce, "Lalle ne al'amari dukansa na Allah ne." Suna ɓoyewa a cikin zukatansu, abin da ba su bayyana shi a gare ka. Suna cewa: "Da muna da wani abu daga al'amarin da ba a kashe mu ba a nan."Ka ce: "Ko da kun kasance a cikin gidajenku, da waɗanda aka rubuta musu kisa sun fita zuwa ga wuraren kwanciyarsu;" kuma (wannan abu ya auku ne) domin Allah Ya jarrabi abin da ke cikin ƙirazanku. Kuma domin Ya tsarkake abin da ke cikin zukatanku. Allah Masani ne ga abin da ke cikin ƙiraza

    [155] Lalle ne waɗanda suka juya daga gare ku a ranar haɗuwar jama'a biyu, shaiɗan kawai ne ya talalaɓantar da su, saboda sashen abin da suka tsirfanta. Kuma lalle ne haƙiƙa, Allah Ya yafe laifidaga gare su. Lalle Allah ne Mai gafara Mai haƙuri

    [156] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku kasance kamar waɗanda suka kafirta kuma suka ce wa'yan'uwansu idan, sun yi tafiya a cikin ƙasa ko kuwa suka kasance a wurin yaƙi: "Da sun kasance a wurinmu da ba su mutun ba, kuma da ba a, kashe su ba." (Wannan kuwa) Domin Allah Ya sanya waccan magana ta zama nadama a cikin zukatansu. Kuma Allah ne Yake rayarwa kuma Yake matarwa. Kuma Allah, ga abin da kuke aikatawa, Mai gani ne

    [157] Kuma lalle ne idan aka kashe, ku a cikin hanyar Allah, ko kuwa kuka mutu, haƙiƙa, gafara daga Allah da rahama ne mafi alheri daga abin da suke tarawa

    [158] Kuma lalle ne idan kun mutu ko kuwa aka kashe ku, haƙiƙa, zuwa ga Allah ake tara ku

    [159] Saboda wata rahama ce daga Allah ka yi sanyin hali a gare su. Kuma da ka kasance mai hushi mai kaurin zuciya, da sun watse daga gefenka. Sai ka yafe musu laifinsu, kuma ka nema musu gafara, kuma ka yi shawara da su a cikin al'amarin. Sa'an nan kuma idan ka yi niyyar zartarwa, to, ka dogara ga Allah, lalle ne, Allah Yana son masu tawakkali

    [160] Idan Allah Ya taimake ku, to, babu marinjayi a gare ku. Kuma idan Ya yarɓe ku, to, wane ne wanda yake taimakon ku bayanSa? Kuma ga Allah sai muminai su dogara

    [161] Kuma ba ya yiwuwa ga wani annabi ya ci gululu. Wanda ya ci gululu zai je da abin da ya ci na gululun, a Ranar ¡iyama. Sa'an nan a cika wa kowane rai sakamakon abin da ya tsirfanta. Kuma su, ba za a zalunce su ba

    [162] Shin fa, wanda ya bibiyi yardar Allah, yana zama kamar wanda ya koma da fushi daga Allah kuma makomarsa Jahannama ce? Kuma tir da makoma ita

    [163] Su, darajoji ne a wurin Allah, kuma Allah Mai gani ne ga abin da suke aikatawa

    [164] Lalle ne haƙiƙa Allah Ya yi babbar falala a kan muminai, domin Ya aika a cikinsu, Manzo daga ainihinsu yana karanta ayoyinSa a gare su, kuma yana tsar kake su, kuma yana karantar da su Littafi da hikima kuma lalle, sun kasance daga gabani, haƙiƙa suna cikin ɓata bayyananniya

    [165] Shin kuma a lokacin da wata masifa, haƙiƙa, ta same ku alhali kuwa kun samar da biyunta, kun ce: "Daga ina wannan yake?" Ka ce: "Daga wurin rayukanku yake." Lalle ne, Allah, a kan dukan kome, Mai ikon yi ne

    [166] Kuma abin da ya same ku a ranar haɗuwar jama'a biyu, to, da izinin Allah ne, kuma domin (Allah) Ya san muminai (na gaskiya)

    [167] Kuma domin Ya san waɗanda suka yi munafunci, kuma an ce musu: "Ku zo ku yi yaƙi a cikin hanyar Allah, ko kuwa ku tunkuɗe." Suka ce: "Da mun san (yadda ake) yaƙi da mun bi ku." Su zuwa ga kafirci a ranar nan, sun fi kusa daga gare su zuwa ga imani. Suna cewa da bakunansu abin da ba shi ne a cikin zukatansu ba. Allah ne Mafi sani ga abin da suke ɓoyewa

    [168] Waɗanda suka ce wa 'yan'uwansu kuma suka zauna abinsu: "Da sun yi mana ɗa'a, da ba a kashe su ba." Ka ce: "To, ku tunkuɗe mutuwa daga rayukanku, idan kun kasance masu gaskiya

    [169] Kada ka yi zaton waɗanda aka kashe a cikin hanyar Allah matattu ne. A'a, rayayyu ne su, a wurin bangijinsu. Ana ciyar da su

    [170] Suna masu farin ciki saboda abin da Allah Ya ba su daga falalarSa, kuma suna yin bushara ga waɗanda ba su risku da su ba, daga bayansu; "Babu tsoro a kansu kuma ba su zama suna yin baƙin ciki ba

    [171] Suna yin bushara saboda wata ni'ima daga Allah da wata falala. Kuma lalle ne, Allah ba Ya tozartar da ijarar muminai

    [172] Waɗanda suka karɓa kira zuwa ga Allah da ManzonSa, daga bayan miki ya same su. Akwai wata lada mai girma ga waɗanda suka kyautata yi daga gare su, kuma suka yi taƙawa

    [173] Waɗanda mutane suka ce musu: "Lalle ne, mutane sun tara (rundunoni) saboda ku, don haka ku ji tsornsu. Sai (wannan magana) ta ƙara musu imani, kuma suka ce: "Mai isarmu Allah ne kuma madalla da wakili Shi

    [174] Sa'an nan sukajuya da wata ni'ima daga Allah da wata falala, wata cuta ba ta shafe su ba, kuma suka bi yardar Allah. Kuma Allah ne Ma'abucin falala Mai girma

    [175] Wancan, Shaiɗan ne kawai yake tsoratar da, ku masoyansa. To, kada ku ji tsoronsu ku ji tsoro Na idan kun kasance masu imani

    [176] Kuma waɗannan da suke gaugawa a cikin kafirci kada su ɓata maka rai. Lalle ne su, ba za su cuci Allah da kome ba. Allah yana nufin cewa, ba zai sanya musu wani rabo ba a cikin Lahira kuma suna da wata azaba mai girma

    [177] Lalle ne, waɗanda suka sayi kafirci da imani, ba za su cuci Allah da kome ba. Koma suna da azaba mai raɗaɗi

    [178] Kuma kada waɗanda suka kafirta su yi zaton cewa, lalle ne jinkirin da Muke yi musu alheri ne ga rayukansu. Muna yi musu jinkirin ne domin su ƙara laifi kawai kuma suna da azaba mai wulaƙantarwa

    [179] Allah bai kasance yana barin muminai a kan abin da kuke kansa ba, sai Ya rarrabe mummuna daga mai kyau. Kuma Al lah bai kasance Yana sanar da ku gaibi ba. Kuma amma Allah Yana zaɓen wanda Ya so daga manzanninSa. Saboda haka ku yi imani da Allah da manzanninSa Kuma idan kun yi imani kuma kuka yi taƙawa, to, kuna da lada mai girma

    [180] Kuma kada waɗannan da suke yin rowa da abin da Allah Ya ba su daga falalarSa su yi zaton shi ne mafi alheri a gare su A'a, shi mafi sharri ne a gare su. Za a yi musu saƙandami da abin da suka yi rowa da Shi a Ranar ¡iyama Kuma ga Allah gadon sammai da ƙasa yake, kuma Allah, ga abin da kuke aikatawa, Masani ne

    [181] Lalle ne, haƙiƙa Allah Ya ji maganar waɗanda suka ce: "Lalle ne, Allah faƙiri ne, mu ne wadatattu." za mu rubuta abin da suka faɗa, da kisan da suka yi wa Annabawa ba da wani haƙƙi ba kuma Mu ce: "Ku ɗanɗani azabar gobara

    [182] Wannan (azabar) kuwa saboda abin da hannuwanku suka gabatar ne. Kuma lalle ne Allah bai zama mai zalunci ga bayinsa ba

    [183] Waɗanda suka ce: "Lalle ne Allah Ya yi alkawari zuwa gare mu, kada mu yi imani saboda wani Manzo sai ya zo mana da Baiko wadda wuta za ta ci." Ka ce: "Lalle ne wasu manzanni sun je muku, a gabanina, da hujjoji bayyanannu, kuma da abin da kuka faɗa, to, don me kuka kashe su, idan kun kasance masu gaskiya

    [184] To, idan sun ƙaryata ka, to lalle ne, an ƙaryata wasu manzanni a gabaninka, sun je musu da hujjoji bayyanannu da littattafai, da kuma Littafi mai haske

    [185] Kowane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne. Kuma ana cika muku ijarorinku kawai ne a Ranar ¡iyama. To, wanda aka nisantar daga barin wuta, kuma aka shigar da shi Aljanna, to, lalle ne ya tsira. Kuma rayuwar duniya ba ta zama ba face jin daɗin ruɗi

    [186] Lalle ne za a jarraba ku a cikin dukiyarku da rayukanku, kuma lalle ne kuna jin cutarwa mai yawa daga waɗanda aka bai wa Littafi a gabaninku da kuma waɗanda suka yi shirki. Kuma idan kun yi haƙuri, kuma kuka yi taƙawa, to lalle ne, wannan yana daga manyan al'amurra

    [187] Kuma a lokacin da Allah Ya riƙi alkawarin waɗanda aka bai wa Littafi, "Lalle ne kuna bayyana shi ga mutane, kuma ba za ku ɓoye shi ba." Sai suka jefarda shi a bayan bayansu, kuma suka sayi 'yan kuɗi kaɗan da shi. To, tir da abin da suke saye

    [188] Kada lalle ka yi zaton waɗanda suke yin farin ciki da abin da suka bayar, kuma suna son a yabe su da abin da ba su aikata ba. To, kada lalle ka yi zaton su da tsira daga azaba. Kuma suna da azaba mai raɗadi

    [189] Kuma ga Allah mulkin sammai da ƙasa yake. Kuma Allah, a kan kome, Mai ikon yi ne

    [190] Lalle ne, a cikin halittar sammai da ƙasa da saɓawar dare da yini akwai ayoyi ga ma'abuta hankali

    [191] Waɗanda suke ambatar Allah a tsaye da zaune da a kan sasanninsu, kuma suna tunani a kan halittar sammai da ƙasa: "Ya Ubangijinmu! Ba Ka halitta wannan a kan banza ba. TsarkinKa! Saboda haka Ka tsare mu daga azabar wuta

    [192] Ya Ubangijinmu! Lalle ne Kai, wanda Ka shigar a cikin wuta to, haƙiƙa, Ka tozarta shi kuma babu wasu mataimaka ga azzalumai

    [193] Ya Ubangijinmu! Lalle ne mu mun ji Mai kira yana kira zuwa ga imani cewa, 'Ku yi imani da Ubangijinku.' Sai muka yi imani. Ya Ubangijinmu! Saboda haka Ka gafarta mana zunubanmu, kuma Ka kankare miyagun ayyukanmu daga gare mu. Kuma Ka karɓi rayukanmu tare da mutanen kirki

    [194] Ya Ubangijinmu! Ka ba mu abin da Ka yi mana wa'adi (alkawari) a kan manzanninKa, kuma kada Ka tozarta mu a Ranar ¡iyama. Lalle ne Kai, ba Ka saɓawar alkawari

    [195] Saboda haka Ubangijinsu Ya karɓa musu cewa, "Lallene Ni ba zan tozartar da aikin wani mai aiki ba daga gare ku, namiji ne ko kuwa mace, sashenku daga sashe. To, waɗanda suka yi hijira kuma aka fitar da su daga gidajensu, kuma aka cutar da su a cikin hanyaTa, kuma suka yi yaƙi, kuma aka kashe su, lalle ne zan kankare musumiyagun ayyukansu, kuma lalle ne zan shigar da su gidajen Aljanna (waɗanda) ƙoramu ke gudana daga ƙarƙashinsu, a kan sakamako daga wurin Allah. Kuma a wurinSa akwai kyakkyawan sakamako

    [196] Kada jujjuyawar waɗanda suka kafirta a cikin garuruwa ta ruɗe ka

    [197] Jin daɗi ne kaɗan sa'an nan makomarsu Jahannama ce, kuma tir da shimfiɗa ita

    [198] Amma waɗanda suka bi Ubangijinsu da taƙawa suna da Gidajen Aljanna (waɗabda) ƙoramu ke gudana a ƙarƙashinsu suna madawwama a cikinsu, a kan, liyafa daga wurin Allah, kuma abin da ke wurin Allah ne mafi alheri ga barrantattu

    [199] Kuma lalle ne daga Mutanen Littafi haƙiƙa akwai wanda yake yin imani da Allah da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar zuwa gare su, suna masu tawalu'i ga Allah, ba su sayen tamani kaɗan da ayoyin Allah. Waɗannan suna da ijararsu a wurin Ubangijinsu. Lalle ne Allah Mai gaugawar sakamako da yawa ne

    [200] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yi haƙuri kuma ku yi dauriya, kuma ku yi zaman dako, kuma ku yi taƙawa, tsammaninku za ku ci nasara

    Mata

    Surah 4

    [1] Ya ku mutane! Ku bi Ubangijinku da taƙawa Wanda Ya halitta ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga gare shi, ma'auransa, kuma Ya watsa daga gare su maza masu yawa da mata. Kuma ku bi Allah da taƙawa Wanda kuke roƙon juna da (sunan), shi, da kuma zumunta. Lalle ne Allah Ya kasance, a kanku, Mai tsaro ne

    [2] Kuma ku bai wa marayu dukiyoyinsu, kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau. Kuma kada ku ci dukiyoyinsu zuwa ga dukiyoyinku. Lalle shi, ya kasance zunubi ne mai girma

    [3] Kuma idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba a cikin marayu, to, (akwai yadda za a yi) ku auri abin da ya yi muku daɗi daga mata; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu. Sa'an nan idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa abin da hannayenku na dama suka mallaka. Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku wuce haddi ba

    [4] Kuma ku bai wa mata sadakokinsu da sauƙin bayarwa. Sa'an nan idan suka yafe muku wani abu daga gare shi, da daɗin rai, to, ku ci shi da jin daɗi da sauƙin haɗiya

    [5] Kada ku bai wa wawaye dukiyarku, wadda Allah Ya sanya ta a gare ku, kuna masu tsayuwa (ga gyaranta). Kuma ku ciyar da su a cikinta, kuma ku tufatar da su, kuma ku gaya musu magana sananniya ta alheri

    [6] Kuma ku jarraba marayu, har a lokacin da suka isa aure. To, idan kun lura da shiriya daga gare su, to, ku miƙa musu dukiyoyinsu. Kada ku ci ta da ɓarna, kuma da gaggawa kafin su girma. Kuma wanda yake wadatacce, to, ya kama kansa, kuma wanda yake faƙiri, to, ya ci, gwargwadon yadda ya kamata. To, idan kun miƙa musu dukiyoyinsu, sai ku shaidar a kansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai bincike

    [7] Maza suna da rabo daga abin da iyaye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, kuma mata suna da rabo daga abin da iyaye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, daga abin da ya ƙaranta daga gare shi ko kuwa ya yi yawa, rabo yankakke

    [8] Kuma idan ma'abuta zumunta da marayu da matalauta suka halarci rabon, to, ku azurta su daga gare shi, kuma ku faɗa musu magana sananniya ta alheri

    [9] Kuma waɗanda suke da sun bar zuriyya masu rauni a bayansu, za su ji tsoro a kansu, su yi sauna, sa'an nan su bi Allah da taƙawa, kuma su faɗi magana madaidaiciya

    [10] Lalle ne, waɗanda suke cin dukiyar marayu da zalunci, to, wuta kawai suke ci a cikin cikkunansu, kuma za su shiga cikin wata wuta mai tsanani

    [11] Allah Yana yi muku wasiyya a cikin 'ya'yanku; namiji yana da rabon mata biyu. Idan sun kasance mata ne fiye da biyu kuwa, to, suna da biyu daga kashi uku ɗin abin da ya bari, kuma idan ta zama guda ce (kawai) to, tana da rabi. Kuma iyayensa biyu kowane ɗaya daga cikinsu yana da ɗaya daga kashi shida ɗin abin da ya bari idan wani reshe ya kasance gare shi, to, idan reshe bai kasance gare shi ba, kuma iyayensa ne (kawai) suka gaje shi, to, uwa tana da sulusi (ɗaya daga cikin kashi uku). Sa'an nan idan 'yan'uwa sun kasance gare shi, to, uwarsa tana da sudusi (ɗaya daga cikin kashi shida) daga bayan wasiyya wadda ya yi ko kuwa bashi. Ubanninku da 'ya'yan ku, ba ku sani ba, wannensu ne mafi kusantar amfani, a gare ku. Yankawa daga Allah. Lalle ne, Allah Ya kasance Masani Mai hikima

    [12] Kuma kuna da rabin abin da matanku na aure suka bari idan reshe bai kasance gare su ba. Sa'an nan idan reshe ya kasance gare su, to, kuna da rubu'i (ɗaya daga cikin kashi huɗu) daga abin da suka barin, daga bayan wasiyya wadda suka yi ko kuma bashi. (Su) kuma suna da rubu'i daga abin da kuka bari idan reshe bai kasance ba gare ku, idan kuwa reshe ya kasance gare ku, to, suna da sumuni (ɗaya daga cikin kashi takwas) daga abin da kuka bari, daga bayan wasiyya wadda kuka yi ko kuwa bashi. Idan wani namiji ya kasance ana gadon sa bisa kalala, ko kuwa wata mace alhali kuwa yana da ɗan'uwa ko 'yar'uwa to, kowane ɗaya daga cikinsu yana da sudusi (ɗaya daga cikin kashi shida), sai idan sun kasance mafi yawa daga wannan, to, su abokan tarayya ne a cikinsulusi (ɗaya bisa uku), daga bayan wasiyya wadda aka yi ko kuma bashi. Ba da yana mai cutarwa ba, ga wasiyya, daga Allah. Kuma Allah Masani ne Mai haƙuri

    [13] Waɗancan iyakokin Allah ne. Wanda ya yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, (Allah) zai shigar da shi gidajen Aljanna (waɗanda) ɗoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, kuma wannan shi ne rabo babba

    [14] Kuma wanda ya saɓa wa Allah da ManzonSa, kuma ya ƙetare iyakokinSa, zai shigarda shi wuta, yana madawwami a cikinta, kuma yana da wata azaba mai walakantarwa

    [15] Kuma waɗanda suka je wa alfasha daga matanku, to, ku nemi Shaidar mutane huɗu daga gare ku a kansu. To, idan sun yi shaida, sai ku tsare su a cikin gidaje har mutuwa ta karɓi rayukansu, ko kuwa Allah Ya sanya wata hanya a gare su

    [16] Kuma waɗanda (maza biyu) suka je mata daga ku, to, ku cutar da su, sa'an nan idan sun tuba kuma suka kyautata halayensu, sai ku kau da kai da ga barinsu. Lalle ne Allah Ya kasance Mai kaɓar tuba ne, Mai jin ƙai

    [17] Abar da take tuba kawai ga Allah, ita ce ga waɗanda suke aikatawar mugun aiki da jahilci sa'an nan su tuba nan kusa to, waɗannan Allah Yana karɓar tu barsu kuma Allah Ya kasance Masani ne, Mai hikima

    [18] Ba tuba ba ce ga waɗanda suke aikatawar munanan ayyuka har idan mutuwa ta halarci ɗayansu ya ce: "Lalle ne ni, na tuba yanzu," kuma ba tuba ba ce ga waɗanda suke mutuwa alhali kuwa suna kafi rai Waɗannan mun yi musu tattalin wata azaba mai raɗaɗi

    [19] Ku waɗanda suka yi imani! Ba ya halatta a gare ku, ku gaji mata a kan tilas kuma kadaku hana su aure domin ku tafi da sashen abin da kuka ba su, face idan suka zo da wata alfasha bayya nanniya kuma ku yi zamantakewa da su da alheri sa'an nan idan kun ƙi su, to akwai tsammanin ku ƙi wani abu alhali kuwa Allah Ya sanya wani alheri mai yawaa cikinsa

    [20] Kuma idan kun yi nufin musanya mata a matsayin wata mata, alhali kuwa kun bai wa ɗayarsu ƙinɗari to kada ku karɓi kome daga gare, shi, shin, za ku karɓe shi da ƙarya da zunubi bayyananne

    [21] Kuma yaya za ku karɓe shi alhali kuwa, haƙiƙa, sashenkuya sadu zuwa ga sashe, kuma sun riƙi alkawari mai kauri daga gare ku

    [22] Kuma kada ku auri abin da ubanninku suka aura daga mata, face abin da ya shige. Lalle ne shi, ya kasance alfasha da abin ƙyama. Kuma ya munana ya zama hanya

    [23] An haramta muku uwayenku, da 'ya'yanku, da 'yan'uwanku mata, da goggonninku, da innoninku, da 'ya'yan ɗan'uwa, da 'ya'yan 'yar'uwa, da uwayenku waɗanan da suka shayar da ku mama, da 'yan'uwanku mata na shan mama, da uwayen matanku, da agololinku waɗanda suke cikin ɗakunanku daga matanku, waɗanda kuka yi duhuli da su, kuma idan ba ku yi duhuli da su ba, to, babu laifi a kanku, da matan 'ya'yanku waɗanda, suke daga tsatsonku, kuma kada ku haɗa tsakanin 'yan'uwa biyu mata, face abin da ya shige. Lalle ne, Allah Ya kasance Mai gafara ne Mai jin ƙai

    [24] Da tsararrun auren wasu maza, face dai abin da hannuwanku suka mallaka. (Ku tsare) Littafin Allah a kanku. Kuma an halatta muku abin da yake bayan wancan. Ku nema da dukiyoyinku, kuna masu yin aure, ba masu yin zina ba. sa'an nan abin da kuka ji daɗi da shi daga gare su, to, ku ba su ijarorinsu bisa farillar sadaki. Babu laifia gare ku ga abin da kuka yi yardatayya da shi a bayan farillar sadaki. Lalle ne Allah Ya kasance Masani ne, Mai hikima

    [25] Kuma wanda bai sami wadata ba daga cikinku bisa ga ya auri 'ya'ya muminai, to, (ya aura) daga abin da hannuwanku na dama suka mallaka, daga kuyanginku muminai. Kuma Allah ne Mafi sani ga imaninku, sashenku daga sashe. Sai ku aure su da izinin mutanensu. Kuma ku ba su ijarorinsu bisa ga abin da aka sani, suna masu kamun kai ba masu zina ba, kuma ba masu riƙon abokai ba. To, idan aka aure su, sai kuma suka zo da wata alfasha, to, akwai a kansu rabin abin da ko a kan, 'ya'ya daga azaba. wancan (auren kuyanga) ga wanda ya ji tsoron wahala ne daga gare ku. Kuma ku yi haƙuri shi ne mafi alheri a gare ku. Kuma Allah Mai gafara ne Mai jin ƙai

    [26] Allah Yana nufin Ya bayyana muku, kuma Ya shiryar da ku hanyoyin waɗanda suke a gabaninku kuma Ya karɓi tubarku. Kuma Allah Masani ne Mai hikima

    [27] Kuma Allah Yana nufin Ya karɓi tubarku. Kuma waɗanda suke bin sha'awoyi suna nufin ku karkata, karkata mai girma

    [28] Allah Yana nufin Ya yi muku sauƙi, kuma an halitta mutum yana mai rauni

    [29] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku ci dukiyoyinku a tsakaninku da yaudara, face idan ya kasance, daga fatauci ne, bisa yardatayya daga gare ku. Kuma kada ku kashe kanku. Lalle ne Allah Ya kasance, game da ku, Mai jin ƙai ne

    [30] Wanda ya aikata wancan bisa ta'adi da zalunci, to, za Mu ƙone shi da Wuta. Kuma wannan ya kasance ga Allah (abu ne) mai sauƙi

    [31] Idan kuka nisanci manyan abubuwan da ake hana ku aikatawa, to, za Mu kankare munanan ayyukanku daga gare ku, kuma Mu shigar da ku mashiga ta karimci

    [32] Kuma kada ku yi gurin abin da Allah Ya fifita sashenku da shi a kan sashe; maza suna da rabo daga abin da suka tsirfanta, kuma mata suna da rabo daga abin da suka tsirfanta. Ku roƙi Allah daga falalarSa. Lalle ne Allah Ya kasance ga dukkan kome, Masani

    [33] Kuma ga kowa, Mun sanya magada daga abin da mahaifa da mafiya kusancin zumunta suka bari. Kuma waɗanda rantsuwoyinku suka ƙulla ku ba su rabonsu. Lalle ne, Allah Ya kasance, a kan dukkan kome, Mahalarci

    [34] Maza masu tsayuwa ne a kan mata, saboda abin da Allah Ya fifita sashensu da shi a kan sashe kuma saboda abin da suka ciyar daga dukiyoyinsu. To, salihanmata masu ɗa'a ne, masu tsarewa ga gaibi saboda abin da Allah Ya tsare. Kuma waɗanda kuke tsoron bijirewarsu, to, ku yi musu gargaɗi, kuma ku ƙaurace musu a cikin wuraren kwanciya, kuma ku doke su. Sa'an nan kuma, idan sun yi muku ɗa'a, to, kada ku nemiwata hanya a kansu. Lalle ne Allah Ya kasance Maɗaukaki, Mai girma

    [35] Kuma idan kun ji tsoron saɓawar tsakaninsu to ku aika da wani mai sulhu daga mutanensa da wani mai sulhu daga mutanenta. Idan sun yi nufin gyarawa, Allah zai daidaita tsakaninsu (ma'auran). Lalle ne Allah Ya kasance Masani Mai jarrabawa

    [36] Kuma ku bauta wa Allah kuma kada ku haɗa wani da Shi, kuma ga mahaifa ku yi kyautatawa, kuma ga ma'abucin zumunta da marayu da matalauta, da maƙwabci ma'abucin kusanta, da maƙwabci manisanci, da aboki a gefe da ɗan hanya, da abin da hannuwanku na dama suka mallaka. Lalle ne Allah ba Ya son wanda ya kasance mai taƙama, mai yawan alfahari

    [37] Waɗanda suke yin rowa, kuma suna umurnin mutane da yin rowa, kuma suna ɓoyewar abin da Allah Ya ba su na falalarSa. Kuma Mun yi tattali, saboda kafirai, azaba mai walakantarwa

    [38] Kuma waɗanda suke ciyar da dukiyoyinsu domin nuna wa mutane, kuma ba su yin imani da Allah, kuma ba su yin imanida Ranar Lahira kuma wanda Shaiɗan ya kasance abokin haɗi a gare shi, to, ya munana ga abokinhaɗi

    [39] Kuma mene ne a kansu, idan sun yi imani da Allah, kumada Ranar Lahira, kuma sun ciyar da abin da Allah Ya azurta su, kuma Allah Ya kasance, gare su, Masani

    [40] Lalle ne, Allah ba Ya zaluncin gwargwadon nauyin zarra, idan ta kasance alheri ce, zai riɓanya ta, kuma Ya kawo daga gunsa ijara mai girma

    [41] To, yaya, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al'umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida

    [42] A ranar nan, waɗanda suka kafirta kuma suka saɓa wa Manzo, suna gurin da an baje ƙasa dasu, kuma ba su ɓoye wa Allah wani labari

    [43] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku kusanci salla alhali kuwa kuna masu maye, sai kun san abin da kuke faɗa kuma haka idan kuna masu janaba, face mai ƙetare hanya, har ku yi wanka. Kuma idan kun kasance majinyata, ko kuwa a kan tafiya ko kuwa wani daga cikinku, idan ya zo daga kashi, ko kuwa kun shafi mata ba ku sami ruwa ba, to ku nufi, fuskar ƙasa mai kyau, ku yi shafa ga fuskokinku da hannuwanku. Lalle ne Allah Ya kasance Mai yafewa Mai gafara

    [44] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda aka bai wa rabo daga Littafi, suna sayen ɓata, kuma suna neman ku ɓace daga hanya

    [45] Kuma Allah ne Mafi sani ga maƙiyanku, kuma Allah Ya isa Ya zama Majibinci, kuma Ya isa Ya zama Mataimaki

    [46] Daga waɗanda suka tuba (Yahudu), akwai wasu suna karkatar da magana daga wurarenta suna cewa: "Munjiya kuma mun ƙiya, kuma ka jiya a wani wurin jiyawa, kuma ra'ina (da ma'anar 'ruɓaɓɓe'), ka tsare mu," domin karkatarwa da harsunansu, kuma domin suka a cikin addini. Kuma da lalle su, sun ce: "Mun jiya kuma mun yi ɗa'a, kuma ka saurara kuma ka dakata mana," haƙiƙa, da ya kasance mafi alheri a gare su, kuma mafi daidaita; amma Allah Ya la'ane su, saboda kafircinsu don haka ba za su yi imani ba, sai kaɗan

    [47] Ya ku waɗanda aka bai wa Littafi! Ku yi imani da abinda Muka saukar, yana mai gaskatawa ga abin da yake tare da ku, tun gabanin Mu shafe wasu fuskoki, sa'an nan Mu mayar da su a kan bayayyakinsu, ko Mu la'ane su kamar yadda Muka la'ani masu Asabar. Kuma umurnin Allah ya kasance abin aikatawa

    [48] Lalle ne, Allah ba Ya gafarta a yi shirki game da Shi, kuma Yana gafarta abin da yake bayan wannan ga wanda Yake so, kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ƙirƙiri zunubi mai girma

    [49] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke tsarkake kansu? A'a, Allah ne Yake tsarkake wanda Yake so. Kuma ba za a zalunce su da zaren gurtsun dabino ba

    [50] Ka duba yadda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah! Kuma shi ya isa ga zama zunubi bayyananne

    [51] Shin, ba ka gani ba zuwa ga waɗanda aka bai wa rabo da ga Littafi suna imani da gunki da Shaiɗan kuma suna cewa ga waɗanda suka kafirta: "Waɗannan ne mafiya shiriya daga waɗanda suka yi imani ga hanya

    [52] Waɗannan ne waɗanda Allah Ya la'ane su, kuma wanda Allah Ya la'ana to ba za ka sami mataimaki a gare shi ba

    [53] Ko suna da rabo ne daga mulki? To, a sa'an nan ba za su iya bai wa mutane hancin gurtsun dabino ba

    [54] Ko suna hasadar mutane ne a kan abin da Allah Ya ba su daga falalarSa? To, lalle ne, Mun bai wa gidan Ibrahim Littafida hikima kuma Mun ba su mulki mai girma

    [55] To, daga cikinsu akwai wanda ya yi imani da shi, kuma daga cikinsu akwai wanda ya kange daga gare shi. Kuma ya isa Jahannama ta huru da shi

    [56] Lalle ne waɗanda suka kafirta da ayoyinMu za Mu ƙone su da wuta, ko da yaushe fatunsu suka nuna, sai Mu musanya musu wasu fatun, domin su ɗanɗani azaba. Lalle ne Allah Ya kasance Mabuwayi, Mai hikima

    [57] Kuma waɗanda suka yiimani, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, za Mu shigar da su gidajen Aljanna, (waɗanda) ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna dawwamammu a cikinsu har abada suna da, a cikinsu, matan aure masu tsarki, Kuma Muna shigar da su a wata inuwa matabbaciyar lumshi

    [58] Lalle ne Allah Yana umurnin ku ku bayar da amanoni zuwa ga masu su. Kuma idan kun yi hukunci a tsakanin mutane, ku yi hukunci da adalci. Lalle ne Allah madalla da abin da Yake yi muku wa'azi da shi. Lalle ne Allah Ya kasance Mai ji ne, Mai gani

    [59] Ya ku waɗanda suka yiimani! Ku yi ɗa'a ga Allah, kuma ku yi ɗa'a ga ManzonSa, da ma'abuta al'amari daga cikinku. Idan kun yi jayayya a cikin wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da ManzonSa idan kun kasance kuna imani da Allah da Ranar Lahira. wannan ne mafi alheri, kuma mafi kyau ga fassara

    [60] Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke riyawar cewa suna imani da abin da aka saukar zuwa gare ka da abin da aka saukar daga gabaninka, suna nufin su kai ƙara zuwa ga ¦agutu alhali kuwa, lalle ne, an umurce su da su kafirta da shi, kuma Shaiɗan yana neman ya ɓatar da su, ɓatarwa mai nisa

    [61] Kuma idan aka ce musu: "Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya saukar, kuma zuwa ga Manzo" za ka ga munafukai suna kange mutane daga gare ka, kangewa

    [62] To, yaya, idan wata masifa ta same su, saboda abin da hannuwansu suka gabatar sa'an nan kuma su je maka suna rantsuwa da Allah cewa, "Ba mu yi nufin kome ba sai kyautatawa da daidaitawa

    [63] Waɗannan ne waɗanda Allah Ya san abin da ke cikin zukatansu. Saboda haka ka kau da kai daga gare su, kuma ka yi musu gargaɗi, kuma ka gaya musu, a cikin sha'anin kansu, magana mai nauyi da fasaha

    [64] Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba face domin a yi masa ɗa'a da izinin Allah. Kuma da dai lalle su a lokacin da suka zalunci kansu, sun zo maka sa'an nan suka nemi gafarar Allah kuma Manzo ya nema musu gafara, haƙiƙa, da sun sami Allah Mai karɓar tuba Mai jin ƙai

    [65] To, a'aha! Ina rantsuwa da Ubangijinka, ba za su yi imani ba, sai sun yarda da hukuncinka ga abin da ya saɓa a tsakaninsu, sa'an nan kuma ba su sami wani ƙunci a cikin zukatansu ba, daga abin da ka hukunta, kuma su sallama sallamawa

    [66] Kuma da dai lalle Mu, Mun wajabta musu cewa, "Ku kashe kanku, ko kuwa ku, fita daga gidajenku," da ba su aikata shi ba, face kaɗan daga gare su. Kuma da dai lalle su sun aikata abin da ake yi musu gargaɗi da shi, haƙiƙa, da ya kasance mafi alheri dagagare su, kuma mafi tsanani ga tabbatarwa

    [67] Kuma a sa'an nan, haƙiƙa, da Mun ba su, lada mai girma, daga gunMu

    [68] Kuma lalle ne, da Mun shiryar da su hanya madaidaiciya

    [69] Kuma waɗannan da suka yi ɗa'a ga Allah da Mazonsa, to, waɗannan suna tare da waɗanda Allah Ya yi ni'ima a kansu, daga annabawa da masu yawan gaskatawa, da masu shahada da salihai. kuma waɗannan sun kyautatu ga zama abokan tafiya

    [70] Waccan falalar daga Allah take, kuma Allah Ya isa zama Masani

    [71] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku riƙi shirinku sa'an nan ku fitar da hari jama'a, jama'a ko ku fitar da yaƙi gaba ɗaya

    [72] Kuma lalle ne daga cikinku akwai mai fasarwa. To idan wata masifa ta same ku, sai ya ce: "Lalle ne, Allah Ya yi mini ni'ima domin ban kasance mahalarci tare da su ba

    [73] Kuma lalle ne idan wata falala daga Allah ta same ku haƙiƙa, tabbas, yana cewa, kamar wata soyayya ba ta kasance a tsakaninku da shi ba: "Ya kaitona! Da na zama tare da su dai, domin in rabonta da rabo mai girma

    [74] Sai waɗanda suke sayar da rayuwar duniya su karɓi ta Lahira su yi yaƙi, a cikin hanyar Allah. Kuma wanda ya yi yaki a cikin hanyar Allah to a kashe shi ko kuwa ya rinjaya, sa'an nan za Mu ba shi ijara mai girma

    [75] Kuma mene ne ya same ku, ba ku yin yaƙi a cikin hanyar Allah, da waɗanda aka raunanar daga maza da mata da yara suna cewa: "Ya Ubangijinmu! Ka fitar da mu daga wannan alƙarya wadda mutanenta suke da zalunci, kuma Ka sanya mana majiɓinci daga gunKa, kuma Ka sanya mana mataimaki daga gunKa

    [76] Waɗanda suka yi imani, suna yaki a cikin hanyar Allah, kuma waɗanda suka kafirta suna yaƙi a cikin hanyar ¦agutu (Shaiɗan). To, ku yaƙi majiɓintan Shaiɗan. Lalle ne kaidin Shaiɗan ya kasance mai rauni

    [77] Shin, ba ka gani ba zuwa ga waɗanda aka ce musu: "Ku kange hannuwanku, kuma ku tsayar da salla, kuma ku bayar da zakka."? To a lokacin da aka wajabta musu yaƙi sai ga wani ɓangare daga cikinsu suna tsoron mutane kamar tsoron Allah ko kuwa mafi tsanani ga tsoron, kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Don me Ka wajabta yaƙi a kanmu? Me ya hana Ka jinkirta mana zuwa ga wani ajali na kusa?"Ka ce: "Jin daɗin duniya kaɗan ne, kuma Lahira ce mafi alheri ga wanda ya yi taƙawa. Kuma ba a zaluntar ku da sililin hancin gurtsun dabino

    [78] Inda duk kuka kasance, mutuwa za ta riske ku, kuma ko da kun kasance ne a cikin ganuwoyi ingatattu!"Kuma idan wani alheri ya same su sai su ce: "Wannan daga wurin Allah ne," kuma idan wata cuta ta same su, sai su ce: "Wannan daga gare ka ne."Ka ce: "Dukkansu daga Allah ne." To, me ya sami waɗannan mutane, ba su kusantar fahimtar magana

    [79] Abin da ya same ka daga alheri, to, daga Allah yake, kuma abin da ya same ka daga sharri, to, daga kanka yake, kuma Mun aike ka zuwa ga mutane, (kana) Manzo, kuma Allah Ya isa ga zama shaida

    [80] Wanda ya yi ɗa'a ga Manzo, to, haƙiƙa, ya yi ɗa'a ga Allah. Kuma wanda ya juya baya, to, ba Mu aike ka ba don ka zama mai tsaro a kansu

    [81] Kuma suna cewa, "Da'a" sa'an nan idan sun fita daga wurinka, sai wata ƙungiya daga cikinsu ta kwana da niyyar wanin abin da take faɗa, alhali kuwa Allah na rubuta abin da suke kwana da niyyarsa. Saboda haka ka kau da kai daga gare su, kuma ka dogara ga Allah, kuma Allah Ya isa ya zama wakili

    [82] Shin, ba su kula da Alƙur'ani, kuma da ya kasance daga wurin wanin Allah haƙiƙa, da sun samu, a cikinsa, saɓa wa junamai yawa

    [83] Kuma idan wani al'amari daga aminci ko tsoro ya je musu, sai su watsa shi. Da sun mayar da shi zuwa ga Manzo da ma'abuta al'amari daga gare su, lalle ne, waɗanda suke yin bincikensa, daga gare su, za su san shi. Kuma ba domin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa, haƙiƙa, da kun bi Shaiɗan face kaɗan

    [84] Saboda haka, ka yi yaƙi a cikin hanyar Allah, ba a kallafa maka ba, face a kanka, kuma ka kwaɗaitar da muminai. Akwai tsammanin Allah Ya kange gafin waɗanda suka kafirta, kuma Allah ne Mafi tsananin gafi, kuma Mafi tsananin azabtawa

    [85] Wanda ya yi ceto, ceto mai kyau, zai sami rabo daga gare shi, kuma wanda ya yi ceto, ceto mummuna, zai sami ma'aunidaga gare shi, Kuma Allah Ya kasance, a kan dukkan kome, Mai ƙayyade lokaci

    [86] Kuma idan an gaishe ku da wata gaisuwa, to, ku yi gaisuwa da abin da yake mafi kyau daga gare ta, ko kuwa ku mayar da ita. Kuma Allah Ya kasance a kan dukkan kome Mai lissafi

    [87] Allah babu abin bautawa face Shi. Lalle ne haƙiƙa Yana tara ku har zuwa ga Yinin ¡iyama babu shakka a cikinsa. Kuma wane ne mafi gaskiya daga Allah ga 1abari

    [88] To, mene ne ya same ku a cikin munafukai kun zama ƙungiya biyu, alhali kuwa Allah ne Ya mayar da su saboda abin da suka tsirfanta? Shin, kuna nufin ku shiryar da wanda Allah Ya ɓatar ne? Kuma wanda Allah Ya ɓatar to ba za ka sami wata hanya ba zuwa gare shi

    [89] Suna gurin ku kafirta kamar yadda suka kafirta, domin ku kasance daidai. Saboda haka kada ku riƙi wasu masoya daga cikinsu, sai sun yo hijira a cikin hanyar Allah. Sa'an nan idan sun juya, to, ku kama su kuma ku kashe su inda duk kuka same su. Kuma kada ku riƙi wani masoyi daga gare su ko wani mataimaki

    [90] Face dai waɗanda suke saduwa zuwa ga wasu mutane waɗanda a tsakaninku da su akwai alkawari, ko kuwa waɗanda suke sun je muku (domin) ƙirazansu sun yi ƙunci ga su yake ku, ko su yaƙi mutanensu. Kuma da Allah Ya so lalle ne, da Ya ba su iko a kanku, sa'an nan, haƙika, su yake ku. To, idan sun nisance ku sa'an nan ba su yaƙe ku ba, kuma suka jefa sulhu zuwa gare ku, to, Allah bai sanya wata hanya ba, a gare ku, a kansu

    [91] Za ku sami wasu suna nufin su amintar da ku kuma su amintar da mutanensu, ko da yaushe aka mayar da su ga fitina, sai a dulmuya su a cikinta. To, idan ba su nisance ku ba, kuma sun jefa sulhu zuwa gare ku, kuma sun kange hannuwansu, to, ku kama su, kuma ku kashe su inda duk kuka kama su, kuma waɗannan, Mun sanya muku dalili bayyanannea kansu

    [92] Kuma ba ya kasancewa ga mumini ya kashe wani mumini, face bisa ga kuskure. Kuma wanda ya kashe mumini bisa ga kuskure, sai ya 'yanta wuya mumina tare da miƙa diyya ga mutanensa, ace idan sun bari sadaka. Sa'an nan idan (wanda aka kashe) ya kasance daga wasu mutane maƙiya a gare ku, kuma shi muminine, sai ya 'yanta wuya mumina. Kuma idan ya kasance daga wasu mutane ne (waɗanda) a tsakaninku da tsakaninsu akwai alkawari, sai ya bayar da diyya ga mutanensa, tare da 'yanta wuya mumina. To, wanda bai sami (wuyan ba) sai azumin watanni biyu jere, domin tuba daga Allah. Kuma Allah Ya kasance Masani, Mai hikima

    [93] Kuma wanda ya kashe wani mumini da ganganci, to, sakamakonsa Jahannama, yana madawwami a cikinta kuma Allah Ya yi fushi a kansa, kuma Ya la'ane shi, kuma Ya yi masa tattalin azaba mai girma

    [94] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun yi tafiya (a cikin ƙasa), domin jihadi, to, ku nemi bayani. Kuma kada ku ce wa wanda ya jifa sallama zuwa gare ku: "Ba Musulmi kake ba." Kuna neman hajar rayuwar duniya, to, a wurin Allah akwai ganimomi masu yawa. Kamar wannan ne kuka kasance a gabanin ku musulunta, sa'an nan Allah Ya yi muku falala. Saboda haka ku zan neman bayani. Lalle ne Allah Ya kasance, ga abin da kuke aikatawa, Masani

    [95] Masu zama daga barin yaƙi daga muminai, wasun ma'abuta larura da masu jihadi a cikin hanyar Allah da dukiyoyinsu da rayukansu, ba su zama daidai. Allah Ya fifita masu jihadi da dukiyoyinsu da rayukansu a kan masu zama, ga daraja. Kuma dukansu Allah Ya yi musu alkawari da abu mai kyau. Kuma Allah ya fifita masu jihadi a kan masu zama da lada mai girma

    [96] Darajoji daga gare Shi da gafara da rahama. Kuma Allah Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [97] Lalle ne, waɗanda mala'iku suka karɓi rayukansu, (alhali) suna masu zaluntar kansu, sun ce (musu): "A cikin me kuka kasance?" (Su kuma) suka ce: "Mun kasance waɗanda aka raunana a cikin ƙasa." Suka ce: "Ashe ƙasar Allah ba ta kasance mayalwaciya ba, domin ku yi hijira a cikinta?" To, waɗannan makomarsu Jahannama ce. Kuma ta munana ta zama makoma

    [98] Face waɗanda aka raunana daga maza da mata da yara waɗanda ba su iya yin wata dabara, kuma ba su shiryuwa ga hanya

    [99] To, waɗannan akwai tsammanin Allah Ya yafe laifi daga gare su, kuma Allah Ya kasance Mai yafewa ne, Mai gafara

    [100] Kuma wanda ya yi hijira a cikin hanyar Allah, zai samu, a cikin ƙasa, wuraren juyawa masu yawa da yalwa. Kuma wanda ya fita daga gidansa yana mai hijira zuwa ga Allah da ManzonSa, sa'an nan kuma mutuwa ta riske shi, to, lalle ne, ladarsa ta auku ga Allah, Kuma Allah Ya kasance, a gare ku, Mai gafara, Mai jin ƙai

    [101] Kuma idan kun yi tafiya a cikin ƙasa to, babu laifi a kanku ku rage daga salla idan kun ji tsoron waɗanda suka kafirta su fitine ku. Lalle ne kafirai sun kasance, a gare ku, maƙiyi bayyananne

    [102] Kuma idan ka kasance a cikinsu, sai ka tsayar musu da salla, to, wata ƙungiya daga gare su ta tsaya tare da kai, kuma sai su riƙe makamansu. Sa'an nan idan sun yi salla, to, sai su kasance daga bayanku. Kuma wata ƙungiya ta dabam (ta) waɗanda ba su yi sallar ba, ta zo, sa'an nan su yi sallar tare da kai. Kuma su riƙi shirinsu da makamansu. Waɗanda suka kafirta sun yi gurin da dai kuna shagala daga makamanku da kayanku domin su karkata a kanku, karkata guda. Kuma babu laifi, a kanku idan wata cuta daga ruwan sama ta kasance a gare ku, ko kuwa kun kasance masu jinya ga ku ajiye makamanku kuma dai ku riƙi shirinku. Lalle ne, Allah Ya yi tattali, ga kafirai, azaba mai walakantarwa

    [103] Sa'an nan idan kun ƙare salla, to ku ambaci Allah tsaye da zaune da a kan sasanninku. Sa'an nan idan kun natsu, to, ku tsayar da Salla. Lalle ne salla ta kasance a kan muminai, farilla mai ƙayyadaddun lokuta

    [104] Kuma kada ku sassauta a cikin neman mutanen idankun kasance kuna jin zogi, to, lalle su ma, suna jin zogi kamar yadda kuke jin zogi. Kuma kuna tsammani, daga Allah, abin da ba su tsammani. Kuma Allah Ya kasance Masani Mai hikima

    [105] Lalle ne, Mu, Mun saukar, zuwa gare ka, Littafi da gaskiya, domin ka yi hukunci a tsakanin mutane da abin da Allah Ya nuna maka, kuma kada ka kasance mai husuma domin masu yaudara

    [106] Kuma ka nemi Allah gafara. Lalle ne Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai

    [107] Kuma kada ka yi jayayya domin tunkuɗe wa waɗanda suka yaudari kansu. Lalle ne Allah ba Ya son wanda ya kasance mai yawan ha'inci mai yawan zunubi

    [108] Suna neman ɓoyewa daga mutane kuma ba su nemanɓoyewa daga Allah, alhali kuwa Shi Yana tare da su a lokacin da suke kwana da niyyar yin abin da ba Ya yarda da shi daga maganar. Kuma Allah Ya kasance ga abin da suke aikatawa Mai kewayewa

    [109] Ga ku, ya waɗannan! Kun yi jidali, domin tunkuɗe musu (kunya) a cikin rayuwar duniya, to, wane ne zai yi jidali domin tunkuɗe musu a Ranar ¡iyama? Ko kuwa wane ne zai kasance wakili a kansu

    [110] Kuma wanda ya aikata cuta ko kuwa ya zalunci kansa, sa'an nan kuma ya nemi Allah gafara, zai sami Allah Mai gafara, Mai jin ƙai

    [111] Kuma wanda ya yi tsirfanci zunubi, to yana tsirfarsa ne a kan kansa kawai. Kuma Allah Ya kasance Masani, Mai hikima

    [112] Kuma wanda ya yi tsiwirwirin kuskure ko kuwa zunubi sa'an nan kuma ya jefi wani barrantacce da shi, to, lalle ne ya tattali ƙirƙiren ƙarya da zunubi bayyananne

    [113] Kuma ba domin falalar Allah ba, a kanka, da rahamarSa, haƙiƙa, da wata ƙungiya daga gare su ta himmatu ga su ɓatar da kai. Kuma ba su ɓatarwa face kansu, kuma ba su cutar ka daga kome, Kuma Allah Ya saukar da Littafi da hikima gare ka, kuma Ya sanar da kai abin da ba ka kasance ka sani ba. Kuma falalar Allah ta kasance mai girma a gare ka

    [114] Babu wani alheri a cikin masu yawa daga ganawarsu face wanda ya yi umurni da wata sadaka ko kuwa wani alheri ko kuwa gyara a tsakanin mutane. Wanda ya aikata haka domin neman yardodin Allah to za Mu ba shi lada mai girma

    [115] Kuma wanda ya saɓa wa Manzo daga bayan shiriya ta bayyana a gare shi, kuma ya bi wanin hanyar muminai, za Mu jiɓintar masa abin da ya jiɓinta, kuma Mu ƙone shi da Jahannama. Kuma ta munana ta zama makoma

    [116] Lalle ne, Allah ba Ya gafarta a yi shirki da Shi, kuma Yana gafarta abin da yake bayan wannan, ga wanda Yake so. Kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ɓace ɓata mai nisa

    [117] Ba su kiran kowa, baicin Shi, face mata kuma ba su kiran kowa face Shaiɗan, mai tsaurin kai

    [118] Allah Ya la'ane shi. Kuma ya ce: "Lalle ne, za ni riƙi rabo yankakke, daga bayinKa

    [119] Kuma lalle ne, ina ɓatar da su, kuma lalle ne ina sanya musu guri, kuma lalle ne ina umurnin su domin su katse kunnuwan dabbobi, kuma lalle ne ina umurnin su domin su canza halittar Allah." Kuma wanda ya riƙi Shaiɗan majiɓinci, baicin Allah, to, haƙiƙa ya yi hasara, hasara bayyananniya

    [120] Yana yi musu alkawari, kuma yana sanya musu guri, alhali Shaiɗan ba ya yi musu wani wa'adin kome face ruɗi

    [121] Waɗannan matattararsu Jahannama ce, kuma ba samun makarkata daga gare ta

    [122] Kuma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, za mu shigar da su gidajen Aljanna (waɗanda) ƙoramu suna gudana a ƙarƙashinsu, suna masu dawwama a cikinsu har abada bisa ga wa'adin Allah tabbatacce. Wane ne mafi gaskiya daga Allah ga magana

    [123] (Al'amari) bai zama gurace- guracenku ba, kuma ba gurace- guracen Mutanen Littafi ba ne. Wanda ya aikata mummunan aiki za a saka masa da shi kuma ba zai sami wani masoyi ba, baicin Allah, kuma ba zai sami mataimaki ba

    [124] Kuma wanda ya yi aiki daga ayyukan ƙwarai, namiji ne ko kuwa mace, alhali kuwa Yana mumini, to, waɗannan suna shiga Aljanna kuma ba za a zalunce su da gwargwadon hancin gurtsun dabi no ba

    [125] Kuma wane ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhali kuwa yana mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrahim, Yana mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Ya riƙi Ibrahim badaɗayi

    [126] Kuma Allah ke da (mallakar) abin da ke cikin sammai da kuma abin da ke cikin ƙasa kuma Allah Ya kasance, a dukkan, kome, Mai kewayewa

    [127] Suna yi maka fatawa a cikin sha'anin mata. Ka ce: "Allah Yana bayyana fatawarku a cikin sha'aninsu, da abin da ake karantawa a kanku a cikin Littafi, a cikin sha'anin marayun mata waɗanda ba ku ba su abin da aka rubuta musu (na gado) ba, kuma kuna kwaɗayin ku aure su, da sha'anin waɗanda aka raunana daga yara, da sha'anin tsayuwarku ga marayu da adalci. Kuma abin da kuka aikata daga alheri, to, lalle ne, Allah Ya kasance Masani a gare shi

    [128] Kuma idan wata mace ta ji tsoron ƙiyo daga mijinta ko kuwa bijirewa to, babu laifi a kansu su yi sulhu a tsakaninsu, sulhu (mai kyau) Kuma yin sulhu ne mafi alheri. Kuma an halartar wa rayuka yin rowa. Kuma idan kun kyautata, kuma kuka yi taƙawa, to, lalle ne, Allah Ya kasance, ga abin da kuke aikatawa, Masani

    [129] Kuma ba za ku iya yin adalci ba a tsakanin mata ko da kun yi kwaɗayin yi. Saboda haka kada ku karkata, dukan karkata, har ku bar ta kamar wadda aka rataye. Kuma idan kun yi sulhu, kuma kuka yi taƙawa, to, lalle ne Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai

    [130] Kuma idan sun rabu, Allah zai wadatar da kowanne daga yalwarSa. Kuma Allah Ya kasance Mayalwaci, Mai hikima

    [131] Kuma Allah ne da mulkin abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa. Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun yi wasiyya ga waɗanda aka bai wa Littafi a gabaninku, da ku, cewa ku bi Allah da taƙawa, kuma idan kun kafirta, to, lalle ne, Allah Yana da abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin ƙasa. Kuma Allah Ya kasance wadatacce, Godadde

    [132] Kuma Allah ne da mulkin abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin ƙasa, kuma Allah Ya isa Ya zama wakili

    [133] Idan Ya so, za Ya tafi da ku, ya ku mutane! kuma Ya zo da wasu. Allah Ya kasance a kan haka, Mai ikon yi ne

    [134] Wanda ya kasance Yana nufin sakamakon duniya, to, a wurin Allah sakamakon duniya da Lahira yake. Kuma Allah Ya kasance Mai ji, Mai gani

    [135] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku kasance masu tsayuwa da adalci, masu shaida saboda Allah, kuma ko da a kanku ne ko kuwa, mahaifa da mafi kusantar zumunta, ko (wanda ake yi wa shaida ko a kansa) ya kasance mawadaci ko matalauci, to, Allah ne Mafi cancanta da al'amarinsu. Saboda haka, kada ku bibiyi son zuciya, har ku karkata. Kuma idan kuka karkatar da magana, ko kuwa kuka kau da kai, to lalle ne Allah Ya kasance Masani ga abin da kuke aikatawa

    [136] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yi imani da Allah da Manzonsa, da Littafin da Ya sassaukar ga ManzonSa da Littafin nan wanda Ya saukar daga gabani. To, wanda ya kafirta da Allah da mala'ikunSa, da LittattafanSa, da ManzanninSa, da Ranar Lahira, to, lalle ne ya ɓace, ɓata mai nisa

    [137] Lalle ne waɗanda suka yi imani, sa'an nan kuma suka kafirta, sa'an nan kuma suka yi imani, sa'an nan kuma suka kafirta sa'an nan kuma suka ƙara kafirci, Allah bai kasance Yana gafarta musu ba, kuma ba zai shiryar da su ga hanya ba

    [138] Ka yi wa munafukai bushara da cewa lalle ne suna da azaba mai raɗaɗi

    [139] Waɗanda suke riƙon kafirai masoya, baicin muminai. Shin suna neman izza ne a wurinsu? To, lalle ne izza ga Allah take gaba ɗaya

    [140] Kuma lalle ne Ya sassaukar muku a cikin Littafi cewa idan kun ji ayoyin Allah, ana kafirta da su, kuma ana izgili da su, to, kada ku zauna tare da su, sai sun shiga cikin wani labari. Lalle ne ku, a lokacin nan misalinsu kuke. Lalle ne, Allah Mai tara munafukai da kafirai ne a cikin Jahannama gaba ɗaya

    [141] Waɗanda suke jiran dako game da ku; har idan wata nasara daga Allah ta kasance a gare ku, sai su ce: "Ashe, ba mu kasance tare da ku ba?" Kuma idan wani rabo ya samu ga kafirai sai su ce: "Ashe ba mu rinjaye ku ba, kuma muka tsare ku daga muminai?" To, Allah ne Yake yin hukunci tsakaninku a Ranar ¡iyama, kuma Allah ba zai sanya hanya ba ga kafirai a kan muminai

    [142] Lalle ne munafukai suna yaudarewa da Allah, alhali kuwa Shi ne mai yaudarasu; kuma idan sun tashi zuwa ga salla, sai su tashi suna masu kasala. Suna nunawa mutane, kuma ba su ambatar Allah sai kaɗan

    [143] Masu kai-kawo ne a tsakanin wancan; ba zuwa ga waɗannan ba, kuma ba zuwa ga waɗannan ba. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, ba za ka samar masa wata hanya ba

    [144] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku riƙi kafirai masoya, baicin muminai. Shin, kana nufin ku sanya wa Allah dalili bayyananne a kanku

    [145] Lalle ne, manafukai suna a magangara mafi ƙasƙanci daga wuta. Kuma ba za ka sama musu mataimaki ba

    [146] Sai waɗanda suka tuba, kuma suka gyara, kuma suka nemi fakuwa ga Allah, kuma suka tsarkake addininsu domin Allah, to, waɗannan suna tare da muminai, kuma Allah zai bai wa muminai lada mai girma

    [147] Mene ne Allah zai amfana da yi maku azaba idan kun gode, kuma kun yi imani? Allah Ya ksance Mai godiya Masani

    [148] Allah ba Ya son bayyanawa da munana daga magana face ga wanda aka zalunta. Kuma Allah Ya kasance Mai ji, Masani

    [149] Idan kun bayyana alheri, ko kuwa kuka ɓoye shi, ko kuwa kuka yafe laifi daga cuta, to, lalle ne Allah Ya kasance Mai yafewa, Mai ikon yi

    [150] Lalle ne, waɗanda uke kafirta da Allah da ManzonSa kuma suna nufin su rarrabe a tsakanin Allah da manzanninSa, kuma suna cewa: "Muna imani da sashe, kuma muna kafirta da sashe." Kuma suna nufin su riƙi hanya a tsakanin wannan

    [151] Waɗannan su ne kafirai sosai, kuma Mun yi tattali, domin kafirai, azaba mai walakantarwa

    [152] Kuma waɗanda suka yi imani da Allah da manzanninSa, kuma ba su rarrabe a tsakanin kowa ba daga gare su, waɗannan za Mu ba su ijarorinsu, kuma Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai

    [153] Mutanen Littafi suna tambayar ka ka saukar da wani littafi daga sama, a kansu, to, lalle ne sun tambayi Musa mufa girma daga wannan, suka ce: "Ka nuna mana Allah bayyane." Sai tsawa ta kama su saboda zaluncinsu, sa'an nan kuma suka riƙi maraƙi (abin bautawa) bayan hujjoji bayyanannu sun je musu. Sa'an nan Muka yafe laifi daga wancan. Kuma Mun bai wa Musa dalili bayyananne

    [154] Kuma Muka ɗaukaka dutse sama da su, saboda alkawarinsu, kuma Muka ce musu: "Ku shiga ƙofar kuna masu tawali'u," Kuma Muka ce musu: "Kada ku ƙetare haddi a cikin Asabat," kuma Muka riƙi alkawari mai kauri daga gare su

    [155] To, saboda warwarewarsu ga alkawarinsu, da kafirtarsu da ayoyin Allah, da kisansu ga Annabawa, ba da hakki ba, da maganarsu: "Zukatanmu suna cikin rufi." A'a, Allah ne Ya yunƙe a kansu saboda kafircinsu, saboda haka ba za su yi imani ba face kaɗan

    [156] Kuma saboda kafircinsu da faɗarsu, a kan Maryama, ƙiren ƙarya mai girma

    [157] Da faɗarsu: "Lalle ne mu, mun kashe Masihu isa ɗan Maryama Manzon Allah," alhali kuwa ba su kashe shi ba, kuma ba su kere shi ba, kuma ammaan kamanta shi ne a gare su. Lalle ne waɗanda sauka saɓa wa juna a cikin sha'aninsa lalle ne, suna shakka daga gare, shi, ba da wani ilmi face bin zato kuma ba su kashe shi ba bisa ga yaƙini

    [158] A'a, Allah Ya ɗauke shi zuwa gare Shi, kuma Allah Ya kasance Mabuwayi, Mai hikima

    [159] Kuma babu kowa daga Mutanen Littafi, face lalle yana imani da shi a gabanin mutuwarsa, kuma a Ranar ¡iyama yana kasancewa mai shaida, a kansu

    [160] To, saboda zalunci daga waɗanda suka tuba (Yahudu) Muka haramta musu abubuwa masu daɗi waɗanda aka halatta su a gare su, kuma saboda taushewarsu daga hanyar Allah da yawa

    [161] Da karɓarsu ga riba, alhali kuwa an hana su daga gare ta, da cin su ga dukiyar mutane daƙarya. Kuma Muka yi tattali, domin kafirai, azaba mai raɗaɗi

    [162] Amma tabbatattu a cikin ilmi daga gare su, da muminai, suna imani da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabaninka, madalla da masu tsai da salla, da masu bayar da zakka, da masu imani daAllah da Ranar Lahira. Waɗannan za Mu ba su lada mai girma

    [163] Lalle ne Mu, Mun yi wahayi zuwa gare ka, kamar yadda Muka yi wahayi zuwa ga Nuhu da annabawa daga bayansa. Kuma Mun yi wahayi zuwa ga Ibrahima da Isma'ila da Is'haƙa da Yaƙubu da jikoki da isa da Ayuba da Yunusa da Haruna da Sulaiman. Kuma Mun bai wa Dawuda zabura

    [164] Da wasu Manzanni, haƙi ƙa, Mun ba da labarinsu a gare ka daga gabani, da wasu manzanni waɗanda ba Mu ba da labarinsu ba a gare ka, kuma Allah Ya yi magana da Musa, magana sosai

    [165] Manzanni masu bayar da bushara kuma masu gargaɗi domin kada wata hujja ta kasance ga mutane a kan Allah bayan Manzannin. Kuma Allah ya kasance Mabuwayi, Mai hikima

    [166] Amma Allah Yana shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Ya saukar da shi da saninSa. Kuma mala'iku suna shaida. Kuma Allah Ya isa Ya zama shaida

    [167] Lalle ne, waɗanda suka kafirta kuma suka kange (wasu mutane) daga hanyar Allah, haƙiƙa, sun ɓace, ɓata mai nisa

    [168] Lalle ne waɗanda suka kafirta, kuma suka yi zalunci, Allah bai kasance Yana yi musu gafara ba, kuma ba Ya shiryar da su ga hanya

    [169] Face hanyar Jahannama, suna masu dawwama a cikinta har abada, kuma wannan ya kasance, ga Allah, mai sauƙi

    [170] Ya ku mutane! Haƙiƙa, Manzo ya je muku da gaskiya daga Ubangijinku. Saboda haka ku yi imani ya fi zama alheri a gare ku. Kuma idan kun kafirta, to, Allah Yana da abin da ke cikin sammai da ƙasa. Kuma Allah Ya kasance Masani, Mai hikima

    [171] Ya Mutanen Littafi! Kada ku zurfafa a cikin addininku. Kuma kada ku faɗa, ga Allah, face gaskiya. Abin da aka sani kawai, Masi hu isa ɗan Maryama Manzon Allah ne, kuma kalmarSa, ya jefa ta zuwa ga Maryama, kuma ruhi ne daga gare Shi. Saboda haka, ku yi imani da Allah da manzanninSa, kuma kada ku ce, "Uku". Ku hanu (daga faɗin haka) ya fi zama alheri a gare ku. Abin da aka sani kawai, Allah Ubangiji ne Guda. TsarkinSa ya tabbata daga wani abin haifuwa ya kasance a gare Shi! Shi ne da abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa kuma Allah Ya isa Ya zama wakili

    [172] Masihu ba ya ƙyamar ya kasance bawa ga Allah, kuma haka mala'ikun nan makusanta. Kuma wanda ya yi ƙyamar bautarSa kuma yi yi girman kai, to, zai tara su zuwa gare shi gaba ɗaya

    [173] To, amma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwaiai, to za Ya cika musu ijarorinsu, kuma Yana ƙara musu daga falalarSa. Kuma amma waɗanda suka yi ƙyama, kuma suka yi girman kai, to, za Ya yi musu azaba, azaba mai raɗɗi kuma ba su samun wani masoyi domin kansu, baicin Allah, kuma ba su samun mataimaki

    [174] Ya ku mutane! Haƙiƙa wani dalili daga Ubangijinku ya je muku kuma Mun saukar da wani haske, bayyananne zuwa gare ku

    [175] To, amma waɗanda suka yi imani da Allah kuma suka faku a gare Shi, to, zai shigar da su cikin wata rahama daga gare Shi da wata falala, kuma Ya shiryar da su zuwa gare Shi ga tafarki madaidaici

    [176] Suna yi maka fatawa. Ka ce: "Allah Yana bayyana muku fatawa a cikin 'Kalala."' Idan mutum ya halaka, ba shi da, reshe kuma yana da 'yar'uwa, to, tana da rabin abin da ya bari, kuma shi yana gadon ta, idan wani reshe bai kasance ba a gare ta. Sa'an nan idan ('yan'uwa mata) suka kasance biyu, to suna da kashi biyu daga kashi uku ɗin abin da ya bari. Kuma idan sun kasance, 'yan'uwa, maza da mata to namiji yana da misalin rabon mata biyu. Allah Yana bayyanawa a gare ku, domin kada ku ɓace. Kuma Allah ne, Masani ga dukan kome

    Gidauniyar Abinci

    Surah 5

    [1] Ya ku waɗanda suka yi imani! ku cika alkawurra. An halatta muku dabbobin jin daɗi face abin da ake karantawa a kanku, ba kuna masu halattar da farauta ba alhali kuwa kuna masu harama. Lalle ne, Allah Yana hukunta abin da yake nufi

    [2] Ya ku waɗanda suka yi imani! kada ku halattar da ayyukan ibadar Allah game da hajji, kuma da wata mai alfarma, kuma da hadaya, kuma da ratayar raƙuman hadaya, kuma da masu nufin ¦aki mai alfarma, suna neman falala daga Ubangijinsu da yarda. Kuma idan kun kwance harama, to, ku yi farauta. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutane ta ɗauke ku, domin sun kange ku daga Masallaci Mai alfarma, ga ku yi zalunci. Kuma ku taimaki juna a kan aikin ƙwarai da taƙawa. Kuma kada ku taimaki juna a kan zunubi da zalunci, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Mai tsananin uƙuba ne

    [3] An haramta muku mushe da jini da naman alade da abin da aka ambaci sunan wanin Allah a gare shi, da maƙararriya da jefaffiya da mai gangarowa da sokakkiya, da abin da masu dagi suka ci, face abin da kuka yanka, da abin da aka yanka a kan gunki (shi ma an haramta). Kuma kada ku yi rabo da kibiyoyi na caca wannan fasiƙanci ne, A yau waɗanda suka kafirta sun yanke ƙauna daga addininku. Saboda haka kada ku ji tsoronsu kuma ku ji tsoroNa. A yau Na kammala muku addininku, Kuma Na cika ni'imaTa a kanku, Kuma Na yarda da Musulunci ya zama addini a gare ku. To, wanda aka sanya wa lalura a cikin yunwa mai tsanani, ba yana mai karkata zuwa ga wani zunubi ba, to, lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [4] Suna tambayar ka cewa mene ne aka halatta musu? Ka ce: "An halatta muku abubuwa masu daɗi da abin da kuka sanar (farauta) daga masu yin miki, kuna masu sakinsu daga hannuwanku, kuna sanar da su daga abin da Allah Ya sanar da ku. To, ku ci daga abin da suka kama saboda ku, kuma ku ambaci sunan Allah a kansa, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Mai gaugawar sakamako da yawa ne

    [5] A yau an halatta muku abubuwa masu daɗi kuma abincin waɗanda aka bai wa Littafi halal ne a gare ku, kuma abincinku halal ne a gare su, da mata masu kamun kai daga muminai da mata 'ya'ya daga waɗanda aka bai wa Littafi a gabaninku idan kun je musu da sadakokinsu, kuna masu yin aure, ba masu yin zina ba, kuma ba masu riƙon abokai ba. Kuma wanda ya kafirta da imani to, lalle ne aikinsa ya ɓaci, kuma shi, a cikin Lahira, yana daga masu hasara

    [6] Ya ku waɗanda suka yi imani! idan kun tashi zuwa ga salla, to, ku wanke fuskokinku da hannuwanku zuwa ga magincirori, kuma ku yi shafa ga kanunku, kuma ku (wanke) ƙafafunku zuwa idanun sawu biyu. Kuma idan kun kasance masu janaba, to, ku yi tsarki, kuma idan kun kasance majinyata, ko kuwa a kan tafiya, ko kuwa ɗaya daga gare ku ya zo daga kashi, ko kuka yi shafayyar juna da mata, sa'an nan ba ku sami ruwa ba to ku yi nufin wuri mai kyau, sa'an nan ku yi shafa ga fuskokinku da hannuwanku daga gare shi. Allah ba Ya nufi domin Ya sanya wani ƙunci a kanku, kuma amma Yana nufi domin Ya cika ni'imarSa a kanku, tsammaninku kuna godewa

    [7] Kuma ku tuna ni'imar Allah akanku da alkawarinku wanda Ya ɗaure ku da shi, a lokacin da kuka ce: "Mun ji kuma mun yi ɗa'a Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle ne Allah Masani ne ga abin da ke a cikin zukata

    [8] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku kasance masu tsayin daka domin Allah masu shaida da adalci. Kuma kada ƙiyayya da wasu mutane ta ɗauke ku a kan ba za ku yi adalci ba. Ku yi adalci Shi ne mafi kusa ga taƙawa. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Masani ne ga abin da kuke aikatawa

    [9] Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Suna da wata gafara da lada mai girma

    [10] Kuma waɗanda suka kafirta, kuma suka ƙaryata, game da ayoyinMu, waɗannan su ne abokan wuta

    [11] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku tuna ni'imar Allah a kanku a lokacin da wasu mutane suka yi niyyar su shimfiɗa hannuwansu zuwa gare ku sai Ya kange hannuwansu daga gare ku, kuma ku bi Allah da taƙawa. Kuma sai muminai su dogara ga Allah kawai

    [12] Kuma lalle Allah Ya riƙi alkawarin Bani lsra' ila kuma Muka ayyana wakilai goma sha biyu daga gare su kuma Allah Ya ce: "Lalle ne Ni, Ina tare da ku, haƙiƙa, idan kun tsayar da salla, kuma kun bayar da zakka, kuma kun yi imani da manzanniNa, kuma kuka taimake su, kuma kuka bai wa Allah rance mai kyau, haƙiƙa, Ina kankare laifukanku daga gare ku, kuma haƙiƙa, Ina shigar da ku gidajen Aljanna (waɗanda) ƙoramu sana gudana a ƙarƙashinsu, sa'an nan wanda ya kafirta a bayan wannan daga gare ku, to, lalle ne, ya ɓace daga tsakar hanya

    [13] To, saboda warwarewarsu ga alkawarinsu Muka la'ane su, kuma Muka sanya zukatansu ƙeƙasassu, suna karkatar da magana daga wurarenta, kuma suka manta da wani yanki daga abin da aka tunatar da su da shi, kuma ba za ka gushe ba kana tsinkayar yaudara daga gare su face kaɗan daga gare su. To, ka yafe laifi daga gare su, kuma ka kau da kai. Lalle ne, Allah Yana son masu kyautatawa

    [14] Kuma daga waɗanda suka ce: "Lalle ne mu Nasara ne" Mun riƙi alkawarinsu, sai suka manta da wani yanki daga abin da aka tunatar da su da shi, sai Muka shushuta adawa da ƙeta a tsakaninsu har ya zuwa ga Ranar ¡iyama. Kuma Allah zai ba su labari da abin da suka kasance suna sana'antawa

    [15] Ya Mutanen littafi! Lalle ne, ManzonMu ya je muku, yana bayyana muku abu mai yawa daga abin da kuka kasance kuna ɓoyewa daga Littafi, kuma yana rangwame daga abu mai yawa. Haƙiƙa, wani haske da wani Littafi mai bayyanawa ya je muku daga Allah

    [16] Dashi, Allah Yana shiryar da wanda ya bi yardarsa zuwa ga hanyoyin aminci, kuma Yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske da izninsa, kuma Yana shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya

    [17] Lalle haƙiƙa waɗanda suka ce: "Lalle Allah Shi ne Masihu ɗan Maryama," sun kafirta. Ka ce: "To, wane ne ke iya mallakar wani abu daga Allah, idan Ya nufi Ya halakar da Masihu ɗanMaryama da uwarsa da wanda yake a cikin ƙasa gaba ɗaya?" Kuma Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu, Yana halitta abin da Yake so. Kuma Allah a kan dukkan kome, Mai ikon yi ne

    [18] Kuma Yahudu da Nasara sun ce: "Mu ne ɗiyan Allah, kuma masoyansa." Ka ce: "To, don me Yake yi muku azaba da zunubanku? A'a ku mutane ne daga waɗanda Ya halitta, Yana gafartawa ga wanda Yake so, kuma Yana azabta wanda Yake so. Kuma Allah ne da mulkin sammai da ƙasa da abin da ke tsakaninsu kuma zuwa gare shi makoma take

    [19] Ya Mutanen Littafi! Lalle ManzonMu ya je muku yana bayyana muku, a kan lokacin fatara daga manzanni, domin kada ku ce: "wani mai bayar da bushara bai zo mana ba, kuma haka wani mai gargaɗi bai zo ba." To, haƙiƙa, mai bayar da bushara da mai gargaɗi sunje muku. Kuma Allah ne, a kan dukkan kome, Mai ikon yi

    [20] Kuma a lokacin da Musa ya ce wa mutanensa: "Ya ku mutanena! Ku tuna ni'imar Allah a kanku; domin Ya sanya annabawa a cikinku, kuma Ya sanya ku sarakuna, kuma Ya ba ku abin da bai bai wa kowa ba daga talikai

    [21] Ya mutanena! Ku shiga ƙasar nan, abar tsarkakewa, wadda Allah Ya rubuta saboda ku, kuma kada ku koma da baya, har ku juya kuna masu hasara

    [22] Suka ce: "Ya Musa! Lalle ne, a cikinta akwai wasu mutane masu ƙarfi kuma lalle ne ba za mu shige ta ba sai sun fice daga gare ta, to, idan sun fice daga gare ta, to, lalle ne mu, masu shiga ne

    [23] Wasu maza biyu daga waɗanda suke tsoron Allah, Allah Ya yi ni'ima a kansu, suka ce: "Ku shiga gare su, daga ƙofar, domin idan kuka shige shi, to, lalle ne ku, masu rinjaya ne, kuma ga Allah sai ku dogara idan kun kasance muminai

    [24] Suka ce: "Ya Musa! Lalle ne mu, ba za mu shige ta ba har abada matuƙar sun dawwama a cikinta sai ka tafi kai da Ubangijinka domin ku yi yaƙi. Lalle ne mu, muna a nan zaune

    [25] Ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne ni, ba ni mallakar kowa face kaina da ɗan'uwana, sai Ka rarrabe a tsakaninmu da tsakanin mutane fasiƙai

    [26] (Allah) Ya ce: "To, lalle ne ita abar haramtawa ce a gare su, shekara arba'in, suna yin ɗimuwa a cikin ƙasa. Saboda haka kada ka yi baƙin ciki a kan mutane fasiƙai

    [27] Kuma karanta musu labarin ɗiya biyu na Adamu, da gaskiya, a lokacin da suka bayar da baiko, sai aka karɓa daga ɗayansu kuma ba a karɓa daga ɗayan ba, ya ce: "Lalle ne zan kashe ka." (¦ayan kuma) ya ce: "Abin sani dai, Allah Yana karɓa daga masu taƙawa ne

    [28] Lalle ne idan ka shimfiɗa hannunka zuwa gare ni domin ka kashe ni, ban zama mai shimfiɗa hannuna zuwa gare ka ba domin in kashe ka. Lalle ne ni ina tsoron Allah Ubangijin talikai

    [29] Lalle ne ni ina nufin ka koma da zunubina game da zunubinka, har ka kasance daga abokan wuta. Kuma wannan shi ne sakamakon azzalumai

    [30] Sai ransa ya ƙawatar masa kashewar ɗan'uwansa, sai kuwa ya kashe shi, sa'an nan ya wayi gari daga masu hasara

    [31] Sai Allah Ya aiki wani hankaka, yana tono a cikin ƙasa domin ya nuna masa yadda zai turbuɗe gawar ɗan'uwansa. Ya ce: "Kaitona! Na kasa in kasance kamar wannan hankaka domin in turbuɗe gawar ɗan'uwana?" Sai ya wayi gari daga masu nadama

    [32] Daga sababin wannan, Muka rubuta a kan Bani lsra'ila cewa, lalle ne wanda ya kashe rai ba da wani rai ba, ko ɓarna a cikin ƙasa, to kamar ya kashe mutane duka ne, kuma wanda ya raya rai, to, kamar ya rayar da mutane ne gaba ɗaya. Kuma lalle ne, haƙiƙa, ManzanninMu sun je musu da hujjoji bayyanannu, sa'an nan kuma lalle ne, masu yawa daga gare su, a bayan wannan, haƙiƙa, masuɓarna ne a cikin ƙasa

    [33] Abin sani kawai sakamakon waɗanda suke Yaƙin Allah da Manzonsa, kuma suna aiki a cikin ƙasa domin ɓarna a kashe su ko kuwa a ƙere su, ko kuwa a kakkatse hannuwansu da ƙafafunsu daga saɓani, ko kuwa a kore su daga ƙasa. Sannan gare su wulakanci ne a cikin rayuwar duniya, kuma a Lahira suna da wata azaba mai girma

    [34] Face fa waɗanda suka tuba tun a gabanin ku sami iko akansu, to, ku sani cewa lalle ne, Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [35] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku nemi tsari zuwa gare shi, kuma ku yi jihadi a cikin hanyarsa, tsammaninku, za ku ci nasara

    [36] Lalle ne waɗanda suka kafirta, lalle da suna da abin da ke a cikin ƙasa gaba ɗaya da misalinsa tare da shi, domin su yi fansa da shi daga azabar Ranar ¡iyama, ba a karɓarsa daga gare su, kuma suna da azaba mai raɗadi

    [37] Suna nufin su fita ne daga wuta, kuma ba su zama masu fita daga gare ta ba, kuma suna da azaba zaunanniya

    [38] Kuma ɓarawo da ɓarauniya sai ku yanke hannuwansu, bisa sakamako ga abin da suka tsirfanta, a kan azaba daga Allah. Kuma Allah Mabuwayi ne, Mai hikima

    [39] To, wanda ya tuba a bayan zaluncinsa, kuma ya gyara (halinsa), to, lalle ne Allah Yana karɓar tubarsa. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [40] Shin, ba ka sani ba cewa lalle ne, Allah Shi ne da mulkin sammai da ƙasa, Yana azabtar da wanda Yake so, kuma Yana yin gafara ga wanda yake so, kuma Allah a dukkan kome, Mai ikon yi ne

    [41] Ya kai Manzo! Kada waɗanda suke tseren gaugawa a cikin kafirci su ɓata maka rai, daga waɗanda suka ce: "Mun yi imani" da bakunansu, alhali zukatansu ba su yi imanin ba, kuma daga waɗanda suka tuba (watau Yahudu) masu yawan saurare ga wasu mutane na dabam waɗanda ba su je maka ba, suna karkatar da zance daga bayan wurarensa, suna cewa: "Idan an ba ku wannan, to, ku karɓa, kuma idan ba a ba ku shi ba, to, ku yi sauna."Kuma wanda Allah Ya yi nufin fitinarsa, to ba za ka mallaka masa kome ba, daga Allah. Waɗannan ne waɗanda Allah bai yi nufin Ya tsarkake zukatansu ba. Suna da kunya a cikin duniya, kuma suna da wata azaba mai girma a cikin 1ahira

    [42] Masu yawan saurare ga ƙarya ne, masu yawan ci ga haram, to, idan sun zo maka, sai ka yi hukunci a tsakaninsu ko ka bijira daga gare su. Kuma idan ka bijira daga gare su, to, ba za su cuce ka da kome ba, kuma idan ka yi hukunci, to, sai ka hukunta a tsakaninsu da adalci. Lalle ne, Allah Yana son masu adalci

    [43] Kuma yaya suke gabatar da kai ga hukunci, alhali a wurinsu akwai Attaura, a cikinta akwai hukuncin Allah, sa'an nan kuma suna karkacewa a bayan wannan? waɗannan ba muminai ba ne

    [44] Lalle ne Mu, Mun saukar da Attaura, a cikinta akwai shiriya da haske Annabawa waɗanda suke sun sallama, suna yin hukunci da ita ga waɗanda suka tuba (Yahudu), da malaman tarbiyya, da manyan malamai ga abin da aka neme su da su tsare daga Littafin Allah, kuma sun kasance, a kansa, masu ba da shaida. To, kada ku ji tsoron mutane kuma ku ji tsoroNa kuma kada ku sayi 'yan kuɗi kaɗan da ayoyiNa. wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukar, to, waɗannan su ne kafirai

    [45] Kuma Mun rubuta a kansu, a cikinta cewa, lalle (ana kashe) rai saboda rai, kuma (ana ɗebe) ido saboda ido, kuma (ana katse) hanci saboda hanci, kuma kunne saboda kunne kuma haƙori saboda haƙori kuma a raunuka a yi sakayya. To, wanda ya yi sadaka da shi, to, shi kaffara ce a gare shi. Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukar, to, waɗannan su ne azzalumai

    [46] Kuma Muka biyar a kan gurabansu da Isa ɗan Maryama, yana mai gaskatawa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma Muka ba shi Injila a cikinsa akwai shiriya da haske, yana mai gaskatawa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma shi shiriya ne da wa'azi ga masu taƙawa

    [47] Kuma sai mutanen injila su yi hukunci da abin da Allah ya saukar a cikinta. Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah ya saukar, to, waɗannan su ne fasiƙai

    [48] Kuma Mun saukar da Littafi zuwa gare ka da gaskiya, yana mai gaskatawa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littafi (Attaura da Injila), kuma mai halartawa a kansa. sai ka yi hukunci a tsakaninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bibiyi son zuciyoyiniu daga abin da ya zo maka daga gaskiya. Ga kowanne daga gare ku Mun sanya sharia da hanya (ta bin ta). Kuma da Allah Ya so, da Ya sanya ku al'umma guda, kuma amma domin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya ba ku. Sai ku yi tsere ga ayyukan alheri. Zuwa ga Allah makomarku take gaba ɗaya. Sa'an nan Ya ba ku labari ga abin da kuka kasance kuna saɓawa a cikinsa

    [49] Kuma ka yi hukunci a tsakaninsu da abin da Allah Ya saukar kuma kada ka bibiyi son zuciyoyinsu, kuma ka yi saunar su fitine ka daga sashen abin da Allah Ya saukar zuwa gare ka. To, idan sun juya baya, to, ka sani cewa, kawai Allah yana nufin Ya same su da masifa ne saboda sashen zunubansu. Kuma lalle ne, masu yawa daga mutane, haƙiƙa, fasiƙai ne

    [50] Shin, hukuncin Jahiliyya suke nema? Kuma wane ne mafi kyau ga hukunci daga Allah saboda mutane waɗanda suke yin yaƙini (tabbataccen imani)

    [51] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku riƙi Yahudu da Nasara majiɓinta. Sashensu majiɓinci ne ga sashe. Kuma wanda ya jiɓince su daga gare ku, to, lalle ne shi, yana daga gare su. Lalle Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [52] Sai ka ga waɗanda a cikin zukatansu akwai cuta, suna tseren gaugawa a cikinsu, suna cewa: "Muna tsoron kada wata masifa ta same mu." To, akwai tsammanin Allah Ya zo da buɗi, ko kuwa wani umurni daga wurinSa, har su wayi gari a kan abin da suka ɓoye a cikin zukatansu, suna masu nadama

    [53] Kuma waɗanda suka yi imani suna cewa: "Shin, waɗannan ne waɗanda suka yi rantsuwa da Allah iyakar rantsuwoyinsu, cewa su, lalle suna tare da ku?" Ayyukansu sun ɓaci, saboda haka suka wayi gari suna masu hasara

    [54] Ya ku waɗanda suka yi imani! wanda ya yi ridda daga gare ku daga addininSa, to, Allah zai zo da wasu mutane, Yana son su kuma suna son Sa, masu tawalu'i a kan muminai masu izza a kan kafurai. Suna yin, jihadi a cikin hanyar Allah, kuma ba su tsoron zargin wani mai zargi. Waccan falalar Allah ce, Yana bayar da ita ga wanda Yake so. Kuma Allah Mayalwaci ne, Mai ilmi

    [55] Abin sani kawai, majiɓincinku Allah ne da ManzonSa da waɗanda suka yi imani, waɗanda suke suna tsayar da salla kuma suna bayar da zakka kuma suna ruku'i

    [56] Kuma wanda ya jiɓinci Allah da ManzonSa da waɗanda suka yi imani, to, ƙungiyar Allah sune masu rinjaya

    [57] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku riƙi waɗanda suka riƙi addininku bisa izgili da wasa, daga waɗanda aka bai wa Littafi daga gabaninku da kafirai, masoya, Kuma ku bi Allah da taƙawa idan kun kasance muminai

    [58] Kuma idan kuka yi kira zuwa ga salla, sai su riƙe ta bisa izgili da wasa. Wannan domin lalle ne su, mutane ne (waɗanda) ba su hankalta

    [59] Ka ce: "Ya Mutanen Littafi! Shin, kuna ganin wani laifi daga gare mu? Face dai domin mun yi imani da Allah da abin da aka Saukar zuwa gare mu da abin da aka saukar daga gabani, kuma domin mafi yawanku fasiƙai ne

    [60] Ka ce: "Shin, in gaya muku mafi sharri daga wannan, domin sakamako daga wurin Allah? wanda Allah Ya la'ane shi kuma Ya yi fushi da shi, kuma Ya sanya daga gare su birai da aladai, kuma ya bauta wa ¦aguta. Waɗannan ne mafiya sharrin wuri, kuma mafiya ɓata daga tsakar hanya

    [61] Kuma idan sun zo muku sai su ce: "Mun yi imani." Alhali kuwa haƙiƙa, sun shigo da kafirci, kuma su lalle ne, sun fita da shi, kuma Allah ne Mafi sani ga abin da suka kasance suna ɓoyewa

    [62] Kuma kana ganin masu yawa daga gare su, suna tseren gaugawa a cikin zunubi da zalunci da cinsu ga haram. Haƙiƙa, tir da abin da suka kasance suna aikatawa

    [63] Don me Malaman Tarbiyya da manyan malamai (na Yahudu) ba su hana su daga faɗarsu ga zunubi da cinsu ga haram ba? Haƙiƙa, tir daga abin da suka kasance suna sana'antawa

    [64] Kuma Yahudu suka ce: "Hannun Allah abin yi wa ƙuƙumi ne. " An sanya hannuwansu a cikin ƙuƙumi! Kuma an la'ane su saboda abin da suka faɗa. A'a, hannuwanSa biyu shimfiɗaɗɗu ne, Yana ciyarwa yadda Yake so. Kuma lalle ne abin da aka saukar zuwa gare ka yana ƙara wa masu yawa daga gare su, girman kai da kafirci. Kuma Mun jefa a tsakaninsu, ƙiyayya da ƙeta, zuwa Ranar ¡iyama, ko da yaushe suka hura wata wuta domin yaƙi, sai Allah Ya bice ta. Suna aiki a cikin ƙasa domin ɓarna, alhali kuwa Allah ba Ya son masu fasadi

    [65] Kuma da dai lalle Mutanen Littafi sun yi imani, kuma sun yi taƙawa, haƙiƙa, da Mun kankare miyagun ayyukansu daga gare su, kuma da Mun shigar da su gidajen Aljannar Ni'ima

    [66] Kuma da dai lalle su, sun tsayar da Attaura da Injila da abin da aka saukar zuwa gare su daga Ubangijinsu, haƙiƙa, da sun ci daga bisansu da kuma daga ƙarƙashin ƙafafunsu. Daga gare su akwai wata al'umma mai tsakaitawa kuma masu yawa daga gare su, abin da suke aikatawa ya munana

    [67] Ya kai Manzo! Ka iyar da abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka. Kuma idan ba ka aikata ba, to, ba ka iyar da manzancinSa ba ke nan. Kuma Allah Yana tsare ka daga mutane. Lalle ne, Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai

    [68] Ka ce: "Ya ku Mutanen Littafi! Ba ku zama a kan kome ba, sai kun tsayar da Attaura da Injila da abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku."Kuma lalle ne, abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka, yana ƙara wa masu yawa daga gare su girman kai da kafirci. To, kada ka yi baƙin ciki a kan mutane kafirai

    [69] Lalle ne, waɗanda suka yi imani da waɗanda sukatuba (Yahudu) da Karkatattu da Nasara, wanda ya yi imani da Allahda Ranar Lahira, kuma ya aikata aiki na ƙwarai, to, babu tsoro a kansu, kuma ba su zamo suna baƙin ciki ba

    [70] Lalle ne haƙiƙa Mun riƙi alkawarin Bani Isra'ila, kumaMun aiki manzanni zuwa gare su, ko da yaushe wani manzo ya je musu da abin da rayukansu ba su so, wani ɓangare sun ƙaryata, kuma wani ɓangare suna kashewa

    [71] Kuma suka yi zaton cewa wata fitina ba za ta kasance ba sai Suka makanta, kuma suka kurubta, sa'an nan Allah Ya karɓi tuba a gare su, sa'an nan suka makanta kuma suka kurunta masu yawa daga gare su, alhali Allah Mai gani ne ga abin da suke aikatawa

    [72] Lalle ne haƙiƙa waɗanda suka ce: "Lalle ne Allah, shine Masihu, ɗan Maryama," sun kafirta. Alhali kuwa Masihu ya ce: "Ya Bani Isra'ila! Ku bauta wa Allah Ubangijina, kuma Ubangijinku." Lalle ne shi, wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne, Allah Ya haramta masa Aljanna. Kuma babu wasu mataimaka ga azzalumai

    [73] Lalle ne, haƙiƙa, waɗanda suka ce: "Allah na ukun uku ne," sun kafirta, kuma babu wani abin bautawa face Ubangji Guda. Kuma idan ba su hanu daga abin da suke faɗa ba, haƙiƙa, wata azaba mai raɗaɗi tana shafar waɗanda suka kafirta daga gare su

    [74] shin fa, ba su tuba zuwa ga Allah, kuma su neme Shi gafara, alhali kuwa Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [75] Masihu ɗan Maryama bai zama ba face Manzo ne kawai, haƙiƙa, manzanni sun shige dage gabaninsa, kuma uwarsa siddika ce. Sun kasance suna cin abinci. Ka duba yadda Muke bayyana musu ayoyi. Sa'an nan kuma ka duba yadda ake karkatar da su

    [76] Ka ce: "Ashe kuna bauta wa, baicin Allah, abin da ba ya mallakar wata cuta saboda ku kuma haka wani amfani alhali kuwa Allah Shi ne Mai ji, Masani

    [77] Ka ce: "Ya ku Mutanen Littafi! Kada ku zurfafa a cikin addininku, abin da ba gaskiya ba, kuma kada ku bibiyi son zuciyoyin waɗansu mutane waɗanda suka riga suka ɓace a gabani, kuma suka ɓatar da wasu masu yawa, kuma suka ɓace daga tsakar hanya

    [78] An la'ani waɗanda suka kafirta daga Bani Isra'ila a kan harshen Dawuda da Isa ɗan Maryama. wannan kuwa saboda saɓawar da suka yi ne, kuma sun kasance suna ta'addi

    [79] Sun kasance ba su hana juna daga abin ƙi, wanda suka aikata. Haƙiƙa abin da suka kasancesuna aikatawa ya munana

    [80] Kana ganin masu yawa daga gare su, suna jiɓintar waɗanda suka kafirta. Haƙiƙa tir da abin da rayukansu suka gabatar saboda su, watau Allah Ya yi fushi da su, kuma a cikin azaba su masu dawwama ne

    [81] Kuma da sun kasance suna imani da Allah da Annabi da abin da aka saukar zuwa gare shi, da ba su riƙe su masoya ba. Kuma amma masu yawa daga gare su, fasiƙai ne

    [82] Lalle ne kana samun mafiya tsananin mutane a adawa ga waɗanda suka yi imani, Yahudu ne da waɗanda suka yi shirki. Kuma lalle ne kana samun mafiya kusantarsu a soyayya ga waɗanda suka yi imani su ne waɗanda suka ce: "Lalle mu ne Nasara." Wancan kuwa saboda akwai ¡issawa da ruhubanawa daga cikinsu. Kuma lalle ne su, ba su yin girman kai

    [83] Kuma idan suka ji abin da aka saukar zuwa ga Manzo, kana ganin idanunsu suna zubar da hawaye, saboda abin da suka sani daga gaskiya, suna cewa: "Ya Ubangijinmu! Mun yi imani, sai ka rubuta mu tare da masu shaida

    [84] Kuma mene ne yake gare mu, ba za mu yi imani daAllah ba, da kuma abin da ya zo mana daga gaskiya, kuma muna gurin Ubangijinmu Ya shigar da mu tare da mutane salihai

    [85] Saboda haka, Allah Ya saka musu, domin abin da suka faɗa da gidajen Aljanna (waɗanda) ƙoramu suna gudana a ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, kuma wannan ne sakamakon masu kyautatawa

    [86] Kuma waɗanda suka kafirta kuma suka ƙaryata game da ayoyinMu, waɗancan ne abokan Wuta

    [87] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku haramta abubuwa masu daɗi da Allah Ya halatta muku, kuma kada ku ƙetare haddi. Lalle ne, Allah ba Ya son masu ƙetare haddi

    [88] Kuma ku ci daga abin da Allah Ya azurta ku, halat mai daɗi, kuma ku bi Allah da taƙawa, wanda yake ku, masu imani ne da shi

    [89] Allah ba Ya kama ku saboda yasassa a cikin rantsuwoyinku, kuma amma Yana kama ku da abin da kuka ƙudurta rantsuwoyi (a kansa). To, kaffararsa ita ce ciyar da miskini goma daga matsakaicin abin da kuke ciyar da iyalanku, ko kuwa tufatar da su, ko kuwa 'yantawar wuya. Sa'an nan wanda bai samu ba, sai azumin kwana uku. wannan ne kaffarar rantsuwoyinku, idan kun rantse. Kuma ku kiyaye rantsuwoyinku. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ayoyinsa, tsammaninku kuna godewa

    [90] Ya ku waɗanda suka yi imani! Abin sani kawai, giya da caca da refu da kiban ƙuri'a, ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nisance shi, wa la'alla ku ci nasara

    [91] Abin sani kawai Shaiɗan yana nufin ya aukar da adawa da ƙeta a tsakaninku, a cikin giya da caca, kuma ya kange ku daga ambaton Allah, kuma daga sallah. To, shin, ku masu hanuwa ne

    [92] Ku yi ɗa'a ga Allah, kuma ku yi ɗa'a ga Manzo, kuma ku kiyaye. To, idan kun juya, to, ku sani abin da kawai yake kan ManzonMu, iyarwa bayyananniya

    [93] Babu laifi a kan waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, a cikin abin da suka ci, idan sun yi taƙawa kuma suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sa'an nan suka yi taƙawa kuma suka yi imani, sa'an nan kuma suka yi taƙawa kuma suka kyautata. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa

    [94] Ya ku waɗanda suka yi imani! Lalle ne, Allah zai jarraba ku da wani abu, daga farauta, hannuwanku da masunku suna samun sa domin Allah Ya san wanda yake tsoron Sa a fake. To, wanda ya yi ta'addi a bayan wannan, to, yana da azaba mai raɗaɗi

    [95] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku kashe farauta alhali kuna masu harama. Kuma wanda ya kashe shi daga gare ku, yana mai ganganci, sai sakamako misalin abin da ya kashe, daga dabbobin ni'ima, ma'abuta adalci biyu daga cikinku suna yin hukunci da shi. Ya zama hadaya mai isa ga Ka'aba ko kuwa kaffara da abincin miskinai ko kuwa a matsayinsa ya yi azumi domin ya ɗanɗani masifar al'amarinsa. Allah Ya yafe laifi daga abin da ya gabata. Kuma wanda ya koma, to, Allah zai yi azabar ramuwa daga gare shi, kuma Allah Mabuwayi ne, ma'abucin azabar ramuwa

    [96] An halatta muku farautar ruwa da abincinsa domin jin daɗi a gare ku, kuma domin matafiya. Kuma an haramta farautar tudu a kanku, matuƙar kun dawwama masu harama. Kuma ku bi Allah da taƙawa, wanda yake zuwa gare Shi ne ake tara ku

    [97] Allah Ya sanya Ka'aba ¦aki Tsararre, ma'aunin addini ga mutane, kuma Ya sanya wata Mai alfarma da hadaya da ratayoyin Allah Ya san abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, kuma cewa lalle Allah, ga dukkan, kome, Masani ne

    [98] Ku sani cewa lalle Allah Mai tsananin uƙuba ne, kuma lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [99] Babu abin da yake a kan Manzo, sai iyarwa, kuma Allah Yana sanin abin da kuke bayyanawa da abin da kuke ɓoyewa

    [100] Ka ce: "Mummuna da mai kyau ba su daidaita, kuma ko da yawan mummuan ya ba ka sha'awa. Saboda haka ku bi Allah da taƙawa, ya ma'abuta hankula ko la'alla za ku ci nasara

    [101] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku yi tambaya ga abubuwa, idan an bayyana muku (hukuncinsu) su ɓata muku rai. Kuma idan kuka yi tambaya a gare su a lokacin da ake saukar da Alƙur'ani, za a bayyana maku. Allah Ya yafe laifi daga gare su, Allah Mai gafara ne, Mai haƙuri

    [102] Lalle ne wasu mutane sun tambaye su daga gabaninku, sa'an nan kuma suka wayi gari da su sana kafirai

    [103] Kuma Allah bai sanya wata bahira ba, kuma haka sa'iba, kuma haka wasila, kuma haka hami, amma waɗanda suka kafirta, su suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma mafi yawansu ba su hankalta

    [104] Kuma idan aka ce musu: "Ku zo zuwa ga abin da Allah Ya saukar, kuma zuwa ga Manzo," sai su ce: "Mai isarmu shi ne abin da muka iske ubanninmu a kansa." Shin, kuma ko da ubanninsu sun kasance ba su sanin kome kuma ba su shiryuwa

    [105] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku lazimci rayukanku, wanda ya ɓace ba zai cuce ku ba idan kun shiryu, zuwa ga Allah makomarku take gaba ɗaya. Sa'an nan Ya ba ku labari ga abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [106] Ya ku waɗanda suka yi imani! Shaidar tsakaninku, idan mutuwa ta halarci ɗayanku, a lokacin wasiyya, maza biyu ne ma'abuta adalci daga gare ku, ko kuwa wasu biyu daga wasunku idan kun tafi a cikin ƙasa sa'an nan masifarmutuwa ta same ku. Kuna tsare su daga bayan salla har su yi rantsuwa da Allah; idan kun yi shakka: "Ba mu sayen kuɗi da shi, ko da ya kasance ma'abucin zumunta kuma ba mu ɓoye shaidar Allah. Lalle ne mu, a lokacin, haƙiƙa, muna daga masu zunubi

    [107] To, idan aka gane cewa lalle su, sun cancanci zunubi to sai wasu biyu su tsayu matsayibsu daga waɗanda suka karɓa daga gare su, mutane biyu mafiya cancanta, sa'an nan su yi rantsuwa da Allah: "Lalle ne shaidarmu ce mafi gaskiya daga shaidarsu, kuma ba mu yi zalunci ba. Lalle mu, a lokacin haƙiƙa, muna daga azzalumai

    [108] Wannan ne mafi kusantar su zo da shaida a kan fuskarta ko kuwa su yi tsoron a ture rantsuwoyi a bayan rantsuwoyinsu. Kuma ku bi Allah da taƙawa kuma ku saurara, kuma Allah ba Ya shiryar da mutane fasiƙai

    [109] A ranar da Allah Yake tara manzanni sa'an nan Ya ce: "Mene ne aka karɓa muku?" (za) su ce: "Babu ilmi a gare mu. Lalle ne Kai, Kai ne Masanin abubuwan fake

    [110] A lokacin da Allah Ya ce: "Ya Isa ɗan Maryama! Ka tuna ni'ima Ta a kanka, kuma a kan mahaifiyarka, a lokacin da Na ƙarfafa ka da Ruhul ¡udusi, kana yiwa mutane magana a cikin shimfiɗar jariri, da kuma kana dattijo. Kuma a lokacin da Na sanar da kai rubutu da hikima da Attaura da Injila, kuma a lokacin da kake yin halitta daga laka kamar surar tsuntsu da iziniNa, sa'an nan ka hura a cikinta sai ta zama tsuntsu da iziniNa, kuma kana warkar da haifaffen makaho da kuturu, da iziniNa, kuma a lokacin da kake fitar da matattu da iziniNa, kuma a lokacin da Na kange Bani Isra'ila daga gare ka, a lokacin da ka je musu da hujjoji bayyanannu, sai waɗanda suka kafirta daga cikinsu suka ce: 'Wannan ba kome ba ne, face sihiri bayyananne

    [111] Kuma a lokacin da Na yi wahayi zuwa ga Hawariyawa cewa ku yi imani da Ni, kuma da ManzoNa. Suka ce: "Mun yi imani, kuma ka shaida da cewa lalle mu, masu sallamawa ne

    [112] A lokacin da Hawarayawa suka ce: "Ya Isa ɗan Maryam! shin, Ubangijinka Yana iyawa Ya saukar da kaɓaki a kanmu daga sama?" (Isa) Ya ce: "Ku bi Allah da taƙawa idan kun kasance muminai

    [113] Suka ce: "Muna nufin mu ci daga gare shi ne, kuma zukatanmu su natsu kuma mu san cewa lalle ne, ka yi mana gaskiya, kuma mu kasance daga masu shaida a kansa

    [114] Isa ɗan Maryam ya ce: "Ya Allah. Ubangijinmu! Ka saukar da kaɓaki a kanmu daga sama domin ya zama idi ga na farkonmu da na ƙarshenmu, kuma ya zama aya daga gare Ka. Ka azurta mu, kuma Kai ne Mafificin masu azurtawa

    [115] Allah Ya ce: "Lalle ne Ni mai saukar da shi ne a kanku sa'an nan wanda ya kafirta daga gare ku, to, lalle ne Ni, Ina azabta shi, da wata azaba wadda ba Ni azabta ta ga kowa daga talikai

    [116] Kuma a lokacin da Allah Ya ce: "Ya Isa ɗan Maryama! Shin, kai ne ka ce wa mutane, 'Ku riƙe ni, ni da uwata, abubuwan bautawa biyu, baicin Allah?" (Isa) Ya ce: "Tsarkinka ya tabbata! Ba ya kasancewa a gare ni, in faɗi abin da babu wani hakki a gare ni. Idan na kasance na faɗe shi, to lalle Ka san shi, Kana sanin abin da ke a cikin raina, kuma ba ni sanin abin da ke a cikin nufinKa. Lalle ne Kai Masanin abubuwan fake ne

    [117] Ban faɗa musu ba face abin da Ka umurce ni da shi; watau: 'Ku bauta wa Allah Ubangijina kuma Ubangijinku;' kuma na kasance mai shaida a kansu matuƙar na dawwama a cikinsu, sa'an nan a lokacin da Ka karɓi raina Ka kasance Kai ne mai tsaro a kansu, kuma Kai, a kan dukkan kome, Halartacce ne

    [118] Idan Ka azabta su, to lalle ne su, bayinKa ne, kuma idan Ka gafarta musu, to, lalle ne Kai ne Mabuwayi Mai hikima

    [119] Allah Ya ce: "Wannan ce ranar da masu gaskiya, gaskiyarsu take amfaninsu. Suna da gidajen Aljanna, ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu har abada. Allah Ya yarda da su, kuma sun yarda da Shi. wannan ne babban rabo mai girma

    [120] Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a cikinsu kuma shi, a kan dukkan kome Mai ikon yi ne

    Dabbobin Ni'ima

    Surah 6

    [1] Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya halitta sammai da ƙasa, kuma Ya sanya duffai da haske, sa'an nan kuma waɗanda suka kafirta, da Ubangijinsu suke karkacewa

    [2] Shi ne wanda Ya halitta ku daga laka, sa'an nan kuma Ya yanka ajali alhali wani ajali ambatacce yana wurinSa. Sa'an nan kuma ku kuna yin shakka

    [3] Kuma Shi ne Allah a cikin sammai, kuma a cikin ƙasa Yana sanin asirinku da bayyanenku, kuma Yana sanin abin da kuke yi na tsirfa

    [4] Kuma wata aya daga Ubangijinsu ba za ta je musu ba, face su kasance, daga gare ta, masu bijirewa

    [5] Saboda haka, lalle sun ƙaryata (Manzo) game da gaskiya, a lokacin da ta je musu, to labarun abin da suka kasance suna izgili da shi, za su je musu

    [6] Shin, ba su gani ba, da yawa Muka halakar da wani ƙarni daga gabaninsu, Mun mallaka musu, a ckikin ƙasa, abin da ba Mu mallaka muku ba kuma Muka saki sama a kansu tana ta zuba, kuma Muka sanya koguna suna gudana daga ƙarƙashinsu, sa'an nan Muka halaka su saboda zunubansu kuma Muka ƙaga halittar wani ƙarni na dabam daga bayansu

    [7] Kuma da Mun sassaukar da wani littafi, zuwa gare ka, a cikin takarda, sa'an nan suka taɓa shi da hannuwansu, lalle da waɗanda suka kafirta sun ce: "Wannan bai zama ba, face sihiri bayyananne

    [8] Suka ce: "Don me ba a saukar da wani mala'ika ba a gare shi?" to da Mun saukar da mala'ika haƙiƙa da an hukunta al'amarin sa'an nan kuma ba za a yi musu jinkiri ba

    [9] Kuma da Mun sanya mala'ika ya zama manzo lalle ne da Mun mayar da shi mutum, kuma da Mun rikita musu abin da suke rikitawa

    [10] Kuma lalle ne, haƙiƙa, an yi izgili da manzanni daga gabaninka, sai waɗanda suka yi izgilin, abin da suka kasance suna izgili da shi ya faɗa musu

    [11] Ka ce: "Ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa'an nan kuma ku duba yadda aƙibar masu ƙaryatawa ta kasance

    [12] Ka ce: "Na wane ne abin da yake a cikin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Na Allah ne." Ya wajabta rahama ga kanSa. Lalle ne Yana tara ku zuwa ga Ranar ¡iyama, babu shakka a gare Shi. Waɗanda suka yi hasarar rayukansu, to, su ba za su yi imani ba

    [13] Kuma Shi ne da mallakar abin da ya yi kawaici a cikin dare da yini, kuma Shi ne Mai ji, Masani

    [14] Ka ce: "Shin, wanin Allah nike riƙo majiɓinci, (alhali Allah ne) Mai ƙaga halittar sammai da ƙasa, kuma Shi, Yana ciyarwa, kuma ba a ciyar da Shi?" Ka ce: "Lalle ne ni, an umurce ni da in kasance farkon wanda ya sallama, kuma kada lalle ku kasance daga masu shirki

    [15] Kace: "Lalle ne ni ina tsoron azabar Yini Mai girma, idan na saɓa wa Ubangijina

    [16] Wanda aka juyar da shi daga gare shi, a wannan Ranar, to, lalle ne, (Allah) Ya yi masa rahama, Kuma wannan ne tsira bayyananniya

    [17] Idan Allah Ya shafe ka da wata cuta, to, babu mai kuranyewa gare ta, face Shi, kuma idanYa shafe ka da wani alheri to shi ne, a kan kome, Mai ikon yi

    [18] Kuma Shi ne mai Tanƙwasa a kan bayinSa, kuma Shi ne Mai hikima, Masani

    [19] Ka ce: "Wane abu ne mafi girma ga shaida?" Ka ce: "Allah ne shaida a tsakanina da tsakaninku. Kuma an yiwo wahayin wannan Alƙur'ani domin in yi muku gargaɗi da shi, da wanda labari ya kai gare shi. Shin lalle ne ku, haƙiƙa, kuna shaidar cewa, lalle ne tare da Allah akwai wasu abubuwan bautawa?" Ka ce: "Ba zan yi shaidar (haka) ba." Ka ce: "Abin sani, Shi ne Abin bautawa Guda kuma lalle ne ni barrantacce ne daga abin da kuke yi na shirki

    [20] Waɗanda Muka ba su Littafi suna sanin sa kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Waɗanda suka yi hasarar rayukansu, to, su ba su yin imani

    [21] Wane ne mafi zalunci daga wanda yake ƙirƙira karya ga Allah, ko kuwa ya ƙaryata game da ayoyinsa? Lalle ne shi, azzalumai ba za su ci nasara ba

    [22] Kuma ranar da Muka tara su gaba ɗaya, sa'an nan Mu ce wa waɗanda suka yi shirki: "Ina abokan tarayyarku waɗanda kuka kasance kuna riyawa

    [23] Sa'an nan kuma fitinarsu ba ta kasance ba, face domin sun ce: "Muna rantsuwa da Allah Ubangijinmu, ba mu kasance masu yin shirki ba

    [24] Ka duba yadda suka ƙaryata kansu! Kuma abin da suka kasance suna ƙirƙira ƙaryarsa, ya ɓace daga gare su

    [25] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake saurare gare ka. Kuma Mun sanya abubuwan rufi a kan zukatansu domin kada su fahimce shi kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi. Kuma idan sun ga kowace aya ba za su yi imani da ita ba har idan sunje maka suna jayayya da kai, waɗanda suka kafirta suna cewa: "Wannan bai zama ba face tatsuniyoyin mutanen farko

    [26] Kuma suna hanawa daga gare shi, kuma suna nisanta daga gare shi, kuma ba su halakarwa, face kansu, kuma ba su sansancewa

    [27] Kuma da kana gani, a lokacin da aka tsayar da su a kan wuta, sai suka ce: "Ya kaitonmu! Da ana mayar da mu, kuma ba za mu ƙaryata ba daga ayoyin Ubangijinmu, kuma za mu kasance Daga muminai

    [28] A'aha, abin da suka kasance suna ɓoyewa, daga gabani, ya bayyana a gare su. Kuma da an mayar da su, lalle da sun koma ga abin da aka hana su daga barinsa. Kuma lalle ne su, haƙiƙa, maƙaryata ne

    [29] Kuma suka ce: "Ba ta zama ba, face rayuwarmu ta duniya, kuma ba mu zama waɗanda ake tayarwa ba

    [30] Kuma da kana gani, a lokacin da aka tsayar da su ga UbangiJinsu, Ya ce: "Ashe wannan bai zama gaskiya ba?" Suka ce: "Na'am, muna rantsuwa da Ubangijinmu!" Ya ce: "To ku ɗanɗani azaba saboda abin da kuka kasance kuna yi na kafirci

    [31] Lalle ne waɗanda suka ƙaryata game da gamuwa da Allah sun yi hasara, har idan Sa'a ta je musu kwatsam, sai su ce: "Ya nadamarmu a kan abin da muka yi sakaci a cikinta!" Alhali kuwa su suna ɗaukar kayansu masu nauyi a kan bayayyakinsu. To, abin da suke ɗauka ya munana

    [32] Kuma rayuwar duniya ba ta zama ba, face wasa da shagala, kuma lalle ne, Lahira ce mafi alheri ga waɗanda suka yi taƙawa. Shin, ba za ku yi hankali ba

    [33] Lalle ne Muna sani cewa haƙiƙa, abin da suke faɗa yana ɓata maka rai. To, lalle ne su, ba su ƙaryata ka (a cikin zukatansu) kuma amma azzalumai da ayoyin Allah suke musu

    [34] Kuma lalle ne, haƙiƙa, an ƙaryata manzanni daga gabaninka, sai suka yi haƙuri a kan abin da aka ƙaryata su, kuma aka cutar da su, har taimakonMu ya je musu, kuma babu mai musanyawa ga kalmomin Allah. Kuma lalle ne (abin da yake natsar da kai) ya zo maka daga labarin (annabawan) farko

    [35] Kuma idan ya kasance cewa finjirewarsu ta yi nauyi a gare ka, to, idan kana iyawa, ka nemi wani ɓullo a cikin ƙasa, ko kuwa wani tsani a cikin sama domin ka zo musu da wata aya, (sai ka yi). Kuma da Allah Ya so haƙiƙa da Yatara su a kan shiriya. Saboda haka, kada lalle ka kasance daga jahilai

    [36] Abin sani kawai, waɗanda suke saurare ne suke karɓawa, kuma matattu Allah Yake tayar da su, Sa'an nan kuma zuwa gare Shi ake mayar da su

    [37] Kuma suka ce: "Don me ba a saukar da aya ba, a kansa, daga Ubangjinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Mai iko ne a kan Yasaukar da aya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba

    [38] Kuma babu wata dabba a cikin ƙasa kuma babu wani tsuntsu wanda yake tashi da fukafukinsa face al'umma ne misalanku. Ba Mu yi sakacin barin kome ba a cikin Littafi, sa'an nan kuma zuwa ga Ubangjinsu ake tara su

    [39] Kuma waɗanda suka ƙaryata gameda ayoyinMu, kurame ne kuma bebaye, acikin duffai. Wanda Allah Ya so Yana ɓatar da shi, kuma wanda Ya so zai sanya shi a kan hanya madaidaiciya

    [40] Ka ce: "Shin, kun gan ku, idan azabar Allah ta zo muku, ko Sa'ar Tashin Kiyama ta zo muku, shin wanin Allah kuke kira, idan dai kun kasance masu gaskiya

    [41] A'a, Shi dai kuke kira sai Ya kuranye abin da kuke kira zuwa gare Shi, idan Ya so, kuma kuna mantawar abin da kuke yin shirkin tare da shi

    [42] Kuma lalle Mun aika zuwa ga al'ummai daga gabaninka, sai Muka kama su da tsanani da cuta, tsammaninsu za su ƙanƙan da kai

    [43] To, don me, a lokacin da tsananinMu ya je musu ba su yi tawalu'i ba? Kuma amma zukatansu sun ƙeƙashe kuma shaiɗan ya ƙawata musu abin da suka kasance suna aikatawa

    [44] Sa'an nan kuma alokacin da suka manta da abin da aka tunatar da su da shi, sai Muka buɗe, a kansu, ƙofofin dukkan kome, har a lokacin da suka yi farin ciki da abin da aka ba su, Muka kama su, kwatsam, sai ga su sun yi tsuru tsuru

    [45] Sai aka katse ƙarshen mutanen, waɗanda suka yi zalunci. Kuma godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai

    [46] Ka ce: "Shin, kun gani, idan Allah Ya riƙe jinku, da gannanku, kuma Ya sanya hatimi a kan zukatanku, wane abin bauttawa ne, wanin Allah, zai je muku da shi?" Ka duba yadda Muke sarrafaayoyi, Sa'an nan kuma su, suna finjirewa

    [47] Ka ce: "Shin, kun gan ku, idan azabar Allah ta je muku, kwatsam, ko kuwa bayyane, shin, ana halakawa, face dai mutane azzalumai

    [48] Kuma ba Mu aikawa da manzanni face masu bayar da bushara, kuma masu gargaɗi. To, wanda ya yi imani kuma yagyara aiki, to, babu tsoro a kansu, kuma ba su yin baƙin ciki

    [49] Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ayoyinMu, azaba tana shafar su saboda abin da suka kasance suna yi na fasiƙanci

    [50] Ka ce: "Ba zan ce muku, a wurina akwai taskokin Allah ba. Kuma ba ni sanin gaibi, kuma ba ni gaya muku cewa ni mala'ika ne. Ba ni bi, face abin da ake yiwo wahayi zuwa gare ni." Ka ce: "Shin, makaho da mai gani suna daidaita? Shin fa, ba ku yin tunani

    [51] Kuma ka yi gargaɗi da shi ga waɗanda suke jin tsoron a tara su zuwa ga Ubangijinsu, ba su da wani masoyi baicinSa, kuma babu mai ceto, tsammaninsu, suna yin taƙawa

    [52] Kuma kada ka kori waɗanda suke kiran Ubangijinsu safe da maraice, suna nufin yardarSa, babu wani abu daga hisabinsu a kanka, kuma babu wani abu daga hisabinka a kansu, har ka kore su ka kasance daga azzalumai

    [53] Kuma kamar wannan ne, Muka fitini sashensu da sashe, domin su ce: "Shin waɗannan ne Allah Ya yi falala a kansu daga tsakaninmu?" Shin, Allah bai zama Mafi sani ba ga masu godiya

    [54] Kuma idan waɗanda suke yin imani da ayoyinMu suka je maka, sai ka ce: "Aminci ya tabbata a gareku; Ubangjinku Ya wajabta rahama ga kanSa, cewa lalle ne wanda ya aikata aibi da jahilci daga cikinku, sa'an nan kuma ya tuba daga bayansa, kuma ya gyara, to, lalle Shi, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [55] Kuma kamar wannan ne Muke bayyana ayoyi, daki-daki, kuma domin hanyar masu laifi ta bayyana

    [56] Ka ce: "Lalle ne ni, an hana ni in bauta wa waɗanda kuke kira daga baicin Allah." Ka cc: "Ba ni bin son zuciyoyinku, (domin in na yi haka) lalle ne, na ɓace. A sa'an nan, kuma ban zama daga shiryayyu ba

    [57] Ka ce: "Lalle ne ina kan hujja daga Ubangjina, kuma kun ƙaryata (ni) game da Shi; abin da kuke neman gaugawarsa, ba ya wurina, hukunci kuwa bai zama ba face, ga Allah, Yana bayar da labarin gaskiya, kuma shi ne mafi alherin masu rarrabewa

    [58] Ka ce: "Lalle ne, da a wurina akwai abin da kuke neman gaugawa da shi, haƙiƙa da an hukunta al'amarin, a tsakanina da tsakaninku, kuma Allah Shi ne Mafi sani ga azzulumai

    [59] Kuma a wurinSa mabudan gaibi suke, babu wanda yake sanin su face Shi, kuma Yana sanin abin da ke a cikin tudu da ruwa, kuma wani ganye ba ya faɗuwa, face Ya san shi, kuma babu wata ƙwaya a cikin duffan ƙasa, kuma babu ɗanye, kuma babu ƙeƙasasshe, face yana a cikin wani Littafi mai bayyanawa

    [60] Kuma Shi ne wanda Yake karɓar rayukanku da dare, kuma Yana sanin abin da kuka yaga da rana, sa'an nan Yana tayar da ku a cikinsa, domin a hukunta ajali ambatacce sa'an nan kuma zuwa gare shi makomarku take, sa'an nan kuma Ya ba ku labari da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [61] Kuma Shi ne Mai rinjaya bisa ga bayinSa, kuma Yana aikan masu tsaro a kanku, har idan mutuwa ta je wa ɗayanku, sai manzanninMu su karɓi ransa alhali su ba su yin sakaci

    [62] Sa'an nan kuma a mayar da su zuwa ga Allah Ubangjinsu na gaskiya. To! A gare shi hukunci yake, kuma Shi ne Mafi gaugawar masu bincike

    [63] Ka ce: "Wane ne Yake tsirar da ku daga duhuhuwan tududa ruwa, kuna kiran Sa bisa ga ƙanƙan da kai Kuma a ɓoye: 'Lalle ne idan Ka tsirar da mu daga wannan (masifa), haƙiƙa, muna kasancewa daga masu godiya

    [64] Ka ce: "Allah ne Yake tsirar da ku daga gare ta, kuma daga dukan baƙin ciki sa'an nan kuma ku, kuna yin shirki

    [65] Ka ce: "Shi ne Mai iko a kan Ya aika da wata azaba a kanku daga bisanku, ko kuwa daga ƙarƙashin ƙafafunku, ko kuwa Ya gauraya ku ƙungiyoyi, kuma Ya ɗanɗana wa sashenku masifar sashe." "Ka duba yadda Muke sarrafa ayoyi, tsammaninsu suna fahimta

    [66] Kuma mutanenka sun ƙaryata (ka) game da Shi, alhali kuwa Shi ne gaskiya. Ka ce: "Niban zama wakili a kanku ba

    [67] Akwai matabbata ga dukan labari, kuma za ku sani

    [68] Kuma idan ka ga waɗanda suke kutsawa a cikin ayoyinMu, to, ka bijire daga gare su, sai sun kutsa a cikin wani labari waninsa. Kuma imma dai shaiɗan lalle ya mantar da kai, to, kada ka zauna a bayan tunawa tare da mutane azzalumai

    [69] Kuma babu wani abu daga hisabinsu (masu kutsawa a cikin ayoyin Allah (a kan masu taƙawa amma akwai tunatarwa (a kansu), tsammaninsu (masu kutsawar) za su yi taƙawa

    [70] Kuma ka bar waɗanda suka riƙi addininsu abin wasa da wargi alhali rayuwar duniya ta ruɗe su, kuma ka tunatar game da shi (Alƙur'ani): Kada a jefa raia cikin halaka saboda abin da ya tsirfanta; ba shi da wani majiɓinci baicin Allah, kuma babu wani mai ceto; kuma, ko ya daidaita dukan fansa, ba za a karɓa ba daga gare shi. Waɗancan ne aka yanke wa tsammani saboda abin da suka tsirfanta; suna da wani abin sha daga ruwan zafi, da wata azaba mai raɗaɗi, saboda abin da suka kasance suna yi na kafirci

    [71] Ka ce: "Shin, za mu yi kiran abin da ba ya amfaninmu, baicin Allah, kuma ba ya cutar damu, kuma a mayar da mu a kan dugaduganmu, a bayan Allah Ya shiryar da mu kamar wanda shaiɗanu suka kayar da shi a cikin ƙasa, yana mai ɗimuwa, yana da abokaisuna kiran sa zuwa ga shiriya, 'Ka zo mana'" Kace: "Lalle ne, shiriyar Allah ita ce shiriya. Kuma an umurce mu, mu sallama wa Ubangijin talikai

    [72] Kuma (an ce mana): Ku tsai da salla kuma ku bi shi (Allah) da taƙawa kuma Shi ne wanda Yake zuwa gare Shi ake tara ku

    [73] Kuma Shi ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa da mulkinSa, kuma a Ranar da Yake cewa: "Ka kasance," sai abu ya yi ta kasancewa. MaganarSa ce gaskiya, kuma gare Shi mulki yake a Ranar da ake busa a cikin ƙaho. Masanin fake da bayyane ne, Kuma Shi ne Mai hikima Masani

    [74] Kuma a lokacin da Ibrahima ya ce wa ubansa Azara: "Shin, kana riƙon gumaka abubuwan bautawa? Lalle ni, ina ganin ka kai damuta- nenka, a cikin ɓata bayyananniya

    [75] Kuma kamar wancan ne, Muke nuna wa Ibrahima mulkin sammai da ƙasa, kuma domin ya kasance daga masu yaƙini

    [76] To, a lokacin da dare ya rufe a kansa, ya ga wani tauraro, ya ce: "Wannan ne, ubangijina?" Sa'an nan a lokacin da ya faɗi, ya ce: "Ba ni son masu faɗuwa

    [77] Sa'an nan a lokacin da ya ga wata yana mai bayyana, ya ce: "Wannan ne Ubangijina?" Sa'an nan a lokacin da ya faɗi, ya ce: "Lalle ne idan Ubangijina bai shiryar da ni ba, haƙiƙa, ina kasancewa daga mutane ɓatattu

    [78] Sa'an nan a lokacin da ya ga rana tana bayyana, ya ce: "Wannan shi ne Ubangijina, wannan ne mafi girma?" Sa'an nan a lokacin da ta faɗi, ya ce: "Ya mutanena! Lalle ne ni barrantacce nake daga abin da kuke yi na shirki

    [79] Lalle ne ni, na fuskantar da fuskata ga wanda, Ya ƙaga halittar sammai da ƙasa, ina mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma ba ni cikin masu shirki

    [80] Kuma mutanensa suka yi musu da shi. Ya ce: "Shin kuna musu da ni a cikin sha'anin Allah, alhali kuwa Ya shiryai da ni? Kuma ba ni tsoron abin da kuke yin shirki da shi, face idan Ubangijina Ya so wani abu. Ubangijina Ya yalwaci dukkan kome da ilmi. Shin, ba za ku yi tunani ba

    [81] Kuma yaya nake jin tsoron abin da kuka yi shirki da shi, kuma ba ku tsoron cewa lalle ne ku, kun yi shirki da Allah, abin da (Allah) bai saukar da wata hujja ba game da shi? To, wane ɓangare daga sashen biyu ne mafi cancanta da aminci, idan kun kasance kuna sani

    [82] Waɗanda suka yi imani, kuma ba su gauraya imaninsu da zalunci ba, waɗannan suna da aminci, kuma su ne shiryayyu

    [83] Kuma waccan ita ce hujjarMu, Mun bayar da ita ga Ibrahima a kan mutanensa. Muna ɗaukaka wanda Muka so da darajoji. Lalle ne Ubangijinka Mai hikima ne, Masani

    [84] Kuma Muka ba shi Is'haƙa da Yaƙubu, dukansu Mun shiryar, kuma Nuhu Mun shiryar da shi a gabani, kuma daga zuriyarsa akwai Dawuda da Sulaimanu da Ayyuba, da Yusufu da Musa da Haruna, kuma kamar wancan ne Muke saka wa masu kyautatawa

    [85] Da Zakariyya da Yahaya da Isa da Ilyasu dukansu daga salihai suke

    [86] Da Isma'la da Ilyasa, a da Yunusa da Luɗu, kuma dukansu Mun fifita su a kan talikai

    [87] Kuma daga ubanninsu, da zuriyarsu, da 'yan'uwansu, kuma Muka zaɓe su, kuma Muka shiryar da su zuwa ga hanya madaidaiciya

    [88] Wancan ne shiryarwar Allah, Yana shiryar da wanda Yake so daga bayinSa. Kuma da sun yi shirki da haƙiƙa abin da suka kasance suna, aikatawa ya lalace

    [89] Waɗancan ne waɗanda Muka bai wa Littafi da hukunci da Annabci. To idan waɗannan (mutane) sun kafirta da ita, to, haƙiƙa, Mun wakkala wasu mutane gare ta, ba su zama game da ita kafirai ba

    [90] Waɗancan ne Allah Ya shiryar, saboda haka ka yi koyi da shiryarsu. Ka ce: "Ba ni tambayar ku wata ijara. Shi (Alƙur'ani) bai zama ba face tunatarwa ga talikai

    [91] Kuma ba su ƙaddara Allah a kan hakkin ƙaddara shi ba, a lokacin da suka ce: "Allah bai saukar da kome ba ga wani mutum." Ka ce: "Wane ne ya saukar da Littafi wanda Musa ya zo da shi, yana haske da shiriya ga mutane, kuna sanya shi takardu, kuna bayyana su, kuma kuna ɓoye mai yawa, kuma an sanar da ku abin da ba ku sani ba, ku da ubanninku?" Ka ce: "Allah," sa'an nan ka bar su a cikin sharholiyarsu suna wasa

    [92] Kuma wannan Littafi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, mai gaskata wanda yake a gabansa ne, kuma domin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu (Makka) da wanda yake gefenta. Kuma waɗanda suke yin imani da Lahira suna imani da shi (Alƙur'ani), kuma su, a kan sallarsu, suna tsarewa

    [93] Kuma wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, ko kuwa ya ce: "An yi wahayi zuwa gare ni," alhali kuwa ba a yi wahayin kome ba zuwa gare shi, da wanda ya ce: "zan saukar da misalin abin da Allah Ya saukar?" Kuma da ka gani, a lokacin da azzalumai suke cikin mayen mutuwa, kuma mala'iku suna masu shimfiɗa hannuwansu, (suna ce musu) "Ku fitar da kanku; a yau ana saka muku da azabar wulaƙanci saboda abin da kuka kasance kuna faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma kun kasance daga ayoyinSa kuna yin girman kai

    [94] Kuma lalle ne haƙiƙa, kun zo Mana ɗai ɗai, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lokaci. Kuma kun bar abin da Muka mallaka muku a bayan bayayyakinku, kuma ba Mu gani a tare da ku ba, macetanku waɗanda kuka riya cewa lalle ne su, a cikinku masu tarayya ne. Lalle ne, haƙiƙa, kome ya yanyanke a tsakaninku, kuma abin da kuka kasance kuna riyawa ya ɓace daga gare ku

    [95] Lalle ne, Allah ne Mai tsagewar ƙwayar hatsi da kwalfar gurtsu. Yana fitar da mai rai daga mamaci, kuma (Shi) Mai fitar da mamaci ne daga mai rai, wannan ne Allah. To, yaya ake karkatar da ku

    [96] Mai tsagewar safiya, kuma Ya sanya dare mai natsuwa, kuma da rana da wata a bisa lissafi. vwannan ne ƙaddarawar Mabuwayi Masani

    [97] Kuma Shi ne Ya sanya muku taurari domin ku shiryu da su a cikin duffan tudu da ruwa. Lalle ne Mun bayyana ayoyi daki-daki, ga mutane waɗanda suke sani

    [98] Kuma Shi ne Ya ƙaga halittarku daga rai guda, sa'an nan da mai tabbata da wanda ake ajewa. Lalle ne Mun bayyana ayoyi daki-daki, ga mutane waɗanda suke fahimta

    [99] Kuma Shi ne Ya saukar da ruwa daga sama, Muka fitar da tsiron dukkan kome game da shi, sa'an nan Muka fitar da kore daga gare shi, Muna fitar da kwaya ɗamfararriya daga gare shi (koren), kuma daga dabino daga hirtsinta akwai dumbuje-dumbuje makusanta, kuma (Muka fitar) da gonaki na inabobi da zaituni da rummani, masu kama da juna da wasun masu kama da juna. Ku duba zuwa 'ya'yan itacensa, idan ya yi 'ya'yan, da nunarsa. Lalle ne a cikin wannan akwai ayoyi ga waɗanda suke yin imani

    [100] Kuma suka sanya wa Allah abokan tarayya, aljannu, alhali kuwa (Shi) Ya halitta su. Kuma sun ƙirƙira masa ɗiya da 'ya'ya, ba da ilmi ba. TsarkinSa ya tabbata! Kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke sifantawa

    [101] Mafarin halittar sammai da ƙasa. Yaya ɗa zai zama a gare Shi alhali kuwa mata ba ta kasance ba, a gare Shi, kuma Ya halitta dukkan, kome, kuma Shi, game da dukan kome, Masani ne

    [102] Wancan ne Allah Ubangijinku. Babu wani abin bautawa face Shi, Mahaliccin dukan kome. Saboda haka ku bauta Masa kuma Shi ne wakili a kan dukan, kome

    [103] Gannai ba su iya riskuwarSa, kuma Shi Yana riskuwar gannai, kuma Shi ne Mai tausasawa, Masani

    [104] Lalle ne abubuwan lura sun je muku daga Ubangijinku, to, wanda ya kula, to, domin kansa, kuma wanda ya makanta, to, laifi yana a kansa, kuma ni, a kanku, ba mai tsaro ba ne

    [105] Kamar wannan ne Muke sarrafa ayoyi, kuma domin su ce: "Ka karanta!" Kuma domin Mu bayyana shi ga mutane waɗanda suna sani

    [106] Ka bi abin da aka yi wahayi zuwa gare ka daga Ubangijinka; babu wani abin bautawa face Shi, kuma ka bijire daga masu shirki

    [107] Kuma da Allah Ya so, da ba su yi shirki ba, kuma ba Mu, sanya ka mai tsaro a kansu ba, kuma ba kai ne wakili a kansu ba

    [108] Kuma kada ku zagi waɗanda suke kira, baicin Allah, har su zagi Allah bisa zalunci, ba, da ilmi ba. Kamar wannan ne Muka ƙawata ga kowace al'umma aikinsu, sa'an nan zuwa ga Ubangijinsu makomarsu take, sa'an nan Ya ba su labari da abin da suka kasance suna aikatawa

    [109] Kuma suka yi rantsuwa da Allah iyakar rantsuwoyinsu (cewa) lalle ne idan wata aya ta jemusu, haƙiƙa, suna yin imani da ita. Ka ce: "Abin sani kawai, ayoyi a wurin Allah suke. Kuma mene nezai sanya ku ku sansance cewa, lalle ne su, idan ayoyin sun je, ba za su yi imani ba

    [110] Kuma Muna jujjuya zukatansu da ganansu, kamar yadda ba su yi imani da shi ba a farkon lokaci kuma Muna barin su a cikin kutsawarsu, suna ɗimuwa

    [111] Kuma da a ce, lalle Mu Mun saukar da Mala'iku zuwa gare su, kuma matattu suka yi musu magana, kuma Muka tara dukkan kome a kansu, gungu-gungu, ba su kasance suna iya yin imani ba, sai fa idan Allah Ya so, Kuma amma mafi yawansu suna jahiltar haka

    [112] Kuma kamar wancan ne Muka sanya wa kowane Annabi maƙiyi; shaiɗanun mutane da aljannu, sashensu yana yin ishara zuwa sashe da ƙawataccen zance bisa ga ruɗi. Kuma da Ubangijinka Ya so, da ba su aikata shi ba, don haka ka bar su da abin da, suke ƙirƙirawa

    [113] Kuma domin zukatan waɗanda ba su yi imani da Lahira ba su karkata saurare zuwa gareshi, kuma domin su yarda da shi, kuma domin su kamfaci abin da suke masu kamfata

    [114] Shin fa, wanin Allah nake nema ya zama mai hukunci, alhali kuwa Shi ne wanda Ya saukar muku da Littafi abin rabewadaki-daki? Kuma waɗanda Muka bai wa Littafi suna sanin cewa lalleshi (Alƙur'ani) abin saukarwa ne daga Ubangijinka, da gaskiya? Saboda haka kada ku kasance daga masu shakka

    [115] Kuma kalmar Ubangijinka ta cika, tana gaskiya da adalci. Babu mai musanyawa ga kalmominSa, kuma Shi ne Maiji, Masani

    [116] Kuma idan ka bi mafiya yawan waɗanda suke a cikin ƙasa da ɗa'a suna ɓatar da kai daga hanyar Allah. Ba su bin kome sai face ƙaddari-faɗi suke yi

    [117] Lalle ne Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda yake ɓacewa daga hanyarsa kuma Shi ne mafi sani ga masu shiryuwa

    [118] Saboda haka ku ci daga abin da aka ambaci sunan Allah kansa, idan kun kasance masu imani da ayoyinSa

    [119] Kuma mene ne ya same ku, ba za ku ci ba daga abin da aka ambaci sunan Allah a kansa, alhali kuwa, haƙiƙa, Ya rarrabe, muku daki-daki, abin da Ya haramta a kanku, face fa abin da aka bukatar da ku bisa lalura zuwa gare shi? Kuma lalle ne masu yawa suna ɓatarwa, da son zuciyoyinsu, ba da wani ilmi ba. Lalle ne Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga masu ta'addi

    [120] Kuma ku bar bayyanannen zunubi da ɓoyayyensa. Lalle ne waɗanda suke tsiwurwurin zunubi za a saka musu da abin da suka kasance suna kamfata

    [121] Kada ku ci daga abin da ba a ambaci sunan Allah ba a kansa. Kuma lalle ne shi fasiƙanci ne. Kuma lalle ne, shaiɗanu, haƙiƙa, suna yin ishara zuwa ga masoyansu, domin su yi jayayya da ku. Kuma idan kuka yi musu ɗa'a, lalle ne ku, haƙiƙa, masu shirki ne

    [122] Shin, kuma wanda ya kasance matacce sa'an nan Muka rayar da shi, kuma Muka sanya wani haske dominsa, yana tafiya da shi, yana zama kamar wanda misalinsa yana cikin duffai, shi kuma ba mai fita ba daga gare su? Kamar wancan ne aka ƙawata wa kafirai abin da suka kasance suna aikatawa

    [123] Kuma kamar wancan ne Mun sanya a cikin kowace alƙarya, shugabanni su ne masu laifinta domin su yi makirci a cikinta, alhali kuwa ba su yin makirci face ga rayukansu, kuma ba su sansancewa

    [124] Kuma idan wata aya ta je musu sai su ce: "Ba za mu yi imani ba, sai an kawo mana kamar abin da aka kawo wa manzannin Allah." Allah Mafi sanin inda Yake sanya manzancinSa. Wani wulaƙanci a wurin Allah da wata azaba mai tsanani za su sami waɗanda suka yi laifi, saboda abin da suka kasance suna yi na makirci

    [125] Domin haka wanda Allah Ya yi nufin ya shiryar da shi sai ya buɗa ƙirjinsa domin Musulunci, kuma wanda Ya yi nufin Ya ɓatar da shi, sai Ya sanya ƙirjinsa mai ƙunci matsattse, kamar dai yana takawa ne a ckin sama. Kamar wannan ne Allah Yake sanyawar ƙazanta a kan waɗanda ba su yin imani

    [126] Wannan ita ce hanya ta Ubangijinka madaidaiciya. Lalle ne Mun bayyana ayoyi daki-daki ga mutane masu karɓar tunatarwa

    [127] Suna da gidan aminci a wurin Ubangjinsu, kuma Shi ne Majiɓincinsu, saboda abin da suka kasance suna aikatawa

    [128] Kuma ranar da yake tara su gaba ɗaya (Yana cewa): "Ya jama'ar aljannu! Lalle ne kun yawaita kanku daga mutane." Kuma majiɓantansu daga mutane suka ce: "Ya Ubangjinmu! Sashenmu ya ji daɗi da sashe, kuma mun kai ga ajalinmu wanda Ka yanka mana!" (Allah) Ya ce: "Wuta ce mazaunarku, kuna madawwama acikinta, sai abin da Allah Ya so. Lalle ne Ubangijinka Mai hikima ne, Masani

    [129] Kuma kamar wancan ne Muke jiɓintar da sashen azzalumai ga sashe, saboda abin da suka kasance suna tarawa

    [130] Ya jama'ar aljannu da mutane! Shin, manzanni daga gare ku ba su je muku ba suna labarta ayoyiNa a kanku, kuma suna yi muku gargaɗin haɗuwa da wannan yini naku? Suka ce: "Mun yi shaida a kan kawunanmu." Kuma rayuwar duniya ta ruɗe su. Kuma suka yi shaida a kan kawunansu cewa lalle ne su, sun kasance kafirai

    [131] Wanan kuwa saboda Ubangijinka bai kasance Mai halaka alƙaryoyi saboda wani zalunci ba ne, alhali kuwa mutanensu suna jahilai

    [132] Kuma ga kowanne, akwai darajoji daga abin da suka aikata. Kuma Ubangijinka bai zama mai shagala ba daga abin da suke aikatawa

    [133] Kuma Ubangijinika Wadatacce ne Ma'abucin rahama. Idan Ya so zai tafi da ku, kuma Ya musanya daga bayanku, abin da Yake so, kamar yadda Ya ƙaga halittarku daga zuriyar wasu mutane na dabam

    [134] Lalle ne abin da ake yi muku wa'adi lalle mai zuwa ne kuma ba ku zama masu buwaya ba

    [135] Ka ce: "Ya ku mutanena! Ku yi aiki a kan halinku, lalle ne ni mai aiki ne, sa'an nan da sannu za ku san wanda aƙibar gida za ta kasance a gare shi. Lalle ne shi, azzalumai ba za su ci nasara ba

    [136] Kuma sun sanya wani rabo ga Allah daga abin da Ya halitta daga shuka da dabbobi, sai suka ce: "Wannan na Allah ne," da riyawarsu "Kuma wannan na abubuwan shirkinmu ne." Sa'an nan

    [137] Kuma kamar wancan ne abubuwan shirkinsu suka ƙawata wa masu yawa, daga masu shirkin; kashewar 'ya'yansu, domin su halaka su kuma domin su rikitar da addininsu a gare su, Kuma da Allah Ya so da ba su aikata shi ba. Saboda haka ka bar su da abin da suke ƙirƙirawa

    [138] Kuma sukace: "Waɗannan dabbobi da shuka hanannu ne; babu mai ɗanɗanar su face wanda muke so," ga riyawarsu. Da wasu dabbobi an hana bayayyakinsu, da wasu dabbobi ba su ambatar sunan Allah a kansu, bisa ƙirƙiren ƙarya gare Shi. Zai saka musu da abin da suka kasance suna ƙirƙirawa

    [139] Kuma suka ce: "Abin da yake a cikin cikkunan waɗannan dabbobi keɓantacce ne ga mazanmu, kuma hananne ne a kan matan aurenmu. Kuma idan ya kasance mushe, to, a cikinsa su abokan tarayya ne, zai saka musu sifantawarsu. Lalle ne Shi, Mai hikima ne, Masani

    [140] Lalle ne waɗanda suka kashe ɗiyansu saboda wauta, ba da ilmi ba, sun yi hasara! Kuma suka haramta abin da Allah Ya azurta su, bisa ƙirƙira ƙarya ga Allah. Lalle ne sun ɓace, kuma ba su kasance masu shiryuwa ba

    [141] Kuma Shi ne Wanda Ya ƙaga halittar gonaki masu rumfuna da wasun masu rumfuna da dabinai da shuka, mai saɓawa ga 'ya'yansa na ci, da zaituni da rummani mai kama da juna da wanin mai kama da juna. Ku ci daga 'ya'yan itacensa, idan ya yi 'ya'yan, kuma ku bayar da hakkinSa a ranar girbinsa, kuma kada ku yi ɓarna. Lalle ne Shi, ba Ya son mafarauta

    [142] Kuma daga dabbobi (Ya ƙaga halittar) mai ɗaukar kaya da ƙanana; Ku ci daga abin da Allah Ya azurta ku, kuma kada ku bi zambiyoyin shaiɗan: LalLe ne shi, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne

    [143] Nau'o'i takwas daga tumakai biyu, kuma daga awakai biyu; ka ce: Shin mazan biyu ne Ya haramta ko matan biyu, ko abin da mahaifar matan biyu suka tattara a kansa? Ku ba ni labari da ilmi, idan kun kasance masu gaskiya

    [144] Kuma daga raƙuma akwai nau'i biyu, kuma daga shanu biyu; ka ce: Shin, mazan biyu ne Ya hana ko matan biyu Ya hana, ko abin da mahaifar matan biyu suka tattara a kansa? Ko kun kasance halarce ne a lokacin da Allah Ya yi muku wasiyya da wannan? To, wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, domin ya ɓatar da mutane ba da wani ilmi ba? Lalle ne, Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [145] Ka ce: "Ba ni samu, a cikin abin da aka yo wahayi zuwa gare Ni, abin haramtawa a kan wani mai ci wanda yake cin sa face idan ya kasance mushe ko kuwa jini abin zubarwa ko kuwa naman alade, to lalle ne shi ƙazanta ne, ko kuwa fasiƙanci wanda aka kururuta, domin wanin Allah da shi." Sa'an nan wanda larura ta kama shi, ba mai fita jama'a ba, kuma ba mai ta'addi ba, to, lalle Ubangijinka Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [146] Kuma a kan waɗanda suka tuba (Yahudu) Mun haramta dukan mai akaifa, kuma daga shanu da bisashe Mun haramta musu kitsattsansu face abin da bayukansu suka ɗauka, ko kuwa kayan ciki, ko kuwa abin da ya garwaya da ƙashi wannan ne Muka saka musu saboda zaluncinsu, kuma Mu, haƙiƙa, Masu gaskiya ne

    [147] To, idan sun ƙaryata ka, sai ka ce: "Ubangijinku Ma'abucin rahama ne Mai yalwa; kuma ba a mayar da azabarSa daga mutane masu laifi

    [148] Waɗanda suka yi shirki za su ce: "Da Allah Ya so da ba mu yi shirki ba, kuma da ubanninmu ba su yi ba, kuma da ba mu haramta wani abu ba." Kamar wannan ne mutanen da suke a gabaninsu suka ƙaryata, har suka ɗanɗani azabarMu. Ka ce: "Shin, kuna da wani ilmi a wurinku domin ku fito mana da shi? Ba ku bin kome face zato kuma ba ku zama ba face ƙiri-faɗi kawai kuke yi

    [149] Ka ce: "To Allah ne da hujja isasshiya, saboda haka: Da Ya so, da Ya shiryar da ku gaba ɗaya

    [150] Ka ce: "Ku kawo shaidunku, waɗanda suke bayar da shaidar cewa Allah ne Ya haramta wannan." To idan sun kawo shaida kada ka yi shaida tare da su. Kuma kada ka bi son zuciyoyin waɗanda suka ƙaryata, game da ayoyinMu, da waɗanda ba su yin imani da Lahira, alhali kuwa su daga Ubangijinsu suna karkacewa

    [151] Ka ce: "Ku zo, in karanta abin da Ubangijinku Ya haramta." wajibi ne a kanku kada ku yi shirkin kome da Shi, kuma ga mahaifa biyu (ku kyautata) kyautatawa, kuma kada ku kashe ɗiyanku saboda talauci, Mu ne Muke azurta ku, ku da su, kuma kada ku kusanci abubuwa alfasha, abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya ɓoyu, kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta, face da hakki. Wannan ne (Allah) Ya yi muku wasiyya da Shi: Tsammaninku, kuna hankalta

    [152] Kada ku kusanci dukiyar maraya face da wadda take ita ce mafi kyau, har ya kai ga ƙarfinsa. Kuma ku cika mudu da sikeli da adalci, ba Mu kallafa wa rai face iyawarsa. Kuma idan kun faɗi magana, to, ku yi adalci, kuma ko da ya kasance ma'abucin zumunta ne. Kuma da alkawarin Allah ku cika. wannan ne Ya yi muku wasiyya da shi: Tsammaninku, kuna tunawa

    [153] Kuma lalle wannan ne tafarkiNa, yana madaidaici: Sai ku bi shi, kuma kada ku bi wasu hanyoyi, su rarrabu da ku daga barin hanyaTa. Wannan ne Allah Ya yi muku wasiyya da shi tsammaninku, kuna yin taƙawa

    [154] Sa'an nan kuma Mun bai wa Musa Littafi, yana cikakke bisa ga wanda ya kyautata (hukuncin Allah) da rarrabewa, daki-daki, ga kowane abu, da shiriya da rahama, tsammaninsu, suna yin imani da haɗuwa da Ubangijinsu

    [155] Kuma wannan Littafi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, sai ku bi shi kuma ku yi taƙawa, tsammaninku, ana jin ƙanku

    [156] (Domin) kada ku ce: "Abin sani kawai, an saukar da littafi a kan ƙungiya biyu daga gabaninmu, kuma lalle ne mu, mun kasance, daga karatunsu, haƙiƙa, gafilai

    [157] Ko kuwa ku ce: "Da dai lalle mu an saukar da Littafi a kanmu, haƙiƙa, da mun kasance mafiya, shiryuwa daga gare su." To, lalle ne wata hujja bayyananniya, daga Ubangijinku, ta zo muku, da shiriya da rahama. To, wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙaryata game da ayoyin Allah, kuma ya finjire daga barinsu? Za Mu saka wa waɗanda suke finjirewa daga barin ayoyinMu da mugunyar azaba, saboda abin da suka kasance suna yi na hinjirewa

    [158] Shin, suna jiran (wani abu), face dai mala'iku su je musu ko kuwa Ubangijinka Ya je, ko kuwa sashen ayoyin Ubangijinka ya je. A ranar da sashen ayoyin Ubangijinka yake zuwa, imanin rai wanda bai kasance ya yi imanin ba a gabani, ko kuwa ya yi tsiwirwirin wani alheri, ba ya amfaninsa. Ka ce: "Ku yi jira: Lalle ne mu, masu jira ne

    [159] Lalle ne waɗanda suka rarraba addininsu, kuma suka kasance ƙungiya-ƙungiya, kai ba ka zama daga gare su ba, a cikin kome: abin sani kawai al'amarinsu zuwa ga Allah yake. Sa'an nan Ya ba su labari game da abin da suka kasance suna aikatawa

    [160] Wanda ya zo da kyakkyawan aiki guda, to, yana da goma ɗin misalansa. Kuma wanda ya zo da mugun aiki guda, to, ba za a saka masa ba face da misalinsa. Kuma su ba a zaluntar su

    [161] Ka ce: "Lalle ni, Ubangijina Ya shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, addini, ƙimantawa (ga abubuwa), mai aƙidar Ibrahim, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga masu shirki ba

    [162] Ka ce: "Lalle ne sallata, da baikona, da rayuwata, da mutuwata, na Allah ne Ubangijin talikai

    [163] Babu abokin tarayya a gare Shi. Kuma da wancan aka umurce ni, kuma ni ne farkon masu sallamawa

    [164] Ka ce: "Shin wanin Allah nake nema ya zama Ubangiji, alhali kuwa Shi ne Ubangijin dukan kome? Kuma wani rai ba ya yin tsirfa face domin kansa, kuma mai ɗaukar nauyi, ba ya ɗaukar nauyin wani, sa'an nan kuma komawarku zuwa ga Ubangijinku take; Sa'an nan Ya ba ku labari ga abin da kuka kasance, a cikinsa, kuna saɓa wa juna

    [165] Kuma Shi ne wanda Ya sanya ku masu maye wa junaga ƙasa. Kuma Ya ɗaukaka sashenku bisa ga sashe da darajoji; domin Ya jarraba ku a cikin abin da Ya ba ku." Lalle ne, Ubangijinka Mai gaggawar uƙkuba ne, kuma lalle ne Shi, haƙiƙa, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    Tsãwãwon Ganuwa

    Surah 7

    [1] L. M. S

    [2] Littafi ne aka saukar zuwa gare ka, kada wani ƙunci ya kasance a cikin ƙirjinka daga gare shi, domin ka yi gargaɗi da shi. Kuma tunatarwa ne ga muminai

    [3] Ku bi abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku, kuma kada ku dinga bin wasu majiɓinta baicinSa. Kaɗan ƙwarai kuke tunawa

    [4] Kuma da yawa wata alƙarya Muka halaka ta, sai azabarMu ta je mata da dare ko kuwa suna masu ƙailula

    [5] Sa'an nan babu abin da yake da'awarsu, a lokacin da azabarMu ta je musu, face suka ce: "Lalle ne mu muka kasance masu zalunci

    [6] Sa'an nan lalle ne Muna tambayar waɗanda aka aika zuwa gare su, kuma lalle Muna tambayar Manzannin

    [7] Sa'an nan haƙiƙa Muna ba su labari da ilmi kuma ba Mu kasance masu fakowa ba

    [8] Kuma awo a ranar nan ne gaskiya. To, wanda sikelansasuka yi nauyi, to, waɗannan su ne masu cin nasara

    [9] Kuma wanda sikelansa suka yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu, saboda abin da suka kasance, da ayoyinMu, suna yi na zalunci

    [10] Kuma lalle ne haƙiƙa, Mun sarautar da ku, a cikin ƙasa, kuma Mun sanya muku abubuwan rayuwa, a cikinta; kaɗan ƙwarai kuke godewa

    [11] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun halitta ku sa'an nan kuma Mun suranta ku, sa'an nan kumaMun ce wa mala'iku: "Ku yi sujada ga Adam." Sai suka yi sujada face Iblis, bai kasance daga masuyin sujadar ba

    [12] Ya ce: "Mene ne ya hana ka, ba ka yi sujada ba, alokacin da Na umurce ka?" Ya ce: "Ni ne mafifici daga gare shi, Ka halitta ni daga wuta alhali kuwa Ka halitta shi daga laka

    [13] Ya ce: "To, ka sauka daga gare ta; domin ba, ya kasancewa a gare ka ga ka yi girman kai a cikinta. Sai ka fita. Lalle ne kana daga masu ƙasƙanci

    [14] Ya ce: "Ka yi mini jinkiri zuwa ga ranar da ake tayar da su

    [15] Ya ce: "Lalle ne, kana daga waɗanda aka yi wa jinkiri

    [16] Ya ce: "To ina rantsuwa da halakarwar da Ka yi mini, lalle ne, ina zaune musu tafarkinKa madaidaici

    [17] Sa'an nan kuma haƙiƙa, Ina je musu daga gaba gare su, kuma daga baya gare su, kuma daga jihohin damansu da jihohin hagunsu; Kuma ba za ka sami mafi yawansu masu godiya ba

    [18] Ya ce: "Ka fita daga gare ta kana abin zargi korarre. Lalle ne wanda ya bi ka daga gare su, haƙiƙa, za Ni cika jahannama daga gare ku, gaba ɗaya

    [19] Kuma ya Adam! Ka zauna kai da matarka a Aljanna sai ku ci daga inda kuka so; kuma kada ku kusanci wannan itaciya, har ku kasance daga azzalumai

    [20] Sai Shaiɗan ya sanya musu waswasi domin ya bayyana musu abin da aka rufe daga barinsu, daga al'aurarsu, kuma ya ce: "Ubangijinku bai hana ku daga wannan itaciya ba face domin kada ku kasance mala'iku biyu ko kuwa ku kasance daga madawwama

    [21] Kuma ya yi musu rantsuwa; Lalle ne ni, a gare ku, haƙiƙa, daga masu nasiha ne

    [22] Sai ya saukar da su da ruɗi. Sa'an nan a lokacin da suka ɗanɗani itaciyar, al'aurarsu ta bayyana gare su, kuma suka shiga suna liƙawar ganye a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Ubangjinsu Ya kira su: "Shin, Ban hana ku ba daga waccan itaciya, kuma Na ce muku lalle ne Shaiɗan, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne

    [23] Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Mun zalunci kanmu. Kuma idan ba Ka gafarta mana ba, kuma Ka yi mana rahama, haƙiƙa, Muna kasancewa daga masu hasara

    [24] Ya ce: "Ku sauka, sashenku zuwa ga sashe yana maƙiyi, kuma kuna da matabbata a cikin ƙasa, da ɗan jin daɗi zuwa ga wani lokabi

    [25] Ya ce: "A cikinta kuke rayuwa, kuma a cikinta kuke mutuwa, kuma daga gare ta ake fitar da ku

    [26] Ya ɗiyan Adam! Lalle ne Mun saukar da wata tufa a kanku, tana rufe muku al'aurarku, kuma da ƙawa. Kuma tufar taƙawa wancan ce mafi alheri. Wancan daga ayoyin Allah ne, tsammaninsu suna tunawa

    [27] Ya ɗiyan Adam! Kada Shaiɗan, lalle, ya fitine ku, kamar yadda ya fitar da iyayenku, biyu daga Aljanna, yana fizge tufarsu daga gare su, domin ya nuna musu al'aurarsu. Lalle ne shi, yana ganin ku, shi da rundunarsa, daga inda ba ku ganin su. Lalle ne Mu, Mun sanyaShaiɗan majiɓinci ga waɗanda ba su yin imani

    [28] Kuma idan suka aikata alfasha su ce: "Mun sami ubanninmu akanta." Kuma Allah ne Ya umurce mu da ita."Ka ce: "Lalle ne, Allah ba Ya umurni da alfasha. Shin kuna faɗar abin da ba ku da saninsa ga Allah

    [29] Ka ce: "Ubangjina Ya yi umurni da adalci; kuma ku tsayar da fuskokinku a wurin kowane masallaci, kuma ku roƙe Shi, kuna masu tsarkake addini gare Shi. Kamar yadda Ya fara halittarku kuke komawa

    [30] Wata ƙungiya (Allah) Ya shiryar, kuma wata ƙungiya ɓata ta wajaba a kansu; lalle ne su, sun riƙi shaiɗanu majiɓinta, baicin Allah, kuma suna zaton, lalle su, masu shiryuwa ne

    [31] Ya ɗiyan Adam! Ku riƙi ƙawarku a wurin kowane masallaci kuma ku ci, kuma ku sha; Kuma kada ku yi ɓarna. Lalle ne Shi (Allah), ba Ya son masu ɓarna

    [32] Ka ce: "Wane ne ya haramta ƙawar Allah, wadda Ya fitar saboda bayinSa, da masu daɗi daga abinci?" Ka ce: "Su, domin waɗanda suka yi imani suke a cikin rayuwar duniya, suna keɓantattu a Ranar Kiyama. "Kamar wannan ne Muke bayyana ayoyi, daki-daki, ga mutanen da suke sani

    [33] Ka ce: "Abin sani kawai, Ubangijina Ya hana abubuwanalfasha; abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya ɓoyu, da zunubi da rarraba jama'a, ba da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da bai saukar da wani dalili ba gare shi, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba, ga Allah

    [34] Kuma ga kowace al'umma akwai ajali. Sa'an nan idan ajalinsu ya je, ba za a yi musu jinkiri ba, sa'a guda, kuma ba za su gabace shi ba

    [35] Ya ɗiyan Adam! Ko dai wasu manzanni, daga cikinku, su je muku, suna gaya muku ayoyiNato, wanda ya yi taƙawa, kuma ya gyara aikinsa, to, babu tsoro a kansu, kuma ba su yin baƙin ciki

    [36] Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ayoyinMu, kuma suka yi girman kai daga gare su, waɗannan su ne abokan wuta, su, a cikinta madawwama ne

    [37] To, wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, ko kuwa ya ƙaryata game da ayoyinSa? Waɗannan rabonsu daga Littafi yana samunsu, har a lokacin da ManzanninMu suka je musu, suna karɓar rayukansu, su ce: "Ina abin da kuka kasance kuna kira, baicin Allah?" Su ce: "Sun ɓace daga gare mu, "Kuma su yi shaida a kansu cewa lalle su, sun kasance kafirai

    [38] Ya ce: "Ku shiga a cikin al'ummai waɗanda, haƙiƙa, sun shige daga gabaninku, daga aljannu da mutane, a cikin Wuta. A ko da yaushe wata al'umma ta shiga sai ta la'ani 'yar'uwarta, har idan suka riski juna, a cikinta, gaba ɗaya, ta ƙarshensu ta ce wa ta farkonsu: "Ya Ubangijinmu! Waɗannan ne suka ɓatar da mu, sai Ka kawo musu azaba ninki daga wuta." Ya ce: "Ga kowane akwai ninki; kuma amma ba ku sani ba

    [39] Kuma ta farkonsu ta ce wa ta ƙarshe: "To, ba ku da wata falala a kanmu, sai ku ɗanɗana azaba saboda abin da kuka kasance kuna tarawa

    [40] Lalle ne waɗanda suka ƙaryata game da ayoyinMu, kuma suka yi girman kai daga barinsu, ba za a bubbuɗe musu kofofin sama ba, kuma ba su shiga Aljanna sai raƙumi ya shiga kafar allura, kuma kamar wannan ne Muke saka wa masu laifi

    [41] Suna da wata shimfiɗa daga Jahannama kuma daga samansu akwai wasu murafai. Kuma kamar wancan ne Muke saka wa azzalumai

    [42] Kuma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, ba Mu ƙallafa wa rai face iyawarsa, Waɗannan ne abokan Aljanna, su, a cikinta, madawwma ne

    [43] Kuma Muka fitar da abin da yake a cikin ƙirazansu, daga ƙiyayya, ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, kuma suka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah, wanda Ya shiryar da mu ga wannan. Kuma ba mu kasance muna iya shiryuwa ba, ba domin Allah Ya shiryar da mu ba. Lalle ne haƙiƙa, Manzannin Ubangjinmu, sun je mana da gaskiya." Kuma aka kira su, cewa: "Waccan Aljlnna an gadar da ku ita, saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [44] Kuma 'yan Aljanna suka kirayi 'yan Wuta suka ce: "Lalle ne mun sami abin da Ubangijinmu Ya yi mana wa'adi, gaskiya ne. To, shin, kun sami abin da Ubangijinku Ya yi muku wa'adi, gaskiya?" Suka ce: "Na'am." Sai mai sanarwa ya yi yekuwa, cewa: "La'anar Allah ta tabbata a kan azzalumai

    [45] Waɗanda suke kangewa daga hanyar Allah, kuma suna neman ta ta zama karkatacciya,. kuma su, game da Lahira, kafirai ne

    [46] Kuma a tsakaninsu akwai wani shamaki, kuma a kan A'araf akwai wasu maza suna sanin kowa da alamarsu; Kuma suka kirayi abokan Aljamia cewa: "Aminci ya tabbata a kanku: "Ba su shige ta ba, alhali kuwa su, suna tsammani

    [47] Kuma idan an juyar da gannansu wajen abokan wuta, su ce: "Ya Ubangijinmu! Kada Ka sanya mu tare da mutane azzalumai

    [48] Kuma abokan A'araf suka kirayi wasu maza, suna sanin su da alamarsu, suka ce: "Tarawar dukiyarku da abin da kuka kasance kuna yi na girman kai, bai wadatar ba daga barinku

    [49] Shin, waɗannan ne waɗanda kuka yi rantsuwa, Allah ba zai same su da rahama ba? Ku shiga Aljanna, babu tsoro akanku, kuma ba ku zama kuna baƙin ciki ba

    [50] Kuma 'yan wuta suka kirayi 'yan Aljanna cewa: "Ku zubo a kaumu daga ruwa ko kuwa daga abin da Allah Ya azurta ku." Su ce: "Lalle ne Allah Ya haramta su a kan kafirai

    [51] Waɗanda suka riƙi addininsu abin shagala da wasa, kuma rayuwar duniya ta ruɗe su." To, a yau Muna mantawa da su, kamar yadda suka manta da haɗuwa da yininsu wannan, da kuma abin da suka kasance da ayoyinMu suna musu

    [52] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun je musu da Littafi, Mun bayyana Shi, daki-daki, a kan ilmi, yana shiriya da rahama ga mutane waɗanda suke yin imani

    [53] Shin, suna jira, face fassararsa, a ranar da fassararsa take zuwa, waɗanda saka manta da Shi daga gabani, suna cewa: "Lalle ne, Manzannin Ubangijin mu svun je da gaskiya. To, shin, muna da wasu masu ceto, su yi ceto gare mu, ko kuwa a mayar da mu, har mu aikata wanin wanda muka kasance muna aikatawa?" Lalle ne sun yi hasarar rayukansu, kuma abin da suka kasance suna ƙirƙirawa ya ɓace musu

    [54] Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin kwanaki shida, sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, Yana sanya dare ya rufa yini, yana neman sa da gaggawa, kuma rana da wata da taurari horarru ne da umurninSa. To, Shi ne da halittar kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu ta bayyana

    [55] Ku kirayi Ubangijinku da ƙanƙan da kai, da kuma a ɓoye: lalle ne Shi, ba Ya son masuwuce iyaka

    [56] Kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa a bayan gyaranta. Kuma ku kiraye shi saboda tsoro da tsammani; lalle ne rahamar Allah makusanciya ce daga masu kyautatawa

    [57] Kuma Shi ne wanda Yake aika iskoki, suna bishara gaba ga rahamarSa, har idan sun ɗauki gizagizai masu nauyi, sai Mu kora su ga wani gari matacce, sa'an nan Mu saukar da ruwa gare shi, sa'an nan Mu fitar, game da shi, daga dukkan 'ya'yan itice. Kamar wancan ne Muke fitar da matattu; tsammaninku, kuna tunani

    [58] Kuma gari mai kyau, tsirinsa yana fita da iznin Ubangijinsa, kuma wanda ya munana, (tsirinsa) ba ya fita, face da wahala; kamar wannan ne, Muka sarrafa ayoyi domin mutane waɗanda suke godewa

    [59] Lalle ne, haƙiƙa Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta waAllah! Ba ku da wani abin bautawa waninSa. Lalle ne ni, ina yimuku tsoron azabar wani Yini mai girma

    [60] Mashawarta daga mutanensa suka ce: "Lalle ne mu, haƙiƙa, Muna ganin ka a cikin ɓata bayyananniya

    [61] Ya ce: "Ya mutanena! Babu ɓata guda gare ni, kuma amma ni Manzo ne daga ubangijin halittu

    [62] Ina iyar muku da saƙonnin Ubangijina; kuma ina yi muku nasiha, kuma ina sani, daga Allah, abin da ba ku sani ba

    [63] Shin, kuna mamakin cewa ambato ya zo muku daga Ubangijinku a kan wani namiji, daga gare ku, domin ya yi muku gargaɗi, kuma domin ku yi taƙawa, kuma tsammaninku ana jin ƙanku

    [64] Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan Muka tsirar da shi da waɗanda suke tare da shi, a cikin jirgin; kuma Muka nutsar da waɗanda suka ƙaryata shi game da ayoyinMu. Lalle ne su, sun kasance wasu mutane ɗimautattu

    [65] Kuma zuwa ga Adawa, ɗan'uwansu Hudu, ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta wa Allah! Ba ku da wani abin bauta wa, waninSa. Shin fa, ba za ku yi taƙawa ba

    [66] Mashawarta waɗanda suka kafirta daga mutanensa suka ce: "Lalle ne mu, haƙiƙka, Muna ganin ka a cikin wata wauta! Kuma lalle ne mu, haƙiƙa, Muna zaton ka daga maƙaryata

    [67] Ya ce: "Ya mutanena! Babu wata wauta a gare ni, kuma amma ni, Manzo ne daga Ubangijin halittu

    [68] Ina iyar muku da saƙonnin Ubangijina, kuma ni, gare ku, mai nasiha ne amintacce

    [69] Shin, kuma kun yi mamaki cewa ambato daga Ubangijinku ya zo muku a kan wani namiji daga gare ku, domin ya yi muku gargaɗi? Kuma ku tuna a lokacin da Ya sanya ku masu mayewa daga bayan mutanen Nuhu, kuma Ya ƙara muku zati a cikin halitta. Saboda haka ku tuna ni'imomin Allah; tsammaninku kuna cin nasara

    [70] Suka ce: "Shin, ka zo mana ne domin mu bauta wa Allah Shi kaɗai, kuma mu bar abin da ubanninmu suka kasance suna bauta wa? To, ka zo mana da abin da kake yi mana wa'adi da shi idan ka kasance daga masu gaskiya

    [71] Ya ce: "Haƙiƙa azaba da fushi sun auku a kanku daga Ubangijinku! Shin, kuna jayayya da ni a cikin wasu sunaye waɗanda ku ne kuka yi musu sunayen, ku da ubanninku, Allah bai saukar da wani dalili ba a gare su? To, ku yi jira. Lalle ne ni, tare da ku mai jira ne

    [72] To, sai Muka tsirar da shi, shi da waɗanda suke tare da shi saboda wata rahama daga gare Mu, kuma Muka katse ƙarshen waɗanda suka ƙaryata game da ayoyinMu, kuma ba su kasance muminaiba

    [73] Kuma zuwa ga Samudawa ɗan'uwansu, Salihu, ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta wa Allah; ba ku da wani abin bauta wa wanninSa. Haƙiƙa hujja bayyananniya ta zo muku daga Ubangijinku! wannan raƙumar Allah ce, a gare ku, wata aya ce. Sai ku bar ta ta ci, a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shafe ta da wata cuta har azaba mai raɗaɗi ta kama ku

    [74] Kuma ku tuna a lokacin da Ya sanya ku mamaya daga bayan Adawa kuma Ya zaunar da ku a cikin ƙasa, kuna riƙon manyan gidaje daga tuddanta, kuma kuna sassaƙar ɗakuna daga duwatsu; saboda haka ku tuna ni'imomin Allah, kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa kuna masu fasadi

    [75] Mashawarta waɗanda suka yi girman kai daga mutanensa suka ce ga waɗanda aka raunanar, ga waɗanda suka yi imani daga gare su: "Shin, kuna sanin cewaSalihu manzo ne daga Ubangijinsa?" Suka ce: "Lalle ne mu, da abin daaka aiko shi, masu imani ne

    [76] Waɗanda suka yi girman kai suka ce: "Lalle ne mu, ga abin da kuka yi imani da shi kafirai ne

    [77] Sai suka soke raƙumar, kuma suka kangare daga barin umurnin Ubangijinsu, kuma suka ce: "Ya Salihu! Ka zo mana da abin da kake yi mana wa'adi da shi, idan ka kasance daga manzanni

    [78] Sai tsawa ta kama su, saboda haka suka wayi gari a cikin gidansu guggurfane

    [79] Sai ya juya daga barinsu, kuma ya ce: "Ya mutanena! Lalle ne, haƙiƙa, na iyar muku damanzancin Ubangijina. Kuma na yi muku nasiha kuma amma ba ku son masu nasiha

    [80] Da Luɗu, a lokacin daya ce wa mutanensa: "Shin, kuna je wa alfasha, babu kowa da ya gabace ku da ita daga halittu

    [81] Lalle ne ku, haƙiƙa kuna je wa maza da sha'awa, baicin mata; A'a, ku mutane ne maɓarnata

    [82] Kuma babu abin da ya kasance jawabin mutanensa, face ɗai suka ce: "Ku fitar da su daga alƙaryarku: lalle ne su, wasumutane ne masu da'awar tsarki

    [83] Sai Muka tsirar da shi, shi da iyalansa, face matarsa, ta kasance daga masu wanzuwa

    [84] Kuma Muka yi ruwa a kansu da wani irin ruwa; Sai ka duba yadda aƙibar masu laifi ta kasance

    [85] Kuma zuwa Madayana ɗan'uwansu Shu'aibu, ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta wa Allah; ba ku da wani abin bauta wa waninSa. Lalle ne, wata hujja bayyananniya daga Ubangijinku ta zo muku! Sai ku cika mudu da sikeli kumakada ku nakasa wa mutane kayansu, kuma kada ku yi fasadi a cikin ƙasa a bayan gyaranta. Wannan ne mafi alheri a gare ku, idan kun kasance muminai

    [86] Kuma kada ku zauna ga kowane tafarki kuna ƙyacewa, kuma kuna kangewa, daga hanyar Allah, ga wanda ya yi imani da shi, kuma kuna neman ta ta zama karkatacciya, kuma ku tuna, a lokacin da kuka kasance kaɗan, sai Ya yawaita ku, kuma ku duba yadda aƙibar masu fasadi ta kasance

    [87] Kuma idan wata ƙungiya daga gare ku ta kasance ta yi imani da abin da aka aiko ni da shi, kuma wata ƙungiya ba ta yi imani ba, to, ku yi haƙuri, har Allah Ya yi hukunci a tsakaninmu; kuma Shi ne Mafi alherin masu hukunci

    [88] Mashawarta waɗanda suka kangare daga mutanensa, suka ce: "Lalle ne, Muna fitar da kai, Ya Shu'aibu, kai da waɗanda suka yi Imani tare da kai, daga alƙaryarmu; ko kuwa lalle ku komo a cikin addininmu." Ya ce: "Ashe! Kuma ko da mun kasance masu ƙi

    [89] Lalle ne mun ƙirƙira ƙarya ga Allah idan mun koma a cikin addininku a bayan lokacin da Allah ya tsirar da mu daga gare shi, kuma ba ya kasancewa a gare mu, mu koma a cikinsa, face idan Al1ah, Ubangijinmu Ya so. Ubangijinmu Ya yalwaci dukan kome ga ilmi. Ga Allah muka dogara. Ya Ubangijinmu! Ka yi hukunci a tsakaninmu da tsakanin mutanenmu da gaskiya, kuma Kai ne Mafi alherin masu hukunci

    [90] Kuma mashawarta waɗanda suka kafirta daga mutanensa, suka ce: "Lalle ne, idan kun bi Shu'aibu haƙiƙa ku, a lokacin nan, masu hasara ne

    [91] Sai tsawa ta kama su, saboda haka suka wayi gari, a cikin gidansu, suna guggurfane

    [92] Waɗanda suka ƙaryata Shu'aibu kamar ba su zauna ba a cikinta, waɗanda suka ƙaryata Shu'aibu, sun kasance su nemasu hasara

    [93] Sai ya juya daga barinsu, kuma ya ce: "Ya mutanena! Haƙiƙa, na iyar muku da saƙonnin Ubangijina, kuma na yi muku nasiha! To, yaya zan yi baƙin ciki a kan mutane kafirai

    [94] Kuma ba Mu aika wani Annabi a cikin wata alƙarya ba, face Mun kama mutanenta da azaba da cuta, tsammaninsu suna yin ƙasƙantar da kai

    [95] Sa'an nan kuma Muka musanya mai kyau a matsayin mummuna, har su yi yawa, kuma su ce: "Cuta da azaba sun shafi ubanninmu." (sai su koma wa kafirci). Sai Mu kama su kwatsam! alhali kuwa su, ba su sansancewa

    [96] Kuma da lalle mutanen alƙaryu sun yi imani kuma suka yi taƙawa da haƙiƙa Mun buɗe albarkoki a kansu daga sama da ƙasa, kuma amma sun ƙaryata, don haka Muka kama su da abin da suka kasance suna tarawa

    [97] Shin, mutanen alƙaryu sun amince wa azabar Mu ta je musu da dare, alhali kuwa suna barci

    [98] Ko kuwa mutanen alƙaryu sun amince wa azabarMu ta je musu da hantsi, alhali kuwa suna wasa

    [99] Shin fa, sun amince wa makarun Allah? To, babu mai amince wa makarun Allah face mutane masu hasara

    [100] Shin, kuma bai shiryar da waɗanda suke gadon ƙasa ba daga bayan mutanenta cewa da Muna so, da Mun same su da zunubansu, kuma Mu rufe a kan zukatansu, sai su zama ba su ji

    [101] Waɗancan alƙaryu Muna gaya maka daga labaransu, kuma lalle ne, haƙiƙa manzanninMu sun je musu da hujjoji bayyanannnu; to, ba su kasance suna yin imanida abin da suka ƙaryata daga gabani ba. Kamar wancan ne Allah Yake rufewa a kan zukatan kafirai

    [102] Kuma ba Mu sami wani alkawari ba ga mafi yawansu, kuma lalle ne, Mun sami mafi yawansu, haƙiƙa, fasiƙai

    [103] Sa'an nan kuma Mun aika Musa, daga bayansu, da ayoyinMu zuwa ga Fir'auna da majalisarsa, sai suka yi zalunci game da su. To, dubi yadda aƙibar maɓarnata take

    [104] Kuma Musa ya ce: "Ya Fir'auna! Lalle ne ni, manzo ne daga Ubangijin halittu

    [105] Tabbatacce ne a kan kada in faɗi kome ga Allah face gaskiya. Lalle ne, na zo muku da hujja bayyananniya daga Ubangijinku; Sai ka saki Bani Isra'ila tareda ni

    [106] Ya ce: "Idan ka kasance ka zo da wata aya, to, ka kawo ta, idan ka kasance daga masu gaskiya

    [107] Sai ya jefa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne

    [108] Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga masu dubi

    [109] Mashawarta daga mutanen Fir'auna suka ce: "Lalle ne, wannan, haƙiƙa, matsafi ne mai ilmi

    [110] Yana son ya fitar da ku daga ƙasarku: To, mene ne kuke shawartawa

    [111] Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shi da ɗan'uwansa, kuma ka aika da masu gayyar mutane a cikin garuruwa

    [112] Su zo maka da duka matsafi, mai ilmi

    [113] Kuma matsafa suka je wa fir'auna suka ce: "Lalle ne, shin, Muna da ijara, idan mun kasance mu ne marinjaya

    [114] Ya ce: "Na, am kuma lalle ne kuna a cikin makusanta

    [115] Suka ce: "Ya Musa! Ko dai ka jefa, ko kuwa mu kasance, mu ne, masu jefawa

    [116] Ya ce: "Ku jefa." To a 1okacin da suka jefa, suka sihirce idanun mutane kuma suka tsoratar da su; Kuma suka je da tsafi mai girma

    [117] Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Musa cewa: "Ka jefa sandarka." Sai ga ta tana laƙumar abin da suke ƙarya da shi

    [118] Gaskiya ta auku, kuma abin da suke aikatawa ya ɓaci

    [119] Sai aka rinjaye su a can, kuma suka juya suna ƙasƙantattu

    [120] Kuma aka jefar da matsafan, suna masu sujada

    [121] Suka ce: "Mun yi imani da Ubangijin halittu

    [122] Ubangijin Musa da Haruna

    [123] Fir'auna ya ce: "Ashe, kun yi imani da shi a gabanin inyi izni a gare ku? Lalle ne, wannan, haƙiƙa, makirci ne kuka makirta a cikin birni, domin ku fitar da mutanensa daga gare shi; To, da sannu za ku sani

    [124] Lalle ne, ina karkatse hannayenku da ƙafafunku daga saɓani, sa'an nan kuma, haƙiƙa, ina tsire, ku gaba ɗaya

    [125] Suka ce: "Lalle ne mu, zuwa ga Ubangijinmu, masu juyawa ne

    [126] Kuma ba ka zargin kome daga gare mu face domin mun yi imani da ayoyin Ubangijinmu a lokacin da suka zo mana! Ya Ubangijinmu! Ka zuba haƙuri a kanmu, kuma Ka cika mana muna Musulmai

    [127] Kuma mashawarta daga mutanen Fir'auna suka ce: "Shin, za ka bar Musa da mutanensa domin su yi ɓarna a cikin ƙasa, kuma ya bar ka, kai da gumakanka?" Ya ce: "Za mu yayyanka ɗiyansu maza kuma mu raya matansu; kuma lalle ne mu, a bisa gare su, marinjaya ne

    [128] Musa ya ce wa mutanensa: "Ku nemi taimako da Allah, kuma ku yi haƙuri; Lalle ne ƙasa ta Allah ce, Yana gadar da ita ga wanda Yake so daga bayinSa, kuma aƙiba ta masu taƙawa ce

    [129] Suka ce: "An cutar da mu daga gabanin ka zo mana, kuma daga bayan da ka zo mana." Ya ce: "Akwai tsammanin Ubangijinku, Ya halaka maƙiyanku, kuma Ya sanya ku, ku maye a cikin ƙasa, sa'an nan Ya duba yadda kuke aikatawa

    [130] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun kama mutanen Fir'auna da tsananin shekaru (fari) da nakasa daga 'ya'yan itace; Tsammaninsu suna tunawa

    [131] Sa'an nan idan wani alheri ya je musu, sai su ce: "Masifa ta same su, sai su yi shu'umci da Musa da wanda yake tare da shi, To, shu'umcinsu a wurin Allah yake, kuma amma mafi yawansu ba su sani

    [132] Kuma suka ce: "Ko me ka zo mana da shi daga aya, domin ka sihirce mu da ita, to, baza mu zama, saboda kai, masu imani ba

    [133] Sai Muka aika a kansu da cikowa, da fara, da ƙwarƙwata da kwaɗi, da jini; ayoyi abubuwan rarrabewa; Sai suka kangare, kuma suka kasance mutane masu laifi

    [134] Kuma a lokacin da masifa ta auku a kansu, sukan ce: "Ya Musa! Ka roƙa mana Ubangijinka, saboda abin da Ya yi alkwari a wurinka, lalle ne idan ka kau da azabar daga barinmu, haƙiƙa Muna imani saboda kai, kuma muna sakin Bani Isra'ila tire da kai

    [135] To, a lokacin da Muka kuranye azaba daga barinsu zuwa a wani ajali wanda suke masu iske shi ne, sai ga su suna warwarewa

    [136] Sai Muka yi azabar ramuwa, daga gare su, saboda haka Muka nutsar da su a cikin teku, domin lalle ne su, sun ƙaryata game da ayoyinMu, kuma sun kasance daga barinsu, gafilai

    [137] Kuma Muka gadar da mutanen, waɗanda sun kasance ana raunana su, a gabacin ƙasa da yammacinta, wadda Muka sanya albarka a cikinta, kuma kalmar Ubangijinka mai kyau ta cika a kan Bani Isra'ila, saboda abin dasuka yi na haƙuri. Kuma Muka murtsuke abin da Fir'auna da mutanensa suka kasance suna sana'antawa, da abin da suka kasance suna shimfiɗawa

    [138] Kuma Muka ƙetarar da Bani Isra'ila ga teku, sai suka je a kan wasu mutane waɗanda suna lizimta da ibada a kan wasu gumaka, nasu suka ce: "Ya Musa! Ka sanya mana wani abin bautawa kamar yadda suke da abubuwan bautawa " Ya ce: "Lalle ne ku, mutane ne kuna jahilta

    [139] Lalle ne waɗannan, abin da suke a cikinsa halakakke ne, kuma abin da suka kasance suna aikatawa ƙarya ne

    [140] Ya ce: "Shin, wanin Allah nike nema muku ya zama abin bautawa, alhali kuwa Shi (Allah) Ya fifita ku a kan halittu

    [141] Kuma a lokacin da Muka tsirar da ku daga mutanen Fir'auna, suna taya muku mugunyar azaba. suna karkashe ɗiyanku maza, kuma suna rayar da matanku. Kuma a cikin wancan akwai jarrabawa daga Ubangijinku, Mai girma

    [142] Kuma Muka yi wa'adi ga Musa da dare talatin kuma Muka cika su da goma, sai miƙatin Ubangijinsa ya cika dare arba'in. Kuma Musa ya ce wa ɗan'uwansa, Haruna: "Ka maye mini a cikin mutanena, kuma ka gyara, kuma kada ka bi hanyar masu fasadi

    [143] Kuma a lokacin da Musa ya je ga mikatinMu, kuma Ubangijinsa Ya yi masa magana, shi Musa ya ce: "Ya Ubangijina! Ka nuna mini in yi dubi zuwa gare Ka!" Ya ce: "Ba za ka gan Ni ba, kuma amma ka duba zuwa ga dutse, to, idan ya tabbata a wurinsa, to, za ka gan Ni." Sa'an nan a lokacin da Ubangijinsa, Ya kuranye zuwa ga dutsen, Ya sanya shi niƙaƙƙe. Kuma Musa ya faɗi somamme. To, a lokacin da ya farka, ya ce: "TsarkinKa ya tabbata! Na tuba zuwa gare Ka, kuma ni ne farkon muminai

    [144] Ya ce: "Ya Musa! Lalle ne Ni, Na zaɓe ka bisa ga mutane da manzanciNa, kuma da maganaTa. Saboda haka ka riƙi abin da Na ba ka, kuma ka kasance daga masu godiya

    [145] Kuma Muka rubuta masa a cikin alluna daga kowane abu, wa'azi da rarrabewa ga dukan kowane abu: "Sai ka riƙe su da ƙarfi, kuma ka umurci mutanenka, su yi riƙo ga abin da yake mafi kyawunsu; za Ni nuna muku gidan fasiƙai

    [146] Za Ni karkatar da waɗanda suke yin girman kai a cikin ƙasa, ba da wani hakki ba, daga ayoyiNa. Kuma idan sun ga dukan aya, ba za su yi imani da ita ba, kuma idan sun ga hanyar shiriya, ba za su riƙe ta hanya ba, kuma idan sun ga hanyar ɓata, sai su riƙe ta hanya. Wancan ne, domin lalle ne su, sun ƙaryata da ayoyinMu, kuma sun kasance, daga barinsu gafilai

    [147] Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ayoyinMu da gamuwa da Lahira, ayyukansu sun ɓaci. Shin, ana saka musu, face da abin da suka kasance suna aikatawa

    [148] Kuma mutanen Musa suka riƙi maraƙi, jikin mutane, yana ruri, daga bayan tafiyarsa, daga kayan ƙawarsu. Shin, ba su gani ba, cewa lalle ne shi, ba ya yi musu magana, kuma ba ya shiryar da su ga hanya, sun riƙa shi, kuma sun kasance masu zalunci

    [149] Kuma a lokacin da suka yi nadama, kuma suka ga cewalalle ne su haƙiƙa sun ɓace, suka ce: "Haƙiƙa, idan UbangijinMu bai yi mana rahama ba, kuma Ya gafarta mana, lalle ne muna kasancewa daga masu hasara

    [150] Kuma a lokacin da Musa ya koma zuwa ga mutanensa, yana mai fushi, mai baƙin ciki, ya ce: "Tir da abin da kuka yi mini wakilci, a bayana! Shin, kun nemi gaggawar umurnin Ubangijinku ne?" Kuma ya jefar da Allunan, kuma ya yi riƙo ga kan ɗan'uwansa yana jan sa zuwa gare shi. Ya ce: "Ya ɗan'uwata! Lalle ne mutanen, sun ɗauke ni mai rauni, kuma sun yi kusa su kashe ni, saboda haka kada ka darantar da maƙiya game da ni, kuma kada ka sanya ni tare da mutane azzalumai

    [151] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka gafarta mini, ni da ɗan'uwana, kuma Ka shigar da mu a cikin rahamarKa, alhali kuwa Kai ne Mafi rahamar masu rahama

    [152] Lalle ne waɗanda suka riƙi maraƙin, wani fushi daga Ubangijinsu da wani walakanci a cikin rayuwar duniya, za su same su: Kuma kamar wancan ne Muke saka wa masu ƙirƙira ƙarya

    [153] Kuma waɗanda suka aikata miyagun ayyuka, sa'an nan suka tuba daga bayansu kuma sukayi imani, lalle ne Ubangijinka daga bayansu, haƙiƙa, Mai gafarane, Mai jin ƙai

    [154] Kuma a lokacin da fushin ya kwanta daga barin Musa, sai ya riƙi Allunan, kuma a cikin kwafensu akwai shiriya da rahama ga waɗanda suke su, ga Ubangijinsu, masu jin tsoro ne

    [155] Kuma Musa ya zaɓi mutanensa, namiji saba'in domin miƙatinMu. To, a lokacin da tsawa ta kama su, ya ce: "Ya Ubangijina! Da Ka so, da Ka halakar da su daga gabani, su da ni. Shin za Kahalaka mu, saboda abin da wawayen daga gare mu suka aikata? Ba ta zama ba face fitinarKa Kana ɓatarwa, da ita, wanda Kake so kuma kana shiryarwa da ita, wanda Kake so; Kai ne Majiɓincinmu. Sai Ka gafarta mana; kuma Ka yi mana rahama, alhali kuwa Kai ne Mafi alherin masu gafara

    [156] Kuma Ka rubuta mana alheri a cikin wannan duniya, kuma a cikin Lahira. Lalle ne mu, mun tuba zuwa gare Ka." Ya ce: "AzabaTa Ina samu, da ita, wanda Nike so, kuma rahamaTa, ta yalwaci dukan kome. Sa'an nan za Ni rubuta ta ga waɗanda suke yin taƙawa, kuma suna bayar da zakka, da waɗanda suke, game da ayoyinMu muminai ne

    [157] Waɗanda suke suna bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke samun sa rubuce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjila

    [158] Ka ce: "Ya ku mutane! Lalle ne ni manzon Allah nezuwa gare ku, gaba ɗaya. (Allah) Wanda Yake Shi ne da mulkin sammai da ƙasa; Babu wani abin bautawa face Shi, Yana rayarwa, kuma Yana matarwa, sai ku yi imani daAllah da ManzonSa, Annabi, Ummiyyi, wanda yake yin imani da Allah da kalmominSa; ku bi shi, tsammaninku, kuna shiryuwa

    [159] Kuma daga mutanen Musa akwai al'umma, suna shiryarwa da gaskiya, kuma da ita suke yin adalci

    [160] Kuma Muka yayyanka su sibɗi goma sha biyu, al'ummai. Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Musa a lokacin da mutanensasuka neme shi, ga shayarwa, cewa: "Ka doki dutsen da sandarka."Sai marmaro goma sha biyu suka ɓuɓɓuga daga gare shi: Lalle ne kowaɗanne mutane sun san mashayarsu. Kuma Muka saukar da darɓa da tantabaru a kansu."Ku ci daga masu daɗin abin da Muka azurta ku."Kuma ba su zalunce Mu ba; kuma amma rayukansu suke zalunta

    [161] Kuma a lokacin da aka ce masu: "Ku zauna ga wannan alƙarya, kuma ku ci daga gare ta, inda kuka so, kuma ku ce: 'Saryarwa,' kuma ku shiga kofa kuna masu sujada; Mu gafarta muku laifuffukanku, kuma za Mu ɗara wa masu kyautatawa

    [162] Sai waɗanda suka yi zalunci daga gare su, suka musanya magana watar wadda aka ce musu, sai Muka aika azaba a kansu, daga sama, saboda abin da suka kasance suna yi na zalunci

    [163] Kuma ka tambaye su daga alƙarya wadda ta kasance kusa ga teku, a lokacin da suke ƙetare haddi a cikin Asabar, a lokacin da kifayensu, suke je musu a ranar Asabar ɗinsu jere. Kuma a ranar da ba su yi Asabar ba, ba su zuwa gare su; Kamar wancan ne Muke jarraba su da abin da suka kasance suna yi na fasiƙanci

    [164] Kuma a lokacin da wata al'umma daga gare su ta ce: "Don me kuke yin wa'azi ga mutane waɗanda Allah Yake Mai halaka su ko kuwa Mai yi musu azaba, azaba mai tsanani?" Suka ce: "Domin neman hanzari zuwa ga Ubangijinku, kuma tsammaninsu, suna yin taƙawa

    [165] To, a lokacin da suka manta da abin da aka tunatar da su da shi, Mun tsirar da waɗanda suke hani daga cuta, kuma Muka kama waɗanda suka yi zalunci, da azaba mai tsanani domin abin da suka kasance suna yi, na fasiƙanci

    [166] Sa'an nan a lokacin da suka yi girman kai daga barin abin da aka hana su daga gare shi, Muka ce musu: "Ku kasance birai ƙasƙantattu

    [167] Kuma a lokacin da Ubangijinku Ya sanar, lalle ne, za Ya aika a kansu (Yahud), zuwa, Ranar¡iyama, wanda zai ɗanɗana musu mummunar azaba, lalle ne Ubangijinka, haƙiƙa, Mai gaggawar uƙuba ne, kuma shi haƙiƙa, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [168] Kuma Muka yayyanka su, a cikin ƙasa, al'ummomi, daga gare su akwai salihai, kuma daga gare su akwai wanda ba haka ba. Muka jarrabe su da abubuwan alheri da na musifa; Tsammaninsu, suna komowa

    [169] Sai wasu' yan baya suka maye daga bayansu, sun gaji Littafin, suna karɓar sifar wannan ƙasƙantacciya, suna cewa: "Za a gafarta mana. "Iadan kuma wata sifa irinta ta zo, za su karɓe ta. Shin, ba a karɓi alkawarin Littafi ba a kansu cewa kada su faɗa ga Allah, face gaskiya, alhali kuwa sun karanta abin da yake a cikinsa, kuma Gidan Lahira ne mafi alheriga wanda ya yi taƙawa? Shin, ba za ku hankalta ba

    [170] Kuma waɗanda suke riƙewa da laittafi kuma suka tsayar da salla, lalle ne Mu, ba Mu tozarta ladar masu gyarawa

    [171] Kuma a lokacin da muka ɗaukaka dutse sama da su, kumar dai shi girgije ne, kuma suka haƙƙaƙe, lalle ne shi, mai faɗuwa ne a gare su, (aka ce): "Ku karɓi abin da Muka kawo muku da ƙarfi, kuma ku tuna abin da yake a cikinsa, tsammaninku kuna yin taƙawa

    [172] Kuma a lokacin da Ubangijinka Ya karɓi (alkawari) daga ɗiyan Adam, daga bayayyakinsu, a zuriyarsu, kuma Ya shaidar da su a kan rayukansu, (Ya ce): "Shin, ba Ni ne Ubangijinku ba?" Suka ce: "Na'am! Mun yi shaida!" (ya ce): "Kada ku ce a Ranar Kiyama: Lalle ne mu, daga wannan, gafalallu ne

    [173] Ko kuwa ku ce: "Abin sani kawai, ubanninmu suka yi shirki daga farko, kuma mu, mun kasance zuriya daga bayansu. Shin fa, Kana halaka mu, saboda abin da masu ɓatawa suka aikata

    [174] Kuma kamar haka Muke rarrabe ayoyi, daki-daki; tsammaninsu, suna komowa

    [175] Ka karanta a kansu labarin wanda Muka kawo masa ayoyinMu, sai ya saɓule daga gare su, sai shaidan ya bi shi, sai ya kasance a cikin halakakku

    [176] Kuma da Mun so, da Mun ɗaukaka shi da su, kuma amma shi, ya nemi dawwama a cikin ƙasa, kuma ya bi son zuciyarsa. To, misalinsa kamar misalin kare ne, idan ka yi ɗauki a kansa ya yi lallage, ko kuwa ka bar shi sai ya yi lallage, wannan ne misalin mutane waɗanda suka ƙaryata game da ayoyinMu: Ka jeranta karatun labarun; tsammaninsu suna tunani

    [177] Tir da zama misali, mutanen da suka ƙaryata game da ayoyinMu, kuma kansu suka kasance suna zalunta

    [178] Wanda Allah Ya shiryar, to, shi ne Mai shiryuwa, kuma wanda Ya ɓatar, to, waɗannan su ne masu hasara

    [179] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun halitta saboda Jahannama, masu yawa daga aljannu da mutane, suna da zukata, ba su fahimta da su, kuma suna da idanu, ba su gani da su, kuma suna da kunnuwa, ba su ji da su; waɗancan kamar bisashe suke. A'a, su ne mafi ɓacewa; Waɗancan su ne gafalallu

    [180] Kuma Allah Yana da sunaye masu kyau. Sai ku roƙe shi da su, kuma ku bar waɗanda suke yin ilhadi a cikin sunayenSa: za a saka musu abin da suka kasance suna aikatawa

    [181] Kuma daga waɗanda Muka halitta akwai wata al'umma, suna shiryarwa da gaskiya, kuma, da ita suke yin adalci

    [182] Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ayoyinMu, za Mu yi musu istidraji daga inda ba su sani ba

    [183] Kuma Ina yi musu jinkiri, lalle ne kaidiNa, mai ƙarfi ne

    [184] Shin, ba su yi tunini ba, cewa babu wata hauka ga ma'abucinsu? shi bai zama ba face mai gargaɗi mai bayyanawa

    [185] Shin, ba su yi dubi ba a cikin mulkin sammai da ƙasa, da kuma abin da Allah Ya halitta daga kome, kuma akwai tsammani kasancewar ajalinsu, haƙiƙa, ya kusanta? To, da wane labari a bayansa suke yin imani

    [186] Wanda Allah Ya ɓatar to babu mai shiryarwa a gare shi: kuma Yana barin su, a cikin ɓatarsu suna ɗimuwa

    [187] Suna tambayar ka daga Sa'a, a yaushe tabbatarta take? Ka ce: "Abin sani kawai, saninta a wurin Ubangijina yake. Babu mai bayyana ta ga lokacinta face shi Ta yi nauyi a cikin sammai da ƙasa. Ba za ta zo muku ba face kwatsam." suna tambayar ka, kamar kai masani ne gare ta. Ka ce: "Abin sani kawai, saninta a wurin Allah yake, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani

    [188] Ka ce: "Ba ni mallaka wa raina wani amfani, kuma haka ban tunkuɗe wata cuta, faceabin da Allah Ya so. Kuma da na kasance ina sanin gaibi, da lalle ne, na yawaita daga alheri kuma cuta ba za ta shafe ni ba, ni ban zama ba fice mai gargaɗi, kumamai bayar da bishara ga mutane waɗanda suke yin imani

    [189] Shi ne wanda Ya halitta ku daga rai guda, kumaYa sanya, daga gare ta, ma'auranta, domin ya natsu zuwa gare ta. Sa'an nan a lokacin da ya rufe ta, ta yi ciki, ciki sassauƙa, sai ta shuɗe dashi. Sa'an nan a lokacin da ya yi nauyi, sai suka roƙi Allah, Ubangijinsu: "Lalle ne idan Ka ba mu abin ƙwarai, haƙiƙa, za mu kasance dagamasu godiya

    [190] To, a lokacin da Ya ba su abin ƙwarai, suka sanya Masa abokan tarayya a cikin abin da Ya ba su. To, Allah Ya tsarkaka daga abin da suke yi na shirki

    [191] Shin, suna shirki da abin da ba ya halittar kome, kuma sune ake halittawa

    [192] Kuma ba su iya bayar da taimako gare su, kuma kansu ma, ba su iya taimaka

    [193] Kuma idan kun kiraye su zuwa ga shiriya, ba za su bi ku ba, daidai ne a gare ku, shin, kun kiraye su, ko kuwa ku masu kawaici ne

    [194] Lalle ne waɗannan da kuke kira, baicin Allah, bayi ne misalanku: to, ku kiraye su, sa'an nan su karɓa muku, idan kun kasance masu gaskiya

    [195] Shin suna da ƙafafu da suke yin tafia da su? Ko suna da hannaye da suke damƙa da su? Ko suna da idanu da suke gani da su? Ko suna da kunnuwa da suke saurare da su? Ka ce: "Ku kirawo abubuwan shirkinku sa'an nan kuma ku yi mini kaidi, sa'an nan kada ku saurara mini

    [196] Lalle ne, Majiɓincina Allah ne Wanda Ya saukar da Littafi kuma Shi ne Yake jiɓintar salihai

    [197] Kuma waɗanda kuke kira, baicinSa, ba su iya taimakon ku, kuma kansu ma, ba su iya taimaka

    [198] Kuma idan ka kiraye su zuwa ga shiriya, ba za su ji ba, kuma kana ganin su, suna dubi zuwa gare ka, alhali kuwa su, ba su gani

    [199] Ka riƙi abin da ya sauƙaƙa; Kuma ka yi umurni da alheri, Kuma ka kau da kai daga jahilai

    [200] Kuma imma wata fizga daga Shaiɗan ta fizge ka, sai ka nemi tsari ga Allah. Lalle ne shi, Mai ji ne, Masani

    [201] Lalle ne waɗanda suka yi taƙawa idan wani tashin hankali daga Shaiɗan ya shafe su, sai su tuna (Allah) sai ga su, sun zama masu basira

    [202] Kuma 'yan'uwan su (shaiɗanu) suna taimakon su a cikin ɓata, sa'an nan kuma ba su taƙaitawa

    [203] Kuma idan ba ka je musu da wata aya ba, su ce: "Don me ba ka ƙaga ta ba?" Ka ce: "Abin sani kawai, ina biyar abin da aka yo wahayi zuwa gare ni ne, daga Ubangjina. Wannan abubuwan kula ne daga Ubangijinku, da shiriya da rahama ga mutane waɗanda suke yin imani

    [204] Kuma idan an karanta Alƙur'ani sai ku saurara gare shi, kuma ku yi shiru; Tsammaninku, ana yi muku rahama

    [205] Kuma ka ambaci Ubangijinka, a cikin ranka da ƙanƙan da kai, da tsoro, kuma komabayan bayyanawa na magana, da safe da marece, kuma kada ka kasance daga gafalallu

    [206] Lalle ne, waɗanda ke wurin Ubangijinka ba su yin girman kai ga bauta Masa, kuma suna tsarake shi da tasbihi, kuma a gare shi suke yin sujada

    Ganĩma

    Surah 8

    [1] Suna tambayar ka ga ganima. ka ce: "Ganima ta Allah daManzonSa ce. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma ku gyara abin da yake a tsakaninku, kuma ku yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, idan kun kasance muminai

    [2] Abin sani kawai, numinai su ne waɗanda suke idan an ambaci, Allah, zukatansu su firgita, kuma idan an karanta ayoyinSa a kansu, su ƙara musu wani imani, kuma ga Ubangijinsu suke dogara

    [3] Waɗanda suke tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azurta su suna ciyarwa

    [4] Waɗannan su ne muminai da gaskiya. Suna da darajoji a wurin Ubangijinsu, da wata gafara da arziki na karimci

    [5] Kamar yadda Ubangijinka Ya fitar da kai daga gidanka da gaskiya, alhali kuwa lalle wani ɓangare na muminai, haƙiƙa, suna ƙyama

    [6] Suna jayayya da kai a cikin (sha'anin) gaskiya a bayan ta bayYana, kamar dai lalle ana kora su zuwa ga mutuwa ne alhali kuwa suna kallo

    [7] Kuma a lokacin da Allah Yake yi muku alkawari da ɗayan ƙungiya biyu, cewa lalle ita taku ce: kuma kuna gurin cewa lalle ƙungiya wadda ba ta da ƙaya ta kasance gare ku, kuma Allah Yana nufin Ya tabbatar da gaskiya da kalmominSa, kuma Ya katse ƙarshen kafirai

    [8] Domin Ya tabbatar da gaskiya, kuma Ya ɓata ƙarya, kuma koda masu laifi sun ƙi

    [9] A lokacin da kuke neman Ubangijinku tairnako, sai Ya karɓa muku cewa: "Lalle ne Ni, Mai taimakon ku ne da dubu daga mala'iku, jere

    [10] Kuma Allah bai sanya shi ba face Domin bishara, kuma domin zukatanku su natsu da shi, kuma taimakon, bai zama ba face daga wurin Allah; Lalle ne Allah Mabuwayi ne, Mai hikima

    [11] A lokacin da (Allah) Yake rufe ku da gyangyaɗi, ɗomin aminci daga gare Shi, kuma Yana saukar da ruwa daga sama, a kanku, domin Ya tsarkake ku da shi, kuma Ya tafiyar da ƙazantar Shaiɗan daga barinku, kuma domin Ya ɗaure a kan zukatanku, kuma Ya tabbatar da ƙafafu da shi

    [12] A lokacin da Ubangijinka Yake yin wahayi zuwa ga Mala'iku cewa: "Lalle ne Ni, Ina tare da ku, sai ku tabbatar da waɗanda suka yi imani: Za Ni jefa tsoro a cikin zukatan waɗanda suka kafirta, sai ku yi duka bisa ga wuyoyi kuma ku yi duka daga gare su ga dukkan yatsu

    [13] Wancan ne, domin lalle ne su, suna saɓa wa Allah da ManzonSa. Kuma wanda ya saɓa wa Allah da ManzonSa, to, lalle ne Allah Mai tsananin uƙuba ne

    [14] Wancan ne: "Ku ɗanɗane shi, kuma lalle ne akwai azabar wuta ga kafirai

    [15] Ya ku wacɗanda suka yiimani! Idan kun haɗu da waɗanda suka kafirta ga yaƙi, to, kada ku juya musu bayayyakinku

    [16] Kuma duka wanda ya juya musu bayansa a yinin nan, face wanda ya karkata domin koɗayya, ko kuwa wanda ya je domin haɗuwa da wata ƙungiya, to, lalle ne ya koma da fushi daga Allah, kuma matattararsa Jahannama, kuma tir da makoma ita

    [17] To, ba ku ne kuka kashe su ba; kuma amma Allah ne Ya kashe su: kuma ba ka yi jifa ba a lokacin da ka yi jifa; kuma amma Allah ne Ya yi jifar. Kuma dominYa jarraba Musulmi da jarrabawa mai kyau daga gare shi. Kuma Allah Mai ji ne, Masani

    [18] Wancan ne, kuma lalle ne, Allah Mai raunana kaidin kafirai ne

    [19] Idan kun yi alfanun cin nasara to lalle nasarar ta je muku, kuma idan kun hanu, to Shi ne Mafi alheri a gare ku, kuma idan kun koma za Mu koma, kuma jama'arku ba za ta wadatar muku da kome ba, ko da ta yi yawa. Kuma lalle ne cewa Allah Yana tare da muminai

    [20] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku juya daga barinSa, alhali kuna ji

    [21] Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka ce: "Mun ji, alhali kuwa su ba su ji

    [22] Lalle ne, mafi sharrin dabbobi a wurin Allah, su ne kurame, bebaye, waɗanda ba, su yin hankali

    [23] Da Allah Ya san wani alheri a cikinsu, da Ya jiyar da su, kuma ko da Yajiyar da su, haƙiƙa, da sun juya, alhali su, suna masu hinjirewa

    [24] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku karɓa wa Allah, kuma ku karɓa wa Manzo, idan Ya kiraye ku zuwa ga abin da Yake rayar da ku; Kuma ku sani cewa Allah Yana shamakacewa a tsakanin mutum da zuciyarsa, kuma lalle ne Shi, a zuwa gare Shi ake tara ku

    [25] Kuma ku ji tsoron fitina wadda ba ta samun waɗanda suka yi zalunci daga gare ku keɓe, kuma ku sani, lalle ne Allah Mai tsananin uƙuba ne

    [26] Ku tuna a lokacin da kuke kaɗan, waɗanda ake raunanarwa a cikin ƙasa kuna tsoron mutane su cafe ku, sai Ya tattara ku (a wurin natsuwa, Maɗina), kuma Ya ƙarfafa ku da taimakonSa kuma Ya azurta ku daga abubuwa masu daɗi; Tsammaninku, kuna godewa

    [27] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku yaudari Allah da ManzonSa, kuma ku yaudari amanoninku, alhali kuwa kuna sane

    [28] Kuma ku sani cewa abin sani kawai, dukiyoyinku da 'ya'yanku, wata fitina ce, kuma lalle ne Allah, a wurinSa, akwai ijara mai girma

    [29] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun bi Allah da taƙawa, zai sanya muku mararraba (da tsoro) kuma Ya kankare ƙananan zunubanku daga barinku. Kuma Ya gafarta muku. Kuma Allah ne Ma'abucin falala Mai girma

    [30] Kuma a lokacin da waɗanda suka kafirta suke yin makirci game da kai, domin su tabbatar da kai, ko kuwa su kashe ka, ko kuwa su fitar da kai, suna makirci kuma Allah Yana mayar musa da makirci kuma Allah ne Mafificin masu makirci

    [31] Kuma idan aka karanta, ayoyinMu a kansu, sukan ce: "Lalle ne mun ji da muna so, haƙiƙa, da mun faɗi irin wannan; wannan bai zama ba face tatsunayoyin mutanen farko

    [32] A lokacin da suka ce: "Ya Allah! Idan wannan ya kasancc shi ne gaskiya daga wurinKa, sai Ka yi ruwan duwatsu, a kanmu, daga sama, ko kuwa Kazo mana da wata azaba, mai raɗaɗi

    [33] Kuma Allah bai kasance Yana yi musu azaba ba alhali kuwa kai kana cikinsu, kuma Allah bai kasance Mai yi musu azaba ba alhali kuwa suna yin istigfari

    [34] Kuma mene ne a gare su da Allah ba zai yi musu azaba ba, alhali kuwa su, suna kangewa daga Masallaci Mai alfarma kuma ba su kasance majiɓintanSa ba? Babu majiɓintanSa face masu taƙawa. Kuma mafi yawansu ba su sani ba

    [35] Kuma sallarsu a wurin ¦akin ba ta kasance ba face shewa da yaya; sai ku ɗanɗani azaba saboda abin da kuka kasance kuna yi na kafirci

    [36] Lalle ne waɗanda suka kafirta, suna ciyar da dukiyoyinsu, domin su kange daga hanyar Allah; to, za a su ciyar da ita, sa' an nan kuma ta kasance nadama a kansu, sa'an nan kuma a rinjaye su. Kuma waɗanda suka kafirta zuwa ga Jahannama ake tara su

    [37] Domin Allah Ya rarrabe mummuna daga mai kyau, kuma Ya sanya mummunan, sashensa a kan sashe, sa'an nan Ya shirga shi gaba daya, sa'an nan Ya sanya shi a cikin Jahannama. Waɗannan su ne masu hasara

    [38] Ka ce wa waɗanda suka kafirta, idan sun hanu, za a gafarta musu abin da ya riga ya shige, kuma idan sun koma, to, hanyar kafiran farko, haƙiƙa, ta shuɗe

    [39] Kuma ku yaƙe su har wata fitina ba za ta kasance ba, kuma addini dukansa ya kasance na Allah. To, idan sun hanu to lalle ne, Allah ia abin da kuke aikatawa Mai gani ne

    [40] Kuma idan sun juya, to, ku sani cewa lalle Allah ne Majiɓincinku: Madalla da Majiɓinci, kuma madalla da Mai taimako, Shi

    [41] Kuma ka sani, abin sani kawai, abin da kuka sami ganima daga wani abu, to, lalle ne Allah Yana da humusinsa kuma da Manzo, kuma da masu zumunta, da marayu da miskinai da ɗan hanya, idan kun kasance kun yi imani da Allah da abin da Muka saukar a kan bawanMu a Ranar Rarrabewa, a Ranar da jama'a biyu suka haɗu, kuma Allah ne, a kan kowane abu, Mai ikon yi

    [42] A lokacin da kuke a gaɓa ta kusa su kuma suna a gaɓa tanesa, kuma ayarin yana a wuri mafi gangarawa daga gare ku, kuma da kun yi wa juna wa'adi, da kun saɓa ga wa'adin; kuma amma domin Allah Ya hukunta abin da yake ya kasance abin aikatawa. Domin wanda yake halaka ya halaka daga shaida, kuma mai rayuwa ya rayu daga shaida, kuma lalle Allah ne, haƙiƙa, Mai ji Masani

    [43] A lokacin da Allah Yake nuna maka su suna kaɗan, a cikin barcinka, kuma da Ya nuna maka su suna da, yawa, lalle ne da kun ji tsoro, kuma lalle ne da kun yi jayayya a cikin al'amarin, kuma amma Allah Ya tsare ku: Lalle Shi ne Masani ga abin da yake a cikin ƙiraza

    [44] Kuma a lokacin da Yake nuna muku su, a lokacin da kuka haɗu, a cikin idanunku suna kaɗan, kuma Ya ƙarantar da ku a cikin idanunsu domin Allah Ya hukunta wani al'amari wanda ya kasance abin aikatawa. Kuma zuwa ga Allah ake mayar da al'umurra

    [45] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun haɗu da wata ƙungiyar yaƙi, to, ku tabbata, kuma ku ambaci Allah da yawa, tsammaninku kuna cin nasara

    [46] Kuma ku yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku yi jayayya har ku raunana kuma iskarku ta tafi, kuma ku yi haƙuri. Lalle ne Allah Yana tare da masu haƙuri

    [47] Kada ku kasance kamar waɗanda suka fita daga gidajensu, suna masu alfahari da yin riya ga mutane, kuma suna kangewa daga hanyar Allah. Kuma Allah ne ga abin da suke aikatawa Mai kewayewa

    [48] Kuma a lokacin da Shaiɗan ya ƙawace musu ayyukansu, kuma ya ce: "Babu marinjayi a gareku a yau daga mutane, kuma ni maƙwabci ne gare ku." To, a lokacin da ƙungiya biyu suka haɗu, ya koma a kan digadigansa, kuma ya ce: "Lalle ne ni barrantacce ne daga gare ku! Ni ina ganin abin da ba ku gani; ni ina tsoron Allah: Kuma Allah Mai tsananin uƙuba ne

    [49] A lokacin da munafukai da waɗanda suke akwai cuta a cikin zukatansu, suke cewa: "Addinin waɗannan ya ruɗe su" Kuma wanda ya dogara ga Allah, to, lalle ne Allah Mabuwayi ne, Mai hikima

    [50] Kuma da ka gani, a lokacin da Mala'iku suke karɓar rayukan waɗanda suka kafirta, suna dukar fuskokinsu da ɗuwawunsu, kuma suna cewa: "Ku ɗanɗani azabar Gobara

    [51] Wancan saboda abin da hannayenku suka gabatar ne. Kuma lalle ne, Allah bai zama Mai zalunci ba ga, bayinSa

    [52] Kamar al'adar mutanen Fir'auna da waɗanda suke gabaninsu, sun kafirta da ayoyin Allah, sai Allah Ya kama su da zunubansu. Lalle Allah ne Mai ƙarfi, Mai tsananin uƙuba

    [53] Wancan ne, domin lalle ne, Allah bai kasance Mai canza wata ni'ima wadda ya ni'imtar da ita a kan wasu mutane ba face sun sake abin da yake ga rayukansu, kuma domin lalle Allah ne Mai ji, Masani

    [54] Kamar al'adar mutanen Fir'auna da waɗanda suke a gabaninsu, sun ƙaryata game da ayoyin Ubangijinsu, sai Muka halaka su, saboda zunubansu, kuma Muka nutsar da mutanen Fir'auna. Kuma dukansu sun kasance ne masu zalunci

    [55] Lalle mafi sharrin dabbobi a wurin Allah, su ne waɗanda suka kafirta, sa'an nan ba za su yi imani ba

    [56] Waɗanda ka yi ƙullin alkawari da su, daga gare su, sa'an nan kuma suna warwarewar alkawarinsu a kowane lokaci kuma su, ba su yin taƙawa

    [57] To, in dai ka kama su a cikin yaƙi, sai ka kore waɗanda suke a bayansu, game da su, tsammaninsu, za su dinga tunawa

    [58] Kuma in ka ji tsoron wata yaudara daga wasu mutane, to, ka jefar da alkawarin, zuwa gare su, a kan daidaita: Lalle ne Allah, ba Ya son mayaudara

    [59] Kuma waɗanda suka kafirta kada su yi zaton sun tsere: Lalle ne su, ba za su gagara ba

    [60] Kuma ku yi tattali, dominsu, abin da kuka sami ikon yi na wani ƙarfi, kuma da ajiye dawaki, kuna tsoratarwa, game da shi, ga maƙiyin Allah kuma maƙiyinku da wasu, baicin su, ba ku san su ba, Allah ne Yake sanin su, kuma abin da kuka ciyar daga wani abu a cikin hanyar Allah, za a cika muku sakamakonsa, kuma ku ba a zaluntar ku

    [61] Kuma idan sun karkata zuwa ga zaman lafiya, to, ka karkata zuwa gare shi, kuma ka dogara ga Allah: Lalle ne Shi, Mai ji ne Masani

    [62] Kuma idan sun yi nufin su yaudare ka, to, lalle ma'ishinka Allah ne, Shi ne wanda Ya ƙarfafa ka da taimakonSa, kuma da muminai

    [63] Kuma Ya sanya soyayya a tsakanin zukatansu. Da ka ciyar da abin da yake cikin ƙasa, gaba ɗaya, da ba ka sanya soyayya a tsakanin zukatansu ba, kuma amma Allah Ya sanya soyayya a tsakaninsu. Lalle Shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [64] Ya kai Annabi! Ma'ishinka Allah ne, kai da wanda ya biye maka daga muminai

    [65] Ya kai Annabi! Ka kwaɗaitar da muminai a kan yaƙi. Idan mutum ashirin masu haƙuri sun kasance daga gare ku, za su rinjayi metan kuma idan ɗari suka kasance daga gare ku, za su rinjayi dubu daga waɗanda suka kafirta, domin su, mutane ne ba su fahimta

    [66] A yanzu Allah Ya sauƙaƙe daga gare ku, kuma Ya sani cewa lalle ne akwai masu rauni a cikinku. To, idan mutum ɗari, masu haƙuri, suka kasance daga gare ku, za su rinjayi metan, kuma idan dubu suka kasance daga gare ku, za su rinjayi dubu biyu, da iznin Allah. Kuma Allah Yana tare da masu haƙuri

    [67] Ba ya kasancewa ga wani annabi, kamammu su kasance a gare shi sai (bayan) ya zubar da jinainai a cikin ƙasa. Kuna nufin sifar duniya kuma Allah Yananufin Lahira. Kuma Allah ne Mabuwayi, Mai hikima

    [68] Ba domin wani Littafi daga Allah ba, wanda ya gabata, da azaba mai girma daga Allah ta shafe ku a cikin abin da kuka kama

    [69] Saboda haka, ku ci daga abin da kuka samu ganima, Yana halal mai kyau. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [70] Ya kai Annabi! Ka ce wa wanda yake a cikin hannayenku daga kamammu: "Idan Allah Ya san akwai wani alheri a cikin zukatanku, zai kawo muku mafi alheri daga abin da aka karɓa daga gare ku, kuma Ya yi muku gafara. Kuma Allah ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [71] Kuma idan sun yi nufin yaudararka, to, haƙiƙa, sun yaudari Allahdaga gabani sai Ya bayar da dama daga gare su: Kuma Allah ne Masani, Mai hikima

    [72] Lalle ne waɗanda suka yi imani, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihadi da dukiyoyinsuda rayukansu, a cikin hanyar Allah, da waɗanda suka bayar da masauki, kuma suka yi taimako. Waɗancan, sashensu waliyyai ne ga sashe. Kuma waɗanda suka yi imani kuma ba su yi hijira ba, ba ku da wani abu daga waliccinsu, sai sun yi hijira. Kuma idan suka neme ku taimako a cikin addini, to taimako ya wajaba a kanku, face a kan mutane waɗanda a tsakaninku da tsakaninsu akwai wani alkwari. Kuma Allah ne, ga abin da kuke aikatawa, Mai gani

    [73] Kuma waɗanda suka kafirta sashensu ne waliyyan sashe, idan ba ku aikata shi ba, wata fitina za ta kasance a cikin ƙasa, da fasadi babba

    [74] Kuma waɗanda suka yi imani kuma suka yi hijira, kuma suka yi Jihadi, a cikin hanyar Allah, kuma da waɗanda suka bayar da masauki, kuma suka yi tamiako, waɗannan su ne muminai da gaskiya, sunada gafara da wani abinci na karimci

    [75] Kuma waɗanda suka yi imani daga baya, kuma suka yi hijira kuma suka yi jihadi tare da ku, to, waɗannan daga gare ku suke. Kuma ma'abuta zumunta, sashensu ne waliyyan sashe a cikin Littafin Allah. Lalle Allah ne ga dukkan kome Masani

    Tuba

    Surah 9

    [1] Barranta daga Allah da ManzonSa zuwa ga waɗanda kuka yi wa alkawari daga masu shirki

    [2] Saboda haka ku yi tafiya a cikin ƙasa wata huɗu, kuma ku sani lalle ku, ba masu buwayar Allah ba ne, kuma lalle Allah ne Mai kunyatar da kafirai

    [3] Kuma da yekuwa daga Allah da ManzonSa zuwa ga mutane, a Ranar Haji Babba cewa lallene Allah Barrantacce ne daga masu shirki, kuma ManzonSa (haka). To, idan kun tuba to shi ne mafi alheri a gare ku, kuma idan kun juya, to, ku sani lalle ne ku, ba masu buwayar Allah ba ne. Kuma ka bayar da bishara ga waɗanda suka kafirta, da azaba mai raɗaɗi

    [4] Sai waɗanda kuka yi wani alkawari daga masu shirki, sa'an nan kuma ba su rage ku da kome ba, kuma ba su taimaki kowa a kanku ba, to, ku cika alkawarin, zuwa gare su, har ga iyakar yarjejeyarsu. Lalle ne Allah Yana son masu taƙawa

    [5] Kuma idan watanni, masu alfarma suka shige, to, ku yaki mushirikai inda kuka same su, kuma ku kama su, kuma ku tsare su, kuma ku zaune musu dukkan madakata. To, idan sun tuba, kuma suka tsayar da salla, kuma suka bayar da zakka to ku sakar musu da hanyarsu. Lalle Allah ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [6] Idan wani daga mushirikai ya nemi maƙwabtakarka to, ka ba shi maƙwabtakar har ya ji, maganar Allah, sa'an nan ka isar da shi ga wurin amincewarsa. Wancan fa domin lalle ne su, mutane ne waɗanda ba su sani ba

    [7] Yaya wani alkawari a wurin Allah a wurin ManzonSa yake kasancewa ga mushirikai, face ga waɗanda kuka yi wa alkawari wurin Masallaci Mai alfarma? To matuƙar sun tsaya sosai gare ku, sai ku tsayu sosai gare su. Lalle ne Allah Yana son masu taƙawa

    [8] Yaya, alhali idan sun ci nasara a kanku, ba za su tsare wata zumun ta ba a cikinku, kuma haka wata amana, suna yardar da ku da bakunansu kuma zukatansu suna ƙi? Kuma mafi yawansu fasiƙai ne

    [9] Sun saya da ayoyin Allah, 'yan kuɗi kaɗan, sa'an nan suka kange daga hanyar Allah. Lalle ne su, abin da suka kasance suna aikatawa ya munana

    [10] Ba su tsaron wata zumunta a cikin muminai, kuma haka basu tsaron wata amana. Kuma waɗannan ne masu ta'adi

    [11] Sa'an nan idan sun tuba kuma suka tsayar da salla, kuma suka bayar da zakka, to, 'yan'uwanku ne a cikin addini, kuma Muna rarrabe ayoyi daki-daki, ga mutane waɗanda suke sani

    [12] Kuma idan suka warware rantsuwoyin amana daga bayan alkawarinsu, kuma suka yi suka a cikin addininku, to, ku yaki shugabannin kafirci. Lalle ne su, babu rantsuwoyin amana a gare su. Tsammaninsu suna hanuwa

    [13] Shin, ba ku yaƙin mutane, waɗanda suka warware rantsuwoyinsu, kuma suka yi niyya ga fitar da Manzo, kuma su ne suka fara muku, tun a farkon lokaci? Shin kuna tsoron su ne? To, Allah ne marfi cancantar ku ji tsoronSa, idan kun kasance muminai

    [14] Ku yaƙe su, Allah Ya yi musu azaba da hannayenku, kuma Ya kunyatar da su, kuma Ya taimake ku, kuma Ya warkar da ƙirazan mutane muminai

    [15] Kuma Ya tafi da fushin zukatansu, kuma Ya karɓi tuba a kan wanda Ya so. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima

    [16] Ko kuna zaton a bar ku, tun Allah bai bayyana waɗanda suka yi jihadi ba daga gare ku, kuma su ba su riƙi wani shigeba, baicin Allah da ManzonSa da muminai? Kuma Allah ne Mai jarrabawa ga abin da kuke aikatawa

    [17] Ba ya kasancewa ga masu shirki su raya masallatan Allah, alhali kuwa suna masu bayar da shaida a kan rayukansu da kafirci, waɗannan ayyukansu sun ɓaci, kuma a cikin wuta su madawwama

    [18] Abin sani kawai, mai raya masallatan Allah, shi ne wanda ya yi imani da Allah da Ranar Lahira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bayar da zakka, kuma bai ji tsoron kowa ba face Allah. To, akwai tsammanin waɗannan su kasance daga shiryayyu

    [19] Shin, kun sanya shayar da mahajjata da rayar da Masallaci Mai alfarma kamar wanda ya yi imani da Allah da Ranar Lahira, kuma ya yi jihaɗi a cikin hanyar Allah? Ba su daidaita a wurin Allah. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [20] Waɗanda suka yi imani, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihadi, a cikin hanyar Allah, da dukiyoyinsu, da rayukansu, su ne mafi girma ga daraja, a wurin Allah, kuma waɗannan su ne masu babban rabo

    [21] Ubangijinsu Yana yi musu bishara da wata rahama daga gare shi, da yarda, da gidajen Aljanna. suna da, a cikinsu, ni'ima zaunanniya

    [22] Suna madawwama a cikinsu, har abada. Lalle ne Allah a wurinSa akwai lada mai girma

    [23] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku riƙi ubanninku da 'yan'uwanku masoya, idan sun nuna son kafirci a kan imani. Kuma wanda ya jiɓince su daga gare ku, to, waɗannan su ne azzalumai

    [24] Ka ce: "Idan ubanninku da ɗiyanku da 'yan'uwanku da matanku da danginku da dukiyoyi, waɗanda kuka yi tsiwirwirinsu, da fatauci wanda kuke tsoron tasgaronsa, da gidaje waɗanda kuke yarda da su, sun kasance mafiya soyuwa a gare ku daga Allah da ManzonSa, da yin jihadi ga hanyarSa, to, ku yi jira har Allah Ya zo da umurninSa! Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane fasiƙai

    [25] Lalle ne, haƙiƙa, Allah Ya taimake ku a cikin wurare masu yawa, da Ranar Hunainu, a lokacin da yawanku ya ba ku sha'awa, sai bai amfanar da ku da kome ba, kuma ƙasa ta yi ƙunci a kanku da yalwarta, sa'an nan kuma kuka juya kuna masu bayar da baya

    [26] Sa'an nan kuma Allah Ya saukar da natsuwarSa a kan ManzonSa kuma a kan muminai, kuma Ya saukar da rundunoni waɗanda ba ku gan su ba, kuma Ya azabtar da waɗanda suka kafirta: Wancan ne sakamakon kafirai

    [27] Sa'an nan kuma Allah Ya karɓi tuba daga bayan wancana kan wanda Ya so. Kuma Allah ne Mai gafara, Mai rahama

    [28] Ya ku waɗanda suka yi imani! Abin sani kawai, mushirikai najasa ne, saboda haka kada su kusanci Masallaci Mai alfarma a bayan shekararsu wannan. Kuma idan kun ji tsoron talauci to, da sannu Allah zai wadata ku daga falalarSa, idan Ya so. Lalle Allah ne Masani, mai hikima

    [29] Ku yaƙi waɗanda ba su yin imani da Allah kuma ba su imani da Ranar Lahira kumaba su haramta abin da Allah da ManzonSa suka haramta, kuma ba su yin addini, addinin gaskiya, daga waɗanda aka bai wa Littafi, har sai sun bayar da jizya daga, hannu, kuma suna ƙasƙantattu

    [30] Kuma Yahudawa suka ce: "Uzairu ɗan Allah ne."Kuma Nasara suka ce: "Masihu ɗan Allah ne." Wancan zancensu ne da bakunansu. Suna kama da maganar waɗanda suka kafirta daga gabani. Allah Ya la'ance su! Yaya aka karkatar da su

    [31] Sun riƙi malamansu (Yahudu) da ruhubanawansu (Nasara) Ubannangiji, baicin Allah, kuma sun riƙi Masihu ɗan Maryama (haka). Kuma ba a umurce su ba face da su bauta wa Ubangiji Guda. Babu abin bautawa face Shi. TsarkinSa ya tabbata daga barin abin da suke yin shirki da shi

    [32] Suna nufin su bice hasken Allah da bakunansu. Kuma Allah Yana ki, face dai Ya cika haskenSa, kuma ko da kafirai sun ƙi

    [33] Shi ne wanda Ya aiko manzonSa da shiriya da addinin gaskiya, domin ya bayyanl shi a kan addini dukansa, kuma ko da mushirikai sun ƙi

    [34] Ya waɗanda suka yi imani! Lalle ne masu yawa daga Ahbar da Ruhbanawa haƙiƙa suna cin dukiyar mutane da ƙarya, kuma suna kangewa daga hanyar Allah. Kuma waɗanda suke taskacewar zinariya da azurfa, kuma ba su ciyar da ita a cikin hanyar Allah, to, ka yi musu bushara da azaba mai raɗaɗi

    [35] A Ranar da ake ƙona shi a kanta a cikin wutar Jahannama, sai a yi lalas da ita ga goshinansu da sashinansu da bayayyakinsu, (a ce musu): "Wannan ne abin da kuka taskace domin rayukanku. To, ku ɗanɗani abin da kuka kasance kuna sanyawa a taska

    [36] Lallai ne ƙidayayyun watanni a wurin Allah wata goma sha biyu ne a cikin Littafin Allah, a Ranar da Ya halicci sammai da ƙasa daga cikinsu akwai huɗu masu alfarma. Wannan ne addini madaidaici. Saboda haka kada ku zalunci kanku a cikinsu. Kuma ku yaƙi mushirikai gaba ɗaya, kamar yadda suke yaƙar ku gaba ɗaya. Kuma ku sani cewa lallai ne Allah Yana tare da masu taƙawa

    [37] Abin sani kawai, "Jinkirtawa" ƙari ne a cikin kafirci, ana ɓatar da waɗanda suka kafirta game da shi. Suna halattar da wata a wata shekara kuma su haramtar da shi a wata shekara domin su dace da adadin abin da Allah Ya haramta. Saboda haka suna halattar da abin da Allah Ya haramtar. An ƙawace musu munanan ayyukansu. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai

    [38] Ya ku waɗanda suka yi imani! Mene ne a gare ku, idan ance muku, "Ku fita da yaƙi a cikin hanyar Allah," sai ku yi nauyi zuwa ga ƙasa. Shin, kun yarda da rayuwar duniya ne daga ta Lahira? To jin daɗin rayuwar duniya bai zama ba a cikin Lahira, face kaɗan

    [39] Idan ba ku fita da yaƙi ba, Allah zai azabta ku da azaba mai raɗaɗi, kuma Ya musanya wasu mutane, wasunku (a maimakonku). Kuma ba za ku cutar da Shida kome ba. Kuma Allah a kan dukan kome Mai ikon yi ne

    [40] Idan ba ku taimake shi ba, to, lalle ne Allah Ya taimake shi, a lokacin da waɗanda suka kafirta suka fitar da shi, Yana na biyun biyu, a lokacin da suke cikin kogon dutse, a lokacin da yake cewa da sahibinsa: "Kada ka yi baƙin ciki, lalle ne Allah Yana tare da mu." Sai Allah Ya saukar da natsuwarSa a kansa, kuma Ya taimake shi da waɗansu rundunoni, ba ku gan su ba, kuma Ya sanya kalmar waɗanda suka kafirta maƙasƙanciya, kuma kalmar Allah ita ce maɗaukakiya. Kuma Allah ne Mabuwayi, Mai hikima

    [41] Ku fita da yaƙi kuna masu sauƙaƙan kaya da masu nauyi, kuma ku yi jihadi da dukiyoyinku da kuma rayukanku a cikin hanyar Allah. Wancan ne mafi alheri a gare ku, idan kun kasance kuna sani

    [42] Da ya kasance wata siffar duniya ce: makusanciya, da tafiya matsakaiciya, da sun bi ka, kuma amma fagen ya yi musu nisa. Kuma za su yi ta yin rantsuwa da Allah, "Da mun sami dama, da mun tafi tare da ku." Suna halakar da kansu (da rantsuwar ƙarya) ne, kuma Allah Yana sanin lalle, haƙiƙa, sumaƙaryata ne

    [43] Allah Ya yafe maka laifi. Domin me ka yi musu izinin zama? Sai waɗanda suka yi gaskiya ssun bayyana a gare ka, kuma ka san maƙaryata

    [44] Waɗanda suke yin imanida Allah da Ranar Lahira, ba za su nemi izininka ga yin, jihadida dukiyoyinsu da rayukansu ba. Kuma Allah ne Masani ga masu taƙawa

    [45] Abin sani kawai, waɗanda ba sa imani da Allah, da Ranar Lahira, kuma zukatansu suka yi shakka, su ne ke neman izininka, sa'an nan a cikin shakkarsu suna ta yin kai kawo

    [46] Kuma da sun yi nufin fita, da sun yi wani tattali saboda shi, kuma amma Allah Ya ƙi zaburarsu, sai Ya nauyayar da zamansu. Kuma aka ce ku zauna tare da masu zama

    [47] Da sun fita a cikinku ba za su ƙare ku da kome ba face da ɓarna, kuma lalle da sun yi gaggawar sanya annamimanci a tsakaninku, suna nema muku fitina. Kuma a cikinku akwai 'yan rahoto saboda su. Kuma Allah ne Masani ga azzalumai

    [48] Kuma lalle ne, haƙiƙa sun nemi fitina daga gabani, kuma, suka juya maka al'amari, har gaskiya ta zo, kuma umurnin Allah Ya bayyana, alhali suna masu ƙyama

    [49] Kuma daga cikinsu akwai mai cewa, "Ka yi mini izinin zama, kuma kada ka fitine ni." To, a cikin fitinar suka faɗa. Kuma lalle ne Jahannama, haƙiƙa, mai ƙewayewa ce ga kafirai

    [50] Idan wani alheri ya same ka, zai ɓata musu rai, kuma idan wata masifa ta same ka sai su ce: "Haƙiƙa, mun riƙe al'amarinmu daga gabani."Kuma sujuya, alhali kuwa suna masu farin ciki

    [51] Ka ce: "Babu abin da yake samun mu face abin da Allah Ya rubuta sahoda mu. Shi ne Majiɓincinmu. Kuma ga Allah, sai muminai su dogara

    [52] Ka ce: "Shin, kuna dako ne da mu? Face dai da ɗayan abubuwan biyu masu kyau, alhali kuwa mu, muna dako da ku, AllahYa same ku da wata azaba daga gare Shi, ko kuwa da hannayenmu. To, ku yi dako. Lalle ne mu, tare da ku masu dakon ne

    [53] Ka ce: "Ku ciyar a kan yarda ko kuwa a kan tilas. Ba za a karɓa daga gare ku ba. Lalle ne ku, kun kasance mutane fasiƙai

    [54] Kuma babu abin da ya hana a karɓi ciyarwarsu daga gare su face domin su, sun kafirta da Allah da ManzonSa, kuma ba su zuwa ga salla face Luma suna masu kasala, kuma ba su ciyarwa face suna masu ƙyama

    [55] Saboda haka, kada dukiyoyinsu su ba ka sha'awa, kuma haka 'ya'yansu. Abin sani kawai, Allah Yana nufin Ya yi musu azaba, da su a cikin rayuwar duniya, kuma rayukansu su fita alhali kuwa suna kafirai

    [56] Kuma suna rantsuwa da Allah cewa, lalle ne su, haƙiƙa, daga gare ku suke, alhali kuwa ba su zamo daga gare ku ba. Kuma amma su mutane ne masu tsoro

    [57] Da suna samun mafaka ko kuwa waɗansu ɓuloli, ko kuwa wani mashigi, da sun, juya zuwa gare shi, kuma suna gaggawar shiga

    [58] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake zunɗen ka a kan sha'anin dukiyoyin sadaka, sai idan an ba su daga cikinta, su yarda, kuma idan ba a ba su ba daga cikinta sai su zamo suna masu fushi

    [59] Kuma da dai su lalle sun yarda da abin da Allah Ya ba su, da ManzonSa kuma suka ce: "Ma'ishinmu Allah ne, zai kawo mana daga falalarSa kuma ManzonSa (zai ba mu). Lalle ne mu, zuwa ga Allah masu kwaɗayi ne

    [60] Abin sani kawai, dukiyoyin sadaka na faƙirai ne da miskinai da masu aiki a kansu, da waɗanda ake lallashin zukatansu, kuma a cikin fansar wuyoyi, da mabarta, da a cikin hanyar Allah da ɗan hanya (matafiyi). Farilla daga Allah. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima

    [61] Kuma daga cikinsu akwai waɗanda suke cutar Annabi, kuma suna cewa "Shi kunne ne." Ka ce: "Kunnen alheri gare ku, Yana imani da Allah, kuma Yana yarda da muminai, kuma rahama ne ga waɗanda suka yi imani daga gare ku."Kuma waɗanda suke cutar Manzon Allah suna da azaba mai raɗaɗi

    [62] Suna rantsuwa da Allah saboda ku, domin su yardar da ku. Kuma Allah da ManzonSa ne mafi cancantar su yardar da Shi, idan sun kasance muminai

    [63] Shin, ba su sani ba cewa "Lalle ne wanda ya saɓa wa Allah da ManzonSa, haƙiƙa Yana da wutar Jahannama, Yana madawwami a cikinta? Waccan ita ce wulakantawa babba

    [64] Munafukai suna tsoron a saukar da wata sura a kansu, wadda take ba su labari ga abin da yake cikin zukatansu. Ka ce: "Ku yi izgili. Lalle ne, Allah ne Mai fitai da abin da kuke tsoro

    [65] Kuma lalle ne, idan ka tambaye, su haƙiƙa, suna cewa, "Abin sani kawai, mun kasance muna hira kuma muna wasa. Ka ce: "Shin da Allah, da kuma ayoyinSa da ManzonSa kuka kasance kuna izgili

    [66] Kada ku kawo wani uzuri, haƙiƙa, kun kafirta a bayanimaninku. Idan Mun yafe laifi ga wata ƙungiya daga gare ku, za Mu azabta wata ƙungiya saboda, lalle, sun kasance masu laifi

    [67] Munafukai maza da munafukai mata, sashensu daga sashe, suna umurni da abin ƙi kuma suna hani daga alheri. Kuma suna damƙewar hannayensu. Sun mance Allah, sai Ya manta da su. Lalle ne munafukai su ne fasiƙai

    [68] Allah ya yi wa'adi ga munafukai maza da munafukai mata da kafirai da wutar Jahannama, suna madawwama a cikinta. Ita ce ma'ishiyarsu. Kuma Allah Ya la'ance su, kuma suna da azaba zaunanniya

    [69] Kamar waɗanda suke a gabaninku, sun kasance mafi tsananin ƙarfi daga gare ku, kuma mafi yawan dukiyoyi da ɗiya. Sai suka ji daɗi da rabonsu, sai kuka ji daɗi da rabonku kamar yadda waɗanda suke a gabaninku suka ji daɗi, da rabonsu, kuma kuka kutsa kamar kutsawarsu. Waɗancan ayyukansu sun ɓaci a duniya da Lahira, kuma waɗannan su ne masu hasara

    [70] Shin labarin waɗanda suke a gabaninsu bai je musu ba, mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa da mutanen Ibrahim da Ma'abuta Madyana da waɗanda aka birkice? Manzanninsu sun je musu da ayoyayi bayanannu. To, Allah bai kasance Yana zaluntar su ba, amma sun kasance rayukansu suke zalunta

    [71] Kuma mummunai maza da mummunai mata sashensu majiɓincin sashe ne, suna umurni da alheri kuma suna hani daga abin da ba a so, kuma suna tsayar da salla, kuma suna bayar da zakka, kuma sunaɗa'a ga Allah da ManzonSa. Waɗannan Allah zai yi musu rahama. Lalle Allah ne Mabuwayi, Mai hikima

    [72] Kuma Allah Ya yi wa'adi ga mummunai maza da mummunai mata da gidajen Aljanna ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu, da wuraren zama masu daɗi a cikin gidajen Aljannar. Kuma yarda daga Allah ce mafi girma. Wancan shi ne babban rabo, mai girma

    [73] Ya kai Annabi! Ka yaƙi kafirai da munafukai kuma ka tsaurara a kansu. Kuma matattararsu Jahannama ce. Tir da ta zama makomar

    [74] Suna rantsuwa da Allah, ba su faɗa ba, alhali kuwa lalle ne, haƙiƙa, sun faɗi kalmar kafirci, kuma; sun kafirta a bayan musuluntarsu, kuma sun yi himma ga abin da ba su samu ba. Kuma ba su zargi kome ba face domin Allah da ManzonSa Ya wadatar da su daga falalarSa. To, idan sun tuba zai kasance mafi alheri gare su, kuma idan sun juya baya, Allah zaiazabta su da azaba mai raɗaɗi a cikin duniya da Lahira, kuma ba su da wani masoyi ko wani mataimaki a cikin kasa

    [75] Kuma daga cikinsu akwai wadɗanda suka yi wa Allah alkawari, "Lalle ne idan ya kawo mana daga falalarSa, haƙiƙa, munabayar da sadaka, kuma lalle ne muna kasancewa, daga salihai

    [76] To, a lokacin da Ya ba su daga falalarSa, sai suka yi rowa da shi, kuma suka juya baya suna masu bijirewa

    [77] Sai Ya biyar musu da munafunci a cikin zukatansu har zuwa ga Ranar da suke haɗuwa da Shi saboda saɓa wa Allah a abin da suka yi Masa alkawari, kuma saboda abin da suka kasance suna yi na ƙarya

    [78] Shin, ba su sani ba cewa lalle ne Allah Yana sanin asirinsuda ganawarsu, kuma lalle Allah ne Masanin abubuwan fake

    [79] Waɗanda suke aibanta masu yin alheri daga mummunaia cikin dukiyoyin sadaka, da waɗanda ba su samu face iyakar ƙoƙarinsu, sai sana yi musu izgili. Allah Yana yin izgili gare su. Kuma suna da azaba mai raɗaɗi

    [80] Ko ka nema musu gafara ko ba ka nema musu ba, idan ka nema musu gafara sau saba'in, to, Allah ba zai gafarta musu ba. Saboda su, sun kafirta da Allah da ManzonSa. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane fasiƙai

    [81] Waɗanda aka bari sun yi farin ciki da zamansu a bayan Manzon Allah, kuma suka ƙi su yi jihadi da dukiyoyinsu da rayukansu a cikin hanyar Allah, kuma suka ce: "Kada ku fita zuwa yaƙi a cikin zafi."Ka ce: "Wutar Jahannama ce mafi tsanlnin zafi." Da sun kasance suna fahimta

    [82] Saboda haka su yi dariya kaɗan, kuma su yi kukada yawa a kan sakamako ga abin da suka kasance suna tsirfatawa

    [83] To, idan Allah Ya mayar da kai zuwa ga wata ƙungiya daga gare su sa'an nan suka neme ka izni domin su fita, to, ka ce: "Ba za ku fita tare da ni ba har abada, kuma ba za ku yi yaƙi tare da ni ba a kan wani maƙiyi. Lalle ne ku, kun yarda da zama a farkon lokaci, sai ku zauna tare da mata masu zaman gida

    [84] Kuma kada ka yi salla a kan kowa daga cikinsu wanda ya mutu, har abada, kuma kada ka tsaya a kan kabarinsa. Lalle ne su, sun kafirta da Allah da ManzonSa, kuma sun mutu alhali kuwa suna fasiƙai

    [85] Kuma kada dukiyoyinsu da ɗiyansu su ba ka sha'awa. Abin sani kawai, Allah Yana nufin Ya yi musu azaba da su a cikin duniya, kuma rayukansu su fita alhali kuwa suna kafirai

    [86] Kuma idan aka saukar da wata sura cewa; Ku yi imani da Allah kuma ku yi jihadi tare da ManzionSa. Sai mawadata daga gare su su nemi izninka, kuma su ce: Ka bar mu mu kasance tare da mazauna

    [87] Sun yarda da su kasance tare da mata masu zama (a cikin gidaje). Kuma aka rufe a kan zukatansu, saboda haka, su, ba su fahimta

    [88] Amma Manzon Allah da waɗanda suka yi imani tare da shi, sun yi jihadi da dukiyoyinsu da rayukansu. Kuma waɗannan suna da ayyukan alheri, kuma waɗannan su ne masu cin nasara

    [89] Allah ya yi musu tattalin gidajen Aljanna, ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu. Wancan ne babban rabo mai girma

    [90] Kuma masu uzuri daga ƙauyawa zuka zo domin a yi musu izini, kuma waɗanda suka yi wa Allah da ManzonSa ƙarya, suka yi zamansu. wata azaba mai raɗaɗi za ta sami waɗanda suka kafirta daga gare su

    [91] Babu laifi a kan maraunana kuma haka majinyata, kuma babu laifi a kan waɗanda ba su samun abin da suke ciyarwa idan sun yi nasiha ga Allah da ManzonSa. Kuma babu wani laifi a kan masu kyautatawa. Kuma Allah ne Mai gafara, Mai tausayi

    [92] Kuma babu (laifi) a kan waɗanda idan sun je maka domin ka ɗauke su ka ce: "Ba ni da abin da nake ɗaukar ku a kansa," suka juya alhali kuwa idanunsu suna zubar da hawaye domin baƙin ciki cewa ba su sami abin da suke ciyarwa ba

    [93] Abin sani kawai, laifi Yana a kan waɗanda suke neman izininka alhali kuwa su mawadata ne. Sun yarda su kasance tare da mata mamaya (gidaje), kuma Allah Ya danne a kan zukatansu, domin haka su, ba su ganewa

    [94] Suna kawo uzurinsu zuwa gare ku idan kun koma zuwa gare su Ka ce: "Kada ku kawo wani uzuri, ba za mu amince muku ba. Haƙiƙa, Allah Ya ba mu labari daga labarunku, Allah zai ga aikinku kuma ManzonSa (zai gani). Sa'an nan kuma a mayar da ku zuwa ga Masanin gaibi da bayyane, sai Ya ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [95] Za su yi rantsuwa da Allah a gare ku idan kun juya zuwa gare su, domin ku kau da kai daga gare su. To, ku kau da kai daga gare su don ko su ƙaranta ne, kuma Jahannama ce matattararsu bisa ga sakamakon abin da suka kasance suna tsirfatawa

    [96] Suna rantsuwa gare ku domin ku yarda da su. To, idan kun yarda da su, to, lalle ne Allah ba shi yarda da mutane fasiƙai

    [97] ¡auyawa ne mafi tsananin kafirci da munafinci, kuma sune mafi kamanta ga, rashin sanin haddojin abin da Allah Ya saukar a kan ManzonSa. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima

    [98] Kuma daga ƙauyawa akwai waɗanda suke riƙon abin da suke ciyarwa a kan tara ce, kuma suna sauraron aukuwar masifa a gare ku, aukuwar mummunar masifa ta tabbata a kansu. Kuma Allah ne Mai ji, Masani

    [99] Kuma daga ƙauyawa akawi waɗanda suke yin imanida Allah da Ranar Lahira, kuma suna riƙon abin da suke ciyarwa (tamkar) waɗansu ibadodin neman kusanta ne a wurin Allah da addu'o'in ManzonSa. To, lalle ne ita (ciyarwar nan) ibadar neman kusanta ce a gare su. Allah zai shigar da su a cikin RahamarSa. Lalle Allah ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [100] Kuma masu tserewa na farko daga Muhajirina da Ansar da waɗanda suka bi su da kyautatawa, Allah Ya yarda daga gare su su kuma sun yarda daga gare Shi, kuma Ya yi masu tattalin gidajen Aljanna; ¡oramu suna gudana a ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma

    [101] Kuma daga waɗanda suke a gefenku daga ƙauyawa akwai munafukai, haka kuma daga mutanen Madnia. Sun goge a kan munafunci, ba ka sanin su, Mu ne Muke sanin su. za Mu yi musu azaba sau biyu, sa'an nan a mayar da su zuwa ga azaba mai girma

    [102] Kuma da waɗansu, sun yi furuci da laifinsu, sun haɗa aiki na ƙwarai da wani mummuna. Akwai tsammanin Allah Ya karɓi tuba a kansu. Lallai Allah ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [103] Ka karɓi sadaka daga dukiyoyinsu kana tsarkake su, kuma kana tabbatar da kirkinsu da ita. Kuma ka yi musu addu'a. Lallai addu'o'inKa natsuwa ne a gare su. Kuma Allah ne Mai ji, Masani

    [104] Shin, ba su sani ba cewa lallai Allah, ne Yake karɓar tuba daga bayinSa, kuma Yana karɓar sadakokinsu, kuma lalle Allah ne Mai karɓar tuba, Mai jin ƙai

    [105] Kuma ka ce: "Ku yi aiki, sa'an nan Allah zai ga aikinku, da ManzonSa da Muminai kuma za a mayar da ku zuwa ga masanin fake da bayyane, sa'an nan Ya ba ku labari ga abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [106] Kuma da waɗansu waɗanda aka jinkirtar ga umurnin Allah, ko dai Ya yi musu azaba ko kuma Ya karɓi tuba a kansu. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima

    [107] Kuma waɗanda suka riƙi wani masallaci domin cuta da kafirci da neman rarrabewa a tsakanin muminai da fakewa ga taimakon wanda ya yaƙi Allah da ManzonSa daga gabani, kuma haƙiƙa suna yin rantsuwa cewa, "Ba mu yi nufin komai ba face alheri", alhali kuwa Allah Yana yin shaida cewa, su, haƙiƙa, maƙaryata ne

    [108] Kada ka tsaya a cikinsa har abada. Lalle ne, Masallaci wanda aka yi harsashinsa a kan taƙawa tun farkon yini, shi ne mafi cancantar ka tsaya a cikinsa. A cikinsa akwai waɗansu maza suna son su tsarkaka. Kuma Allah Yana son masu neman tsarkakuwa

    [109] Shin, wanda ya sanya harsashin gininsa a kan taƙawa daga Allah da yarda, shi ne mafi alheri ko kuwa wanda ya sanya harsashin gininsa a kan gaɓar rami mai tusgawa? Sai ya rusa da shi a cikin wutar Jahannama. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [110] Gininsu, wanda suka gina, ba zai gushe ba Yana abin shakka a cikin zukatansu face idan zukatansu sun yanyanke. Kuma Allah ne Masani, Mai Hikima

    [111] Lalle ne, Allah Ya saya daga mummunai, rayukansu da dukiyoyinsu, da cewa suna da Aljanna, suna yin yaƙi a cikin hanyar Allah, saboda haka suna kashewa ana kashe su. (Allah Ya yi) wa'adi a kanSa, tabbace a cikin Attaura da Linjila da Alƙur'ani. Kuma wane ne mafi cikawa da alkawarinsa daga Allah? Saboda haka ku yi bushara da cinikinku wanda kuka ƙulla da Shi. Kuma wancan shi ne babban rabo, mai girma

    [112] Masu tuba, masu bautawa, masu godewa, masu tafiya, masu ruku'i, masu sujada masu umurni da alheri da masu hani daga abin da aka ƙi da masu tsarewaa ga iyakokin Allah. Kuma ka bayar da bushara ga muminai

    [113] Ba ya kasancewa ga Annabi da waɗanda suka yi imani, su yi istigifari ga mushirikai, kuma ko da sun kasance ma'abuta zumunta ne daga bayan sun bayyana a gare su, cewa lalle ne, su, 'yan Jahim ne

    [114] Kuma istigifarin Ibrahim ga ubansa bai kasance ba face saboda wani wa'adi ne da ya ƙulla alƙawarinsa da shi, sa'an nan a lokacin da ya bayyana a gare shi (Ibrahim) cewa lalle ne shi (ubansa) maƙiyi ne ga Allah, sai ya barranta daga gare shi. Lalle ne Ibrahim, haƙiƙa, mai yawan addu'a ne, mai haƙuri

    [115] Kuma Allah bai kasance mai ɓatar da mutane a bayan Ya shiryar da su ba, sai Ya bayyana musu abin da za su yi taƙawa da shi. Lalle ne Alllh, ga kome, Masani ne

    [116] Lalle ne Allah Yana da mulkin sammai da ƙasa, Yana rayarwa kuma Yana matarwa. Kuma ba ku da wani masoyi, kuma ba ku da mataimaki, baicin Allah

    [117] Lalle ne, haƙiƙa, Allah Ya karɓi tubar Anbabi da Muhajirina da Ansar waɗanda suka bi shi, a cikin sa'ar tsanani, daga baya zukatan wani ɓangare daga gare su sun yi kusa su karkata, sa'an nan (Allah) Ya karɓi tubarsu. Lalle, Shi ne Mai tausayi, Mai jin ƙai gare su

    [118] Kuma (Allah) Ya karɓi tuba a kan ukun nan waɗanda aka jinkirtar har ƙasa da yalwarta ta yi ƙunci a kansu, kuma rayukansu suka yi ƙunci a kansu, kuma suka yi zaton babu wata mafaka daga Allah face (komawa) zuwa gare Shi. Sa'an nan Allah Ya karɓi tubarsu, domin su tabbata a kan tuba. Lalle Allah ne Mai karɓar tuba, Mai jin ƙai

    [119] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku kasance tare da masu gaskiya

    [120] Ba ya kasancewa ga mutanen Madina da wanda yake a gefensu, daga ƙauyawa, su saba daga bin Manzon Allah, kuma kada su yi gudu da rayukansu daga ransa. Wancan, saboda ƙishirwa ba ta samun su, haka kuma wata wahala, haka kuma wata yunwa, a cikin hanyai Allah, kuma ba su takin wani mataki wanda yake takaitar da kafirai kuma ba su samun wani samu daga maƙiyi face an rubuta musu da shi, ladar aiki na ƙwarai. Lallai ne Allah ba Ya tozarta ladar masu kyautatawa

    [121] Kuma ba su ciyar da wata ciyarwa, ƙarama ko babba, kuma ba su keta wani rafi sai an rubuta musu, domin Allah Ya saka musu da mafi kyawon abin da suka kasance suna aikatawa

    [122] Kuma ba ya kasancewa ga muminai su fita zuwa yaƙi gaba ɗaya. Saboda haka, don me ne wata jama'a daga kowane ɓangare daga gare su ba ta fita (zuwa neman ilimi ba) domin su nemi ilimi ga fahimtar addini kuma domin su yi gargaɗi ga mutanensu idan sun koma zuwa gare su, tsammaninsu, suna yin sauna

    [123] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yaƙi waɗanda suke kusantar ku daga kafirai. Kuma su sami tsanani daga gare ku. Kuma ku sani cewa Allah Yana tare da masu taƙawa

    [124] Kuma idan aka saukar da wata sura, to, daga gare su akwai waɗanda suke cewa: "Wane a cikinku wannan sura ta ƙara masa imani?" To amma waɗanda suka yi imani, kuma su, suna yin bushara (da ita)

    [125] Amma kuma waɗanda suke a cikin zukatansu akwai cuta, to, ta ƙara musu ƙazanta zuwa ga ƙazantarsu, kuma su mutu alhalin kuwa suna kafirai

    [126] Shin, ba su ganin cewa ana fitinar su a cikin kowace shekara: Sau ɗaya ko kuwa sau biyu, sa'an nan kuma ba su tuba, kuma ba su zama suna tunani ba

    [127] Kuma idan haƙiƙa, aka saukar da wata sura, sai sashensu ya yi dubi zuwa ga wani sashe, (su ce): "Shin, wani mutum yana ganin ku?" Sa'an nan kuma sai su juya. Allah Ya juyar da zukatansu, domin, haƙiƙa su mutane ne, ba su fahimta

    [128] Lalle ne, haƙiƙa, Manzo daga cikinku ya je muku. Abin da kuka wahala da shi mai nauyi ne a kansa. Mai kwaɗayi ne saboda ku. Ga muminai Mai tausayi ne, Mai jin ƙai

    [129] To, idan sun juya, sai ka ce: Ma'ishina Allah ne. Babu abin bautawa face shi. A gare Shi nake dogara. Kuma Shi ne Ubangijin Al'arshi mai girma

    Yũnus

    Surah 10

    [1] L.R. Waɗancan ayoyin littafi ne kyautatacce

    [2] Shin, ya zama abin mamaki ga mutane domin Mun yi wahayi zuwa ga wani namiji daga gare su cewa, "Ka yi gargaɗi ga mutane kuma ka yi bushara ga waɗanda suka yi imani da cewa: Lalle ne suna da abin gabatarwar gaskiya a wurin Ubangijinsu."Kafirai suka ce: "Lalle ne wannan, haƙiƙa, masihirci ne bayyananne

    [3] Lalle Allah ne Ubangijinku wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwana shida, sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi Yana gudanar da al'amari. Babu wani maceci face a bayan izninSa. Wannan ne Allah, Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Shin fa, ba ku tunani

    [4] zuwa gare Shi makomarku take gaba ɗaya, wa'adin Allah gaskiya ne. Haƙiƙa, Shi ne Yake fara halitta, sa'an nan kuma Ya mayar da ita domin Ya saka wa waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai da adalci, kuma waɗanda suka kafirta suna da abin sha daga ruwan zafi, da azaba mai raɗaɗi, saboda abin da suka kasance suna yi na kafirci

    [5] Shi ne wanda Ya sanya muku rana, babban haske, da wata mai haske, kuma Ya ƙaddara shi ga Manziloli, domin ku san ƙidayar shekaru da lissafi. Allah bai halitta wannan ba, face da gaskiya, Yana bayyana ayoyi daki-daki domin mutane waɗanda suke sani

    [6] Lalle ne a cikin saɓawar dare da yini, da abin da Allah Ya halitta a cikin sammai da ƙasa, haƙiƙaakwai ayoyi ga mutane waɗanda suke yin taƙawa

    [7] Lalle ne waɗanda ba su ƙaunar gamuwa da Mu, kuma suka yarda da rayuwar duniya kuma suka natsu da ita, da waɗanda suke gafalallu ne daga ayoyinMu

    [8] Waɗannan matattararsu Jahannama ce saboda abin da suka kasance suna tsirfatawa

    [9] Lalle ne waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, Ubangijinsu Yana shiryar da su saboda imaninsu, ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, a cikin gidajen Aljannar ni'ima

    [10] Kiransu a cikinta, "TsarkinKa ya Allah!" Kuma gaisuwarsu a cikinta,"Salamun", kuma ƙarshen kiransu, cewa, "Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu

    [11] Kuma da Allah Yana gaggawa ga mutane da sharri kamar yadda Yake gaggauta musu da alheri, haƙiƙa da an hukunta ajalinsu zuwa gare su. Saboda haka Muna barin waɗanda ba su ƙaunar gamuwa da Mu, a cikin kangararsu suna ta ɗimuwa

    [12] Kuma idan cuta ta shafi mutum, sai ya kiraye Mu, yana (kwance) ga sashensa ko kuwa zaune, ko kuwa a tsaye. To, a lokacin, da Muka kuranye cutar daga gare shi, sai ya shuɗe kamar ɗai bai kiraye Mu ba zuwa ga wata cuta wadda ta shafe shi. Kamar wannan ne aka ƙawata ga maɓannata, abin da suka kasance suna aikatawa

    [13] Kuma, haƙiƙa, Mun halakar da al'ummomi daga gabaninku, a lokacin da suka yi zalunci, kuma manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu, amma ba su kasance suna imani ba. Kamar wannan ne, Muke sakawa ga mutane masu laifi

    [14] Sa'an nan kuma Muka sanya ku masu mayewa a cikin ƙasa daga bayansu, domin Mu ga yaya kuke aikatawa

    [15] Kuma idan ana karatun ayoyinMu bayyanannu a kansu, sai waɗanda ba su ƙaunar gawuwa da Mu, su ce: "Ka zo da wani Alƙur'ani, wanin wannan, ko kuwa ka musunya shi." Ka ce: "Ba ya kasancewa a gare ni in musanya shi da kaina. Ba ni biyar kome face abin da aka yiwo wahayi zuwa gare ni. Kuma, haƙiƙa ni ina tsoro idan na saɓa wa Ubangijina, ga azabar wani yini mai girma

    [16] Ka ce: "Da Allah Ya so da ban karanta shi ba a kanku, kuma da ban sanar da ku ba gameda shi, domin lalle ne na zauna a cikinku a zamani mai tsawo daga gabanin (fara saukar) sa. Shin fa, ba ku hankalta

    [17] Saboda haka wane ne mafi Zalunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, ko kuwa ya ƙaryata ayoyinSa? Haƙiƙa, masu laifiba su cin nasara

    [18] Kuma suna bauta wa, baicin Allah, abin da ba ya cutar dasu kuma ba ya amfaninsu, kuma suna cewa: "Waɗannan ne macetanmu a wurin Allah."Ka ce: "Shin, kuna bai wa Allah labari ne, ga abin da bai sani ba, a cikin sammai ko a cikin ƙasa? TsarkinSa ya tabbata kuma Ya ɗaukaka daga gabin da duk suke yin shirki da Shi

    [19] Kuma mutane ba su kasance ba face al'umma guda, sa'an nan kuma suka saɓa wa juna, kuma ba domin wata kalma ba wadda ta gabata daga Ubangijinka, da an yi hukunci a tsakaninsu a kan abin da yake a cikinsa suke saɓa wa juna

    [20] Kuma suna cewa: "Don me ba a saukar da wata aya ba a gare shi, daga Ubangijinsa?" To, ka ce: "Abin sani kawai, gaibi ga Allah yake. Sai ku yi jira. Lalle ne ni, tare da ku, ina daga masu jira

    [21] Kuma idan Muka ɗanɗana wa mutane wata rahama, a bayan wata cuta ta shafe su, sai ga su da makirci a cikin ayoyinMu. Ka ce: "Allah ne mafi gaggawar (sakamakon) makirci." Lalle ne ManzanninMu suna rubuta abin da kuke yi na makirci

    [22] Shi ne wanda Yake tafiyar da ku a cikin tudu da (kuma) teku, sai idan kun kasance a cikin jirage, su gudana tare da su da iska mai daɗi, kuma su yi farin ciki da ita, sai wata guguwa ta je wa jiragen, kuma taguwar ruwa ta je musu daga kowane wuri, kuma su tabbata cewa su, an kewaye su, sai su kirayi Allah, suna masu tsarkake addini gare Shi, (suna cewa): Lalle ne idanKa kuɓutar da mu daga wannan, haƙiƙa muna kasancewa daga masu godiya

    [23] To, a lokacin da Ya kuɓutar da su, sai, ga su suna zalunci a cikin ƙasa, ba da wani hakki ba. Ya ku mutane! Abin sani kawai, zaluncinku a kanku yake, a bisa rayuwar duniya. Sa'an nan kuma zuwa gare Mu makomarku take, sa'an nan Mu ba ku labari game da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [24] Abin sani kawai, misalin rayuwar duniya kamar ruwa ne Muka saukar da shi daga sama, sa'an nan tsiron ƙasa ya garwaya da shi. Daga abin da mutane da dabbobi suke ci, har idan ƙasa ta riƙi zinariyarta kuma ta yi ƙawa, kuma mutanenta suka zaci cewa su ne masu ikon yi a kanta, sai umurninMu ya je mata da dare ko kuma da rana, sai Mu maisheta girbabba kamar ba ta wadata ba a jiya. Kamar wannan ne Muke rarrabe ayoyi, daki-daki, ga mutane waɗanda suke tunani

    [25] Kuma Allah Yana kira zuwa ga gidan aminci, kuma, Yana shiryar da wanda Yake so zuwa ga tafarki madaidaici

    [26] Waɗanda suka kyautata yi, suna da abu mai kyawo kuma da ƙari, wata ƙura ba ta rufe fuskokinsu, kuma haka wani ƙasƙanci. waɗancan ne abokan Aljanna, suna madawwama a cikinta

    [27] Kuma waɗanda suka yi tsirfar munanan ayyuka, sakamakon mummuna da kamarsa yake, kuma ƙasƙanci yana rufe su. Ba su da wani matsari daga Allah, kamar an rufe fuskokinsu da guntayen ƙiraruwa daga dare mai duhu. Waɗannan ne abokan wuta, suna madawwama a cikinta

    [28] Kuma a ranar da Muke tara su gaba ɗaya, sa'an nan kuma Mu ce wa waɗanda suka yi shirki, "Ku kama matsayinku, ku da abubuwan shirkinku." Sa'an nan Mu rarrabe a tsakaninsu, kuma abubuwan shirkinsu su ce: "Ba mu kuka kasance kuna bauta wa ba

    [29] To, kuma Allah Ya isa zama shaida a tsakaninmu da tsakaninku. Haƙiƙa mun kasance ba mu san kome ba na bautawarku a gare mu

    [30] A can ne kowane rai yake jarraba abin da ya bayar bashi, kuma aka mayar da su zuwa ga Allah, Majiɓincinsu Tabbatacce kuma, abin da suka kasance suna ƙirƙirawa ya ɓace musu

    [31] Ka ce: "Wane ne Yake azurta ku daga sama da ƙasa? Shin ko kuma Wane ne Yake mallakar ji da gani, kuma Wane ne Yake fitar da mai rai daga mamaci, kuma Ya fitar da mamaci daga mai rai, Kuma Wane ne Yake shirya al'amari?" To, za su ce: "Allah ne." To, ka ce: "Shin fa, ba za ku yi taƙawa ba

    [32] To, Wancan ne Allah, Ubangijinku Tobbatacce. To, mene ne a bayan gaskiya face ɓata? To, yaya ake karkatar da ku

    [33] Kamar wancan ne kalmar Ubangijinka, ta tabbata a kan waɗanda suka yi fasiƙanci, cewa haƙiƙa su, ba za su yi imani ba

    [34] Ka ce: "Shin, daga abubuwan shirkinku akwai wanda yake fara halitta, sa'an nan kuma ya mayar da ita?" Ka ce: "Allah ne Yake fara halitta, sa'an nan kuma Ya mayar da ita. To, yaya akejuyar da ku

    [35] Ka ce: "Shin, daga abubuwan shirkinku akwai wanda yake shiryarwa zuwa ga gaskiya?" Ka ce: "Allah ne Yake shiryarwa zuwa ga gaskiya. Shin fa, wanda Yake shiryarwa ne mafi cancantar a bi Shi, ko kuwa wanda ba ya shiryarwa face dai a shiryar da shi? To, mene ne a gare ku? Yaya kuke yin hukunci

    [36] Kuma mafi yawansu ba su biyar kome face zato. Lalle ne zato ba ya wadatar da kome daga gaskiya. Lalle Allah ne Masani ga abin da suke aikatawa

    [37] Kuma wannan Alƙur'ani bai kasance ga a ƙirƙira shi ba daga wanin Allah, kuma amma shi gaskatawar wannan ne da yake a gabaninsa da bayanin hukuncin littaffan Allah, Babu shakka a cikinsa, daga Ubangijin halittu yake

    [38] Ko suna cewa, "Ya ƙirƙira shi?" Ka ce: "Ku zo da sura guda misalinsa, kuma ku kirayi wanda kuka iya duka, baicin Allah, idan kun kasance masu gaskiya

    [39] A'a, sun ƙaryata game da abin da ba su kewaye da saninsa ba, kuma fassararsa ba ta riga ta je musu ba. Kamar waɗancan ne waɗanda suke a gabaninsu. Sai ka duba, yaya aƙibar azzalumai ta kasance

    [40] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake yin imani da Shi, kuma daga cikinsu akwai wanda ba ya yin imani da Shi. Kuma Ubangijinka ne Mafi sani ga maɓarnata

    [41] Kuma idan sun ƙaryata ka, to, ka ce: "Ina da aikina kuma kuna da aikinku, ku kuɓutattu ne daga abin da nake aikatawa kuma ni kuɓutacce ne daga abin da kuke aikatawa

    [42] Kuma daga cikinsu akwai waɗanda suke saurare zuwa gare ka. Shin fa, kai kana jiyar da kurma, kuma ko da sun kasance ba su hankalta

    [43] Kuma daga cikinsu akwai wanda yake tsokaci zuwa gare ka. Shin fa, kai kana shiryar da makafi, kuma ko da sun kasance ba su gani

    [44] Lalle ne Allah ba Ya zaluntar mutane da kome, amma mutanen ne ke zaluntar kansu

    [45] Kuma ranar da Yake tara su, kamar ba su zauna ba face sa'a guda daga yini. Suna gane juna a tsakaninsu. Haƙiƙa, waɗanda suka ƙaryata game da gamuwa da Allah sun yi hasara. Kuma ba su kasance masu shiryuwa ba

    [46] Kuma imma dai, haƙiƙa, Mu nuna maka sashen abin da Muke yi musu alkawari, ko kuwa Mu karɓi ranka, to, zuwa gare Mu makomarsu take. Sa'an nan kuma Allah ne shaida a kan abin da suke aikatawa

    [47] Kuma ga kowace al'umma akwai Manzo. Sa'an nan idan Manzonsu ya je, sai a yi hukunci a tsakaninsu da adalci, kuma su, ba a zaluntar su

    [48] Kuma suna cewa, "A yaushe wannan wa'adi zai auku, idan kun kasance masu gaskiya

    [49] Ka ce: "Ba na mallaka wa kaina wata cuta, haka kuma wani amfani, sai abin da Allah Ya so. Ga kowace al'umma akwai ajali, idan ajalinsu ya zo, to, ba za su yi jinkiri daga gare shi ba, ko da sa'a guda, kuma ba za su gabata ba

    [50] Ka ce: "Shin, kun gani, idan azabarSa ta zo muku da dare ko da rana? Mene ne daga gare shimasu laifi suke neman gaggawarsa

    [51] Shin sa'an nan kuma idan har ya auku, kun yi imani da shi? Ashe? Yanzu kuwa, alhali kun kasance game da shi kuna neman gaggawar aukuwarsa

    [52] Sa'an nan kuma aka ce ga waɗanda suka yi zalunci, "Ku ɗanɗani azabar dawwama! Shin, ana saka muku face da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [53] Kuma suna tambayar ka: Shin gaskiya ne? Ka ce: "I, ina rantsuwa da Ubangijina. Lalle gaskiya ne, kuma ba ku zama masu buwaya ba

    [54] Kuma da kowane rai wanda ya yi zalunci ya mallaki duka abin da yake a cikin ƙasa, to, da ya yi fansa da shi. Kuma suka dinga nadama a lokacin da suka ga azaba. Sa'an nan aka yi hukunci a tsakaninsu da adalci, kuma ba za a zalunce su ba

    [55] To! Haƙiƙa Allah Ya mallaki abin da yake a cikin sammai da ƙasa. To! Haƙiƙa wa'adin Allah gaskiya ne. Amma kuma mafi yawansu ba su sani ba

    [56] Shi ne Yake rayarwa kuma Yake matarwa. Kuma zuwa gare Shi ne ake mayar da ku

    [57] Ya ku mutane! Lalle wa'azi ya je muku daga Ubangijinku, da waraka ga abin da yake a cikin ƙiraza, da shiriya da rahama ga muminai

    [58] Ka ce: "Da falalar Allah da rahamarSa. Sai su yi farin ciki da wannan." Shi ne mafi alheri daga abin da suke tarawa

    [59] Ka ce: "Shin, kun ga abin da Allah Ya saukar saboda ku na arziki, sai kuka sanya hukuncin haramci da halacci a gare shi?" Ka ce: "Shin, Allah ne Ya yi muku izni, ko ga Allah kuke ƙirƙirawar ƙarya

    [60] Kuma mene ne zaton waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, a Ranar ¡iyama? Lalle haƙiƙa, Allah Ma, abucin falala ne a kan mutane, amma kuma mafi yawansu ba su godewa

    [61] Kuma ba ka kasance a cikin wani sha'ani ba, kuma ba ka karanta wani abin karatu daga gare shi ba, kuma ba ku aikata wani aiki ba, face Mun kasance Halarce a lokacin da kuke zubuwa a cikinsa. Kuma wani ma'aunin zarra ba zai yi nisa ba daga Ubangijinka a cikin ƙasa, haka kuma a cikin sama, kuma babu wanda yake mafi ƙaranci daga haka, kuma babu mafi girma, face yana a cikin littafi bayyananne

    [62] To, Lalle ne masoyan Allah babu tsoro a kansu, kuma ba za su kasance suna yin baƙin ciki ba

    [63] Waɗanda suka yi imani kuma suka kasance suna yin taƙawa

    [64] Suna da bushara a cikin rayuwar duniya da ta Lahira. Babu musanyawa ga kalmomin Allah. Wancan shi ne babban rabo mai girma

    [65] Kada maganarsu ta sanya ka a cikin baƙin ciki. Lalle ne alfarma ga Allah take gaba ɗaya. Shi ne Mai ji, Masani

    [66] To! Haƙiƙa Allah Yana da mulkin wanda ke a cikin sammai da wanda ke a cikin ƙasa kuma waɗanda suke kiran wanin Allah, ba su biyar waɗansu abokan tarewa (ga Allah a MulkinSa). Ba su biyar kome face zato. Kuma ba su zama ba face suna ƙiri faɗi kawai

    [67] Shi ne wanda Ya sanya muku dare, domin ku natsu a cikinsa, da yini mai sanya a yi gani. Lalle ne a cikin wannan akwai ayoyi ga mutane waɗanda suke ji

    [68] Suka ce: "Allah Ya riƙi ɗa." Tsarkinsa ya tabbata! Shi ne wadatacce Yana da mallakar abin da yake, a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa, A wurinku babu wani dalili game da wannan! Shin, kuna faɗar abin da ba ku sani ba game da Allah

    [69] Ka ce: "Haƙiƙa waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah, ba za su ci nasara ba

    [70] Jin daɗi ne a cikin duniya, sa'an nan kuma makomarsu zuwa gare Mu take, sa'an nan Mu ɗanɗana musu azaba mai tsanani saboda abin da suka kasance suna yi na kafirci

    [71] Kuma ka karanta musu labarin Nuhu, a lokacin da ya ce wa mutanensa, "Ya mutanena! Idan matsayina da tunatarwata ameda ayoyin Allah sun kasance sun yi nauyi a kanku, to, ga Allah na dogara. Sai ku tara al'amarinku, ku da abubuwan shirkinku, sa'annan kuma kada al'amarinku ya kasance rufaffe a kanku, sa'an nan kuma ku kashe ni, kada ku yi mini jinkiri

    [72] Kuma idan kuka juya baya, to, ban tambaye ku wata ijara ba. ljarata ba ta zama ba face daga Allah, kuma an umurce ni da in kasance daga masu sallamawa

    [73] Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan Muka kuɓutar da shi da wanda yake tare da shi, a cikin jirgi, kuma Muka sanya su masu mayewa, kuma Muka nutsar da waɗanda suka ƙaryata ayoyinMu. Sai ka duba yadda aƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance

    [74] Sa'an nan kuma Muka aika waɗansu Manzanni daga bayansa zuwa ga mutanensu, suka jemusu da hujjoji bayyanannu, to, ba su kasance za su yi imani ba saboda sun ƙaryata shi a gabani. Kamar wannan ne Muke rufewa a kan zukatan masu ta'addi

    [75] Sa'an nan kuma a bayansu Muka aika Musa da Haruna zuwa ga Fir'auna da mashawartansa, tare da ayoyinMu. Sai suka kangara kuma sun kasance mutane masu laifi

    [76] Sa'an nan a lokacin da gaskiya ta je musu daga gare Mu, suka ce: "Wannan haƙiƙa sihiri ne bayyananne

    [77] Musa ya ce: " Shin, kuna cewa ga gaskiya a lokacin data zo muku? Shin, sihiri ne wannan? Lalle masihirci, ba ya cin nasara

    [78] Suka ce: "Shin, ka zo mana ne domin ka juyar da mu daga abin da muka iske ubanninmu a kansa, kuma girma ya kasance gare ku, ku biyu a cikin ƙasa? Ba za mu zama masu imani ba saboda ku

    [79] Kuma Fir'auna ya ce: "Ku zo mini da dukan masihirci, masani

    [80] To, a lokacin da masihirta suka je, Musa ya ce musu,"Ku jefa abin da kuke jefawa

    [81] To, a lokacin da suka jefa, Musa ya ce: "Abin da kuka zo da shi sihiri ne. Lalle ne Allah zai ɓata shi. Haƙiƙa Allah ba Ya gyara aikin maɓarnata

    [82] Kuma Allah Yana tabbatar da gaskiya da kalmominSa, ko da masu laifi sun ƙi

    [83] Sa'an nan babu wanda ya yi imani da Musa face zuriya daga mutanensa, a kan tsoron kada Fir'auna da shugabanninsu su fitine su. Lalle, haƙiƙa, Fir'auna marinjayi ne a cikin ƙasa, kuma lalle shi haƙiƙa, yana daga masu ɓarna

    [84] Kuma Musa ya ce: "Ya ku mutanena! Idan kun kasance kun yi imani da Allah, to, a gare Shi sai ku dogara, idan kun kasance Musulmi

    [85] Sai suka ce: "Ga Allah muka dogara. Ya Ubangijinmu! Kada Ka sanya mu fitina ga mutane azzalumai

    [86] Kuma Ka kuɓutar da mu domin RahamarKa, daga mutane kafirai

    [87] Kuma Muka yi wahayi zuwa ga Musa da ɗan'uwansa, cewa: Ku biyu, ku zaunar da mutanenku a Masar a cikin wasu gidaje. Kuma ku sanya gidajenku su fuskanci Alƙibla, kuma ku tsayar da salla. Kuma ku bayar da bushara ga masu imani

    [88] Sai MuSa ya ce: "Ya Ubangijinmu! Haƙiƙa Kai ne Ka bai wa Fir'auna da majalisarsa ƙawa da dukiyoyi a cikin rayuwar duniya, ya Ubangijinmu, domin su ɓatar (damutane) daga hanyarKa. Ya Ubangijinmu! Ka shafe a kan dukiyarsu kuma Ka yi ɗauri a kan zukatansu yadda ba za su yi imani ba har su ga azaba mai raɗaɗi

    [89] (Allah) Ya ce: "Lalle ne an karɓi addu'arku. Sai ku daidaitu kuma kada ku bi hanyar waɗanda ba su sani ba

    [90] Kuma Muka ƙetarar da Bani Isra'ila teku sai Fir'auna da rundunarsa suka bi su bisa ga zalunci da ƙetare haddi, har a lokacin da nutsewa ta riske shi ya ce: "Na yi imani cewa, haƙiƙa, babu abin bautawa face wannan da Banu Isra'il suka yi imani da Shi, kumani, ina daga Musulmi

    [91] Ashe! A yanzu! Alhali kuwa, haƙiƙa ka saɓa a gabani, kuma ka kasance daga masu ɓarna

    [92] To, a yau Muna kuɓutar da kai game da jikinka, domin ka kasance aya ga waɗanda suke a bayanka. Kuma lalle ne masu yawa daga mutane, haƙiƙa, gafalallu ne ga ayoyinMu

    [93] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun zaunar da Bani Isra'ilamazaunar gaskiya kuma Muka arzuta su daga abubuwa masu daɗi. Sa'an nan ba su saɓa ba har ilmi ya je musu. Lalle ne Ubangijinka Yana yin hukunci a tsakaninsu a Ranar Kiyama a cikin abin da suka kasance suna saɓa wa juna

    [94] To, idan ka kasance a cikin shakka daga abin da Muka saukar zuwa gare ka, sai ka tambayi waɗanda suke karatun Littafi daga gabaninka. Lalle ne, haƙiƙa, gaskiya ta je maka daga Ubangijinka domin haka kada ka kasance daga masu kokanto

    [95] Kuma kada ka kasance daga waɗanda suke ƙaryatawa game da ayoyin Allah, har ka kasance daga masu hasara

    [96] Lalle ne waɗanda kalmar Ubangijinka ta wajaba a kansu, ba za su yi imani ba

    [97] Kuma ko da kowace aya ta je musu, sai sun ga azaba mai raɗaɗi

    [98] To, domin me wata alƙarya ba ta kasance ta yi imaniba har imaninta ya amfane ta, facemutanen Yunus? A lokacin da suka yi imani, Munjanye azabar wulakanci daga gare su a cikin rayuwar duniya. Kuma Muka jiyar da su daɗi zuwa wani lokaci

    [99] Kuma da Ubangijinka Ya so, da waɗanda suke a cikin ƙasa sun yi imani dukansu gaba ɗaya. Shin, kai kana tilasta mutanene har su kasance masu imani

    [100] Kuma ba ya kasancewa ga wani rai ya yi imani face da iznin Allah, kuma (Allah) Yana sanya ƙazanta a kan waɗanda ba su yin hankali

    [101] Ka ce: "Ku dubi abin da yake cikin sammai da ƙasa."Kuma ayoyi da gargaɗi ba su wadatarwa ga mutane waɗanda ba su yin imani

    [102] To, Shin suna jiran wani abu face kamar misalin kwanukan waɗanda suka shuɗe daga gabaninsu? Ka ce: "Ku yi jira! Lalle ni tare da ku, ina daga masu jira

    [103] Sa'an nan kuma Muna kuɓutar da manzanninMu da waɗanda suka yi imani, kamar wannan ne, tabbatacce ne a gare Mu, Mu kuɓutar da masu imani

    [104] Ka ce: "Ya ku mutane! Idan kun kasance a cikin kokanto daga addinina, to ba ni bauta wa, waɗanda kuke, bauta wa, baicin Allah, kuma amma ina bauta wa Allah wanda Yake karɓar rayukanku. Kuma an umurce ni da in kasance daga masu imani

    [105] Kuma (an ce mini): Ka tsayar da fuskarka ga addini, kana karkatl zuwa ga gaskiya, kuma kada ka kasance daga masu shirka

    [106] Kuma kada ka kirayi, baicin Allah, abin da ba ya amfanin ka kuma ba ya cutar ka. To, idan ka aikata haka, sa'an nan lalle kai, a lokacin, kana daga masu zalunci

    [107] Kuma idan Allah Ya shafe ka da wata cuta, to, babu mai yaye ta face shi, kuma idan Yana nufin ka da wani alheri, to, babumai mayar da falalarSa. Yana samun wanda Yake so daga cikin bayinSa da shi. Kuma Shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [108] Ka ce: "Ya ku mutane! Lalle ne gaskiya, ta zo muku daga Ubangijinku. To, wanda ya shiryu, ya shiryu ne domin kansa kawai, kuma wanda ya ɓace yana ɓacewa ne a kansa kawai. Kuma ban zama wakili a kanku ba

    [109] Kuma ka bi abin da ake yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ka yi haƙuri har Allah Ya yi hukunci. Kuma Shi ne Mafi alherin masu hukunci

    Hũdu

    Surah 11

    [1] L.R. Littafi ne an kyautata ayoyinsa, sa'an nan an bayyana su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai ƙididdigewa

    [2] Kada ku bauta wa kowa face Allah. Lalle ne ni a gare ku mai gargaɗi ne kuma mai bushara daga gare Shi

    [3] Kuma ku nemi gafara gun Ubangijinku. Sa'an nan ku tuba zuwa gare Shi, Ya jiyar da ku daɗi, jiyarwa mai kyau zuwa ga ajali ambatacce, kuma Ya bai wa dukkan ma'abucin, girma girmansa. Amma idan kun juya, to, lalle ni, ina tsoron azabar yini mai girma a kanku

    [4] Zuwa ga Allah makomarku take, kuma Shi a kan komeMai ikon yi ne

    [5] To, lalle su suna karkatar da ƙirjinsu domin su ɓoye daga gare shi. To, a lokacin da suke lulluɓewa da tufafinsu Yana sanin abin da suke ɓoyewa da abin da suke bayyanawa. Lalle Shi Masani ne ga abin da yake a cikin ƙiraza

    [6] Kuma babu wata dabba a cikin ƙasa face ga Allah arzikinta yake, kuma Yana sanin matabbatarta da ma'azarta, duka suna cikin littafi bayyananne

    [7] Kuma shi ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwanaki shida, kuma Al'arshinSa ya kasance akan ruwa, domin Ya jarraba ku, wannan ne daga cikinku mafi kyawon aiki. Kuma haƙiƙa idan ka ce: "Lalle ku waɗanda ake tayarwa ne a bayan mutuwa," haƙiƙa waɗanda suka kafirta suna cewa: "Wannan bai zama ba face sihiri bayyananne

    [8] Kuma lalle ne idan Mun jinkirta da azaba gare su zuwa ga wani lokaci ƙidayayye, haƙiƙa sunacewa me yake tsare ta? To, a ranar da za ta je musu, ba ta zama abin karkatarwa ba daga gare su. Kuma abin da suka kasance suna yin izgili da shi, ya wajaba a kansu

    [9] Kuma lalle ne idan Mun ɗanɗana wa mutum wata rahama daga gare Mu, sa'an nan kuma Muka zare ta daga gare shi, lalle ne shi, hakika, mai yanke tsammanine, mai yawan kafrci

    [10] Kuma lalle ne idan Mun ɗanɗana masa ni'ima a bayan cuta ta shafe shi, Yana cewa munanan halaye sun tafi daga wurina. Lalle shi mai farin ciki ne, mai alfahari

    [11] Sai waɗanda suka yi haƙuri kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai. Waɗannan suna da gafara da lada mai girma

    [12] Saboda haka tsammaninka kai mai barin sashen abin da aka yi wahayi zuwa gare ka ne, kuma mai ƙuntata ƙirjinka da shi ne domin sun ce: "Domin me ba a saukar masa da wata taska ba, ko kuma Mala'ika ya zo tare de shi?" Kai mai gargaɗi ne kawai. Kuma Allah ne wakili a kan kome

    [13] Ko suna cewa: "Ya ƙirƙira shi ne."Ka ce: "Sai ku zo da surori goma misalinsa ƙirƙirarru, kuma ku kirayi wanda kuke iyawa, baicin Allah, idan kun kasance masu gaskiya

    [14] To, idan ba su amsa muku ba, to, ku sani cewa an saukar da shi kawai ne da sanin Allah, kuma cewa babu abin bauta wa face Shi. To, shin, ku masu sallamawa ne

    [15] Wanda ya kasance ya yi nufin rayuwar duniya da ƙawarta, Muna cika musu ayyukansu zuwa gare su a cikinta, kuma a cikinta ba za a rage su ba

    [16] Waɗannan ne waɗanda ba su da kome a cikin Lahira face wuta, kuma abin da suka sana'anta a cikinta (duniya) ya ɓaci, kuma abin da suka kasance suna aikatawa ɓatacce ne

    [17] Shin, wanda ya kasance a kan hujja bayyananna daga Ubangijinsa, kuma wata shaida tana biyar sa daga gare Shi, kuma a gabaninsa akwai littafin Musaabin koyi da rahama? Waɗannan suna yin imani da shi, kuma wanda ya kafirta da shi daga ƙungiyoyi, to, wuta ce makomarsa. Saboda haka kada ka kasance a cikin shakka daga gare shi. Lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinka, amma kuma mafi yawan mutane ba su yin imani

    [18] Kuma wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah? Waɗannan ana gitta su ga Ubangijinsu, kuma masu shaida su ce: "Waɗannan ne suka yi ƙarya ga Ubangijinsu. To, la'anar Allah ta tabbata a kan azzalumai

    [19] Waɗanda suke kangewa daga hanyar Allah kuma suna neman ta karkace, kuma su ga Lahira suna kafirta

    [20] Waɗannan ne ba su kasance mabuwaya ba a cikin ƙasa, kuma waɗansu masoya ba su kasance ba a gare su, baicin Allah. Ana ninka musu azaba, ba su kasance suna iya ji ba, kuma ba su kasance suna gani ba

    [21] Waɗannan ne wɗanda suka yi hasarar rayukansu, kuma abin da suka kasance suna ƙirƙirawa ya ɓace musu

    [22] Babu makawa cewa, haƙiƙa, su a lahira, su ne mafi hasara

    [23] Lalle ne waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka yi tawalu'i zuwa ga Ubangijinsu, waɗannan ne abokan Aljanna, suna madawwama a cikinta

    [24] Misalin ɓangaren biyu kamar makaho ne da kurma, da mai gani da mai ji. Shin, suna daidaita ga misali? Ashe, ba ku yin tunani

    [25] Kuma haƙiƙa Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa, (ya ce): "Lalle ne ni, a gare ku mai gargaɗi bayyananne ne

    [26] Kada ku bauta wa kowa face Allah. Lalle ni, ina jin tsoron azabar yini mai raɗaɗi a kanku

    [27] Sai mashawarta waɗanda suka kafirta, daga mutanensa, suka ce: "Ba mu ganin ka face mutum kake kamarmu, kuma ba mu ganin wani ya bi ka face waɗanda suke su ƙasƙantattunmu ne marasa tunani. Kuma ba mu ganin wata falala agare ka a kanmu. A'a, Muna zaton ku maƙaryata ne

    [28] Ya ce: "Ya mutanena! Shin, kun gani idan na kasance a kan wata hujja bayyananna daga Ubangijina, kuma Ya ba ni wata Rahama daga wurinSa, Sa'an nan aka rufe ta (ita Rahamar) daga gare ku, shin, za mu tilasta mukuita, alhali kuwa ku masu ƙi gare ta ne

    [29] Kuma ya mutanena! Ba zan tambaye ku wata dukiya ba akansa, ijarata ba ta zama ba, face daga Allah, kuma ban zama mai korar waɗanda suka yi imani ba. Haƙiƙa su, masu haɗuwa da Ubangijinsu ne, kuma amma ni, ina ganin ku mutane ne jahilai

    [30] Kuma ya mutanena! Wane ne yake taimakona daga Allah idan na kore su? Ashe, ba ku tunani

    [31] Kuma ba ni ce muku a wurina taskokin Allah suke kuma ba ina sanin gaibi ba ne. Kuma ba ina cewa ni Mala'ika ba ne. Kuma ba ni cewa ga waɗanda idanunku suke wulakantawa, Allah ba zai ba su alheri ba. Allah ne Mafi sani ga abin da yake cikin zukatansu. Lalle ne ni, idan (na yi haka) da ina daga cikin azzalumai

    [32] Suka ce: "Ya Nuhu, lalle ne ka yi jayayya da mu, sa'an nan ka yawaita yi mana jidali, to, ka zo mana da abin da kake yi mana wa'adi idan ka kasance daga masu gaskiya

    [33] Ya ce: "Allah kawai ne Yake zo muku da shi idan Ya so. Kuma ba ku zama mabuwaya ba

    [34] Kuma nasihata ba za ta amfane ku ba, idan na yi nufin in yi muku nasiha, idan Allah Yakasance Yana nufin Ya halaka ku. Shi ne Ubangijinku, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [35] Ko suna cewa: (Nuhu) ya ƙirƙira shi. Ka ce: "Idan ni (Nuhu) na ƙirƙira shi to, laifina a kaina yake, kuma ni mai barranta ne daga abin da kuke yi na laifi

    [36] Kuma aka yi wahayi zuwa ga Nuhu cewa: Lalle ne babu mai yin imani daga mutanenka face wanda ya riga ya yi imanin, sabodahaka kada ka yi baƙin ciki da abin da suka kasance suna aikatawa

    [37] Kuma ka sassaƙa jirgi da kyau a kan idanunMu da wahayinMu, kuma kada ka yi Mini magana a cikin sha'anin waɗanda suka kafirta, lalle ne su, waɗanda akenutsarwa ne

    [38] Kuma Yana sassaƙa jirgin cikin natsuwa, kuma a ko yaushe waɗansu shugabanni daga mutanensa suka shuɗe a gabansa, sai su yi izgili gare shi. Ya ce: "Idan kun yi izgili gare mu, to, haƙiƙa mu ma za mu yi izgili gare ku, kamar yadda kuke yin izgili

    [39] Sa'an nan da sannu za ku san wanda azaba za ta zo masa, ta wulakanta shi (a duniya), kuma wata azaba zaunanna ta sauka a kansa (a Lahira)

    [40] Har a lokacin da umurninMu ya je, kuma tanda ta ɓulɓula. Muka ce: "Ka ɗauka, a cikinta, daga kome, ma'aura biyu, da kuma iyalanka, face wanda magana ta gabata a kansa, da wanda ya yi imani." Amma kuma babu waɗanda suka yi imani tare da shi face kaɗan

    [41] Kuma ya ce: "Ku hau a cikinta, da sunan Allah magudanarta da matabbatarta. Lalle ne Ubangijina, haƙiƙa, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [42] Kuma ita tana gudana da su a cikin taguwar ruwa kamai duwatsu, sai Nuhu ya kirayi ɗansa alhali, kuwa ya kasance can wuri mai nisa. "Ya ƙaramin ɗana! zo ka hau tare da mu, kuma kada ka kasance tare da kafirai

    [43] Ya ce: "Zan tattara zuwa ga wani dutse ya tsare ni daga ruwan." (Nuhu) ya ce: "Babu mai tsarewa a yau daga umurnin Allah face wanda Ya yi wa rahama." Sai taguwar ruwa ta shamakace a tsakaninsu, sai ya kasance daga waɗanda aka nutsar

    [44] Kuma aka ce: "Ya ƙasa! Ki haɗiye ruwanki, kuma ya sama! Ki kame."Kuma aka faƙar da ruwan kuma aka hukunta al'amarin, kuma Jirgin ya daidaita a kan Judiyyi, kuma aka ce: "Nisa ya tabbata ga mutane azzalumai

    [45] Kuma Nuhu ya kira Ubangijinsa, sa'an nan ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne ɗana na daga iyalina! Kuma haƙiƙa wa'adinKa gaskiya ne, kuma Kai ne Mafi hukuncin masu yin hukunci

    [46] Ya ce: "Ya Nuhu! Lalle ne shi ba ya a ciki iyalanka, lalle ne shi, aiki ne wanda ba na ƙwarai ba, saboda haka kada ka tambaye Ni abin da ba ka da ilmi a kansa. Haƙiƙa, Ni Ina yi maka gargaɗi kada ka kasance daga jahilai

    [47] Ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne ni, ina neman tsari gare Ka da in tambaye Ka abin da ba ni da wani ilmi a kansa. Idan ba Ka gafarta mini ba, kuma Ka yi mini rahama, zan kasance daga masu hasara

    [48] Aka ce: "Ya Nuhu! Ka sauka da aminci da, a gare Mu da albarka a kanka, kuma rahama ta tabbata a kan waɗansu al'ummomi daga waɗanda suke tare da kai. Da waɗansu al'ummomi da za Mu jiyar da su daɗi, sa'an nan kuma azaba mai raɗaɗi ta shafe su daga gare Mu

    [49] Waccan ƙissa tana daga labaran gaibi, Muna yin wahayinsu zuwa gare ka (Muhammadu). Ba ka kasance kana sanin su ba, haka kuma mutanenka ba su sani ba daga gabanin wannan. Sai ka yi haƙuri. Lalle ne aƙiba tana ga masu taƙawa

    [50] Kuma zuwa ga Adawa, (Mun aika) ɗan'uwansu Hudu. Ya ce: "Ya ku mutanena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautawa face Shi. Ba ku kasance ba face kuna masu ƙirƙirawa

    [51] Ya ku mutanena! Ba ni tambayar ku wata ijara a kansa, ijarata ba ta zama ba, face ga wanda Ya ƙaga halittata. Shin fa, ba ku hankalta

    [52] Kuma, ya mutanena! Ku nemi Ubangijinku gafara, sa'an nan kuma ku tuba zuwa gare Shi, zai saki sama a kanku, tana mai yawan zubar da ruwa, kuma Ya ƙara muku wani ƙarfi ga ƙarfinku. Kuma kada ku juya kuna masu laifi

    [53] Suka ce: "Ya Hudu! Ba ka zo mana da wata hujja bayyananna ba, kuma ba mu zama masu barin abubuwan bautawarmu ba domin maganarka, kuma ba mu zama masu yin imani da kai ba

    [54] Ba mu cewa, sai dai kurum sashen abubuwan bautawarmu ya same ka da cutar hauka." Yace: "Lalle ne ni, ina shaida waAllah, kuma ku yi shaidar cewa" lalle ne ni mai barranta ne dagb abin da kuke yin shirki da shi

    [55] Baicin Allah: Sai ku yi mini kaidi gaba ɗaya, sa'an nan kuma kada ku yi mini jinkiri

    [56] Haƙiƙa, ni na dogara ga Allah, Ubangijina kuma Ubangijinku. Babu wata dabba face Shi ne Mai riko ga kwarkwaɗarta. Haƙiƙa, Ubangijina Yana (kan) tafarki madaidaici

    [57] To! Idan kun juya, haƙiƙa, na iyar muku abin da aka aiko ni da shi zuwa gare ku. Kuma Ubangijina Yana musanya waɗansu mutane, waɗansunku su maye muku. Kuma ba ku cutar Sa da kome. Lalle Ubangijina a kan dukkan kome, Matsari ne

    [58] Kuma a lokacin da umurninmu ya je, Muka kuɓutar da Hudu da waɗanda suka yi imani tare da shi, sabodawata rahama daga gare Mu. Kuma Muka kuɓutr da su daga azaba mai kauri

    [59] Haka Adawa suka kasance, sun yi musun ayoyin Ubangijinsu, kuma sun saɓa wa ManzanninSa, kuma sun bi umurnin dukan mai girman kai, makangari

    [60] Kuma an biyar musu da la'ana a cikin wannan duniyada Ranar Kiyama. To! Lalle ne Adawa sun kafirta da Ubangijinsu. To, Nisa ya tabbata ga Adawa, mutanen Hudu

    [61] Kuma zuwa ga Samudawa (an aika) ɗan'uwansu Salihu. Ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautawa face Shi. Shi ne Ya ƙaga halittarku daga ƙasa, kuma Ya sanya ku masu yin kyarkyara a cikinta. Sai ku neme Shi gafara, sa'an nan kuma ku tuba zuwa gare Shi. Lalle Ubangijina Makusanci ne Mai karɓawa

    [62] Suka ce: "Ya Salihu! Haƙiƙa, ka kasance a cikinmu, wanda ake fatan wani alheri da shi a gabanin wannan. Shin kana hana mu bauta wa abin da ubanninmu suke bauta wa? Kuma haƙiƙa mu, muna cikin shakka daga abin da kake kiran mu gare shi, mai sanya kokanto

    [63] Ya ce: "Ya mutanena! Kun gani? Idan na kasance a kan hujja bayyananna daga Ubangijina, kuma Ya ba ni rahama daga gare Shi, to, wane ne zai taimake ni daga Allah idan na saɓa Masa? Sa'an nan ba za ku ƙare ni da kome ba face hasara

    [64] Kuma ya mutanena! wannan raƙumar Allah ce, tana aya a gare ku. Sai ku bar ta ta ci a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shafe ta da wata cuta kar azaba makusanciya ta kama ku

    [65] Sai suka soke ta. Sai ya ce: "Kuji daɗi a cikin gidajenku kwana uku. Wannan wa'adi ne ba abin ƙaryatawa ba

    [66] To, a lokacin da umurninMu ya je, muka kuɓutar da Salihu da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare Mu, kuma daga wulakancin ranar nan. Lalle ne Ubangijinka Shi neMai ƙarfi, Mabuwayi

    [67] Sai tsawa ta kama waɗanda suka yi zalunci, sai suka wayi gari suna guggurfane a cikin gidajensu

    [68] Kamar dai ba su zauna a cikinta ba. To! Lalle ne samudawa sun kafirce wa Ubangijinsu. To, Nisa ya tabbata ga Samudawa

    [69] Kuma haƙiƙa, manzanninMu sun je wa Ibrahim da bushara suka ce: "Aminci." Ya ce: "Aminci (ya tabbata a gare ku)." Sa'an nan bai yi jinkiri ba ya je da maraƙi ƙawatacce

    [70] Sa'an nan a lokacin da ya ga hannayensu ba su saduwa zuwa gare shi (maraƙin), sai ya yi ƙyamarsu, kuma ya ji tsoronsu. Suka ce, "Kada kaji tsoro lalle ne mu, an aiko mu ne zuwa ga mutanen Luɗu

    [71] Kuma matarsa tana tsaye. Ta yi dariya. Sai Muka yi mata bushara (da haihuwar) Is'haƙa, kuma a bayan Is'haƙa, Yaƙubu

    [72] Sai ta ce: "Ya kaitona! Shin, zan haihu ne alhali kuwa ina tsohuwa, kuma ga mijina tsoho ne? Lalle wannan, haƙiƙa, abu ne mai ban mamaki

    [73] Suka ce: "Shin kina mamaki ne daga al'amarin Allah? Rahamar Allah da albarkarSa su tabbata a kanku, ya mutanen babban gida! Lalle ne Shi abin godewa ne, Mai girma

    [74] To, a lokacin da firgita ta tafi daga Ibrahim, kuma bushara ta je masa, Yana mai jayayya a gare Mu, saboda mutanen Luɗu

    [75] Lalle Ibrahim, haƙiƙa mai haƙuri ne, mai yawan addu'a, mai tawakkali

    [76] Ya Ibrahim! Ka bijira daga wannan. Lalle shi, haƙiƙa, umurnin Ubangijinka ne ya zo, kuma lalle ne su, abin da yake mai je musu azaba ce wadda ba a iya hanawa

    [77] Kuma a lokacin da manzanninMu suka je wa Luɗu aka ɓata masa rai game da su, ya, ƙuntata rai saboda su. Ya ce: "Wannan yini ne mai tsananin masifa

    [78] Kuma mutanensa suka je masa suna gaggawa zuwa gare shi, kuma a gabani, sun kasance suna aikatawar munanan ayyuka. Ya ce: "Ya mutanena! waɗannan, 'ya'ya na su ne mafiya tsarki a gare ku. Sai ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku wulakanta ni a cikin baƙina. Shin, babu wani namiji shiryayye daga gare ku

    [79] Suka ce: "Lalle, haƙiƙa ka sani, ba mu da wani hakki a cikin 'ya'yanka, kuma lalle kai haƙiƙa, kana sane da abin da muke nufi

    [80] Ya ce: "Da dai ina da wani ƙarfi game da ku, ko kuwa ina da goyon baya daga wani rukuni mai ƙarfi

    [81] (Manzannin) Suka ce: "Ya Luɗu! Lalle mu, manzannin Ubangijinka ne. Ba za su iya saduwa zuwa gare ka ba. Sai ka yi tafiyarka a wani yankin dare da iyalinka, kuma kada wani daga gare ku ya waiwaya face matarka. Lalle ne abin da ya same su mai samunta ne. Lalle wa'adinsu lokacin safiya ne. Shin lokacin safiya ba kusa ba ne

    [82] Sa'an nan a lokacin da umurninMu ya je, Muka sanya na samanta ya zama na ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwatsu a kanta (ƙasar Luɗu) daga taɓocurarre

    [83] Alamtacce a wurin Ubangijinka. Kuma ita (ƙasar Luɗu) ba ta zama mai nisa ba daga azzalumai (kuraishawa)

    [84] Kuma zuwa ga Madyana (Mun aika) ɗan'uwansu Shu'aibu. Ya ce: "Ya Mutanena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautawa face shi kuma kada ku rage mudu da sikeli. Lalle ni, ina ganin ku da wadata. Kuma lalle ina ji muku tsoron azabar yini mai kewayewa

    [85] Ya mutanena! Ku cika mudu da sikeli da adalci, kuma kada ku naƙasta wa mutane kayansu, kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa kuna masu fasadi

    [86] Falalar Allah mai wanzuwa ita ce mafi alheri a gare ku idan kun kasance muminai, kuma ni ba mai tsaro ne a kanku ba

    [87] Suka ce: "Ya Shu'aibu! Shin sallarka ce take umurtar ka ga mu bar abin da ubanninmu suke bautawa, ko kuwa mu bar aikata abin da muke so a cikin dukiyoyinmu? Lalle, haƙiƙa kai ne mai haƙuri shiryayye

    [88] Ya ce: "Ya mutanena! Kun gani idan no kasance a kan hujja bayyananniya daga Ubangijina, kuma Ya azurta ni da arzikimai kyawo daga gare Shi? Kuma ba ni nufin in saɓa muku zuwa ga abin da nake hana ku daga gare shi. Ba ni nufin kome face gyara, gwargwadon da na sami dama. Kuma muwafaƙata ba ta zama ba face daga Allah. A gare shi na dogara, kuma zuwa gare Shi na wakkala

    [89] Kuma ya mutanena! Kada saɓa mini ya ɗauke ku ga misalin abin da ya sami mutanen Nuhu ko kuwa mutanen Hudu ko kuwa mutanen Salihu ya same ku. Mutanen Luɗu ba su zama a wuri mai nisa ba daga gare ku

    [90] Kuma ku nemi Ubangijinku gafara, sa'an nan kuma ku tuba zuwa gare shi. Lalle Ubangijina Mai Jin ƙai ne, Mai nuna soyayya

    [91] Suka ce: "Ya Shu'aibu! Ba mu fahimta da yawa daga abin da kake faɗi, kuma muna ganin ka mai rauni a cikinmu. Kuma ba domin jama'arka ba da mun jefe ka, saboda ba ka zama mai daraja a gunmu ba

    [92] Ya ce: "Ya mutanena! Ashe, jama'ata ce mafi daraja a gare ku daga Allah, kuma kun riƙe Shi a bayanku abin jefarwa? Lallene Ubangijina Mai kewayewa nega abin da kuke aikatawa

    [93] Kuma ya mutanena! Ku yi aiki a kan halinku. Lalle nimai aiki ne. Da sannu za ku san wane ne azaba za ta zo masa, ta wulakanta shi, kuma wane ne maƙaryaci. Kuma ku yi jiran dako, lalle ni mai dako ne tare da ku

    [94] Kuma a lokacin da umurninMu ya je, Muka kuɓutar da Shu'aibu da waɗanda suka yi imani tare da shi, saboda wata rahama daga gare, Mu. Kuma tsawa ta kama waɗanda suka yi zalunci. Sai suka wayi gari guggurfane a cikin gidajensu

    [95] Kamar ba su zauna ba a cikinsu. To, halaka ta tabbata ga Madyana kamar yadda Samudawa suka halaka

    [96] Kuma haƙiƙa Mun aiki Musa da ayoyinMu, da dalili bayyananne

    [97] Zuwa ga Fir'auna da majalisarsa. Sai suka bi umurnin Fir'auna, amma al'amarin Fir'auna bai zama shiryayye ba

    [98] Yana shugabantar mutanensa a Ranar Kiyama, har ya tuzgar da su a wuta. Kuma tir da irin tuzgawarsu

    [99] Kuma aka biyar musu da la'ana a cikin wannan duniyada Ranar Kiyama. Tir da kyautar da ake yi musu

    [100] Wancan Yana daga labaran alƙaryoyi. Muna ba ka labarinsu, daga gare su akwai wanda ke tsaye da kuma girbabbe

    [101] Kuma ba Mu zalunce su ba, amma sun zalunci kansu sa'an nan abubuwan bautawarsu waɗanda suke kiran su, baicin Allah, ba su wadatar musu kome ba a lokacin da umurnin Ubangijinka ya je, kuma (gumakan) ba su ƙara musu wani abu ba face hasara

    [102] Kuma kamar wancan ne kamun Ubangijinka, idan Ya kama alƙaryoyi alhali kuwa suna masu zalunci. Lalle kamunSa mai raɗaɗi ne, mai tsanani

    [103] Lalle ne a cikin wancan akwai aya ga wanda ya ji tsoron azabar Lahira. Wancan yini ne wanda ake tara mutane a cikinsa kuma wancan yini ne abin halarta

    [104] Ba Mu jinkirta shi ba face domin ajali ƙidayayye

    [105] Ranar da za ta zo wani rai ba ya iya magana face da izninSa. Sa'an nan daga cikinsu akwai shaƙiyyi da mai arziki

    [106] To, amma waɗanda suka yi shaƙawa, to, suna a cikin wuta. Suna masu ƙara da sheka acikinta

    [107] Suna madawwama a cikinta matuƙar sammai da ƙasa sun dawwama, face abin da Ubangijinka Ya so. Lalle Ubangijinka Mai aikatawa ne ga abin da Yake nufi

    [108] Amma waɗanda suka yi arziki to, suna a cikin Aljanna suna madawwama, a cikinta, matuƙar sammai da ƙasa sun dawwama, face abin da Ubangijinka Ya so. Kyauta wadda ba ta yankewa

    [109] Saboda haka kada ka kasance a cikin shakka daga abin da waɗannan suke bautawa. Ba su wata ibada face kamar yadda ubanninsu ke aikatawa a gabani. Kuma haƙiƙa Mu, Masu cika musu rabon su ne, ba tare da nakasawa ba

    [110] Kuma haƙiƙa, Mun bai wa Musa littafi, sai aka saɓa wa juna a cikinsa. Kuma ba domin wata kalma wadda ta gabata daga Ubangijinka ba, haƙiƙa, da an yi hukunci a tsakaninsu. Kuma haƙiƙa, suna a cikin wata shakka, game da shi, mai sanya kokanto

    [111] Kuma lalle, haƙiƙa, Ubangijinka Mai cika wa kowa (sakamakon) ayyukansa ne. Lalle Shi, Mai ƙididdigewa ne ga abin da suke aikatawa

    [112] Sai ka daidaitu kamar yadda aka umurce ka, kai da waɗanda suka tuba tare da kai kuna ba masu ƙetara haddi ba. Lalle shi, Mai gani ne ga abin da kuke aikatawa

    [113] Kada ku karkata zuwa ga waɗanda suka yi zalunci har wuta ta shafe ku. Kuma ba ku da waɗansu majiɓinta baicin Allah, sa'an nan kuma ba za a taimake ku ba

    [114] Kuma ka tsai da salla a gefe guda biyu na yini da wani yanki daga dare. Lalle ne ayyukan ƙwarai suna kore munanan ayyuka. wancan ne tunatarwa ga masu tunawa

    [115] Kuma ka yi haƙuri. Allah ba Ya tozartar da ladar masu kyautatawa

    [116] To, don me masu hankali ba su kasance daga mutanen ƙarnonin da suke a gabaninku ba, suna hani daga ɓarna a cikin ƙasa? face kaɗan daga wanda Muka kuɓutar daga gare su (sun yi hanin). Kuma waɗanda suka yi zalunci suka bin abin da aka ni'imtar da su a cikinsa, suka kasance masu laifi

    [117] Kuma Ubangijinka bai kasance Yana halakar da alƙaryu saboda wani zalunci ba, alhali mutanensu suna masu gyarawa

    [118] Kuma da Ubangijinka Ya so, da Ya sanya mutane al'umma guda. Kuma ba za su gushe ba suna masu saɓa wa juna

    [119] Sai wanda Ubangijinka Ya yi wa rahama, kuma domin wannan ne Ya halicce su. Kuma kalmar "Ubangijinka" Lalle ne za Ni cika Jahannama da aljannu da mutane gaba ɗaya" ta cika

    [120] Kuma dubi dai Muna ba da labari a gare ka daga labarun Manzanni, abin da Muke tabbatar da zuciyarka da shi. Kuma gaskiya ta zo maka a cikin wannan da wa'azi da tunatarwa ga masu imani

    [121] kuma kace wa waɗanda ba su yin imani, "Ku yi aiki a kan halinku, lalle mu masu aiki ne

    [122] Kuma ku yi Jiran dako, lalle mu masu Jiran dako ne

    [123] Kuma ga Allah gaibin sammai da ƙasa yake. Kuma zuwa gare Shi ake mayar da dukan al'amari. Saboda haka ku bauta Masa kuma ku dogara a kanSa. Kuma Ubangijinka bai zama Mai gafala daga abin da kuke aikatawa ba

    Yusufu

    Surah 12

    [1] L.R. Waɗancan ayoyin Littafi mai bayyanawa ne

    [2] Lalle ne Mu, Mun saukar da shi, yana abin karantawa na Larabci; tsammaninku, kuna hankalta

    [3] Mu, Muna bayar da labari a gare ka, mafi kyawon labari ga abin da Muka yi wahayin wannan Alƙur'ani zuwa gare ka. Kuma lalle ne ka kasance a gabaninsa, haƙiƙa, daga gafalallu

    [4] A lokacin da Yusufu ya ce wa ubansa, "Ya baba! Lalle ne ni, na ga taurari goma sha ɗaya, da rana da wata. Na gan su suna masu sujada a gare ni

    [5] Ya ce: "Ya ƙaramin ɗana! Kada ka faɗi mafarkinka ga 'yan'uwanka, har su ƙulla maka wani kaidi. Lalle ne Shaidan ga mutum, haƙiƙa, maƙiyi ne bayyananne

    [6] Kuma kamar wancan ne, Ubangijinka Yake zaɓen ka, kuma Ya sanar da kai daga fassarar labarai, kuma ya cika ni'imominSa a kanka, kuma a kan gidan Yaƙuba kamar yadda ya cika su a kan ubanninka biyu, a gabani, Ibrahim da Is'haƙa. Lalle Ubangijinka ne Masani, Mai hikima

    [7] Lalle ne, haƙiƙa, ayoyi sun kasance ga Yusufu da 'yan'uwansa domin masu tambaya

    [8] A lokacin da suka ce: lalle ne Yusufu da ɗan'uwansa ne mafiya soyuwa ga ubanmu daga gare mu, alhali kuwa mu jama'a guda ne. Lalle ubanmu, haƙiƙa, yana cikin ɓata bayyananniya

    [9] Ku kashe Yusufu, ko kuwa ku jefa shi a wata ƙasa, fuskar ubanku ta wofinta saboda ku, kuma ku kasance a bayansa mutane salihai

    [10] Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Kada ku kashe Yusufu. Ku jefa shi a cikin duhun rijiya, wasu matafiya su tsince shi, idan kun kasance masu aikatawa ne

    [11] Suka ce: "Ya babanmu! Mene ne a gare ka ba ka amince mana ba a kan Yusufu, alhalikuwa lalle ne mu, haƙaƙa masu nashiha muke a gare shi

    [12] Ka bar shi tare da mu a gobe, ya ji daɗi, kuma ya yi wasa. Kuma lalle ne mu, a gare shi, masu tsaro ne

    [13] Ya ce: "Lalle ne ni, haƙaƙa yana ɓata mini rai ku tafii da shi, Kuma ina tsoron kerkeci ya cinye shi, alhali ku kuwa kuna masu shagala daga gare shi

    [14] Suka ce: "Haƙiƙa idan kerkeci ya cinye shi, alhali kuwa muna dangin juna, lalle ne mu, a sa'an nan, hakika, mun zama masu hasara

    [15] To, a lokacin da suka tafi da shi, kuma suka yi niyyar su sanya shi a cikin duhun rijiya, Muka yi wahayi zuwa gare shi, "Lalle ne, kana ba su labari game da wannan al'amari nasu, kuma su ba su sani ba

    [16] Kuma suka je wa ubansu da dare suna kuka

    [17] Suka ce: "Ya babanmu! Lalle ne, mun tafi muna tsere, kuma muka bar Yusufu a wurin kayanmu, sai kerkeci ya cinye shi, kuma kai, ba mai amincewa da mu ba ne, kuma ko da mun kasance masu gaskiya

    [18] Kuma suka je, a jikin rigarsa akwai wani jinin ƙarya. Ya ce: "A'a, zukatanku suka ƙawata muku wani al'amari. Sai haƙuri mai kyau! Kuma Allah ne wanda ake neman taimako (a gunSa) a kan abin da kuke siffantawa

    [19] Kuma wani ayari ya je, sai suka aika mai neman musu ruwa, sai ya zura gugansa, ya ce: "Ya busharata! Wannan yaro ne." Kuma suka ɓoye shi yana abin sayarwa. Kuma Allah ne Masani ga abin da suke aikatawa

    [20] Kuma suka sayar da shi da 'yan kuɗi kaɗan, dirhamomi ƙidayayyu, Kuma sun kasance, a wurinsa, daga masu isuwa da abu kaɗan

    [21] Kuma wanda ya saye shi daga Masar ya ce wa matarsa, "Ki girmama mazauninsa, akwai tsammanin ya amfane mu, ko kuwa mu riƙe shi ɗa."Kuma kamar wancan ne Muka tabbatar ga Yusufu, a cikin ƙasa kuma domin Mu sanar da shi daia fassarar luburu, kuma Allah ne Marinjayi a kan al'amarinSa, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [22] Kuma a lokacin da ya isa mafi ƙarfinsa, Muka ba shi hukunci da ilmi. Kuma kamar wancan ne Muke saka wa masu kyautatawa

    [23] Kuma wadda yake a cikin ɗakinta, ta neme shi ga kansa, kuma ta kukkulle ƙofofi, kuma ta ce, "Ya rage a gare ka!" ya ce: "Ina neman tsarin Allah! Lalle shine Ubangijina. Ya kyautata mazaunina. Lalle ne shi, masu zalunci ba su cin nasara

    [24] Kuma lalle ne, ta himmantu da shi. Kuma ya himmantu da ita in ba domin ya ga dalilin Ubangijinsa ba. Kamar haka dai, domin Mu karkatar da mummunan aiki da alfasha daga gare shi. Lalle ne shi, daga bayinMu zaɓaɓɓu yake

    [25] Kuma suka yi tsere zuwa ga ƙofa. Sai ta tsage rigarsa daga baya, kuma suka iske mijinta a wurin ƙofar. Ta ce: "Menene sakamakon wanda ya yi nufin cuta game da iyalinka? Face a ɗaure shi, ko kuwa a yi masa wata azaba mai raɗaɗi

    [26] Ya ce: "Ita ce ta neme ni a kaina."Kuma wani mai shaida daga mutanenta ya bayar da shaida: "Idan rigarsa ta kasance an tsage ta daga gaba, to, ta yi gaskiya, kuma shi ne daga maƙaryata

    [27] Kuma idan rigarsa ta kasance an tsage ta daga baya, to, ta yi ƙarya, kuma shi ne daga masu gaskiya

    [28] Sa'an nan a lokacin da ya ga rigarsa an tsage ta daga baya, ya ce: "Lalle ne shi, daga kaidinku ne, mata! Lalle ne kaidinku mai girma ne

    [29] Yusufu! Ka kau da kai daga wannan. Kuma ki nemi gafara domin laifinki. Lalle ne ke, kin kasance daga masu kuskure

    [30] Kuma waɗansu mata a cikin Birnin suka ce: "Matar Aziz tana neman hadiminta daga kansa! Haƙiƙa, ya rufe zuciyarta da so. Lalle ne mu, Muna ganin taa cikin ɓata bayyananna

    [31] Sa'an nan a lokacin da ta ji labari game da makircinsu, sai ta aika kiran liyafa zuwa gare su, kuma ta yi tattalin abincin da ake dogara wajen cinsa, kuma ta bai wa kowace ɗaya daga cikinsu wuƙa, kuma ta ce: "Ka fito a kansu." To, a lokacin da, suka gan shi, suka girmama shi, kuma suka yanyanke hannayensu, kuma suka ce: "Tsarki yana ga Allah! Wannan ba mutum ba ne! Wannan bai zama ba face Mala'ika ne mai daraja

    [32] Ta ce: "To wannan ne fa wanda kuka, zarge ni a cikinsa! Kuma lalle ne, haƙeƙa na neme shi daga kansa, sai ya tsare gida, kuma ni ina rantsuwa, idan bai aikata abin da nake umurnin sa ba, haƙeƙa ana ɗaure shi. Haƙiƙa, yana kasan, cewa daga ƙasƙantattu

    [33] Ya ce: "Ya Ubangijina! Kurkuku ne mafi soyuwa a gare ni daga abin da suke kira na zuwa gare shi. Kuma idan ba Ka karkatar da kaidinsu daga gare ni ba, zan karkata zuwa gare su, kuma in kasance daga jahilai

    [34] Sai Ubangijinsa Ya karɓa masa saboda haka Ya karkatar da kaidinsu daga gare shi. Lalle Shi ne Mai ji, Masani

    [35] Sa'an nan kuma ya bayyana a gare su a bayan sun ga alamomin, lalle ne dai su ɗaure shi har zuwa wani lokaci

    [36] Kuma waɗansu samari biyu suka shiga kurkuku tare da shi. ¦ayansu ya ce: "Lalle ne ni, na yi mafarkin ga ni ina matsar giya." Kuma ɗayan ya ce: "Lalle ne ni, na yi Mafarkin ga ni ina ɗauke da waina a bisa kaina, tsuntsaye suna ci daga gare ta. Ka ba mu labari game da fassararsu. Lalle ne mu, Muna ganin ka daga masu kyautatawa

    [37] Ya ce: "Wani abinci ba zai zo muku ba wanda ake azurta ku da shi face na ba ku labarin fassararsa, kafin ya zo muku. Wannan kuwa yana daga abin da Ubangijina Ya sanar da ni. Lalle ne ni na bar addinin mutane waɗanda ba su yi imani da Allah ba, kuma game da lahira, su kafirai ne

    [38] Kuma na bi addinin iyayena, Ibrahim da Is'haka da Yaƙuba. Ba ya yiwuwa a gare mu mu yi shirka da Allah da kome. Wannan yana daga falalar Allah a kanmu da mutane, amma mafi yawan mutane ba su godewa

    [39] Ya abokaina biyu na kurkuku! Shin iyayen giji dabam-dabam ne mafiya alheri ko kuwa Allah Makaɗaici Mai tanƙwasawa

    [40] Ba ku bauta wa kome, baicinSa, face waɗansu sunaye waɗanda kuka ambace su, ku da ubanninku. Allah bai saukar da wani dalili ba game da su. Babu hukunci face na Allah. Ya yi umurnin kada ku bauta wa kowa face Shi. Wancan ne addini madaidaici, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [41] Ya abokaina biyu, na kurkuku! Amma ɗayanku, to, zai shayar da uban gidansa giya, kuma gudan, to, za a tsire shi, sa'an nan tsuntsaye su ci daga kansa. An hukunta al'amarin, wanda a cikinsa kuke yin fatawa

    [42] Kuma ya ce da wanda ya tabbatar da cewa shi mai kuɓuta ne daga gare su, "Ka ambace ni a wurin uban gidanka." Sai Shaiɗan ya mantar da shi tunawar Ubangijinsa, saboda haka ya zauna a cikin kurkuku 'yan shekaru

    [43] Kuma sarki ya ce: "Lalle ne, na yi mafarki; na ga shanu bakwai masu ƙiba, waɗansu bakwai ramammu, suna cin su, da zangarku bakwai kore-kore da waɗansu ƙeƙasassu. Ya ku jama'a! Ku yi mini fatawa a cikin mafarkina, idan kun kasance ga mafarki kuna fassarawa

    [44] Suka ce: "Yaye-yayen mafarki ne, kuma ba mu zamo masana ga fassarar yaye-yayen mafarki ba

    [45] Kuma wannan da ya kuɓuta daga cikinsu ya ce: a bayan ya yi tunani a lokaci mai tsawo, "Ni, ina ba ku labari game da fassararsa. Sai ku aike ni

    [46] Ya Yusufu! Ya kai mai yawan gaskiya! Ka yi mana fatawa a cikin shanu bakwai masu ƙiba, waɗansu bakwai ramammu suna cin su, da zangarku bakwai koraye da waɗansu ƙeƙasassu, tsammanina in koma ga mutane, tsammaninsu za su sani

    [47] Ya ce: "Kuna shuka, shekara bakwai tutur, sa'an nan abin da kuka girbe, sai ku bar shi, a cikin zanganniyarsa, sai kaɗan daga abin da kuke ci

    [48] Sa'an nan kuma waɗansu bakwai masu tsanani su zo daga hayan wancan, su cinye abin da kuka gabatar dominsu, face kaɗan daga abin da kuke adanawa

    [49] Sa'an nan kuma wata shekara ta zo daga bayan wancan, a cikinta ake yi wa mutane ruwa mai albarka, kuma a cikinta suke matsar abin sha

    [50] Kuma sarkin ya ce: "Ku zo mini da shi." To, a lokacin da manzo ya je masa (Yusufu), ya ce: "Ka koma zuwa ga uban gidanka, sa' an nan ka tambaye shi; Menene halin matayen nan waɗanda suka yanyanke hannayensu? Lalle ne Ubangijina ne Masani game da kaidinsu

    [51] Ya ce: "Mene ne babban al'amarinku, a lokacin da kaka nemi Yusufu daga kansa?" Suka ce: "Tsarki ga Allah yake! Ba mu san wani mummunan aiki a kansaba." Matar Aziz ta ce: "Yanzu fagaskiya ta bayyana. Ni ce na neme shi daga kansa. Kuma lalle ne shi, haƙiƙa, yana daga masu gaskiya

    [52] Wancan ne, domin ya san cewa lalle ne ni ban yaudareshi ba a ɓoye, kuma lalle Allah ba Ya shiryar da kaidin mayaudara

    [53] Kuma ba ni kuɓutar da kaina. Lalle ne rai, haƙiƙa, mai yawan umurni ne da mummunan aiki, face abin da Ubangjina Ya yi na; rahama. Lalle Ubangjina Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [54] Kuma sarkin ya ce: "Ku zo mini da shi in keɓe shi ga kaina." To, a lokacin da Yusufu ya yi masa magana sai ya ce: "Lalle ne kai a yau, a gunmu, mai daraja ne, amintacce

    [55] Ya ce: "Ka sanya ni a kan taskokin ƙasa. Lalle ne ni, mai tsarewa ne, kuma masani

    [56] Kuma kamar wancan ne Muka bayar da iko ga Yusufu a cikin ƙasa yana sauka a inda duk yake so. Muna samun wanda Muke so da rahamar Mu, kuma ba Mu tozartar da ladar masu kyautatawa

    [57] Kuma lalle ladar Lahira ce mafi alheri ga waɗandasuka yi imani, kuma suka kasance masu taƙawa

    [58] Kuma 'yan'uwan Yusufu suka je, sa'an nan suka shiga a gare shi, sai ya gane su, alhali kuwa su, suna masu musunsa

    [59] Kuma a lokacin da ya yi musu tattali da tattalinsu, ya ce: "Ku zo mini da wani ɗan'uwa naku daga ubanku. Ba ku gani ba cewa lalle ne ni, ina cika ma'auni, kuma ni ne mafi alherin masu saukarwa

    [60] Sa'an nan idan ba ku zo mini da shi ba, to, babu awoa gare ku a wurina, kuma kada ku, kasance ni

    [61] Suka ce: "Za mu neme shi daga ubansa. Kuma lalle ne mu, haƙiƙa, masu aikatawa ne

    [62] Kuma ya ce wa yaransa, "Ku sanya hajjarsu a cikin kayansu, tsammaninsu suna gane ta idan sun juya zuwa ga mutanensu, tsamma ninsu, za su komo

    [63] To, a lokacin da suka koma zuwa ga ubansu, suka ce: "Ya babanmu! An hana mu awo sai ka aika ɗan'uwanmu tare da mu. Za mu yi awo. Kuma lalle ne, haƙiƙa mu, masu lura da Shi ne

    [64] Ya ce: "Ashe, za ni amince muku a kansa? Face dai kamar yadda na amince muku a kan ɗan'uwansa daga gabani, sai dai Allah ne Mafificin masu tsari, kuma Shi ne Mafi rahamar masu rahama

    [65] Kuma a lokacin da suka buɗe kayansu, suka sami hajjarsu an mayar musu da ita, suka ce: "Ya babanmu! Ba mu zalunci! Wannan hajjarmu ce an mayar mana da ita, kuma mu nemo wa iyalinmu abinci, kuma mu kiyaye ɗan'uwanmu, kuma mu ƙara awon kayan raƙumi guda, wancan awo ne mai sauki

    [66] Ya ce: "Ba zan sake shi tare da ku ba, sai kun kawo mini alkawarinku baga Allah, haƙiƙa, kuna dawo mini da shi, sai fa idan an kewaye ku." To, a, lokacinda suka yi masa alkawari, ya ce: "Allah ne wakili a kan abin da muke faɗa

    [67] Kuma ya ce: "Ya ɗiyana! Kada ku shiga ta ƙofa guda, ku shiga ta ƙofofi dabam-dabam, kuma ba na wadatar muku kome daga Allah. Babu hukunci face daga Allah, a gare Shi na dogara, kuma a gare Shi masu dogara sai su dogara

    [68] Kuma a lokacin da suka shiga daga inda ubansu ya umurce su wani abu bai kasance yana wadatarwa ga barinsu daga Allah ba face wata bukata ce a ran Yaƙubu, ya bayyana ta. Kuma lalle ne shi, haƙiƙa, ma'abucin wani ilmi ne ga abin da Muka sanar da shi, kuma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [69] Kuma a lokacin da suka shiga wajen Yusufu, ya tattara ɗan'uwansa zuwa gare shi, ya ce: "Lalle ni ne ɗan'uwanka, saboda haka kada ka yi baƙin ciki da abin da suka kasance suna aikatawa

    [70] Sa'an nan a lokacin da ya yi musu tattali da tattalinsu, sai ya sanya ma'auni a cikin kayan ɗan'uwansa sa'an nan kuma mai yekuwa ya yi yekuwa," Ya ku ayari! lalle ne, haƙiƙa ku ɓarayi ne

    [71] Suka ce: kuma suka fuskanta zuwa gare su: "Mene ne kuke nema

    [72] Suka ce: "Muna neman ma'aunin sarki. Kuma wanda ya zo da shi, yana da kayan rakumi ɗaya, kuma ni ne lamuni game da shi

    [73] Suka ce: "Tallahi! Lalle ne, haƙiƙa, kun sani, ba mu zodon mu yi ɓarna a cikin ƙasa ba, kuma ba mu kasance ɓarayi ba

    [74] Suka ce: "To mene ne sakamakonsa idan, kun kasance maƙaryata

    [75] Suka ce: "Sakamakonsa, wanda aka same shi a cikin kayansa, to, shi ne sakamakonsa, kamar wancan ne muke saka wa azzalumai

    [76] To, sai ya fara (bincike) da jikunansu a gabanin jakar ɗan'uwansa. Sa'an nan ya fitar da ita daga jakar ɗan'uwansa. Kamar wancan muka shirya wa Yusufu. Bai kasance ya kama ɗan'uwansa a cikin addinin (dokokin) sarki ba, face idan Allah Ya so. Muna ɗaukaka darajoji ga wanda Muka so, kuma a saman kowane ma'abucin ilmi akwai wani masani

    [77] Suka ce: "Idan ya yi sata, to, lalle ne wani ɗan'uwansa ya taɓa yin sata a gabaninsa." Sai Yusufu ya boye ta a cikin ransa. Kuma bai bayyana ta ba a gare su, ya ce: "Ku ne mafi sharri ga wuri. Kuma Allah ne Mafi sani daga abin da kuke siffantawa

    [78] Suka ce: "Ya kai Azizu! Lalle ne yana da wani uba, tsoho mai daraja, saboda haka ka kama ɗayanmu amatsayinsa. Lalle ne mu, muna ganin ka daga masu kyautatawa

    [79] Ya ce: "Allah Ya tsare mu daga mu kama wani face wanda muka sami kayanmu a wurinsa. Lalle ne mu, a lokacin nan, haƙiƙa, azzalumai ne

    [80] Saboda haka, a lokacin da suka yanke tsammani daga gare shi, sai suka fita suna masu ganawa. Babbansu ya ce: "Shin, ba ku sani ba cewa lalle ne ubanku yariƙi alkawari daga Allah a kanku, kuma daga gabanin haka akwai abin da kuka yi na sakaci game da Yusufu? Saboda haka, ba zan gushe daga ƙasar nan ba face ubana ya yi mini izni, ko kuwa Allah Ya yi hukunci a gare ni, kuma Shi ne Mafi alherin mahukunta

    [81] Ku koma zuwa ga ubanku, ku gaya masa: Ya babanmu, lalle ne ɗanka ya yi sata, kuma ba mu yi shaida ba face da abin da muka sani, kuma ba mu kasance mun san gaibu ba

    [82] Kuma ka tambayi alƙarya wadda muka kasance a cikinta da ayari wanda muka gabato acikinsa, kuma lalle ne haƙiƙa, mu masu gaskiya ne

    [83] Ya ce: "A'a, zukatanku sun ƙawata wani al'amari a gare ku. Sai haƙuri mai kyawo, akwai tsammanin Allah Ya zo mini da su gaba ɗaya (Yusufu da 'yan'uwansa). Lalle ne Shi ne Masani, Mai hikima

    [84] Kuma ya juya daga gare su, kuma ya ce: "Ya baƙin cikina a kan Yusufu!" Kuma idanunsa suka yi fari saboda huznu sa'an nan yana ta haɗewar haushi

    [85] Suka ce: "Tallahi! Ba za ka gushe ba, kana ambaton Yusufu, har ka kasance Mai rauni ƙwarai, ko kuwa ka kasance daga masu halaka

    [86] Ya ce: "Abin sani kawai, ina kai ƙarar baƙin cikina da sunona zuwa ga Allah, kuma na san abin da ba ku sani ba daga Allah

    [87] Ya ɗiyana! Sai ku tafi ku nemo labarin Yusufu da ɗan'uwansa. Kada ku yanke tsammani daga rahamar Allah. Lalle ne, babu Mai yanke tsammani daga rahamar Allah face mutane kafirai

    [88] Sa'an nan a lokacin da suka shiga gare shi suka ce: "Ya kai Azizu! Cuta ta shafe mu, mu da iyalinmu, kuma mun zo da wata haja maras kuma. Sai ka cika mana ma'auni, kuma ka yi sadaka a gare mu. Lalle ne Allah Yana saka wa masu yin sadaka

    [89] Ya ce: "Shin, kan san abin da kuka aikata ga Yusufu da ɗan'uwansa a lokacin da kuke jahilai

    [90] Saka ce: "Shin ko, lalle ne, kai ne Yusufu?" Ya ce: "Ni ne Yusufu, kuma wamian shi ne ɗan'uwana. Hƙiƙa Allah Ya yi falala a gare mu. Lalle ne, shi wanda ya bi Allah da taƙawa, kuma ya yi haƙuri, to, Lalle ne Allah ba Ya tozarta ladar masu kyautatawa

    [91] Suka ce: "Tallahi! Lalle ne haƙiƙa, Allah Ya zaɓe ka akannmu, kuma lalle ne mun kasance, haƙiƙa, masu kuskure

    [92] Ya ce: "Babu zargi akanku a yau, Allah Yana gafarta muku, kuma Shi ne Mafi rahamar masu rahama

    [93] Ku tafi da rigata wannan, sa'an nan ku jefa ta a kan fuskar mahaifina, zai koma mai gani. Kuma ku zo mini da iyalinku baki ɗaya

    [94] Kuma, a lokacin da ayari ya bar (Masar) ubansa ya ce: "Lalle ne ni ina shaƙar iskar Yusufu, ba domin kana ƙaryata ni ba

    [95] Suka ce: "Tallahi lalle ne, kai, haƙiƙa, kana a cikin ɓatarka daɗaɗɗa

    [96] Sa'an nan a lokacin da mai bayar da bushara ya je, sai ya jefa ta a kan fuskarsa, sai ya koma mai gani. Ya ce: "Shin, ban gaya muku ba, lalle ne, ni ina sanin abin da ba ku sani ba, daga Allah

    [97] Suka ce: "Ya ubanmu! ka nema mana gafara ga zunubanmu, lalle ne mu, mun kasance masu kuskure

    [98] Ya ce: "Da sannu za ni nema muku gafara daga Ubangijina. Shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [99] Sa'an nan a lokacin da suka shiga gun Yusufu, ya tattara mahaifansa biyu a gare shi, kuma ya ce: "Ku shiga Masar in Allah Ya so, kuna amintattu

    [100] Kuma ya ɗaukaka iyayensa biyu a kan karaga, sa'an nan suka faɗi a gare shi, suna masu sujada. Kuma ya ce: "Ya babana! Wannan ita ce fassarar mafarkin nan nawa. Lalle ne Ubangijina Ya sanya shi ya tabbata sosai, kuma lalle ne Ya kyautata game da ni a lokacin da Ya fitar da ni daga kurkuku. Kuma Ya zo da ku daga ƙauye, a bayan Shaiɗan ya yi fisgar ɓarna a tsakanina da tsakanin 'yan'uwana, Lalle ne Ubangijina Mai tausasawa ne ga abin da Yake so. Lalle ne Shi, Shi ne Masani, Mai hikima

    [101] Ya Ubangijina lalle ne Ka ba ni daga mulki, kuma Ka sanar da ni daga fassarar labaru. Ya Mahaliccin sammai da ƙasa! Kai ne Majiɓincina a duniya da Lahira Ka karɓi raina ina Musulmi, kuma Ka riskar da ni ga salihai

    [102] Wannan daga labarun gaibi ne, Muna yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ba ka kasance a wurinsu ba a lokacin da suke yin niyyar zartar da al'amarinsu, alhali suna yin makirci

    [103] Kuma mafi yawan mutane ba su zama masu imani ba, ko da ka yi kwaɗayin haka

    [104] Kuma ba ka tambayar su wata lada a kansa. Shi bai zama ba face ambato domin halittu

    [105] Kuma da yawa, wata aya a cikin sammai da ƙasa suna shuɗewa a kanta kuma su, suna bijirewa daga gare ta

    [106] Kuma mafi yawansu ba su yin imani da Allah face kuma suna masu shirki

    [107] Shin fa, sun amince cewa wata masifa daga azabar Allah ta zo musu ko kuwa Tashin ¡iyama ta zo musu kwatsam, alhali su ba su sani ba

    [108] Ka ce: "Wannan ce hanyata; ina kira zuwa ga Allah a kan basira, ni da waɗanda suka bi ni, kuma tsarki ya tabbata ga Allah! Ni kuma, ban zama daga masu shirki ba

    [109] Kuma ba Mu aika ba a gabaninka face mazaje, Muna wahayi zuwa gare su, daga mutanen ƙauyuka. Shin fa, ba su yi tafiya a cikin ƙasa ba, domin su dubayadda aƙibar waɗanda suka kasance daga gabaninsu ta zama? Kuma lalle ne gidan Lahira shi ne mafi alheri ga waɗanda suka yi taƙawa? Shin fa, ba ku hankalta

    [110] Har a lokacin da Manzanni suka yanke tsammani, kuma suka yi zaton cewa an jingina suga ƙarya, sai taimakonMu ya je masu, Sa'an nan Mu tserar da wanda Muke so, kuma ba a mayar da azabarMu daga mutane masu laifi

    [111] Lalle ne haƙiƙa abin kula ya kasance a cikin ƙissoshinsu ga masu hankali. Bai kasance wani ƙirƙiran labari ba kuma amma shi gaskatawa ne ga, abin da yake a gaba gare shi, da rarrabewar dukan abubuwa, da shiriya da rahama ga mutane waɗanda suka yi imani

    Ar'Ra'ad

    Surah 13

    [1] L. M.R. Waɗancan ayoyin littafi ne kuma abin da aka saukar gare ka daga Ubangijinka ne gaskiya, kuma amma mafi yawan mutane ba su yin imani

    [2] Allah Shi ne wanda Ya ɗaukaka sammai, ba da ginshiƙai ba waɗanda kuke ganin su. Sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, kuma Ya hore rana da wata, kowane yana gudana zuwa ga ajali ambatacce. Yana shirya al'amari, Yana rarrabe ayoyi daki-daki, mai yiwuwa ne ku yi yaƙini da haɗuwa da Ubangijinku

    [3] Kuma shi, ne wanda Ya shimfiɗa kasa, kuma Ya sanya duwatsu da koguna a cikinta, kuma daga dukan 'ya'yan itace Ya sanya ma'aura biyu cikinsu. Yana sanya dare ya rufe yini. Lalle ne a cikin wancan, haƙiƙa akwai ayoyi ga mutane waɗanda suke yin tunani

    [4] Kuma a cikin ƙasa akwai yankuna masu maƙwabtaka, da gonaki na inabobi da shuka da dabinai iri guda, da waɗanda ba iri guda ba, ana shayar da su da ruwa guda. Kuma Muna fifita sashensa a kan sashe a wajen ci. Lalle ne a cikin wancan akwai ayoyi ga muiane waɗanda suke hankalta

    [5] Kuma idan ka yi mamaki, to, mamakin kam shi ne maganarsu, "Shin, idan muka kasance turɓaya, za mu zama a cikin wata halitta sabuwa?" Waɗancan ne waɗanda suka kafirta da Ubangijinsu, kuma waɗanda akwai ƙuƙumai a cikin wuyoyinsu, kuma waɗancan ne abokan wuta. Su, a cikinta, masu dawwama ne

    [6] Kuma suna neman ka da gaggawa da azaba a gabanin rahama, alhali kuwa abubuwan misali sun gabata a gabaninsu. Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙiƙa, Ma'abucin gafara ne ga mutane a kan zaluncinsu, kuma lalle ne Ubangijinka, haƙiƙa, Mai tsananin uƙuba ne

    [7] Kuma waɗanda suka kafirta suna cewa don me ba a saukar da wata aya a gare shi ba daga Ubangijinsa? Abin sani kawai, kai dai mai gargaɗi ne kuma a cikin kowaɗanne mutane akwai mai shiryarwa

    [8] Allah Yana sanin abin da kowace mace take ɗauke da shi a cikinta da abin da mahaifu suke ragewa da abin da suke ƙarawa. Kuma dukkan kome, a wurinSa, da gwargwado yake

    [9] Shi ne Masanin fake da bayyane, Mai girma, Maɗaukaki

    [10] Daidai ne daga gare ku, wanda ya asirta magana da wanda ya bayyana game da ita, da wanda yake shi mai neman ɓoyewa ne da dare, da mai bayyana a cikin tafiyarsa a hanya da rana

    [11] (Kowannenku) Yana da waɗansu mala'iku masu maye wa juna a gaba gare shi da baya gare shi, suna tsare shi daga umurnin Allah. Lalle ne Allah ba Ya canja abin da yake ga, mutane sai sun canja abin da yake ga zukatansu. Kuma idan Allah Ya yi nufin wata azaba game da mutane, to, babu mai mayar da ita, kuma ba su da wani majiɓinci baicin Shi

    [12] Shi ne Wanda Yake nuna muku walƙiya domin tsoro da tsammani, kuma Ya ƙaga halittar giragizai masu nauyi

    [13] Kuma aradu tana tasbihi game da gode Masa, da mala'iku domin tsoronsa. Kuma Yana aiko tsawawwaki, sa'an nan Ya sami wanda Yake so da su alhali kuwa su, suna jayayya a cikin (al'amarin) Allah kuma shi ne mai tsananin hila

    [14] Yana da kiran gaskiya, kuma waɗanda (kafirai) suke kira baicinsa, ba su karɓa musu da kome face kamar mai shimfiɗa tafukansa Zuwa ga ruwa (na girgije) domin (ruwan) ya kai ga bakinsa, kuma shi ba mai kaiwa gare shi ba. Kuma kiran kafirai (ga wanin Allah) bai zama ba face yana a cikin ɓata

    [15] Kuma saboda Allah wanda yake a cikin sammai da ƙasa suke yin sujada, so da ƙi, kuma da inuwoyinsu, a safe da maraice

    [16] Ka ce: "Wane ne Ubangijin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Allah". Ka ce: "Ashe fa, kun riƙi waɗansu masoya baicin Shi, waɗanda ba su mallaka wa kansu wani amfani ba kuma haka ba su ture wata cuta?" Ka ce: "Shin makaho da mai gani suna daidaita? Ko shin duhu da haske suna daidaita? ko sun sanya ga Allah waɗansu abokan tarayya waɗanda suka yi halitta kamar halittarSa sa'an nan halittar ta yi kama da juna a gare su?" Ka ce: "Allah ne Mai halitta kome kuma Shi ne Maɗaukaki, Marinjayi

    [17] Ya saukar da ruwa daga sama, sai magudanai suka gudana da gwargwadonsu, Sa'an nan kogi ya ɗauki kumfa mai ƙaruwa, kuma daga abin da suke zuga a kansa (azurfa ko zinari ko ƙarfe) a cikin wuta domin neman ado ko kuwa kayan ɗaki akwai kumfa misalinsa (kumfar ruwa). Kamar wancan ne Allah Yake bayyana gaskiya da ƙarya. To, amma kumfa, sai ya tafi ƙeƙasasshe, kumaamma abin da yake amfanin mutane sai ya zauna a cikin ƙasa. Kamar wancan ne Allah Yake bayyana misalai

    [18] Ga waɗanda suka karɓa wa Ubangijinsu akwai abu mafi kyau a gare su, kuma waɗanda suke ba su karɓa Masa ba, to, lalle da suna da abin da yake a cikin ƙasa gaba ɗaya da misalinsa tare da shi, haƙiƙa, da sun yi fansa da shi. Waɗancan suna da mummunan bincike kuma matabbatarsu Jahannama ce, kuma tir da ita ta zama shimfida

    [19] Shin, fa, wanda yake sanin cewa lalle abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka ne gaskiya yana zama kamar wanda yake makaho? Abin sani kawai masu hankali su ke yin tunani

    [20] Su ne waɗanda suke cikawa da alkawarin Allah, kuma ba su warware alkawari

    [21] Kuma su ne waɗanda suke sadar da abin da Allah Ya yi umurni da shi domin a sadar da shi kuma suna tsoron Ubangijinsu, kuma suna tsoron mummunan bincike

    [22] Kuma waɗanda suka yi haƙuri domin neman yardar Ubangijinsu, kuma suka tsayar da salla, kuma suka ciyar da abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane, kuma suna tunkuɗe mummunan aiki da mai kyau. Waɗancan suna da aƙibar gida mai kyau

    [23] Gidajen Aljannar zama suna shigarsu, su da waɗandasuka kyautatu daga iyayensu, da matansu da zuriyarsu. Kuma mala'iku suna shiga zuwa gunsu ta kowace kofa

    [24] Aminci ya tabbata a kanku saboda abin da kuka yi wa haƙuri. Saboda haka madalla da ni'imar aƙibar gida

    [25] Kuma waɗanda suka warware alkawarin Allah daga bayan ƙulla shi, kuma suna yanke abin da Allah Ya yi umurui da shi domin a sadar da shi kuma suna ɓarna a cikin ƙasar. Waɗancan suna da wata la'ana, kuma suna da munin gida

    [26] Allah ne Yake shimfiɗa arziki ga wanda Yake so, kuma Yana ƙuntatawa. Kuma sun yi farin ciki da rayuwar duniya, alhalikuwa rayuwar duniya ba ta zama ba dangane ga ta Lahira face jin daɗi kaɗan

    [27] Kuma wanɗanda suka kafirta, suna cewa, "Don me ba a saukar da wata aya ba a kansa daga Ubangijinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Yana ɓatar da wanda Yake so kuma Yana shiryar da wanda ya tuba zuwa gare shi

    [28] Waɗanda suka yi imani kuma zukatansu sukan natsu da ambaton Allah. To, da ambaton Allah zukata suke natsuwa

    [29] Waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata aiki nagari, farin ciki ya tabbata a gare su, da kyakkyawar makoma

    [30] Kamar wancan ne Muka aika ka a cikin al'umma wanda take waɗansu al'ummai sun shuɗe daga gabaninta, domin ka karanta musu abin da Muka yi wahayi zuwa a gare ka, alhali kuwa su, sunakafirta da Rahaman. Ka ce: "Shi ne Ubangijina, babu abin, bautawa face Shi, a gare Shi na dogara, kuma zuwa gare Shi tubata take

    [31] Kuma da lalle an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwatsu game da shi, ko kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu da shi (da ba su yi imani ba). A'a ga Allah al'amari yake gaba ɗaya! Shin fa, waɗanda suka yi imani ba su yanke tsammani ba da cewa da Allah Ya so, da Ya shiryar da mutane gaba ɗaya? Kuma waɗanda suka yi kafirci ba za su gushe ba wata masifa tana samun su saboda abin da suka aikata, ko kuwa ka sauka kusa da gidajensu, har wa'adin Allah ya zo. Kuma lalle ne Allah ba ya saɓa wa lokacin alkawari

    [32] Kuma lalle ne, haƙiƙa, an yi izgili da Manzanni kafinka, sai Na yi jinkiri ga waɗanda suka kafirta, sa'an nan Na kama su. To, yaya uƙubata take

    [33] Shin fa, wanda shi Yake tsaye a kan kowane rai game da abin da ya tanada (zai zama kamar wanda ba haka ba)? Kuma suka sanya abokan tarayya ga Allah! Ka ce: "Ku ambaci sunayensu."Ko kuna bai wa Allah labari ne game da abin da bai sani ba a cikin ƙasa? Ko da bayyananniyar magana kuke yin shirka, (banda a cikin zuciya)? A'a, an dai ƙawata wa waɗanda suka kafirta makircinsu kuma an kange su daga hanya. Kuma wanda Allah Ya ɓatar to, babu wani mai shiryarwa a gare shi

    [34] Suna da wata azaba a cikin rayuwar duniya, kuma haƙiƙa azabar Lahira ce mafi tsanani kuma babu wani mai tsare su daga Allah

    [35] Misalin Aljanna wadda aka yi alkawarinta ga masu taƙawa, ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinta. Abincinta yana madawwami da inuwarta. Waccan ce aƙibar waɗanda suka yi taƙawa, kuma aƙibar kafirai, ita ce wuta

    [36] Kuma waɗanda Muka ba su Littafi suna farin ciki da abin da aka saukar zuwa gare ka, kuma daga ƙungiyoyi akwai mai musun sashensa. Ka ce: "Abin sani kawai, an umurce ni da in bauta wa Allah kuma kada in yi shirka da Shi, zuwa gare Shi nake kira, kuma zuwa gare Shi makomata take

    [37] Kuma kamar wancan ne Muka saukar da shi, Hukunci a cikin Larabci. Kuma lalle ne idan ka bi son zuciyoyinsu a bayan abin da ya zo maka na ilmi, babu wani masoyi a gare ka mai kare ka daga Allah, kuma babu matsari

    [38] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun aika waɗansu manzanni, daga gabaninka, kuma Muka sanya matan aure a gare su da zuriyya, kuma ba ya kasancewa ga wani Manzo ya zo da wata aya, sai da iznin Allah. Ga kowane ajali akwai littafi

    [39] Allah Yana shafe abin da Yake so, kuma Yana tabbatarwa kuma a wurinsa asalin Littafin yake

    [40] Kuma imma lalle Mu nuna maka sashen abin da Muke yi musu wa'adi, ko kuwa lalle Mu karɓi ranka to abin sani kawai iyarwa ce a kanka, kuma hisabi yana gare Mu

    [41] Shin, kuma ba su gani ba cewa lalle ne, Muna je wa ƙasar (su), Muna rage ta daga gefunanta? Kuma Allah ne Yake yin hukuncinsa. Babu mai bincike ga hukuncinsa. Kuma shi ne Mai gaggawar sakamako

    [42] Kuma lalle ne waɗanda suke a gabaninsu sun yi makirci. To, ga Allah makircin yake gaba ɗaya. Ya san abin da kowane rai yake tanada. Kuma kafirai za su sani, ga wane aƙibar gida take

    [43] Kuma waɗanda suka kafirta suna cewa: "Ba a aiko ka ba." Ka ce, "Allah Ya isa zama shaida a tsakanina da tsakaninku da wanda yake a wurinsa akwai ilmin Littafi

    Ibrahim

    Surah 14

    [1] L.R. Littafi ne mun saukar da shi zuwa gare ka domin ka fitar da mutane daga duhunhuna zuwa ga haske, da iznin Ubangijinsu, zuwa ga tafarkin Mabuwayi, Abin godewa

    [2] Allah wanda Yake Yana da abin da ke cikin sammai da cikin ƙasa. Kuma bone ya tabbata ga kafirai daga azaba mai tsanani

    [3] Waɗanda suka fi son rayuwar duniya fiye da ta Lahira, kuma suna kangewa daga hanyar Allah, kuma suna neman ta karkace. Waɗancan na a cikin ɓata mai nisa

    [4] Kuma ba Mu aika wani Manzo ba face da harshen mutanensa domin ya bayyana musu. Sa'an nan Allah Ya ɓatar da wanda Yake so kuma Ya shiryar da wanda Yake so, Kuma shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [5] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun aika Musa game, da ayoin Mu cewa, "Ka fitar da mutanenkadaga duhu zuwa ga haske. Kuma ka tunar musu da kwanukan (masifun) Allah." Lalle ne a cikin wancan akwai ayoyi domin dukan mai yawan haƙuri, mai godiya

    [6] Kuma a lokacin da Musa yace wa mutanensa, "Ku tuna ni'imar Allah a kanku a lokacin da Ya tsirar da ku daga mutanen Fir'auna, suna yi muku mummunar azaba, kuma suna yanyanka ɗiyanku, kuma suna rayar da matanku. Kuma a cikin wancan akwai jarrabawa mai girma daga Ubangijinku

    [7] Kuma a lokacin da Ubangijinku Ya sanar, "Lalle ne idan kun gode, haƙiƙa, Ina ƙaramuku, kuma lalle ne idan kun kafirta haƙiƙa azabata, tabbas, mai tsanani ce

    [8] Kuma Musa ya ce: "Idan kun kafirta ku da waɗanda suke a cikin ƙasa, gaba ɗaya, to, lalle ne Allah haƙiƙa Mawadaci ne, Mai yawan godiya

    [9] Shin labarin waɗanda suke a gabaninku, mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa bai zomuku ba? Kuma da waɗanda suke daga bayansu babu wanda yake sanin su face Allah? Manzanninsu sun je musu da hujjoji mabayyana, sai suka mayar da hannayensu a cikin bakunansu, kuma suka ce: "Lalle ne mu, mun kafirta da abinda aka aiko ku da shi. Kuma lalle ne mu haƙiƙa muna a cikin shakkada abin do kuke kiran mu zuwa gare shi, mai sanya kokanto

    [10] Manzanninsu suka ce "Ashe, akwai shakka a cikin (sha'anin) Allah, Mai ƙaga halittar sammai da ƙasa Yana kiran ku domin Ya gafarta muku zunubanku, kuma Ya jinkirta muku zuwa ga ajali ambatacce?" Suka ce: "Ba ku zama ba face mutane misalinmu kuma nufinku ku kange mu daga abin da iyayenmu suka kasance suna bautawa sai ku zo mana da dalili mabayyani

    [11] Manzanninsu suka ce musu, "Ba mu zama ba face mutane misa, linku, kuma amma Allah Yana yin falala a kan wanda Yake so daga bayinsa, kuma ba ya kasancewa a gare mu, mu zo muku da wani dalili face da iznin Allah. Kuma ga Allah sai muminai su dogara

    [12] Kuma mene ne a gare mu, ba za mu dogara ga Allah ba, alhali kuwa haƙiƙa Ya shiryar da mu ga hanyoyinmu? Kuma lalle ne muna yin haƙuri a kan abin da kuka cutar da mu, kuma ga Allah sai masu dogaro su dogara

    [13] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce wa Manzanninsu, "Lalle ne muna fitar da ku daga ƙasarmu, ko kuwa haƙiƙa, kuna komowa acikin addininmu." Sai Ubangijinsu Ya yi wahayi zuwa gare su, "Lalle ne, Muna halakar da azzalumai

    [14] Kuma haƙiƙa, Muna zaunar da ku ga ƙasa a bayansu. Wancan ne abin gargaɗi ga wanda ya ji tsoron matsayiNa, kuma ya ji tsoron ƙyacewaTa

    [15] Kuma suka yi addu'ar alfanu. Kuma kowane kangararre mai tsaurin kai ya taɓe

    [16] Daga bayansa akwai Jahannama, kuma ana shayar da shi daga wani ruwa, surkin jini

    [17] Yana kwankwaɗarsa, kuma ba ya jin sauƙin haɗiyarsa, kuma mutuwa ta je masa daga kowane wuri kuma bai zama mai mutuwa ba, kuma daga bayansa akwai azaba mai kauri

    [18] Misalin waɗanda suka kafirta da Ubangijinsu, ayyukansu sun yi kama da toka wadda iska ta yi tsananin bugawa da ita a cikin yini mai guguwa. Ba su iya amfani daga abin da suka yi tsirfa a kan kome. Wancan ita ce ɓata mai nisa

    [19] Shin, ba ka gani ba cewa lalle ne Allah Ya halicci sammai bakwai da ƙasa da mallakarSa. Idan Ya so zai tafiyar da ku, kuma Ya zo da wata halitta sabuwa

    [20] Kuma wancan bai zama mabuwayi ba ga Allah

    [21] Kuma suka bayyana ga Allah gaba daya, sai masu rauni suka ce wa waɗanda suka kangara, "Lalle ne mu, mun kasance masu bi a gare ku, to, shin, ku masu karewa ga barinmu ne daga azabar Allah daga wani abu?" Suka ce: "Da Allah Ya shiryar da mu, da mun shiryar da ku, daidai ne a kanmu, mun yi raki ko mun yi haƙuri ba mu da wata mafaka

    [22] Kuma Shaiɗan ya ce a lokacin da aka ƙare al'amarin, "Lalle ne Allah Ya yi muku wa'adi, wa'adin gaskiya, kuma na yi muku wa'adi, sa'an nan na saɓa muku. Kuma babu wani dalili a gare ni a kanku face na kira ku, sa'an nan kun karɓa mini. Saboda haka kada ku zarge ni, kuma ku zargi kanku. Ban zama mai amfaninku ba, kuma ba ku zama masu amfanina ba. Lalle na barranta da abin da kuka haɗa ni da shi gabanin wannan (matsayi). Lalle azzalumai suna da azaba mai raɗaɗi

    [23] Kuma aka shigar da waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, a gidajen Aljanna, koramu suna gudana daga ƙarƙashinsu suna madawwama a cikinsu da iznin Ubangijinsu, gaisuwarsu a cikinta "Salam", (watau Aminci)

    [24] Shin, ba ka gani ba, yadda Allah Ya buga wani misali, kalma mai kyau kamar itaciya ce mai kyau, asalinta yana tabbatacce, kuma reshenta yana cikin sama

    [25] Tana bayar da abincinta a kowane lokaci da iznin Ubangijinta! Kuma Allah Yana buga misali ga mutane, mai yiwuwa ne, suna tunawa

    [26] Kuma misalin kalma mummuna kamar itaciya mummuna ce, an tumɓuke ta daga bisa ga ƙasa, ba ta da wata tabbata

    [27] Allah Yana tabbatar da waɗanda suka yi imani da magana tabbatacciya a cikin rayuwar duniya, da cikin Lahira, Kuma Allah Yana ɓatar da azzalumai, kuma Allah Yana aikata abin da Yake so

    [28] Shin ba ka lura ba da waɗanda suka musanya ni'imar Allah da kafirci kuma suka saukar da mutanensu a gidan halaka

    [29] Suna ƙonuwa a wutar jahannama, kuma tir da matabbatarsu

    [30] Kuma suka sanya wa Allah kishiyoyi, domin ɓatarwa daga hanyarSa, Ka ce: "Ku ji daɗi, sa'an nan, lalle ne, makomarku Wutar ce

    [31] Ka ce wa bayiNa waɗanda suka yi imani su tsayar da salla kuma su ciyar daga abin da Muka azurta su, a asirce da bayyane, daga gabanin wani wuni ya zo, babu ciniki a ciki, kuma babu abotaka

    [32] Allah ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya fitar game da shi, daga 'ya'yan itace arziki dominku kuma Ya hore jirgin ruwa domin ya yi gudu a cikin teku da umurninSa, kuma Ya hore muku koguna

    [33] Kuma Ya hore muku rana da wata suna madawwama biyu, kuma Ya hore muku dare da wuni

    [34] Kuma Ya ba ku dukkan abin da kuka roƙe Shi kuma idan kun ƙidaya, ni'imar Allah ba za ku lissafe ta ba. Lalle ne mutum, haƙiƙa, mai yawan zalunci ne, mai yawan kafirci

    [35] Kuma a lokacin da Ibrahim ya ce: "Ya Ubangijina! Ka sanya wannan gari amintacce kuma Ka nisanta ni, ni da ɗiyana daga bauta wa gumaka

    [36] Ya Ubangijina! Lalle ne su, sun ɓatar da masu yawa daga mutane sa'an nan wanda ya bi ni, to, lalle shi, yana daga gare ni, kuma wanda ya saɓa mini, to, lalle ne Kai Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [37] Ya Ubangijinmu! Lalle ne ni, na zaunar da zuriyata ga rafi wanda ba ma'abucin shuka ba, a wurin ¦akinka mai alfarma. Ya Ubangijinmu! Domin su tsayar da salla. Sai Ka sanya zukata daga mutane suna gaggawar begenzuwa gare su, kuma ka azurta su daga 'ya'yan itace, mai yiwuwa ne suna godewa

    [38] Ya Ubangijinmu! Lalle ne Kai Kana sanin abin da muke ɓoyewa, da abin da muke bayyanawa. Kuma babu abin da yake ɓoyewa ga A1lah, daga wani abu a cikin ƙasa, kuma babu a cikin sama

    [39] Godiya ta tabbata ga Allah wanda Yake Ya ba ni ina a cikin tsufa Isma'ila da Is'haƙa. Lalle ne Ubangijina, haƙiƙa, Mai jin addu'a ne

    [40] Ya Ubangijina! Ka sanya ni mai tsayar da salla. Kuma daga zuriyyata. Ya Ubangijinmu! Kuma Ka karɓi addu'ata

    [41] Ya Ubangijinmu! Ka yi gafara gare ni, kuma ga mahaifana, kuma da muminai, a ranar da hisabi yake tsayawa

    [42] Kuma kada ka yi zaton Allah Mai shagala ne daga abin da azzalumai suke aikatawa. Abin sani kawai, Yana jinkirta musu ne zuwa ga wani wuni, wanda idanuwa suke fita turu- turu a cikinsa

    [43] Suna masu gaggawa, masu ɗaukaka kawunansu zuwa sama ƙiftawar ganinsu ba ta komawa gare su. Kuma zukatansu wofintattu

    [44] Kuma ka yi gargaɗi ga mutane ga ranar da azaba take je musu, sai waɗanda suka yi zalunci su ce: "Ya Ubangijinmu! Ka yi mana jinkiri zuwa ga wani ajali makusanci, mu karɓa wa kiranKa, kuma mu bi Manzanni."(Allah Ya ce musu) "Ashe, ba ku kasance kun yi rantsuwa ba daga gabani, cewa ba ku da wata gushewa

    [45] Kuma kuka zauna a cikin gidajen waɗanda suka zalunci kansu, kuma ya bayyana a gare ku yadda Muka aikata game da su, kuma Muka buga muku misalai

    [46] Kuma lalle sun yi makirci irin makircinSu kuma a wurin Allah makircinsu, yake, kuma lalle ne makircinsu ya kasance, haƙiƙa, duwatsu suna gushewa saboda shi

    [47] Saboda haka, kada ka ƙarfafa zaton Allah Mai saɓa wa'adinSa ne ga ManzanninSa. Lalle ne Allah ne Mabuwayi, Ma'abucin azabar ramuwa

    [48] A ranar da ake musanya ƙasa ba ƙasar nan ba, da sammai kuma su bayyana ga Allah Makaɗaici, Mai tanƙwasawa

    [49] Kuma kana ganin masu laifi, a ranar nan, suna waɗanda aka yi wa ciri daidai a cikin maruruwa

    [50] Rigunansu daga farar wuta ne, kuma wuta ta rufe fuskokinsu

    [51] Domin Allah Ya saka wa kowane rai da abin da ya tsuwurwurta. Lalle ne, Allah Mai gaggawar hisabi ne

    [52] Wannan iyarwa ce ga mutane, kuma domin a yi musu gargaɗi da shi, kuma domin su sani cewa, abin sani kawai, shi ne abin bautawa guda. Kuma domin masu hankali su riƙa tunawa

    Hinjir

    Surah 15

    [1] L.R. Waɗancan ayoyin littafi ne da abin karantawa mai bayyanawa

    [2] Da yawa waɗanda suka kafirta suke gurin da dai sun kasance Musulmi

    [3] Ka bar su su ci kuma su ji dadi, kuma guri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu za su sani

    [4] Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba face tana da littafi sananne

    [5] Wata al'umma ba ta gabatar ajalinta, kuma ba za su jinkirta ba

    [6] Suka ce: "Ya kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ani) a kansa! Lalle ne kai, haƙiƙa, mahaukaci ne

    [7] Domin me ba za ka zo mana da mala'iku ba idan ka kasance daga masu gaskiya

    [8] Ba Mu sassaukar da mala'iku face da gaskiya, ba za su kasance, a wannan lokacin, waɗanda ake yi wa jinkiri ba

    [9] Lalle Mu ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ani), kuma lal1e Mu, haƙiƙa, Masu kiyayewane gare shi

    [10] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyoyin farko, gabaninka

    [11] Kuma wani Manzo ba ya zuwa gare su face sun kasance suna masu, izgili a gare shi

    [12] Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukatan masu laifi

    [13] Ba su yin imani da shi, kuma haƙiƙa, hanyar mutanen farko ta shige

    [14] Kuma da Mun buɗe wata ƙofa daga sama a kansu har suka wuni a ciki suna takawa

    [15] Lalle ne da sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idanuwanmu ne. A'a, mu mutane ne waɗanda aka sihirce

    [16] Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawata ta ga masu kallo

    [17] Kuma Muka kiyaye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jifa

    [18] Face wanda ya saci saurare sai wutar yula bayyananniya ta bi shi

    [19] Kuma ƙasa Mun mike ta kuma Mun jefa duwatsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunawa da sikeli

    [20] Kuma Muka sanya muku, a cikinta, abubuwan rayuwa da wanda ba ku zama masu ciyarwa gare shi ba

    [21] Kuma babu wani abu face a wurinMu, akwai taskokinsa kuma ba Mu saukar da shi ba face kan gwargwado sananne

    [22] Kuma Muka aika iskoki masu barbarar juna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shayar da ku shi, kuma ba ku zama masu taskacewa a gare shi ba

    [23] Kuma lalle ne Mu Muke rayarwa, kuma Muke kashewa kuma Mu ne magada

    [24] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun san masu gabata daga cikinku, kuma Mun san masu jinkiri

    [25] Kuma lalle ne Ubangijinka Shi ne Yake tara su, lalle Shi ne Mai hikima, Masani

    [26] Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar laka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja

    [27] Kuma Aljani Mun halicce shi daga gabani, daga wutar iskar zafi

    [28] Kuma a lokacin da Ubangijinka ya ce wa mala'iku: "Lalle Ni mai halittar wani jiki ne daga ƙeƙasasshen yumɓu wanda ya canja

    [29] To idan Na daidaita shi kuma Na hura daga RuhiNa a cikinsa, to, ku faɗi a gare shi, kuna masu yin sujada

    [30] Sai mala'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya

    [31] Face Iblis, ya ƙi kasancewa daga masu yin sujadar

    [32] Ya ce: "Ya Iblis mene ne a gare ka, ba ka kasance tare da masu yin sujuda ba

    [33] Ya ce: "Ban kasance ina yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga busasshen yumɓun laka wadda ta canja

    [34] Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, domin lalle kai abin jifa ne

    [35] Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa ranar sakamako

    [36] Ya ce: "Ya Ubangjina! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa ranar da ake tashin su

    [37] Ya ce: "To, lalle ne kana daga waɗanda ake yi wa jinkiri

    [38] Zuwa ga Yinin Lokacin nan sananne

    [39] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ina rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙiƙa ina ƙawata musu (rayuwa) a cikin ƙasa kuma haƙiƙa ina ɓatar da su gaba ɗaya

    [40] Face bayinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake

    [41] Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici

    [42] Lalle ne bayiNa, ba ka da iko a kansu, face wanda ya bi ka daga ɓatattu

    [43] Kuma lalle Jahannama ce haƙiƙa, ma'a1kawartarsu gaba ɗaya

    [44] Tana da ƙofofi bakwai, ga kowace ƙofa akwai wani juz'i daga gare su rababbe

    [45] Lalle masu taƙawa suna a cikin gidajen Aljanna mai idandunan ruwa

    [46] Ku shige ta da aminci, kuna amintattu

    [47] Kuma Muka ɗebe abinda ke a cikin zukatansu na daga ƙullin zuci, suka zama 'yan'uwa a kan gadaje, suna masu fuskantar juna

    [48] Wata wahala ba za ta shafe su ba a cikinta kuma ba su zama masu fita daga, cikinta ba

    [49] Ka bai wa bayiNa labari cewa lalle ne Ni, Mai gafarane, Mai jin ƙai

    [50] Kuma azabaTa ita ce azaba mai raɗaɗi

    [51] Kuma ka ba su labarin baƙin Ibrahim

    [52] A lokacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mu, daga gare ku, masu firgita ne

    [53] Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mu, muna yi makabushara game da wani yaro masani

    [54] Ya ce: "Shin kun ba ni bushara ne a kan tsufa ya shafe ni? To, da me kuke ba ni bushara

    [55] Suka ce: "Muna yi maka bushara da gaskiya ne, saboda haka, kada da kasance daga masu yanke tsammani

    [56] Ya ce: "Kuma wane ne yake yanke tsammani daga rahamar Ubangijinsa, face ɓatattu

    [57] Ya ce: "To, mene ne babban al'amarinku? Ya ku manzanni

    [58] Suka ce: "Lalle ne mu, an aika mu zuwa ga wasu mutane masu laifi

    [59] Face mutanen Luɗu, lalle ne mu, haƙiƙa, masu tsirar dasu ne gaba ɗaya

    [60] Face matarsa mun ƙaddara cewa lalle ne ita, haƙiƙa, tana daga masu halaka

    [61] To, a lokacin da mazannin suka je wa mutanen Luɗu

    [62] Ya ce: "Lalle ne ku mutane ne waɗanda ba a sani ba

    [63] Suka ce: "A'a, mun zo maka saboda abin da suka kasance suna shakka a cikinsa

    [64] Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mu, haƙiƙa, masu gaskiya ne

    [65] Sai ka yi tafiya da iyalinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bayansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku

    [66] Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cewa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankewa ne a lokacin da suke masu shiga asuba

    [67] Kuma mutanen alƙaryar suka je suna masu bushara

    [68] Ya ce: "Lalle ne waɗannan baƙina ne, saboda haka kada ku kunyata ni

    [69] Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki

    [70] Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga talikai ba

    [71] Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yana idan kun kasance masu aikatawa ne

    [72] Rantsuwa da rayuwarka! Lalle ne su a cikin mayensu suna ta ɗimuwa

    [73] Sa'an nan tsawa ta kama su, suna masu shiga lokacin hudowar rana

    [74] Sa'an nan Muka sanya samanta ya koma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwatsu na lakar wuta a kansu

    [75] Lalle ne a cikin wancan akwai ayoyi ga masu tsokaci da hankali

    [76] Kuma lalle ne ita, haƙiƙa suna a gefen wata hanya tabbatacciya

    [77] Lalle ne a cikin wancan akwai aya ga masu imani

    [78] Kuma lalle ne ma'abuta Al'aika sun kasance, haƙiƙa, masu zalunci

    [79] Sai Muka yi azabar ramuwa a gare su, kuma lalle su biyun, haƙiƙa, suna a gefen wani tafarki mabayyani

    [80] Kuma lalle ne haƙiƙa ma'abuta Hijiri sun ƙaryata Manzanni

    [81] Kuma Kuka kai musu ayoyinMu, sai suka kasance masu bijirewa daga gare su

    [82] Kuma sun kasance suna sassaƙa gidaje daga duwatsu, alhali suna amintattu

    [83] Sai tsawa ta kama su suna masu shiga asuba

    [84] Sa'an nan abin da suka kasance suna tsirfantawa bai wadatar ga barinsu ba

    [85] Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakaninsu ba face da gaskiya. Kuma lalle ne Sa'a (Ranar Alƙiyama) haƙiƙa mai zuwa ce. Sabodahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau

    [86] Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani

    [87] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun ba ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ani mai girma

    [88] Kada lalle kaƙiƙa idanunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su daɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikafikanka ga masu imani

    [89] Kuma ka ce: "Lalle ni ni ne mai gargaɗi bayyananne

    [90] Kamar yadda Muka saukar a kan masu yin rantsuwa

    [91] Waɗanda suka sanya Alƙur'ani tatsuniyoyi

    [92] To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙiƙa, Muna tambayarsugaba ɗaya

    [93] Daga abin da suka kasance suna aikatawa

    [94] Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki

    [95] Lalle ne Mu Mun isar maka daga masu izgili

    [96] Waɗanda suke sanyawar wani abin bautawa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu za su sani

    [97] Kuma lalle ne haƙiƙa Muna sanin cewa lalle kai, ƙirjinka yana yin ƙunci game da abin da suke faɗa (na izgili)

    [98] Saboda haka ka yi tasbihi game da gode wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga masu sujada

    [99] Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka

    Kudan Zuma

    Surah 16

    [1] Al'amarin Allah ya zo, saboda haka kada ku nemi hanzartawarsa. Tsarkin Allah ya tabbata, kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke yi na shirka

    [2] Yana sassaukar da mala'iku da Ruhi daga umurninSaa kan wanda Yake so daga bayinSa, cewa ku yi gargaɗi cewa: Lalle ne shi, babu abin bautawa face Ni, saboda haka ku bi Ni da taƙawa

    [3] Ya halicci sammai da ƙasa da gaskiya. Ya ɗaukaka daga abin da suke yi na shirka

    [4] Ya halicci mutum daga maniyyi, sai ga shi yana mai husuma bayyananniya

    [5] Da dabbobin ni'ima, Ya halicce su dominku. A cikinsu akwai abin yin ɗumi da waɗansu amfanoni, kuma daga gare su kuke ci

    [6] Kuma kuna da kyau a cikinsu a lokacin da suke komowa daga kiwo da maraice da lokacin da suke sakuwa

    [7] Kuma suna ɗaukar kayanku masu nauyi zuwa ga wani gari, ba ku kasance masu isa gare shi ba, face da tsananin wahalar rayuka, Lalle ne Ubangijinka ne, haƙiƙa, Mai tausayi, Maijin ƙai

    [8] Kuma da dawaki da alfadarai da jakuna, domin ku hau su, kuma da ƙawa. Kuma Yana halitta abin da ba ku sani ba

    [9] Kuma ga Allah madaidaiciyar hanya take kuma daga gare ta akwai mai karkacewa. Kuma da Ya so, da Ya shiryar da ku gaba ɗaya

    [10] Shi ne Wanda Ya saukar da ruwa daga sama dominku, daga gare shi akwai abin sha, kuma daga gare shi itace yake, a cikinsa kuke yin kiwo

    [11] Yana tsirar da shuka game da shi, dominku zaituni da dabinai da inabai, kuma daga dukan 'ya'yan itace. Lalle ne a cikin wancan haƙiƙa, akwai aya ga mutane waɗanda suke yin tunani

    [12] Kuma Ya hore muku dare da wuni da rana da wata kuma taurari horarru ne da umurninSa. Lalle ne a cikin wancan, haƙiƙa, akwai ayoyi ga mutane waɗanda suke hankalta

    [13] Kuma abin da Ya halitta muku a cikin ƙasa, yana mai saɓanin launukansa. Lalle ne a cikin wancan, haƙiƙa, akwai aya ga mutane waɗanda suke tunawa

    [14] Kuma Shi ne Ya hore teku domin ku ci wani nama sabo daga gare shi, kuma kuna fitarwa, daga gare shi, ƙawa wadda kuke yin ado da ita. Kuma kuna ganin jirage suna yankan ruwa a cikinsa kuma domin ku yi neman (fatauci) daga falalarSa. Kuma mai yiwuwa ne kuna godewa

    [15] Kuma Ya jefa, a cikin ƙasa, tabbatattun duwatsu domin kada ta karkata da ku, da koguna da hanyoyi, ɗammaninku kuna shiryuwa

    [16] Kuma da waɗansu alamomi, kuma da taurari suna masu neman shiryuwa (ga tafiyarsu ta fatauci)

    [17] Shin, wanda Yake yin halitta yana yin kama da wanda ba ya yin halitta? Shin fa, ba ku tunawa

    [18] Kuma idan kun ƙidaya ni'imar Allah, ba ku iya lissafa ta. Lalle ne Allah, haƙiƙa, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [19] Kuma Allah Yana sanin abin da kuke asirtawa da abin da kuke bayyanawa

    [20] Kuma waɗanda suke kira, baicin Allah, ba su halicci kome ba, kuma su ne ake halittawa

    [21] Matattu ne, ba su da rai, kuma ba su san a wane lokaci ake tayar da su ba

    [22] Abin bautawarku, abin bautawa ne guda, to, waɗanda ba su yin imani da Lahira, zukatansu masu musu ne, kuma su makangara ne

    [23] Haƙiƙa, lalle ne, Allah Yana sanin abin da suke asirtawa da abin da suke bayyanawa. Lalle ne Shi, ba Ya Son masu girman kai

    [24] Idan aka ce musu: "Mene ne Ubangijinku Ya saukar?" Sai su ce: "Tatsuniyoyin mutanen farko

    [25] Domin su ɗauki zunubansu cikakku a Ranar ¡iyama, kuma daga zunuban waɗanda suke ɓatarwa ba da wani ilmi ba. To, abin da suke ɗauka na zunubi ya munana

    [26] Lalle ne waɗanda suke a gabaninsu sun yi makirci, sai Allah Ya je wa gininsu daga harsashensa, sai rufi ya faɗa a kansu daga bisansu, kuma azaba ta je musu daga inda ba su sani ba

    [27] Sa'an nan a Ranar ¡iyama (Allah) Yana kunyata su, kuma Yana cewa: "Ina abokan tarayyaTa, waɗanda kuka kasance kuna gaba a cikin ɗaukaka sha'aninsu?" Waɗanda aka bai wa ilmi suka ce: "Lalle ne wulakanci a yau da cuta sun tabbata a kan kafirai

    [28] Waɗanda malaiku suke karɓar rayukansu suna masu zaluntar kansu. Sai suka jefa neman sulhu (suka ce) "Ba mu kasance muna aikata wani mummunan aiki ba." Kayya! Lalle Allah ne Masani ga abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [29] Sai ku shiga ƙofofin Jahannama, kuna madawwama a cikinta. Sa'an nan tir da mazaunin masu girman kai

    [30] Kuma aka ce wa waɗanda suka yi taƙawa, "Mene ne Ubangijinku Ya saukar?" Suka ce, "Alheri Ya saukar, ga waɗanda suka kyautata a cikin wannan duniya akwai wani abu mai kyau, kuma haƙiƙa, Lahira ce mafi alheri." Kuma haƙiƙa, madalla da gidan masu taƙawa

    [31] Gidajen Aljannar zama suna shigarsu, ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, suna da abin da suke so a cikinsu. Kamar haka Allah ke saka wa masu taƙawa

    [32] Waɗanda mala'iku suke karɓar rayukansu suna masu jin daɗin rai, mala'ikun suna cewa. "Aminci ya tabbata a kanku. Ku shiga Aljanna saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [33] Shin suna jiran wani abu? Face mala'iku su je musu ko kuwa umurnin Ubangijinka. Kamar wancan ne waɗanda suke a gabaninsu, suka aikata. Kuma Allah bai zalunce su ba, kuma amma kansu suka kasance suna zalunta

    [34] Sai munanan abubuwan da suka aikata ya same su, kuma abin da suka kasance suna yi na izgili ya wajaba a kansu

    [35] Kuma waɗanda suka yi shirki suka ce: "Da Allah Ya so, da bamu bauta wa kome ba, baicinSa, mu ko ubannimmu kuma da ba mu haramta kome ba, baicin abin da Ya haramta." Kamar wancan ne waɗanda suke a gabaninsu suka aikata. To, shin, akwai wani abu a kan Manzanni, face iyarwa bayyananniya

    [36] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun aika a cikin kowace al'umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nisanci ¦agutu." To, daga gare su akwai wanda Allah Ya shiryar, kuma daga cikinsu akwai wanda ɓata ta wajaba a kansa. Sai ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa'an nan ku duba yadda aƙibar masu ƙaryatawa ta kasance

    [37] Idan ka yi kwaɗayi a kan shiryuwarsu, to, lalle ne, Allah ba Ya shiryar da wanda yake ɓatarwa, kuma ba su da waɗansu mataimaka

    [38] Kuma suka rantse da Allah iyakar rantsuwarsu (cewa) Allah ba ya tayar da wanda yake mutuwa! Na'am, Yana tayarwa. Wa'adi ne (Allah) Ya yi a kanSa tabbatacce, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [39] Domin Ya bayyana musu abin da suke saɓa wa juna a cikinsa, kuma domin waɗanda suka kafirta su sani cewa lalle su ne suka kasance maƙaryata

    [40] Abin sani kawai, MaganarMu ga wani abu idan Mun nufe shi, Mu ce masa, "Ka kasance; sai yana kasancewa

    [41] Kuma waɗanda suka yi hijira a cikin sha'anin Allah daga bayan an zalunce su, haƙiƙa Muna zaunar da su a cikin duniya da alheri kuma lalle ladar Lahira ce mafi girma, da sun kasance suna sani

    [42] Waɗanda suka yi haƙuri, kuma ga Ubangijinsu suke dogara

    [43] Kuma ba Mu aika daga gabaninka ba, face waɗansu mazaje Muna yin wahayi zuwa gare su. Sai ku tambayi mutanen Ambato idan kun kasance ba ku sani ba

    [44] Da hujjoji bayyanannu da littattafai kuma Mun saukar da Ambato zuwa gare ka, domin ka bayyana wa mutane abin da aka sassaukar zuwa gare su, kuma don ɗammaninsu su yi tunani

    [45] Shin fa, waɗanda suka yi makircin munanan ayyuka sun amince da Allah, ba zai shafe ƙasa da su ba ko kuwa azaba ba za ta je musu daga inda ba su sani ba

    [46] Ko kuwa Ya kama su a cikin jujjuyawarsu? Saboda haka ba su zama masu buwaya ba

    [47] Ko kuwa Ya kama su a kan naƙasa? To, lalle ne Ubangijinka haƙiƙa Mai tausayi ne, Mai jin ƙai

    [48] Shin, ba su Iura ba da abin da Allah Ya halitta ko mene ne inuwoyinsu suna karkata daga dama da wajajen hagu, suna masu sujada ga Allah, alhali suna masu ƙasƙantar da kai

    [49] Kuma ga Allah, abin da yake a cikin sammai da ƙasa na dabba da mala'iku, suke yin sujada, kuma ba su kangara

    [50] Suna tsoron Ubangijinsu daga bisansu, kuma suna aikata abin da ake umuruin su

    [51] Kuma Allah Ya ce: "Kada ku riƙi abubuwan bautawa biyu. Abin sani kawai, wanda ake bautawa guda ne, sa'an nan sai kuji tsoroNa, Ni kawai

    [52] Kuma Yana da abin da yake a cikin sammai da ƙasa, kuma Yana da addini wanda yake dawwamamme. Shin fa, wanin Allah kuke bi da taƙawa

    [53] Kuma abin da yake a gare ku na ni'ima, to, daga Allah ne. Sa'an nan kuma idan cuta ta shafeku, to, zuwa gare Shi kuke hargowa

    [54] sa'an nan idan Ya kuranye cutar daga gare ku, sai ga wani ɓangare daga gare ku game da Ubangijinsu suna shirki

    [55] Domin su kafirta da abin da Muka ba su. To, ku ji daɗi, sa'an nan da sannu za ku sani

    [56] Kuma suna sanya rabo ga abin da ba su sani ba daga abin da Muka azurta su. Ranstuwa da Allah! Lalle ne za a tambaye ku daga abin da kuka kasance kuna ƙirƙirawa

    [57] Kuma suna danganta 'ya'ya mata ga Allah. Tsarkinsa ya tabbata! Kuma su ne da abin da suke sha'awa

    [58] Kuma idan aka yi wa ɗayansu bushara da mace sai fuskarsa ta wuni baƙa ƙirin, alhali kuwa yana mai cike da baƙin ciki

    [59] Yana ɓoyewa daga mutane domin munin abin da aka yimasa bushara da shi. Shin, zai riƙe shi a kan wulakanci ko zai turbuɗe shi a cikin turɓaya To, abin da suke hukuntawa ya munana

    [60] Ga waɗanda ba su yi imani da Lahira ba akwai sifar cuta kuma ga Allah akwai sifa mafi ɗaukaka. Kuma shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [61] Kuma da Allah Yana kama mutane da zaluncinsu, da bai bar wata dabba ba a kan ƙasa. Kuma amma Yana jinkirta musu zuwa ga ajali ambatacce. Sa'an nan idan ajalinsu ya zo, ba za a yi musu jinkiri ba ko da sa'a guda, kuma ba za su gabata ba

    [62] Kuma suna sanya wa Allah abin da suke ƙi, kuma harsunansu na siffanta ƙarya cewa lalle ne suna da abubuwa masu kyau. Babu shakka lalle ne suna da wuta, kuma lalle su, waɗanda ake ƙyalewa ne (a cikinta)

    [63] Rantsuwar Allah! Lalle ne haƙiƙa Mun aika zuwa ga al'ummomi daga gabaninka, sai Shaiɗan ya ƙawace musu ayyukansu, saboda haka shi ne majiɓincinsu, a yau, kuma suna da azaba mai raɗaɗi

    [64] Lalle ba Mu saukar da Littafi ba a kanka, face domin ka bayyana musu abin da suka saɓa wa juna a cikinsa, kuma domin shiriya da rahama ga mutane waɗanda suke yin imani

    [65] Kuma Allah Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya rayar da ƙasa da shi a bayan mutuwarta. Lalle ne a cikin wannan haƙiƙa akwai aya ga mutane waɗanda suke saurare

    [66] Kuma lalle ne, kuna da abin lura a cikin dabbobin ni'ima; Muna shayar da ku daga abin da yake a cikin cikunansu, daga tsakanin tukar tumbi da jini nono tsantsan mai sauƙin haɗiya ga masu sha

    [67] Kuma daga 'ya'yan itacen dabino da inabi. Kuna samudaga gare shi, abin maye da abinci mai kyau. Lalle a cikin wannan, haƙiƙa, akwai aya ga mutane waɗanda suke hankalta

    [68] Kuma Ubangjinka Ya yi wahayi zuwa ga ƙudan zuma cewa: "Ki riƙi gidaje daga duwatsu, kuma daga itace, kuma daga abin da suke ginawa

    [69] Sa'an nan ki ci daga dukan 'ya'yan itace, saboda haka ki shiga hanyoyin Ubangijinka, suna horarru." Wani abin sha yana fita daga cikunanta, mai saɓawar launukansa a cikinsa akwai wata warkewa ga mutane. Lalle ne, a cikin wannan, haƙiƙa, akwaiayoyi ga mutane waɗanda suke yin tunani

    [70] Kuma Allah ne Ya halicce ku, sa'an nan Yana karɓar rayukanku, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙncin rayuwa, domin kada ya san kome a bayan da ya zama mai ilmi. Lalle Allah ne Masani Mai ikon yi

    [71] Kuma Allah Ya fifita sashenku a kan sashe a arziki. Sa'an nan waɗanda aka fifita ba su zama masu mayar da arzikinsu a kan abin da hannayensu na dama suka mallaka ba, har su zama daidai a cikinsa. Shin fa, da ni'imar Allah suke musu

    [72] Kuma Allah Ya sanya muku matan aure daga kawunanku, kuma Ya sanya muku daga matan aurenku ɗiya da jikoki, kuma Ya arzuta ku daga abubuwa masu daɗi. Shin fa, da ƙarya suke yin imani, kuma da ni'imar Allah su, suke kafirta

    [73] Kuma suna bauta wa, baicin Allah, abin da yake ba ya mallakar wani arziki dominsu, daga sammai da ƙasa game da kome, kuma ba su iyawa (ga aikata kome)

    [74] Sa'an nan kada ku bayar da waɗansu misalai ga Allah. Lalle ne Allah Yana sani, kuma ku, ba ku sani ba

    [75] Allah Ya buga wani misali da wani bawa wanda ba ya iya samun iko a kan yin kome, da (wani bawa) wanda Muka azurta shi daga gare Mu da arziki mai kyau. Sa'an nan shi yana ciyarwa daga arzikin, a asirce da bayyane. Shin suna daidaita? Godiya ta tabbata ga Allah. A'a mafi yawansu ba su sani ba

    [76] Kuma Allah Ya buga wani misali, maza biyu, ɗayansu bebe ne, ba ya iya samun ikon yin kome, kuma shi nauyi ne a kan mai mallakarsa, inda duk ya fuskantar da shi, ba ya zuwa da wani alheri. Shin, yana daidaita, shi da (namiji na biyu) wanda yake umurni da a yi adalci kuma yana a kan tafarki madaidaici

    [77] Kuma ga Allah gaibin sammai da ƙasa yake, kuma al'amarin Sa'a bai zama ba face kamar walƙawar gani, ko kuwa shi ne mafi kusa! Lalle Allah a kan dukan kome Mai ikon yi ne

    [78] Kuma Allah ne Ya fitar da ku daga cikunan iyayenku, ba da kuna sanin kome ba, kuma Ya sanya muku ji da gannai da zukata, tsammaninku za ku gode

    [79] Shin ba su ga tsuntsaye ba suna horarru cikin sararin sama babu abin da yake riƙe su face Allah? Lalle ne a cikin wancan haƙiƙa, akwai ayoyi ga mutane waɗanda suke yin imani

    [80] Kuma Allah ne Ya sanya muku daga gidajenku wurin natsuwa, kuma Ya sanya muku daga fatun dabbobin ni'ima wasu gidaje kuna ɗaukar su da sauƙi a ranar tafiyarku da ranar zamanku, kuma daga sufinsu da gashinsu da gezarsu (Allah) Ya sanya muku kayan ɗaki da na jin daɗi zuwa ga wani loƙaci

    [81] Kuma Allah ne Ya sanya muku inuwa daga abin da Ya halitta, kuma Ya sanya muku ɗakuna daga duwatsu, kuma Ya sanya muku waɗansu riguna suna tsare muku zafi, da waɗansu riguna suna tsare muku makaminku. Kamar wancan ne (Allah) Yake cika ni'imarSa a kanku, tsammanin ku, kuna sallamawa

    [82] To, idan sun juya, to, abin da ya wajaba a kanka, shi ne iyarwa kawai, bayyananniya

    [83] Suna sanin ni'imar Allah, sa'an nan kuma suna musunta, kuma mafi yawansu kafirai ne

    [84] Kuma a ranar da Muke tayar da mai shaida daga kowace al'umma, sa'an nan kuma ba za a yi izni ba ga waɗanda suka kafirta, kuma ba su zama ana neman komawarsu ba

    [85] Kuma idan waɗanda suka yi zalunci suka ga azaba, sa'an nan ba za a saukake ta daga gare su ba, kuma ba su zama ana yi musu jinkiri ba

    [86] Kuma idan waɗanda suka yi shirka suka ga abubuwan shirkarsu sai su ce: "Ya Ubangijinmu! Waɗannan ne abubuwanshirkarmu waɗanda muka kasance muna kira baicinKa". Sai su jefamagana zuwa gare su, "Lalle ne ku, haƙiƙa, maƙaryata ne

    [87] Kuma su shiga neman sulhu zuwa ga Allah a ranar nan, kuma abin da suka kasance suna ƙirƙirawa ya ɓace daga gare su

    [88] Waɗanda suka kafirta kuma suka kange daga hanyar, Allah, Mun ƙara musu wata azaba bisa ga azabar, saboda abin da suka kasance suna yi na fasadi

    [89] Kuma a ranar da Muke tayar da shaidu a cikin kowace al'umma a kansu daga kawunansu, kuma Muka zo da kai kana mai bayar da shaida a kan waɗannan, kuma Mun saussaukar da Littali a kanka domin yin bayani ga dukkan kome da shiriya da rahama da bushara ga masu miƙa wuya (Musulmi)

    [90] Lalle Allah na yin umurni da adalci da kyautatawa, da bai wa ma'abucin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka ƙi da rarrabe jama'a. Yana yi muku gargaɗi, ɗammanin ku, kuna tunawa

    [91] Kuma ku cika da alkawarin Allah idan kun yi alkawari, kuma kada ku warware rantsuwoyinku a bayan ƙarfafa su, alhali kuma haƙiƙa kun sanya Allah Mai lamuncewa a kanku. Kuma lalle Allah ne Yake sanin abin da kuke aikatawa

    [92] Kuma kada ku kasance kamar wadda ta warware zarenta a bayan tukka, ya zama warwararku, kuna riƙon rantsuwoyinku domin yaudara a tsakaninku, domin kasancewar wata al'umma tafi riba daga wata al'umma! Abin sani kawai Allah Yana jarrabar ku da shi, kuma lalle ne yana bayyana muku a Ranar ¡iyama, abin da kuka kasance, a cikinsa, kuna saɓa wajuna

    [93] Kuma da Allah Ya so, haƙi ƙa, da Ya sanya ku al'umma guda, kuma Yana ɓatar da wanda Ya so. kuma Yana shiryar da wanda Ya so. Lalle ne ana tambayarku abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [94] Kada ku riƙi rantsuwoyinku domin yaudara a tsakaninku, har ƙafa ta yi sulɓi a bayan tabbatarta, kuma ku ɗanɗani azaba saboda abin da kuka kange daga hanyar Allah. Kuma kuna da wata azaba mai girma

    [95] Kada ku sayi 'yan kuɗi kaɗan da alkawarin Allah. Lalle ne abin da yake a wurin Allah shi ne mafi alheri a gare ku, idan kun kasance kuna sani

    [96] Abin da yake a wurinku yana ƙarewa, kuma abin da yake a wurin Allah ne mai wanzuwa. Kuma lalle ne, Muna saka wa waɗanda suka yi haƙuri da ladarsu da mafi kyawun abin da suka kasance suna aikatawa

    [97] Wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji ko kuwa mace, alhali yana mumini, to, haƙiƙa Muna rayar da shi, rayuwa mai daɗi. Kuma haƙiƙa Muna saka musu ladarsu da mafi kyawun abin da suka kasance suna aikatawa

    [98] Sa'an nan idan ka karanta Alƙur'ani, sai ka nemi tsari ga Allah daga shaiɗan jefaffe

    [99] Lalle ne shi, ba shi da wani ƙarfi a kan waɗanda suka yi imani, kuma suna dogara ga Ubangijinsu

    [100] Abin sani kawai ƙarfinsa yana a kan waɗanda suke jiɓintar sa, kuma waɗanda suke su, game da shi, masu shirki ne

    [101] Kuma idan Muka musanya wata aya a matsayin wata aya, kuma Allah ne Mafi sani ga abin da Yake saukarwa sai su ce: "Abin sani kawai, kai, aƙirƙiri ne." A'a, mafi yawansu ba swa sani

    [102] Ka ce: "Ruhul ¡udusi ne ya sassaukar da shi, daga Ubangijinka da gaskiya, domin ya tabbatar da waɗanda suka yi imani, kuma (domin) shiriya da bushara ga Musulmi

    [103] Kuma lalle ne, haƙiƙa Muna sanin (cewa) lalle ne su, suna cewa, "Abin sani kawai wani mutum ne yake karantar da shi." Harshen wanda suke karkatai da maganar zuwa gare shi, Ba'ajame ne, kuma wannan (Alƙur'ani) harshe ne Balarabe bayyananne

    [104] Lalle ne waɗanda ba su yin imani da ayoyin Allah, Allahba zai shiryar da su ba, kuma suna da azaba mai raɗaɗi

    [105] Abin sani kawai waɗanda ba su yin imani da ayoyin Allah, su ne suke ƙirƙira ƙarya. Kuma waɗannan su ne maƙaryata

    [106] Wanda ya kafirta da Allah daga bayan imaninsa, face wanda aka tilasta alhali kuwa zuciyarsa tana natse da imani kuma wanda ya yi farin ciki da kafirci, to, akwai fushi a kansa daga Allah, kuma suna da wata azaba mai girma

    [107] Waɗancan ne kafirai domin sun fifita son duniya a kan Lahira, kuma lalle ne Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai

    [108] Waɗancan ne waɗanda Allah Ya bice hasken zukatansu da jinsu da gannansu. Kuma waɗancan su ne gafalallu

    [109] Babu shakka lalle ne a Lahira su ne masu hasara

    [110] Sa'an nan kuma lalle ne Ubangijinka ga waɗanda suka yi hijira daga bayan an fitine su, sa'an nan kuma suka yi jihadi, kuma suka yi haƙuri, lalle ne Ubangijinka, daga bayanta haƙiƙa Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [111] A ranar da kowane rai zai je yana jayayyar tunkuɗewa daga kansa, kuma a cika wa kowane rai (sakamakon) abin da ya aikata, kuma su ba za a zalunce su ba

    [112] Kuma Allah Ya buga misali, wata alƙarya ta kasance amintacciya, natsattsiya, arzikinta yana je mata a wadace daga kowane wuri sai ta kafirta da ni'imomin Allah, saboda haka Allah ya ɗanɗana mata tufafin yunwa da tsoro, saboda abin da suka kasance suna sana'antawa

    [113] Kuma lalle ne haƙiƙa wani Manzo daga gare su, ya jemusu, sai suka ƙaryata shi, saboda haka azaba ta kama su, alhali kuwa su ne masu zalunci

    [114] Sa'an nan ku ci daga abin da Allah Ya azurta ku da shi, halas, kuma mai daɗi, kuma ku gode wa ni'imar Allah idan kun kasance shi kuke bautawa

    [115] Abin sani kawai (Allah) Ya haramta muku mussai da jini da naman alade da abin da aka ambaci sunan wanin Allah game da shi. Sa'an nan wanda aka tilastaa kan jama'a kuma baicin mai zalunci, to, lalle Allah ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [116] Kuma kada ku ce, domin abin da harsunanku suke siffantawa da ƙarya, "Wannan halas ne, kuma wannan haramun ne." Domin ku ƙirƙira ƙarya ga Allah. Lalle ne, waɗanda suke ƙirƙira ƙarya ga Allah ba za su ci nasara ba

    [117] Jin daɗi ne kaɗan. Kuma suna da wata azaba mai raɗaɗi

    [118] Kuma kan waɗanda suka tuba (Yahudu) Mun haramta abin da Muka bayar da labari a gare ka daga gabani, kuma ba Mu zalunce su ba, amma sun kasance kansu suke zalunta

    [119] Sa'an nan kuma lalle ne Ubangijinka ga waɗanda suka aikata mummunan aiki da jahilci, sa'an nan suka tuba daga bayan wancan, kuma suka gyara, lalle ne Ubangijinka, daga bayanta haƙiƙa Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [120] Lalle ne Ibrahim ya kasance shugaba, mai ƙasƙantar da kai ga Allah, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga masu shirki ba

    [121] Mai godiya ga ni'imominSa (Allah), Ya zaɓe shi, kuma Ya shiryar da shi zuwa ga tafarki madaidaici

    [122] Kuma Muka ba shi alheri a cikin duniya, Kuma lalle shi, a Lahira, yana daga salihai

    [123] Sa'an nan kuma Muka yi wahayi zuwa gare ka (cewa), "Ka bi aƙidar Ibrahim, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga masu shirki ba

    [124] Abin sani kawai, an sanya Asabar a kan waɗanda suka saɓa wajuna a cikin sha'aninsa. Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙiƙa, Yana yin hukunci a tsakaninsu a Ranar ¡iyama a cikin abin da suka kasance a cikinsa suna saɓa wa juna

    [125] Ka yi kira zuwa ga hanyar Ubangijinka da hikima da wa'azi mai kyau kuma ka yi jayayya da su da magana wadda take mafi kyau. Lalle ne Ubangijinka Shi neMafi sani ga wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga masu shiryuwa

    [126] Kuma idan kuka saka wa uƙuba to ku saka wa uƙuba da misalin abin da aka yi muku uƙubar da shi. Kuma idan kun yi haƙuri, lalle shi ne mafi alheri ga masu haƙuri

    [127] Kuma ka yi haƙuri, kuma haƙurinka ba zai zama ba face domin Allah, kuma kada ka yi baƙin ciki sabo da su, kuma kada ka kasance a cikin ƙuncin rai daga abin da suke yi na makirci

    [128] Lalle Allah Yana tare da waɗanda suka yi taƙawa da waɗanda suke su masu kyautatawa ne

    Isra'i (Tafiyar dare)

    Surah 17

    [1] Tsarki ya tabbata ga wanda Ya yi tafiyar dare da bawanSa da dare daga Masallaci mai alfarma zuwa ga Masallaci mafi nisa wanda Muka sanya albarka a gefensa domin Mu nuna masa daga ayoyinMu. Lalle ne Shi shi ne Mai ji, Mai gani

    [2] Kuma Mun bai wa Musa littafi, kuma Mun sanya shi shiriya ga Bani Isra'ila, cewa kada ku riƙi wani wakili baiciNa

    [3] Zuriyar waɗanda Muka ɗauka tare da Nuhu. Lalle ne shi ya kasance wani bawa mai godiya

    [4] Kuma Mun hukunta zuwa ga Bani Isra'ila a cikin Littafi, cewa lalle ne, kuna yin ɓarna a cikin ƙasa sau biyu, kuma lalle ne kuna zalunci, zalunci mai girma

    [5] To idan wa'adin na farkonsu yaje, za Mu aika, a kanku waɗansu bayi Namu, ma'abuta yaƙi mafi tsanani, har su yi yawo a tsakanin gidajenku, kuma ya zama wa'adi abin aikatawa

    [6] Sa'an nan kuma Mu nwayar da ɗauki a gare ku a kansu, kuma Mu taimake ku da dukiyoyi da ɗiya kuma Mu sanya ku mafiya yawan masu fita yaƙi

    [7] Idan kun kyautata, kun kyautata domin kanku, kuma idan kun munana to dominsu. Sa'an nan idan wa'adin na ƙarshe ya je, (za su je) domin su baƙanta fuskokinku, kuma su shiga masallaci kamar yadda suka shige shi a farkon lokaci, kuma domin su halakar da abin da suka rinjaya a kansa, halakarwa

    [8] Akwai tsammanin Ubangijinku Ya yi muku rahama. Kuma idan kun sake Mu sake. Kuma Mun sanya Jahannama matsara ga kafirai

    [9] Lalle ne wannan Alƙur'ani yana shiryarwa ga (halayen) waɗanda suke mafi daidaita kuma yana bayar da bushara ga muminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cewa) "Lalle ne suna da wata ijara. mai girma

    [10] Kuma lalle ne, waɗanda ba su yin imani da Lahira, Mun yimusu tattalin wata azaba mai raɗaɗi

    [11] Kuma mutum yana yin addu'a da sharri kamar addu'arsa da alheri, kuma mutum ya kasance mai gaggawa

    [12] Kuma Mun sanya dare da rana, ayoyi biyu, sa'an nan Muka shafe ayar dare, kuma Muka sanya ayar rana mai sanyawa a yi gani, domin ku nemi falala daga Ubangijinku, kuma domin ku san ƙidayar shekara da lissafi. Kuma dukan kome Mun bayyana shi daki-dakin bayyanawa

    [13] Kuma kowane mutum Mun lazimta masa abin rekodinsa a cikin wuyansa, kuma Mu fitar masa a Ranar ¡iyama da littafi wanda zai haɗu da shi buɗaɗɗe

    [14] Karanta Littafinka. Ranka ya isa ya zama mai hisabi a kanka a yau

    [15] Wanda ya nemi shiryuwa, to, ya nemi shiryuwa ne dominkansa kawai kuma wanda ya ɓace, to, ya ɓace ne a kansa kawai kuma rai mai ɗaukar nauyi ba ya ɗaukar nauyin wani ran, kuma ba Mu zama masu yin azaba ba, sai Mun aika wani Manzo

    [16] Kuma idan Mun yi nufin Mu halakar da wata alƙarya, sai Mu umurci mawadatanta, har su yi fasicci a cikinta, sa'an nan maganar azaba ta wajaba a kanta, sa'an nan Mu darkake ta, darkakewa

    [17] Kuma da yawa Muka halakar da al'ummomi a bayan Nuhu. Kuma Ubangijinka Ya isa ya zama Mai ƙididdigewa ga zunubban bayinSa, Mai gani

    [18] Wanda ya kasance yana nufin mai gaggawa, sai Mu gaggauta masa a cikinta, abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa'an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya ƙonu da ita, yana abin zargi kuma abin tunkuɗewa

    [19] Kuma wanda ya nufi Lahira, kuma ya yi aiki saboda ita irin aikinta alhali kuwa yana mumini, to, waɗannan aikinsu ya kasance godadde

    [20] Dukkansu Muna taimakon waɗannan da waɗancan daga kyautar Ubangijinka, kuma kyautar Ubangijinka ba ta kasance hananna ba

    [21] Ka duba yadda Muka fifitar da sashensu a kan sashe! Kuma lalle ne Lahira ce mafi girman darajoji, kuma mafi girman fifitawa

    [22] Kada ka sanya wani abin bautawa na daban tare da Allah har ka zauna kana abin zargi, yarɓaɓɓe

    [23] Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kowa face Shi, kum game da mahaifa biyu ku kyautata kyautatawa, ko dai ɗayansu ya kai ga tsufa a wurinka ko dukansu biyu, to, kada ka ce musu 'tir' kuma kada ka tsawace su kuma ka faɗa musu magana mai karimci

    [24] Kuma ka sassauta musu fikafikan tausasawa na rahama. Kuma ka ce: "Ya Ubangijina! Ka yi musu rahama, kamar yadda suka yi renona, ina ƙarami

    [25] Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da yake a cikin rayukanku. Idan kun kasance salihai to lalle ne shi Ya kasance ga masu komawa gare Shi, Mai gafara

    [26] Kuma ka bai wa ma'abucin zumunta hakkinsa da miskina da ɗan hanya. Kuma kada ka bazzara dukiyarka, bazzarawa

    [27] Lalle ne mubazzarai sun kasance 'yan'uwan shaiɗanu. Kuma Shaiɗan ya kasance ga Ubangijinsa, mai yawan kafirci

    [28] Ko dai ka kau da kai daga gare su domin neman rahama daga Ubangijinka, wadda kake fatanta, to sai ka gaya musu magana mai laushi

    [29] Kuma kada ka sanya hannunka ƙuƙuntacce zuwa ga wuyanka, kuma kada ka shimfiɗa shi dukan shimfiɗawa har ka zama abin zargi, wanda ake yanke wa

    [30] Lalle ne Ubangijinka Yana shimfiɗa arziki ga wanda Yake so, kuma Yana ƙuƙuntawa. Lalle Shi, Ya kasance Mai sani ga bayinSa, Mai gani

    [31] Kuma kada ku kashe 'ya'yanku domin tsoron talauci. Mu ne ke arzuta su, su da ku. Lalle ne kashe su ya kasance kuskure babba

    [32] Kuma kada ku kusanci zina. Lalle ne ita ta kasance alfasha ce kuma ta munana ga zama hanya

    [33] Kuma kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta face da haƙƙi, kuma wanda aka kashe, yana wanda aka zalunta to, haƙiƙa Mun sanya hujja ga waliyyinsa, sai dai kada ya ƙetare haddi a cikin kashewar. Lalle shi ya kasance wanda ake taimako

    [34] Kuma kada ku kusanci dukiyar maraya face dai da sifa wadda take ita ce mafi kyau, har ya isa ga mafi ƙarfinsa. Kuma ku cika alkawari. Lalle alkawari ya kasance abin tambayawa ne

    [35] Kuma ku cika mudu idan kun yi awo, kuma ku auna nauyi da sikeli madaidaici. Wancan ne mafi alheri, kuma mafi kyau ga fassara

    [36] Kuma kada ka bi abin da ba ka da ilmi game da shi. Lalle ne ji da gani da zuciya, dukan waɗancan (mutum) ya kasance daga gare shi wanda ake tambaya

    [37] Kuma kada ka yi tafiya a cikin ƙasa da alfahari. Lalle kai ba za ka huda ƙasa ba kuma ba za ka kai a duwatsu ba ga tsawo

    [38] Dukan wancan mli muninsa ya kasance abin ƙyama a wurin Ubangijinka

    [39] Wancan yana daga abin da Ubangijinka Ya yi wahayi zuwa gare ka na hikima. Kuma kada ka sanya wani abin bautawa na daban tare da Allah har a jefa ka a cikin Jahannama kana wanda ake zargi, wanda ake tunkuɗewa

    [40] Shin fa, Ubangijinku Ya zaɓe ku da ɗiya maza ne, kuma Ya riƙi 'ya'ya mata daga mala'iku? Lalle ne ku, haƙiƙa, kuna faɗar magana mai girma

    [41] Kuma lalle ne haƙiƙa, Mun sarrafa bayani a cikin wannan Alƙur'ani domin su yi tunani, kuma ba ya ƙara musu kome face gudu

    [42] Ka ce: "Da akwai waɗansu abubuwan bautawa tare da shi, kamar yadda suka faɗa, a lokacin, da (abubuwan bautawar) sun nemi wata hanya zuwa ga Ma'abucin Al'arshi

    [43] TsarkinSa ya tabbata kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke faɗa, ɗaukaka mai girma

    [44] Sammai bakwai da ƙasa da wanda yake a cikinsu suna yi Masa tasbihi. Kuma babu wani abu face yana tasbihi game da gode Masa, kuma amma ba ku fahimtar tasbihinsu. Lalle ne shi, Ya kasance Mai haƙuri ne, Mai gafara

    [45] Kuma idan ka karanta Alƙur'ani, sai Mu sanya a tsakaninka da tsakanin waɗanda ba su yin imani da Lahira wani shamaki mai suturcewa

    [46] Kuma Mu sanya marufai a kan zukatansu domin kada su fahimce shi, da, wani nauyi a cikin kunnuwansu, kuma idan ka ambaci Ubangijinka, a cikin Alƙur'ani shi kaɗai, sai su juya a kan bayayyakinsu domin gudu

    [47] Mu ne Mafi sani game da abin da suke saurare da shi a lokacin da suke yin sauraren zuwa gare ka, kuma a lokacin da suke masu ganawa a tsakaninsu a lokacin da azzalumai suke cewa, "Ba ku biyar kowa face wani namiji sihirtacce

    [48] Ka duba yadda suka buga maka misalai, sai suka ɓace ba su iya samun hanya

    [49] Kuma suka ce: "Shin, idan mun kasance ƙasusuwa da, niƙaƙƙun gaɓaɓuwa ashe, lalle ne mu haƙiƙa, waɗanda ake tayarwa ne a wata halitta sabuwa

    [50] Ka ce: "Ku kasance duwatsu ko kuwa baƙin ƙarfe

    [51] Ko kuwa wata halitta daga abin da yake da girma a cikin ƙirazanku." To za su ce "Wane ne zai mayar da mu?" Ka ce: "Wanda Ya ƙaga halittarku a fabkon lokaci." To, za su gyaɗa kansu zuwa gare ka, kuma suna cewa, "A yaushene shi?" Ka ce: "Akwai tsammaninsa ya kasance kusa

    [52] A ranar da Yake kiran ku, sa'an nan ku riƙa karɓawa game da gode Masa, kuma kuna zaton ba ku zauna ba face kaɗan

    [53] Kuma ka ce wa bayiNa, su faɗi kalma wadda take mafi kyau. Lalle ne Shaiɗan yana sanya ɓarna a tsakaninsu. Lalle ne Shaiɗan ya kasance ga mutum, maƙiyi bayyananne

    [54] Ubangijinku ne Mafi sani game da ku. Idan Ya so, zai yi muku rahama, ko kuwa idan Ya so zai azabtaku. Kuma ba Mu aika ka kana wakili a kansu ba

    [55] Kuma Ubangijinka ne Mafi sani game da wanda yake a cikin sammai da ƙasa. Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun fifita sashen Annabawa a kan sashe kuma Mun bai wa Dawuda zabura

    [56] Ka ce: "Ku kirayi waɗanda kuka riya, baicinSa." To, ba su mallakar kuranyewar cuta daga gare ku, kuma haka juyarwa

    [57] Waɗancan, waɗanda suke kiran, suna neman tsani zuwa ga Ubangijinsu. Waɗanne ne suke mafifita a kusanta? Kuma suna fatan samun rahamarSa, kuma suna tsoron azabarSa. Lalle ne azabar Ubangijinka ta kasance abar tsoro ce

    [58] Kuma babu wata alƙarya face, Mu ne masu halaka ta a gabanin Ranar ¡iyama ko kuwa Mu masu azabta ta ne da azaba mai tsanani. Wancan ya kasance a cikin littafi rubutacce

    [59] Kuma babu abin da ya hana Mu, Mu aika da ayoyi face saboda mutanen farko sun ƙaryata game da su. Kuma Mun bai wa Samudawa taguwa, aya bayyananna, sai suka yi zalunci game da ita. Kuma ba Mu aikawa da ayoyi face domin tsoratarwa

    [60] Kuma a lokacin da Muka ce maka, "Lalle ne Ubangijinka Ya kewaye mutane." Kuma ba Mu sanya abin da ya gani wanda Muka nuna maka ba, face domin fitina ga mutane, da itaciya wadda aka la'anta a cikin Alƙur'ani. Kuma Muna tsoratar da su, sa'an nan (tsoratarwar) ba ta ƙara su face da kangara mai girma

    [61] Kuma a lokacin da Muka ce wa mala'iku, "Ku yi sujada ga Adamu," sai suka yi sujada, face Ibilisa, ya ce: "shin, zan yi sujada ga wanda ka halitta shi yana laka

    [62] Ya ce: "Shin, ka gan ka! Wannan wanda ka girmama a kaina, lalle ne idan ka jinkirta mini zuwa ga Ranar ¡iyama lalle ne, zan tumɓuke zuriyarsa, face kaɗan

    [63] Ya ce: "Ka tafi. Sa'an nan wanda ya bi ka daga gare su, to, Jahannama ce sakamakonku, (Mu ba ku shi) sakamako cikakke

    [64] Kuma ka rikitar da wanda ka sami iko a kansa, daga gare su, da sautinka, kuma ka yi hari a kansu da dawakinka da dakarunka kuma ka yi tarewa da su a cikin dukiyoyi da ɗiya, kumaka yi musu wa'adi. Alhali kuwa Shaiɗan ba ya yi musu wa'adin kome face da ruɗi

    [65] Lalle ne bayiNa, ba ka da wani ƙarfi a kansu. Kuma Ubangijinka Ya isa Ya zama wakili

    [66] Ubangijinku ne Yake gudanar da jirgi a cikin teku, domin ku nema daga falalarSa. Lalle ne Shi, Ya kasance a gare ku Mai jin ƙai

    [67] Kuma idan cuta ta shafe ku, a cikin teku, sai wanda kuke kira ya ɓace face Shi. To, a lokacin da Ya tsira da ku zuwa, ga tudu sai kuka bijire. Kuma mutum ya kasance mai yawan butulci

    [68] Shin fa kun amince cewa (Allah) ba Ya shafe gefen ƙasa game da ku ko kuwa Ya aika da iska mai tsakuwa a kanku, sa'an nan kuma ba za ku sami wani wakili ba dominku

    [69] Ko kun amince ga Ya mayar da ku a cikin tekun a wani lokaci na dabam, sa'an na Ya aika wata guguwa mai karya abubuwa daga iska, har ya nutsar da ku saboda abin da kuka yi na kafirci? Sa'an nan kuma ba ku samun mai bin hakki saboda ku, a kanMu, game da Shi

    [70] Kuma lalle ne Mun girmama 'yan Adam, kuma Muka ɗauke su a cikin ƙasa da teku kuma Muka azurta su daga abubuwa masu daɗi kuma Muka fifita su a kan masu yawa daga waɗanda Muka halitta, fifitawa

    [71] A ranar da Muke kiran kowane mutane da limaminsu to, wanda aka bai wa littafinsa a da, mansa, to, waɗannan suna karatun littafinsu, kuma ba a zaluntar su da zaren bakin gurtsin dabino

    [72] Kuma wanda ya kasance makaho a cikin wannan saboda haka shi a Lahira makaho ne kuma mafi ɓata ga hanya

    [73] Kuma lalle ne sun yi kusa haƙiƙa, su fitine ka daga abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, domin ka ƙirƙira waninsa a gare Mu, a lokacin, haƙiƙa, da sun riƙe ka masoyi

    [74] Kuma ba domin Mun tabbatar da kai ba, lalle ne, haƙiƙa, da ka yi kusa ka karkata zuwa gare su ta wani abu kaɗan

    [75] A lokacin, lalle ne, da Mun ɗanɗana maka ninkin azabar rayuwa da ninkin azabar mutuwa, sa'an nan kuma ba za ka sami mataimaki ba a kanMu

    [76] Kuma lalle ne, sun yi kusa, haƙiƙa, su tayar da hankalinka daga ƙasar, domin su fitar da kai daga gare ta. Kuma a lokacin, ba za su zauna ba a kan saɓaninka face kaɗan

    [77] Hanyar waɗanda, haƙiƙa, Muka aika a gabaninka, daga ManzanninMu, kuma ba za ka sami juyarwa ba ga hanyarMu

    [78] Ka tsayar da salla a karkatar rana zuwa ga duhun dare da lokacin fitar alfijir lalle ne karatun fitar alfijir ya kasance wanda ake halarta

    [79] Kuma da dare, sai ka yi hira da shi (Alƙur'ani) akan ƙari gare ka. Akwai tsammanin Ubangijinka Ya tayar da kai a wani matsayi godadde

    [80] Kuma ka ce: "Ya Ubangijina! Ka shigar, da ni shigar gaskiya, kuma Ka fitar da ni fitar gaskiya. Kuma Ka sanya mini, daga gunKa, wani ƙarfi mai taimako

    [81] Kuma ka ce: "Gaskiya ta zo, kuma ƙarya ta lalace. Lalle ne ƙarya ta kasance lalatacciya

    [82] Kuma Muna sassaukarwa daga Alƙur'ani, abin da yake waraka ne da rahama ga muminai. Kuma ba ya ƙara wa azzalumai (kome) face hasara

    [83] Kuma idan Muka yi ni'ima a kan mutum, sai ya hinjire, kuma ya nisanta da gefensa, kuma idan sharri ya shafe shi, sai ya kasance mai yanke ƙauna

    [84] Ka ce: "Kowa ya yi aiki a kan hanyarsa. Sa'an nan Ubangijinka ne Mafi sani ga wanda yake mafi shiryuwa ga hanya

    [85] Suna tambayar ka ga ruhi. Ka ce: "Ruhi daga al'amarin Ubangijina ne, kuma ba a ba ku (kome) ba daga ilmi face kaɗan

    [86] Kuma lalle ne idan Mun so, haƙiƙa, Muna tafiya da abinda Muka yi wahayi zuwa gare ka. Sa'an nan kuma ba za ka sami wani wakili ba dominka game da shi a kanMu

    [87] Face da rahama daga Ubangijinka. Lalle ne falalarSa ta kasance mai girma a kanka

    [88] Ka ce: "Lalle ne idan mutane da aljannu sun taru a kan su zo da misalin wannan Alƙur'ani ba za su zo da misalinsa ba, kuma ko da sashinsu ya kasance, mataimaki ga sashi

    [89] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun caccanza domin mutane, a cikin wannan Alƙur'ani, daga kowane misali sai mafi yawan mutane suka ƙi (kome) face kafirci

    [90] Kuma suka ce: "Ba za mu yi imani ba dominka sai ka ɓuɓɓugar da idan ruwa daga ƙasa

    [91] Ko kuma wata gona daga dabinai da inabi ta kasance a gare ka. Sa'an nan ka ɓuɓɓugar da ƙoramu a tsakaninta ɓuɓɓugarwa

    [92] Ko kuwa ka kayar da sama a kanmu kaɓukka ko kuwa ka zo da Allah, da mala'iku banga-banga

    [93] Ko kuwa wani gida na zinariya ya kasance a gare ka, ko kuwa ka taka a cikin sama. Kuma ba za mu yi imani ba ga takawarka, sai ka sassauko da wani littafi a kanmu, muna karanta shi." Ka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijina! Ban kasance ba face mutum, Manzo

    [94] Kuma babu abin da ya hana mutane su yi imani, a lokacin da shiriya ta je musu, face sunce, "Shin, Allah zai aiko mutum ya zamo yana Manzo

    [95] Ka ce: "Da mala'iku sun kasance a cikin ƙasa, kuma suna tafiya, suna masu natsuwa, lalle ne da mun saukar da mala'ika daga sama ya zama manzo a kansu

    [96] Ka ce: "Allah Ya isa zama shaida a tsakanina da ku. Lalle Shi Ya kasance ga bayinsa, mai ƙididdigewa ne Mai gani

    [97] Kuma wanda Allah Ya shiryar, to, shi ne shiryayye, kuma wanda Ya ɓatar to ba za ka sami waɗansu masoya gare su ba baicinSa. Kuma Muna tara su a Ranar ¡iyama a kan fuskokinsu, suna makafi, kuma bebaye da kurame. Matattararsu Jahannama ce, ko da yaushe ta bice, sai Mu ƙara musu wata wuta mai tsanani

    [98] Wancan ne sakamakonsu saboda lalle su, sun kafirta da ayo yinMu, kuma suka ce: "Shin idan muka kasance ƙasusuwa da niƙaƙƙun gaɓuɓuwa, shin lalle mu, haƙi ka, waɗanda ake tayarwa ne a cikin wata halitta sabuwa

    [99] Shin, kuma ba su gani ba (cewa) lalle ne Allah, wandaYa halicci sammai da ƙasa, Mai ikon yi ne a kan Ya halicci misalinsu? Kuma Ya sanya wani ajali wanda babu kokwanto a cikinsa? Sai azzalumai suka ƙi face kafirci

    [100] Ka ce: "Da dai ku, kuna mallakar taskokin rahamar Ubangijina, a lokacin, haƙiƙa da kun kame domin tsoron ƙarewar taskokin. Kuma mutum ya kasance mai ƙwauro ne

    [101] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun bai wa Musa ayoyi guda tara bayyanannu, sai ka tambayi Bani Isra'ila, a lokacin da ya je musu, sai Fir'auna ya ce masa, "Lalle ni, ina zaton ka, ya Musa, sihirtacce

    [102] Ya ce: "lalle ne haƙiƙa ka sani babu wanda ya saukar da waɗannan, face Ubangijin sammai da ƙasa domin su zama abubuwan lura. Kuma lalle ne ni, haƙiƙa, ina zaton ka, ya Fir'auna, halakakke

    [103] Sai ya yi nufin fitar da su daga ƙasar, sai Muka nutsar da shi, shi da wanda yake tare da shi gaba ɗaya

    [104] Kuma Muka ce: daga bayansa ga Bani Isra'ila, "Ku zauni ƙasar. Sa'an nan idan wa'adin ƙarshe ya zo, za Mu je da ku jama'a-jama'a

    [105] Kuma da gaskiya Muka saukar da shi, kuma da gaskiya ya sauka. Kuma ba Mu aike ka ba face kana mai bayar da bushara kuma mai gargaɗi

    [106] Kuma yana abin karatu Mun rarraba shi domin ka karanta shi ga mutane a kan jinkiri kuma Mun sassaukar da shi sassaukarwa

    [107] Ka ce: "Ku yi imani da Shi, ko kuwa kada ku yi imani, lalle ne waɗanda aka bai wa ilmi daga gabaninsa, idan ana karatunsa a kansu, suna faɗuwa ga haɓoɓinsu, suna masu sujada

    [108] Kuma suna cewa: Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle ne wa'adin Ubangijinmu ya kasance, haƙiƙa, abin aikatawa

    [109] Kuma suna faɗuwa ga haɓoɓinsu suna kuka, kuma yana ƙara musu tsoro

    [110] Ka ce: "Ku kirayi Allah ko kuwa ku kirayi Mai rahama. Kowane kuka kira to Yana da sunaye mafi kyau. Kuma, kada ka bayyana ga sallarka, kuma kada ka ɓoye ta. Ka nemi hanya a tsakanin wancan

    [111] Kuma ka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah wanda bai riƙi ɗa ba kuma abokin tarayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa, kuma wani masoyi saboda wulakancin bai kasance a gare Shi ba." Kuma ka girmama Shi, girmamawa

    Kogo

    Surah 18

    [1] Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya saukar da Littafi a kan bawansa kuma bai sanya karkata ba a gare shi

    [2] Madaidaici, domin Ya yi gargaɗi da azaba mai tsanani daga gare shi, kuma Ya yi bushara ga muminai, waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai da (cewa) suna da wata lada mai kyau

    [3] Suna masu zama a cikinta har abada

    [4] Kuma Ya yi gargaɗi ga waɗanda suka ce: "Allah yana da ɗa

    [5] Ba su da wani ilmi game da wannan magana, kuma iyayensu ba su da shi, abin da ke fita daga bakunansu ya girma ga ya zama kalmar faɗa! Ba su faɗan kome face ƙarya

    [6] To, ka yi kusa ka halaka ranka a gurabbansu, wai domin ba su yi imani da wannan labari ba saboda baƙin ciki

    [7] Lalle ne Mu, Mun sanya abin da ke kan ƙasa wata ƙawa ce gare ta, domin Mu jarraba su; wanne daga cikinsu zai zama mafi kyau ga aiki

    [8] Kuma lalle Mu, Masu sanya abin da ke a kanta (ya zama) turɓaya ƙeƙasasshiya ne

    [9] Ko kuwa ka yi zaton cewa ma'abuta kogo da allo sun kasance abin mamaki daga ayoyin Allah

    [10] A lokacin da samarin suka tattara zuwa ga kogon, sai suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka ba mu wata rahama daga gare Ka, kuma Ka sauƙaƙe mana (samun) shiriya daga al'amarinmu

    [11] Sai Muka yi duka a kan kunnunwansu, a cikin kogon, shekaru masu yawa

    [12] Sa'an nan Muka tayar da su, domin Mu san wane ɗayan ƙungiyoyin biyu suka fi lissafi ga abin da suka zauna na lokacin

    [13] Mu ne ke jeranta maka labarinsu da gaskiya. Lalle ne su, waɗansu samari ne. Sun yi imani da Ubangijinsu, kuma Muka ƙara musu wata shiriya

    [14] Kuma Muka ɗaure a kan zukatansu, a lokacin da suka tsayu, sa'an nan suka ce: "Ubangijinmu Shi ne Ubangijin sammai daƙasa. Ba za mu kirayi waninSa abin bautawa ba. (Idan mun yi haka) lalle ne, haƙiƙa, mun faɗi abin da ya ƙetare haddi a sa'an nan

    [15] Ga waɗannan mutanenmu sun riƙi waninSa abin bautawa! Don me ba su zuwa da wata hujja bayyananna a kansu (waɗanda ake bautawar)? To, wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙaga ƙarya ga Allah

    [16] Kuma idan kun nisance su su da abin da suke bautawa, face Allah, to, ku tattara zuwa ga kogon sai Ubangijinku Ya watsa muku daga rahamarSa kuma Ya sauƙaƙe muku madogara daga al'amarinku

    [17] Kuma kana ganin rana idan ta fito tana karkata daga kogonsu wajen dama kuma idan ta faɗi tana gurgura su wajen hagu, kuma su, suna a cikin wani fili daga gare shi. Wannan abu yana daga ayoyin Allah. Wanda Allah Ya shiryar, to shi ne mai shiryuwa, kuma wanda Allah Ya ɓatar to ba za ka samar masa wani majiɓinci mai shiryarwa ba

    [18] Kuma kana zaton su farkakku ne, alhali kuwa su masu barci ne. Muna juya su wajen dama da wajen hagu, kuma karensu yana shimfiɗe da zira'o'in ƙafafuwansa ga farfajiya (ta kogon). Da ka leka (a kan) su (da) lalle ne, ka juya daga gare su a guje kuma (da) lalle ne ka cika da tsoro daga gare su

    [19] Kuma kamar wannan ne Muka tayar da su, domin su tambayi juna a tsakaninsu. Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Mene ne lokacin da kuka zauna?" suka ce: "Mun zauna yini ɗaya ko sashen yini." Suka ce: "Ubangijinku ne Mafi sani ga abin da kuka zauna. To, ku aika da ɗayanku, game da azurfarku wannan, zuwa ga birnin. Sai ya duba wanne ne mafi tsarki ga abin dafawa, sai ya zo muku da abinci daga gare shi. Kuma sai ya yi da hankali, kada ya sanar da ku ga wani mutum

    [20] Lalle ne su idan sun kama ku, za su jefe ku, ko kuwa su mayar da ku a cikin addininsu kuma ba za ku sami babban rabo, ba, a sa'an nan har abada

    [21] Kuma kamar wancan ne, Muka nuna su (gare su) domin su san lalle wa'adin Allah gaskiya ne, kuma lalle ne Sa'a babu shakka a cikinta. A lokacin da suke jayayyar al'amarinsu a tsakaninsu sai suka ce: "Ku gina wani gini a kansu, Ubangijinsu ne Mafi sani game da su." Waɗanda suka rinjaya a kan al'amarinsu suka ce: "Lalle mu riƙi masallaci a kansu

    [22] Za su ce: "Uku ne da na huɗunsu karensu."Kuma suna cewa, "Biyar ne da na shidansu karensu," a kan jifa a cikin duhu. Kuma suna cewa, "Bakwaine da na takwas ɗinsu karensu."Ka ce: "Ubangijina ne Mafi saniga ƙidayarsu, babu wanda ya san su face kaɗan."Kada ka yi jayayya bayyananna. Kuma kada ka yi fatawa ga kowa daga gare su a cikin al'amarinsu

    [23] Kuma kada lalle ka ce ga wani abu, "Lalle ni, mai aikatawa ne ga wancan a gobe

    [24] Face idan Allah Ya so. Kuma ka ambaci Ubangijinka idan ka manta, kuma ka ce: "¦ammani ga Ubangijina, Ya shiryar da ni ga abin da yake shi ne mafi kusa ga wannan na shiriya

    [25] Kuma suka zauna a cikin kogonsu shekaru ɗari uku kuma suka daɗa tara

    [26] Ka ce: "Allah ne Mafi sani ga abin da suka zauna. Shi ne da (sanin) gaibin sammai da ƙasa. Mune ne ya yi ganinSa da jinSa! Ba su da wani majiɓinci baicinSa kuma ba Ya tarayya da kowa a cikin hukuncinsa

    [27] Ka karanta abin da aka yi wahayi zuwa gare ka, na littafin Ubangijinka. Babu mai musanyawa ga kalmominSa kuma ba za ka sami wata madogara ba daga waninsa

    [28] Ka haƙurtar da ranka tare da waɗanda ke kiran Ubangijinsu, safe da maraice, suna nufin yardarSa. Kuma kada idanunka su juya daga barinsu, kana nufin ƙawar rayuwar duniya. Kuma kada ka biwanda Muka shagaltar da zuciyarsa daga hukuncinMu, kuma ya bi son zuciyarsa, alhali kuwa al'amarinsa ya kasance yin ɓarna

    [29] Kuma ka ce: "Gaskiya daga Ubangijinku take." Saboda haka wanda ya so, to, ya yi imani, kuma wanda ya so, to, ya kafirta. Lalle ne Mu, Mun yi tattali domin azzalumai wata wuta wadda shamakunta, sun ƙewaye da su. Kuma idan sun nemi taimako sai a taimake su da wani ruwa kamar dabzar mai, yana soye fuskoki. Tir da abin shansu, kuma wutar ta yi munin zama mahutarsu

    [30] Lalle ne waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai lalle ne Mu ba Mu tozartar da ladar wanda ya kyautata aiki

    [31] Waɗannan suna da gidajen Aljannar zama, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu, ana sanya musu ƙawa, a cikinsu, daga mundaye na zinariya, kuma suna tufantar waɗansu tufafi kore, na alharini raƙiƙi da alharini mai kauri suna kishingiɗe a cikinsu, a kan, karagu. Madalla da sakamakonsu. Kuma Aljanna ta kyautatu da zama wurin hutawa

    [32] Kuma ka buga musu misali da waɗansu maza biyu. Mun sanya wa ɗayansu gonaki biyu na inabobi, kuma Muka kewayesu da itacen dabinai, kuma Muka sanya shuka a tsakaninsu (su gonakin)

    [33] Kowace gona daga biyun, ta bayar da amfaninta, kuma ba ta yi zaluncin kome ba daga gare shi. Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙoramu a tsakaninsu

    [34] Kuma ɗan itace ya kasance gare shi. Sai ya ce wa abokinsa, alhali kuwa yana muhawara da shi, "Ni ne mafifici daga gare ka a wajen dukiya, kuma mafi izza a wajen jama'a

    [35] Kuma ya shiga gonarsa, alhali yana mai zalunci ga kansa, ya ce: "Ba ni zaton wannan za ta halaka har abada

    [36] Kuma ba ni zaton sa'a mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan an mayar da ni zuwa ga Ubangijiina, to, lalle ne, zan sami abin da yake mafi alheri daga gare ta ya zama makoma

    [37] Abokinsa ya ce masa, alhali kuwa yana muhawara da shi, "Ashe ka kafirta da wanda Ya halitta ka daga turɓaya, sa'an nan daga ɗigon maniyi, sa, an nan Ya daidaita ka, ka zama mutum

    [38] Amma ni, shi ne Allah Ubangijina, kuma ba zan tara kowa da Ubangijina ba

    [39] Kuma don me, a lokacin da ka shiga gonarka, ka, ce, 'Abin da Allah ya so (shi ke tabbata) babu wani ƙarfi face game da Allah.' Idan ka gan ni, ni ne mafi ƙaranci daga gare ka a wajen dukiya da ɗiya

    [40] To, akwai fatan Ubangijina Ya ba ni abin da yake mafi alheri daga gonarka, kuma ya aika azaba a kanta (ita gonarka) daga sama, sai ta wayi gari turɓaya mai santsi

    [41] Ko kuma ruwanta ya wayi gari faƙaƙƙe, saboda haka, ba za ka iya nemo shi ba dominta

    [42] Kuma aka halaka dukan 'ya'yan itacensa, sai ya wayi gari yana juyar da tafunansa biyu, saboda abin da ya kashe a cikinta, alhali kuwa ita tana kwance a kan rassanta, kuma yana cewa, "Kaitona, da dai ban tara wani da Ubangijina ba

    [43] Kuma wata jama'a ba ta kasance a gare shi ba, waɗanda ke taimakon sa, baicin Allah, kuma bai kasance mai taimakon kansa ba

    [44] A can taimako da jiɓinta ga Allah yake. Shi ne kawai Gaskiya, shi ne Mafifici ga lada kumaMafi fici ga aƙiba

    [45] Ka buga musu misalin rayuwar duniya, kamar ruwane wanda Muka saukar da shi daga sama sa'an nan tsirin ƙasa ya garwaya da shi, sa'an nan ya wayi gari dudduga, iska tana shiƙar sa. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan ikon yi ne a kan dukan kome

    [46] Dukiya da ɗiya, su ne ƙawar rayuwar duniya, kuma ayyuka masu wanzuwa na ƙwarai sun fi zama alheri a wurin Ubangijinka ga lada kuma sun fi alheri ga buri

    [47] Kuma a ranar da Muke tafiyar da duwatsu, kuma ka ga ƙasa bayyane, kuma Mu tara su har ba Mu bar kowa ba daga gare su

    [48] Kuma a gitta su ga Ubangijinka suna sahu guda, (Mu ce musu), "Lalle ne haƙiƙa kun zo Mana, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lokaci. A'a, kun riya cewa ba za Mu sanya mukuwani lokacin haɗuwa ba

    [49] Kuma aka aza littafin ayyuka, sai ka ga masu laifi suna masu jin tsoro daga abin da ke cikinsa, kuma suna cewa "Kaitonmu! Mene ne ga wannan littafi, ba ya barin ƙarama, kuma ba ya barin babba, face ya ƙididdige ta?" Kuma suka sami abin da suka aikata halarce. Kuma Ubangijinka ba Ya zaluntar kowa

    [50] Kuma a lokacin da Muka ce wa malaiku, "Ku yi sujada ga Adamu." Sai suka yi sujada face Iblisa, ya kasance daga aljannu sai ya yi fasiƙanci ga barin umurnin Ubangijinsa, To fa, ashe, kuna riƙon sa, shi da zuriyarsa, su zama majiɓinta baicin Ni, alhali kuwa su maƙiya ne a gare ku? Tir da ya zama musanya ga azzalumai

    [51] Ban shaida musu halittar sammai da ƙasa ba, kuma ban (shaida musu) halittar rayukansu ba kuma ban kasance mai riƙon masu ɓatarwa (da wani) su zama mataimaka ba

    [52] Kuma da ranar da Allah Yake cewa, "Ku kirayi abokan tarayyaTa, waɗanda kuka riya." Sai su kiraye su, sai ba za su karɓa musu ba, kuma Mu sanya Maubiƙa (Mahalaka) a tsakaninsu

    [53] Kuma masu laifi suka ga wuta suka tabbata lalle ne, su masu, auka mata ne, kuma ba su sami majuya ba daga gare ta

    [54] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun jujjuya, a cikin wannan Alƙur'ani, daga kowane irin misali ga mutane (domin su gane, su bi shari'a), kuma mutum ya kasance mafi yawan abu ga jidali

    [55] Kuma babu abin da ya hana mutane su yi imani a lokacinda shiriya ta zo musu, kuma su nemi gafara daga Ubangijinsu, face hanyar farko ta je musu ko kuma azaba ta je musu nau'i-nau'i

    [56] Kuma ba Mu aika Manzanni ba face suna masu bayar da bushara kuma masu gargaɗi, kuma waɗanda suka kafirta suna jidali da ƙarya domin su ɓata gaskiya da ita, kuma suka riƙi ayoyiNa da abin da aka yi musu gargaɗi da shi abin izgili

    [57] Kuma wane ne mafi zalunci daga wanda aka tunatar game da ayoyin Ubangijinsa, sai ya bijire daga barinsu, kuma ya manta abin da hannayensa suka gabatar? Lalle ne Mu, Mun sanya abubuwan rufi a kan zukatansu domin kada su fahimce shi, kuma a cikin kunnuwansu (Mun sanya) wani nauyi, kuma idan ka kiraye su zuwa ga shiriya, to, ba za su shiryu ba, a sa'an nan, har abada

    [58] Kuma Ubangijinka Mai gafara ne, Ma'abucin rahama. Da Yana kama su saboda abin da suka sana'anta, lalle ne, da Ya gaggauta azaba a gare su. A'a, suna da lokacin alkawari, (wanda) ba za su sami wata makoma ba, baicinSa

    [59] Kuma waɗancan alƙaryu Mun halaka su, a lokacin da suka yi zalunci, kuma Muka sanya lokacin alkawarin, ga halaka su

    [60] Kuma a lokacin da Musa ya ce wa yaronsa, "Ba zan gushe ba sai na isa mahaɗar teku biyu, ko in shuɗe da tafiya shekara da shekaru

    [61] To, a lokacin da suka isa mahaɗar tsakaninsu sai suka manta kifinsu, sai ya kama tafarkinsa a cikin teku kamar biga

    [62] To, a lokacin da suka wuce ya ce wa yaronsa, "Ka kawo mana kalacinmu. Lalle ne haƙiƙa mun haɗu da wahala daga tafiyarmu wannan

    [63] (Yaron) ya ce: "Ka gani! A lokacin da muka tattara zuwa ga falalen nan to, lalle ni, na manta kifin, kuma babu abin da yamantar da ni shi, face Shaiɗan, domin kada in tuna shi, sai ya kama tafarkinsa a cikin teku, da mamaki

    [64] Ya ce: "Wancan ne abin da muka kasance muna biɗa." Sai suka koma a kan gurabunsu, suna bibiya

    [65] Sai suka sami wani bawa daga bayinMu, Mun ba shi wata rahama daga wurinMu, kuma Mun sanar da shi wani ilmi daga gunMu

    [66] Musa ya ce masa, "Ko in bi ka a kan ka sanar da ni daga abin da aka sanar da kai na shiriya

    [67] Ya ce: "Lalle ne kai ba za ka iya yin haƙuri tare da ni, ba

    [68] Kuma yaya za ka yi haƙuri a kan abin da ba ka kewayeda shi ba ga jarrabawa

    [69] Ya ce: "Za ka same ni, in Allah Ya so mai haƙuri kuma ba zan saɓa maka ba ga wani umurni

    [70] Ya ce: "To idan ka bi ni to kada ka tambaye ni daga kome sai na labarta maka ambato daga gare shi

    [71] Sai suka tafi har a lokacin da suka hau a cikin jirgi, ya huje shi, ya ce, "Ka huje shi domin ya nutsar da mutanensa? Lalle ne, haƙiƙa, ka zo da wani babban abu

    [72] Ya ce: "Ashe ban ce, lalle kai, ba za ka iya yin haƙuri tare da ni ba

    [73] Ya ce: "Kada ka kama ni da abin da na manta kuma kada ka kallafa mini tsanani ga al'amarina

    [74] Sai suka tafi, har suka haɗu da wani yaro, sai ya kashe shi. Ya ce: "Ashe ka kashe rai tsarkakakke, ba da wani rai ba? Lalle ne haƙiƙa ka zo da wani abu na ƙyama

    [75] Ya ce: "Shin, ban ce maka ba, lalle ne kai ba za ka iya yin haƙuri tare da ni ba

    [76] Ya ce: "Idan na tambaye ka daga wani abu a bayanta, to, kada ka abuce ni. Lalle ne, ka isa ga iyakar uzuri daga gare ni

    [77] Sai suka tafi, har a lokacin da suka je wa mutanen wata alƙarya, suka nemi mutanenta da su ba su abinci, sai suka ƙi su yi musu liyafa. Sai suka sami wani bango a cikinta yana nufin ya karye, sai (Halliru) ya tayar da shi miƙe. (Musa) ya ce: "Da ka so, lalle ne da ka karɓi ijara a kansa

    [78] Ya ce: "Wannan shi ne rabuwar tsakanina da tsakaninka. Za ni gaya maka fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa

    [79] Amma Jirgin, to, ya zama na waɗansu matalauta ne suna aiki a cikin teku, sai na yi niyyar in aibanta shi, alhali kuwa wani sarki ya kasance a gaba gare su, yana karɓewar kowane jirgi (lafiyayye) da ƙwace

    [80] Kuma amma yaron, to, uwayensa sun kasance muminai, to, sai muka ji tsoron ya kallafa musu kangara da kafirci

    [81] Sai muka yi nufin Ubangijinsu Ya musanya musu mafi alheri daga gare shi ga tsarkakuwa, kuma mafi kusantar tausayi

    [82] Kuma amma bangon, to, ya kasance na waɗansu yara biyu ne, marayu a cikin birnin, kuma akwai wata taska tasu a ƙarƙashinsa, kuma ubansu ya kasance sahihin mutum ne, domin haka Ubangijinka Ya yi nufin su isa iyakar ƙarfinsu, kuma su, su fitar da taskarsu, saboda rahama ne daga Ubangijinka. Kuma ban yi shi ba daga umurnina. Wancan shi ne fassarar abin da ba ka iya yin haƙuri ba a kansa

    [83] Kuma suna tambayar ka daga zulƙarnaini, ka ce: "Zan karanta muku ambato daga gare shi

    [84] Lalle ne Mu Mun ba shi mulki a cikin ƙasa kuma Muka ba shi daga kowane abu, hanya (zuwa ga muradinsa)

    [85] Sai ya bi hanya

    [86] Har a lokacin da ya isa ga mafaɗar rana, kuma ya same ta tana ɓacewa a cikin wani ruwa mai baƙar laka, kuma ya sami waɗansu mutane a wurinta. Muka ce: "Ya Zulƙarnaini imma dai ka azabtar kuma imma ka riƙi kyautatawa a cikinsu

    [87] Ya ce: "Amma wanda ya yi zalunci, to za mu azabta shi, sa'an nan a mayar da shi zuwa ga Ubangijinsa, sai kuma Ya yi masa azaba, azaba abar ƙyama

    [88] Kuma amma wanda ya yi imani kuma ya aikata aikin ƙwarai to, za mu yi sakamako a gare shi (watau kyauta) mai kyau, kuma za mu gaya masa sauƙi daga umurninmu

    [89] Sa'an nan kuma ya bi hanya

    [90] Har a lokacin da ya isa ga mafitar rana, ya same ta tana fita a kan waɗansu mutane (waɗanda) ba Mu sanya musu wata kariya ba daga barinta

    [91] Kamar wancan alhali kuwa haƙiƙa, Mun kewaye da jarrabawa ga abin da ke gunsa

    [92] Sa'an nan kuma ya bi hanya

    [93] Har a lokacin da ya isa a tsakanin duwatsu biyu, ya sami waɗansu mutane daga gabaninsu. Ba su yi kusa su fahimci magana ba

    [94] Suka ce: "Ya Zulƙarnaini! Lalle ne Yajuja da Majuja masu ɓarna ne a cikin ƙasa. To, ko za mu Sanya haraji saboda kai, a kan ka sanya wani danni a tsakaninmu da tsakaninsu

    [95] Ya ce: "Abin da Ubangijina Ya mallaka mini, a cikinsa ya fi zama alheri. Sai ku taimakeni da ƙarfi, in sanya babbar katanga a tsakaninku da tsakaninsu

    [96] Ku kawo mini guntayen baƙin ƙarfe". (Suka kai masa) har a lokacin da ya daidaita a tsakanin duwatsun biyu (ya sanya wuta a cikin ƙarfen) ya ce: "Ku hura (da zugazugai)." Har a lokacin da ya mayar da shi wuta, ya ce: "Ku kawo mini gaci (narkakke) in zuba a kansa

    [97] Domin haka ba za su iya hawansa ba, kuma ba za su iya hujewa gare shi ba

    [98] Ya ce: "Wannan wata rahama ce daga Ubangijina. Sai idan wa'adin Ubangijina ya zo, ya mayar da shi niƙaƙƙe. Kuma wa'adin Ubangijina ya kasance tabbatacce

    [99] Kuma Muka bar sashensu a ranar nan, yana garwaya a cikin sashe, kuma aka busa a cikin ƙaho sai muka tara su, tarawa

    [100] Kuma Muka gitta Jahannama, a ranar nan ga kafirai gittawa

    [101] Waɗanda idanunsu suka kasance a cikin rufi daga tuna Ni, kuma sun kasance ba su iya saurarawa

    [102] Shin fa, waɗanda suka kafirta sun yi zaton (daidai ne) su riƙi waɗansu bayiNa, majiɓinta baiciNa? Lalle ne, Mun yi tattalin Jahannama ta zama liyafa ga kafirai

    [103] Ka ce: "Ko mu gaya muku game da mafifita hasara ga ayyuka

    [104] Waɗanda aikinsu ya ɓace a cikin rayuwar duniya, alhali kuwa suna zaton lalle ne su, suna kyautata, (abin da suke gani) aikin ƙwarai

    [105] Waɗancan ne waɗanda suka kafirta da ayoyin Ubangijinsu, da kuma haɗuwa da Shi, sai ayyukansu suka ɓaci. Saboda haka ba za Mu tsayar musu da awo ba a Ranar ¡iyama

    [106] Wancan ne sakamakonsu shi ne Jahannama, saboda kafircinsu, kuma suka riƙi ayoyiNa da ManzanniNa abin izgili

    [107] Lalle ne, waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Aljannar Firdausi ta kasance ita ce liyafa a gare su

    [108] Suna madawwama a cikinta, ba su neman makarkata daga barinta

    [109] Ka ce: "Da teku ta kasance tawada ga (rubutun) kalmomin Ubangijina, lalle ne da tekun ta ƙare a gabanin kalmomin Ubangijina su ƙare, kuma koda mun je da misalinsa domin ƙari

    [110] Ka ce: "Ni, mutum ne kawai kamarku, ana yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, saboda haka wanda ya kasance yana fatan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kowa ga bauta wa Ubangijinsa

    Maryam

    Surah 19

    [1] K.H. Y.I. S

    [2] Ambaton rahamar Ubangijinka ne ga BawanSa Zakariyya

    [3] A lokacin da ya kirayi Ubangijinsa, kira ɓoyayye

    [4] Ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne ni, ƙashi na daga gare ni ya yi rauni, kuma kaina ya kunnu da furfura, kuma ban kasance marashin arziki ba game da kiranKa, ya Ubangiji

    [5] Kuma lalle ni, na ji tsoron dangi a bayana, kuma matata ta kasance bakarariya! Sai ka ba ni wani mataimaki daga wajenKa

    [6] Ya gaje ni, kuma ya yi gado daga gidan Yaƙuba. Kuma Ka sanya shi yardajje, ya Ubangiji

    [7] (Allah Ya karɓa) "Ya zakariyya! Lalle ne Mu, Muna yi maka bushara da wani yaro, sunansa Yahaya. Ba Mu sanya masa wani takwara ba a gabani

    [8] Ya ce: "Ya Ubangijina! Yaya wani yaro zai kasance a gare ni, alhali kuwa matata ta kasance bakarariya, kuma ga shi na kai ga matuƙa ta tsufa

    [9] Ya ce: "Kamar wancan Ubangijinka Ya ce. Shi, a gare Ni mai sauƙi ne, kuma haƙiƙa Na halitta ka a gabanin haka, alhali ba ka kasance kome ba

    [10] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka sanya mini alama." Ya ce: "Alamarka ita ce ka kasa yi wa mutane magana a daruruwa uku daidai

    [11] Sai ya fita a kan mutanensa daga masallaci, sa'an nan ya yi ishara zuwa gare su da cewa, "Ku yi tasbihi safe da yamma

    [12] Ya Yahaya! Ka kama littafi da ƙarfi. Kuma Muka ba shi hukunci yana yaro

    [13] Kuma (Muka sanya shi) abin girmamawa daga gunMu, kuma mai albarka, kuma ya kasance mai ɗa'a da taƙawa

    [14] Kuma mai biyayya ga mahaifansa biyu, kuma bai kasance mai girman kai mai saɓo ba

    [15] Kuma aminci ya tabbata a gare shi a ranar da aka haife shi da ranar da yake mutuwa da ranar da ake tayar da shi yana mai rai

    [16] Kuma ka ambaci Maryamu a cikin Littafi, a lokacin da ta tsallake daga mutanenta a wani wuri, a gefen gabas

    [17] Sa'an nan ta riƙi wani shamaki daga barinsu. Sai Muka aika ruhinMu zuwa gare ta. Sai ya bayyana a gare ta da siffar mutum madaidaci

    [18] Ta ce: "Lalle ni ina neman tsari ga Mai, rahama daga gare ka, idan ka kasance mai tsaron addini

    [19] Ya ce: "Abin sani kawai, ni Manzon Ubangijinki ne domin in bayar da wani yaro tsarkakke gare ki

    [20] Ta ce: "A ina yaro zai kasance a gare ni alhali kuwa wani mutum bai shafe ni ba, kuma ban kasance karuwa ba

    [21] Ya ce: "Kamar wancan Ubangijinki Ya ce. Shi, a gare Ni mai sauƙi ne. Kuma domin Mu sanya shi wata alama ga mutane, kuma wata rahama ce daga gare Mu.' Kuma abin ya kasance wani al'amari hukuntacce

    [22] Sai ta yi cikinsa, sai ta tsallake da shi ga wani wuri mai nisa

    [23] Sai naƙuda ta kai ta zuwa ga wani kututturen dabiniya, ta ce "Kaitona, da dai na mutu a gabanin wannan kuma na kasance wani abu wulakantacce wanda aka manta

    [24] Sai (yaron da ta haifa) ya kira ta daga ƙarƙashinta, "Kada ki yi baƙin ciki! Haƙiƙa Ubangijinki Ya sanya wani marmaro a ƙarƙashinki

    [25] Kuma ki girgiza zuwa gare ki game da kututturen dabinon ya zuba a kanki yana 'ya'yan dabino, ruɗabi nunannu

    [26] Sai ki ci kuma ki sha kuma ki ji sanyi ga idanunki. To, idan kin ga wani aya daga mutane, sai ki ce, 'Lalle ni, na yi alwashin azumi domin Mai rahama saboda haka ba zan yi wa wani mutum magana ba

    [27] Sai ta je wa mutanenta tana auke da shi. Suka ce: "Ya Maryamu! Lalle ne, haƙiƙa kin zo da wani abu mai girma

    [28] Ya 'yar'uwar Haruna! Ubanki bai kasance mutumin alfasha ba, kuma uwarki ba ta kasance karuwa ba

    [29] Sai ta yi ishara zuwa gare shi, suka ce: "Yaya za mu yi magana da wanda ya kasance a cikin shimfiar tsumma yana jariri

    [30] Ya ce: "Lalle ne, ni bawan Allah ne Allah Ya ba ni Littafi kuma Ya sanya ni Annabi

    [31] Kuma Ya sanya ni mai albarka a inda duk na kasance kuma Ya umurce ni da yin salla da zakka matuƙar ina da rai

    [32] Kuma mai biyayya ga uwata, kuma bai sanya ni mai kaushin zuciya ba marashin alheri

    [33] Kuma aminci ya tabbata a gare ni a ranar da aka haife ni da ranar da nake mutuwa da ranar da ake tayar da ni ina mai rai

    [34] Wancan ne Isa ɗan Maryamu, maganar gaskiya wadda suke shakka a cikinta

    [35] Ba ya kasancewa ga Allah Ya riƙi wani ɗa. Tsarki ya tabbata a gare shi! Idan Ya hukunta wani al'amari sai kawai Ya ce masa, "Kasance." Sai ya dinga kasan cewa

    [36] Kuma lalle Allah ne Ubangijina kuma Ubangijinku, sai ku bauta Masa. Wannan shi ne tafarki madaidaici

    [37] Sai ƙungiyoyin suka saɓa wa juna a tsakaninsu. To, bone ya tabbata ga waɗanda suka kafirta daga halartar yini mai girma

    [38] Mene ne ya yi jinsu, kuma mene ne ya yi ganinsu a ranar da suke zo Mana! Amma azzalumai suna a cikin ɓata bayyananna

    [39] Kuma ka yi musu gargaɗi da ranar nadama a lokacin da aka hukunta al'amari alhali kuwa suna a cikin ɓata, kuma su ba su yin imani

    [40] Lalle ne Mu, Mu ne ke gadon ƙasa da wanda yake a kanta, kuma zuwa gare Mu ake mayar da su

    [41] Kuma ambaci Ibrahim a cikin Littafi. Lalle shi ya kasance mai yawan gaskatawa, Annabi

    [42] A lokacin da ya ce wa ubansa, "Ya baba! Don me kake bauta wa abin da ba ya ji, kuma ba ya ga ni, kuma ba ya wadatar da kome daga barinka

    [43] Ya baba! Lalle ni, haƙiƙa abin da bai je maka ba na ilmi ya zo mini, saboda haka ka bi ni in shiryar da kai wani tafarki madaidaici

    [44] Ya baba! Kada ka bauta wa Shaiɗan. Lalle Shaiɗan ya kasance mai saɓawa ga Mai rahama

    [45] Ya baba! Lalle ne ni ina tsoron wata azaba daga Mai rahama ta shafe ka, har ka zama masoyi ga Shaiɗan

    [46] Ya ce: "Ashe, mai gudu ne kai daga gumakana? Ya Ibraim! Lalle ne, idan ba ka hanu ba, haƙi ƙa, zan jefe ka. Kuma ka ƙaurace mini tun kana mai mutunci

    [47] Ya ce: "Aminci ya tabbata a gare ka! zan nemi Ubangijina Ya gafarta maka. Lalle Shi Ya kasance Mai girmamawa gare ni

    [48] Kuma ina nisantar ku da abin da kuke kira, baicin Allah kuma ina kiran Ubangijina, tsammanin kada in zama marashin arziki game da kiran Ubangijina

    [49] To, sa'ad da ya nisance su da abin da suke bautawa baicin Allah, Muka ba shi Is'haƙa da Ya'aƙuba alhali kuwa kowanensu Mun mayar da shi Annabi

    [50] Kuma Muka yi musu kyauta daga RahamarMu, kuma Muka sanya musu harshen gaskiya maɗaukaki

    [51] Kuma ka ambaci Musa a cikin Littafi. Lalle ne shi, ya kasance zaɓaɓɓe, kuma ya kasance Manzo, Annabi

    [52] Kuma Muka kira shi daga gefen dutse na dama kuma Muka kusanta shi yana abokin ganawa

    [53] Kuma Muka yi masa kyauta daga RahamarMu da ɗan'uwansa Haruna, ya zama Annabi

    [54] Kuma ka ambaci Isma'ila a cikin Littafi. Lalle shi, ya kasance mai gaskiyar alkawari, kuma ya kasance Manzo, Annabi

    [55] Kuma ya kasance yana umurnin mutanens da salla da zakka. Kuma ya kasance yardajje a wurin Ubangijinsa

    [56] Kuma ka ambaci Idrisa a cikin Littafi. Lalle shi, ya kasance mai yawan gaskatawa, Annabi

    [57] Muka ɗaukaka shi a wuri maɗaukaki

    [58] Waɗancan su ne waɗanda Allah Ya yi wa ni'ima daga Annabawa daga zurriyar Adamu, kuma daga waɗanda muka ɗauka tare da Nuhu, kuma daga zurriyar Ibrahim da Isra'ila, kuma daga waɗanda Muka shiryar kuma Muka zaɓe su. Idan ana karatun ayoyin Mai rahama a kansu, sai su faɗi suna masu sujada kuma masu kuka

    [59] Sai waɗansu 'yan baya suka maye a bayansu suka tozarta salla, kuma suka bi sha'awowinsu. To, da sannu za su hau da wani sharri

    [60] Face wanda ya tuba, kuma ya yi imani, kuma ya aikata aiki na ƙwarai. To, waɗannan suna shiga Aljanna, kuma ba a zaluntar su da kome

    [61] Gidajen Aljannar zama wadda Mai rahama ya yi alkawarin bayarwa ga bayinSa (masu aikin imani) a fake. Lalle ne shi, alkawarin ya kasance abin riskuwa

    [62] Ba su jin yasassar magana a cikinta, face sallama. Kuma suna da abinci, a cikinta, safe da maraice

    [63] Wancan Aljannar ce wadda Muke gadar da wanda ya kasance mai aiki da taƙawa daga bayiNa

    [64] (Suna masu cewa) "Kuma ba mu sauka Face da umuruin Ubangijinka (Muhammad). Shi ne da mulkin abin da ke a gaba gare mu da abin da ke a bayanmu da abin da ke a tsakanin wannan." Kuma (Ubangijinka bai kasance wanda ake mantawa ba)

    [65] Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakaninsu. sai ka bauta Masa, kuma ka yi haƙuri ga bautarsa. Shin ka san wani takwara a gare shi

    [66] Kuma mutum yana cewa, "Shin idan na mutu lalle ne haƙi ƙa da sannu za a fitar da ni ina mai rai

    [67] Shin, kuma mutum ba zai tuna ba cewa lalle ne Mun halitta shi a gabani, alhali kuwa bai kasance kome ba

    [68] To, Muna rantsuwa da Ubangijinka, lalle ne, Muna tayar da su da kuma shaianun sa'an nan, kuma lalle Muna halatar da su da kuma Shaiɗanun sa'an nan, kuma, lalle Muna halatar da su a gefen Jahannama suna gurfane

    [69] Sa'an nan kuma lalle Muna fizge wanda yake mafi tsananin girman kai ga Mai rahama daga kowace ƙungiya

    [70] Sa'an nan kuma lalle Mu ne Mafi sani ga waɗanda suke su ne mafiya cancantar ƙonuwa da ita

    [71] Kuma babu kowa daga gare ku sai mai tuzga mata. Ya kasance wajibi ga Ubangijinka, hukuntacce

    [72] Sa'an nan kuma Mu tserar da waɗanda suka yi aiki da taƙawa, kuma Mu bar azzalumai a cikinta gurfane

    [73] Kuma idan ana karatun ayoyinMu, bayyanannu a kansu, sai waɗanda suka kafirta su ce wa waɗanda suka yi imani, "Wanne daga ƙungiyoyin biyu ya fi zama mafi alheri ga matsayi, kuma mafi kyaun majalisa

    [74] Kuma da yawa daga mutanen ƙarni Muka halakar a gabaninsu su (waɗandaMuka halakar) in ne mafi kyaun kayan aki da magana

    [75] Ka ce: "Wanda ya kasance a cikin ɓata sai Mai rahama Ya yalwata masa yalwatawa, har idan sun ga abin da ake yi musu wa'adi, imma azaba ko sa'a, to za su sani, wane ne yake shi ne, mafi sharri ga wuri, kuma mafi rauni ga runduna

    [76] Kuma Allah na ƙara wa wa ɗanda suka nemi shiryuwa da shiriya. Kuma ayyuka masu wanzuwa na ƙwarai ne mafi alheri awurin Ubangijinka ga lada, kuma mafi alheri ga makoma

    [77] Shin, ka ga wanda ya kafirta da ayoyinMu, kuma ya ce: "Lalle ne za a ba ni dukiya da ɗiya

    [78] Shin, ya tsinkayi gaibi ne, ko kuwa ya ɗauki wani alkawari daga Mai rahama ne

    [79] A'aha! za mu rubuta abin da yake faɗa, kuma Mu yalwata masa, daga azaba, yalwatawa

    [80] Kuma Mu gade shi ga abin da yake faɗa, kuma ya zo Mana yana shi kɗai

    [81] Kuma suka riƙi gumaka, baicin Allah, domin su kasance mataimaka a gare su

    [82] A'aha! Za su kafirta da ibadarsu, kuma su kasance maƙiya a kansu

    [83] Shin, ba ka gani ba cewa Mun saki shaiɗanu a kan kafirai suna shushuta su ga zunubi shushutawa

    [84] Saboda haka kada ka yi gaggawa a kansu, Muna yi musu ƙidayar ajali ne kawai, ƙidayawa

    [85] A ranar da Muka tara masu taƙawa zuwa ga Mai rahama suna baƙin girma

    [86] Kuma Muna kora masu laifi zuwa Jahannama, gargaawa

    [87] Ba su mal1akar ceto face wanda ya riƙi alkawari a wurin Mai rahama

    [88] Kuma suka ce: "Mai rahama Ya riƙi a

    [89] Lalle ne haƙiƙa kun zo da wani abu mai girman muni

    [90] Sammai suna kusa su tsattsage saboda shi, kuma ƙasa ke kece kuma duwatsu su faɗi suna karyayyu

    [91] Domin sun yi da'awar ɗa ga Mai rahama

    [92] Alhali ba ya kamata ga Mai rahama ya riƙi wani ɗa

    [93] Dukkan wanda yake a cikin sammai da ƙasa bai zama ba face mai je wa Mai rahama ne yana bawa

    [94] Lalle ne haƙiƙa Ya lissafe su, kuma ya ƙidaye su, ƙidaya

    [95] Kuma dukan kowanensu mai je Masa ne a Ranar ¡iyama yana shi kaɗai

    [96] Lalle ne waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, Mai rahama zai sanya musu so

    [97] Sa'an nan Ibin sani kawai Mun sauƙaƙar da shi (Alƙur'ani) a harshenka, domin ka yi bushara da shi ga masu aiki da taƙawa kuma ka yi gargaɗi da shi ga mutane masu tsananin husuma

    [98] Kuma da yawa Muka halakar da mutanen ƙarnoni a gabaninsu. Shin kana jin motsin wani guda daga gare su, ko kuwa kana jin wata ɗuriya tasu

    Daha

    Surah 20

    [1] ¦.H

    [2] Ba Mu saukar da Alƙur'ani a gare ka domin ka wahala ba

    [3] Face domin tunatarwa ga wanda ke tsoron Allah

    [4] (An saukar da shi) saukarwa daga wanda Ya halitta ƙasa da sammai maɗaukaka

    [5] Mai rahama, Ya daidaita a kan Al'arshi

    [6] Abin da yake a cikin sammai naSa ne, da abin da yake a cikin ƙasa da abin da yake a tsakaninsu da abin da ke ƙarƙashin turɓaya

    [7] Kuma idan ka bayyana da magana, to, lalle Shi, Yana sanin asiri da mafi boyuwa

    [8] Allah babu abin bautawa face Shi. Yana da sunaye mafiya kyau

    [9] Kuma shin, labarin Musa yaje maka

    [10] A lokacin da ya ga wata wuta, sai ya ce wa iyalinsa, "Ku dakata. Lalle ne ni, na tsinkayi wata wuta tsammanina in zo mukuda makamashi daga gare ta, ko kuwa in sami wata shiriya a kan wutar

    [11] Sa'an nan a lokacin da ya je mata, aka kira shi, "Ya Musa

    [12] Lalle ne, Ni ne Ubangijnka, sai ka ɗebe takalmanka Lalle ne kana a rafin nan abin tsarkakewa, ¦uwa

    [13] Kuma Ni Na zaɓe ka. Sai ka saurara ga abin da ake yin wahayi

    [14] Lalle, Ni Ni ne Allah. Babu abin bautawa face Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla domin tuna Ni

    [15] Lalle ne Sa'a mai zuwa ce, lna kusa da In ɓoye ta domin a saka wa dukan rai da abin da yake aikatawa

    [16] Saboda haka, kada wanda ba ya yin imani da ita kumaya bi son zuciyarsa, ya taushe ka daga gare ta har ka halaka

    [17] Kuma wace ce waccan ga damanka ya Musa

    [18] Ya ce: "Ita sandata ce, ina dogara a kanta, kuma ina kakkaɓar ganye da ita a kan ƙananan bisashena kuma ina da waɗansu bukatoci na dabam a gare ta

    [19] Ya ce: "Ka yi jifa da ita, ya Musa

    [20] Sai ya jefa ta. Sai ga ta dabbar macijiya, tana tafiya da gaggawa

    [21] Ya ce: "Ka kama ta kuma kada ka ji tsoro. Za Mu mayar da ita ga halinta na farko

    [22] Kuma ka haɗa hannunka zuwa ga damtsenka, ya fita yana fari, babu sofane, wata aya ta dabam

    [23] Domin Mu nuna maka daga ayoyinMu manya

    [24] Ka tafi zuwa ga Fir'auna. Lalle shi ya ƙetare haddi (da girman kai)

    [25] Ya ce: "Ya Ubangiji! Ka buɗa mini, ƙirjina

    [26] Kuma ka sauƙaƙe mini al'amarina

    [27] Kuma Ka warware mini wani ƙulli daga harshena

    [28] Su fahimci maganata

    [29] Kuma Ka sanya mini wani mataimaki daga mutanena

    [30] Haruna ɗan'uwana

    [31] Ka ƙarfafa halittata da shi

    [32] Kuma Ka shigar da shi a cikin al'amarina

    [33] Domin mu tsarkake Ka da yawa

    [34] Kuma mu tuna Ka da yawa

    [35] Lalle Kai, Ka kasance Mai gani gare mu

    [36] Ya ce: "Lalle ne, an ba ka roƙonka, ya Musa

    [37] Kuma lalle ne haƙiƙa, Mun yi wata baiwa gare ka a wani lokacin na dabam

    [38] A lokacin da Muka yi wahayin abin da aka yi wahayi zuwa ga uwarka

    [39] Cewa, Ki jefa shi a cikin akwatin nan, sa'an nan ki jefa shi a cikin kogi, sa'an nan kogin ya jefa shi a gaɓa, wani maƙiyi Nawa kuma maƙiyi nasa ya ɗauke shi.' Kuma Na jefa wani so daga gare Ni a kanka. Kuma domin a riƙe ka da kyau a kan ganiNa

    [40] A sa'ad da 'yar'uwrka ke tafiya har ta ce, shin, in shiryar da ku ga wanda ke renonsa?' Sai Muka mayar da kai zuwa ga uwarka domin idonta ya yi sanyi kuma ba za ta yi baƙin ciki ba. Kuma ka kashe wani rai, sa'an nan Muka tserar da kai daga baƙin ciki, kuma Muka fitine ka da waɗansu fitinoni. Sa'an nan ka zauna shekaru a cikin mutanen Madyana. Sa'an nan kuma ka zo a kan wata ƙaddara, ya Musa

    [41] Kuma Na zaɓe ka domin Kaina

    [42] Ka tafi kai da ɗan'uwanka game da ayoyiNa, kuma kada ku yi rauni ga ambatoNa

    [43] Ku tafi ku biyu zuwa ga Fir'auna. Lalle shi ya ƙetare haddi (ga girman kai)

    [44] Sai ku gaya masa magana mai laushi, tsammaninsa yana tunawa ko kuwa ya ji tsoro

    [45] Su biyu suka ce: "Ya Ubangijinmu! Lalle ne muna tsoron ya yi gaggawa a kanmu, ko ya ƙetare haddi

    [46] Ya ce: "Kada ku ji tsoro. Lalle Ni, Ina tare da ku, Inaji, kuma Ina gani

    [47] Sai ku je masa sa'an nan ku ce, Lalle mu, Manzanni biyune na Ubangijinka, sai ka saki Bani Isra'ila tare da mu. Kuma kada ka yi musu azaba. Haƙiƙa mun zomaka da wata aya daga, Ubangijinka. Kuma aminci ya tabbata ga wanda ya bi shiriya

    [48] Lalle mu, haƙiƙa, an yi wahayi zuwa gare mu, cewaazaba tana a kan wanda ya ƙaryata, kuma ya juya baya

    [49] Ya ce: "To, wane ne Ubangijinku? Ya Musa

    [50] Ya ce: "Ubangijinmu Shi ne wanda Ya bai wa dukan kome halittarsa, sa'an nan Ya shiryar

    [51] Ya ce: "To, mene halin ƙarnonin farko

    [52] Ya ce: "Saninsu yana a wurin Ubangijina, Ubangijina ba Ya ɓacewa kuma ba Ya mantuwa

    [53] Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma Ya shigar muku da hanyoyi a cikinta, kuma Ya saukar da ruwa daga sama." Sa'an nan game da shi Muka fitar da nau'i-nau'i daga tsiruruwa dabam-dabam

    [54] Ku ci kuma ku yi kiwon dabbobin ni'imarku. Lalle ne, a cikin wannan akwai ayoyi ga masu hankali

    [55] Daga gare ta Muka halitta ku, kuma a cikinta Muke mayar da ku, kuma daga gare ta Muke fitar da ku a wani lokaci na dabam

    [56] Kuma lalle, haƙiƙa, Mun nuna masa ayoyinMu dukansu sai ya ƙaryata, kuma ya ƙiya

    [57] Ya ce: "Shin ka zo mana ne domin ka fitar da mu daga ƙasarmu game da sihirinka, ya Musa

    [58] To, lalle ne muna zo maka da wani sihiri irinsa. Sai ka sanya wani wa'adi a tsakaninmu da tsakaninka ba mu saɓa masa mu kai kuma, ba ka saɓawa, a wani wuri mai dacewa

    [59] Ya ce: "Wa'adinku shi ne ranar ƙawa kuma a tara mutane da hantsi

    [60] Sai Fir'auna ya juya, sa'an nan ya tara mugunyar dabararsa, sa'an nan kuma ya zo

    [61] Musa ya ce musu, "Kaitonku! Kada ku ƙirƙira ƙarya ga Allah har Ya tumɓuke ku da wata azaba. Kuma wanda ya ƙirƙira ƙarya, ya taɓe

    [62] Sai suka yi jayayya ga al'amarinsu a tsakaninsu kuma suka asirta ganawa

    [63] Suka ce: "Lalle ne waɗannan biyun, haƙiƙa masihirta ne suna nufin su fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinsu kuma su tafi da tabi'arku mafificiya

    [64] Sai ku haɗa dabararku sa'an nan kuma ku tafi a sahu guda, kuma haƙiƙa, wanda ya rinjaya, a yau, ya rabbanta

    [65] Suka ce: "Ya Musa! Imma ka jefa, ko kuma mu kasance farkon mai jefawa

    [66] Ya ce: "A'a, ku jefa." Sai ga igiyoyinsu da sandunansu ana suranta su a gare shi, daga sihirinsu, lalle suna tafiya da sauri

    [67] Sai Musa ya ji tsoro a cikin ransa

    [68] Muka ce: "Kada ka ji tsoro. lalle kai ne mafi ɗaukaka

    [69] Kuma ka jefa abin da ke a cikin hannun damanka, ta cafe abin da suka aikata. Lalle ne abin da suka aikata makircin masihirci ne kuma masihirci ba ya cin nasara a duk inda ya je

    [70] Sai aka jefar da masihirtan suna masu sujada, suka ce: "Mun yi imani da Ubangijin Haruna da Musa

    [71] Ya ce: "Kun yi imani saboda shi a gabanin in yi muku izni? Lalle shi, haƙiƙa, babbanku ne wanda ya sanar da ku sihirin! To, lalle ne zan kakkatse hannayenku da ƙafafunku a tarnaƙi kuma lalle zan tsire ku a cikin kututturan itacen dabino, kuma lalle za ku sani wanenmu ne mafi tsananin azaba kuma wane ne mafi wanzuwar (azaba)

    [72] Suka ce: "Ba za mu fifita ka ba faufau a kan abin da ya zo mana na hujjoji. Muna rantsuwa da wanda Ya ƙaga halittarmu sai ka hukunta abin da kake mai hukuntawa, ai kana ƙare wannan rayuwar duniya kawai ne

    [73] Lalle mu, mun yi imani da Ubangijinmu domin Ya gafarta mana laifuffukanmu da abin da ka tilasta mu a kansa na sihiri. Kuma Allah ne Mafi alheri, kumaMafi wanzuwa

    [74] Lalle shi wanda ya je wa Ubangijinsa yana mai laifi, to lalle ne yana da Jahannama, ba ya mutuwa a cikinta kuma ba ya rayuwa

    [75] Kuma wanda ya je Masa yana mai imani, alhali kuwaya aikata aikin ƙwarai to waɗannan suna da darajoji maɗaukaka

    [76] Gidajen Aljannar zama koguna na gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu. Kuma wannan ne sakamakon wanda ya tsarkaku

    [77] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun yi wahayi zuwa ga Musa cewa, "Ka yi tafiyar dare da bayiNa. Sa'an nan ka doka musu hanya a cikin teku tana ƙeƙasasshiya, ba ka tsoron riskuwa, kuma ba ka fargabar nutsewa

    [78] Sai Fir'auna ya bi su game da rundunarsa. Sai abin da ya rufe su daga teku ya rufe su

    [79] Kuma Fir'auna ya ɓatar da mutanensa, kuma bai shiryar (dasu) ba

    [80] Ya Bani Isra'ila! Lalle Mun tserar da ku daga maƙiyinku, kuma mun yi muku wa'adi a gefen Dutsen nan na dama, kuma Mun sassaukar da darɓa da tattabaru dominku

    [81] Ku ci daga masu daɗin abin da Muka azurta ku kuma kada ku ƙetare haddi a cikinsa har hushiNa ya sauka a kanku. Kuma wanda hushiNa ya sauka a kansa, to, lalle ne, ya faɗi

    [82] Kuma lalle Ni haƙiƙa Mai gafara ne ga wanda ya tuba kuma ya yi imani, kuma ya aikata aikin ƙwarai, sa'an nan kuma ya nemi shiryuwa

    [83] Kuma mene ne ya gaggautar da kai ga barin mutanenka? Ya Musa

    [84] Ya ce: "Su ne waɗannan a kan sawuna, kuma na yi gaggawa zuwa gare Ka, ya Ubangiji! Domin Ka yarda

    [85] Ya ce: "To, lalle ne, haƙiƙa, Mun fitini, mutanenka daga bayanka, kuma samiri ya ɓatar da su

    [86] Sai Musa ya koma zuwa ga mutanensa yana mai hushi, mai baƙin ciki, ya ce: "Ya mutanena! shin, Ubangijinku bai yi muku wa'adi ba, wa'adi mai kyau? Shin, lokacin ya yi tsawo a kanku ne, ko kun yi nufi ne wani hushi ya sauka a kanku daga Ubangijinku, saboda haka kuka saɓa wa alkawarina

    [87] Suka ce: "Ba mu saɓa wa alkawarinka ba da ikonmu kuma amma an ɗora mana waɗansu kaya masu nauyi daga abin ƙawar mutanen ne, sai muka jefar da su. Sa'an nan kamar haka ne samiri ya jefa

    [88] Sai ya fitar musu da wani maraƙi, jikin mutane, yana ruri, sa'an nan suka ce: wannan ne gunkinku kuma gunkin Musa, sai ya manta

    [89] Shin, to, ba su ganin cewaba ya mayar musu da magana, kuma ba ya mallakar wata cuta a gare su, kuma ba ya mallakar amfani

    [90] Kuma, haƙiƙa, Haruna ya ce musu daga gabani, "Ya mutanena! Lalle an fitine ku da shi ne kawai. Kuma lalle Ubangijinku Mai rahama ne, sai ku bi ni, kuma ku yi ɗa'a ga umurnina

    [91] Suka ce: "Ba za mu gushe ba faufau a kansa muna masu lazimta, sai Musa ya komo zuwa gare mu

    [92] (Musa) ya ce: "Ya Haruna! Me ya hane ka, sa'ad da kagan su sun ɓace

    [93] Ba ka bi ni ba! Shin, to, ka saɓa wa umurnina ne

    [94] (Haruna) ya ce: "Ya ɗan'uwana! Kada ka yi kamu ga gemuna ko ga kaina. Lalle ni, na ji tsoron ka ce: Ka rarraba a tsakanin Bani Isra'ila kuma ba ka tsare maganata ba

    [95] (Musa) ya ce: "Mene ne babban al'amarinka? Ya Samiri

    [96] (Samiri) ya ce: "Na ga abin da ba su gan shi ba shi, sai na yi damƙa, damƙa guda daga kufan sawun Manzon, sa'an nan na jefa ta. Kuma haka dai raina ya ƙawata mini

    [97] (Musa) ya ce: "To, ka tafi, saboda haka lalle ne kana da a cikin rayuwarka, ka ce 'Babu shafa' kuma kana da wani ma'alkawarta, ba za a saɓa maka gare ta ba. Kuma ka duba zuwa ga gunkinka wanda ka yini a kansa kana mai lazimta. Lalle ne muna ƙone shi, sa'an nan kuma muna sheƙe shi, a cikin teku, sheƙewa

    [98] Abin sani kawai abin bautawarku Allah kawai ne wanda babu wani abin bautawa, face Shi kuma Ya yalwaci dukkan kome da ilmi

    [99] Kamar wancan ne Muke labartawa a gare ka, daga labaran abin da ya gabata, alhali kuwa haƙiƙa, Mun ba ka zikiri (Alƙur'ani) daga gunMu

    [100] Wanda ya kau da kai daga gare shi, to, lalle shi, yanaɗaukar wani nauyi a Ranar ¡iyama

    [101] Suna madawwama a cikinsa, kuma ya munana ya zama abin ɗauka, a Ranar ¡iyama

    [102] A Ranar da ake hurawa a cikin ƙaho kuma Muna tara masu laifi, a ranar nan, suna masu shuɗayen idanu

    [103] Suna ɓoye magana a tsakaninsu, (Suna ce wa juna) "Ba ku zauna ba (a cikin duniya) face kwana goma

    [104] Mu ne mafi sani ga abin da suke faɗa a sa'ad da mafificinsu ga hanya ke cewa, "Ba ku zauna ba face a yini guda

    [105] Kuma suna tambayar ka daga duwatsu sai ka ce: "Ubangijina Yana sheƙe su sheƙewa

    [106] Sa'an nan Yana barin (wurinsu) faƙo mai santsi

    [107] Ba ka ganin karkata a cikinsa, kuma ba ka ganin wani tudu

    [108] A ranar nan suna biyar mai kira, babu karkata a gare shi, kuma sautuka suka yi kawaici ga Mai rahama, ba ka sauraren kome face sautin tafiya

    [109] A yinin nan ceto ba ya yin amfani face wanda Mai rahama Ya yi masa izni kuma Ya yarda da shi, da magan

    [110] Yana sanin abin da ke a gaba gare su da abin da ke bayansu, kuma ba su kewayewa da shi ga sani

    [111] Kuma fuskoki suka ƙanƙan da kai ga Rayayye, Tsayayye, alhali kuwa wanda ya ɗauko wani zalunci ya taɓe

    [112] Kuma wanda ya aikata wani abu daga ayyukan ƙwarai alhali kuwa yana mai imani, to, ba ya tsoron wani zalunci ko wata naƙasa

    [113] Kuma haka Muka saukar da shi, Alƙur'ani, yana abin karantawa, da Larabci kuma Muka jujjuya misalai, a cikinsa, na tsoratarwa, tsammaninsu, suna yin taƙawa ko ya sabbaba musu wata wa'aztuwa

    [114] Sa'an nan Allah Mamallaki, Tabbatacce Ya ɗaukaka. Kuma kada ka yi gaggawa da Alƙur'ani a gabanin a ƙare wahayinsa zuwa gare ka. Kuma ka ce: "Ya Ubangiji! Ka ƙara mini ilmi

    [115] Kuma lalle, haƙiƙa, Mun yi alkawari zuwa ga Adamu a gabanin wannan, sai ya manta, kuma ba Mu sami ƙarfin zuciya a gare shiba

    [116] Kuma sa'ad da Muka ce wa mala'iku, "Ku yi sujada ga Adamu." Sai suka yi sujada, face Iblisa, ya ƙiya

    [117] Sai Muka ce: "Ya Adamu! Lalle ne wannan maƙiyi ne gare ka da kuma ga matarka, saboda haka kada ya fitar da ku daga Aljanna har ku wahala

    [118] Lalle ne ka samu ba za ka ji yunwa ba a cikinta, kuma ba za ka yi tsiraici ba

    [119] Lalle kai, ba za ka ji ƙishirwa ba, kuma ba za ka shiga hantsi ba

    [120] Sai shaiɗan ya sanya waswasi zuwa gare shi, ya ce: "Ya Adamu! Shin, in shiryar da kai ga itaciyar dawwama da mulki wanda ba ya ƙarewa

    [121] Sai suka ci daga gare ta, saboda haka al'aurunsu suka bayyana, kuma suka shiga suna lulluɓawa a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Adamu ya saɓa wa Ubangijinsa, saboda haka ya ɓace

    [122] Sa'an nan kuma Ubangjinsa Ya zaɓe shi, Ya karɓi tuba gare shi, kuma Ya shiryar (da shi)

    [123] Ya ce: "Ku sauka ku biyu daga gare ta gaba ɗaya, sashenku yana maƙiyi ga sashe. To, imma dai wata shitiya ta je muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiryarwata, to, ba ya ɓacewa, kuma ba ya wahala

    [124] Kuma wanda ya bijire daga ambatoNa (Alƙur'ani) to, lalle ne rayuwa mai ƙunci ta tabbata a gare shi, kuma Muna tayar da shi a Ranar ¡iyama yana makaho

    [125] Ya ce: "Ya Ubangiji! Don me Ka tayar da ni makaho alhali kuwa na kasance mai gani

    [126] Ya ce: "Kamar wancan ne ayoyinMu suka je maka sai ka mance su, kuma kamar hakar a yau ake mance ka

    [127] Kuma kamar haka Muke saka wa wanda ya yawaita, kuma bai yi imani da ayoyin Ubangijinsa ba. Kuma lalle ne azabar Lahira ce mafi tsanani, kuma mafi wanzuwa

    [128] Shin, to, bai shiryar da su ba cewa da yawa Muka halakarda (kafirai) daga ƙarnuka, a gabaninsu, suna tafiya a cikin masaukansu? Lalle ne, a cikin wancan akwai ayoyi ga masu hankula

    [129] Kuma ba domin wata kalma ba wadda ta gabata daga Ubangijinka, da kuma ajali ambatacce haƙiƙa, da azabarta kasance mai lazimta

    [130] Sai ka yi haƙuri a kan abin da suke cewa, kuma ka yi tasbihi da gode wa Ubangijinka a gabanin fitowar rana da gabanin ɓacewarta, kuma daga sa'o'in dare sai ka yi tasbihi da sasannin yini, tsammaninka za ka sami yarda

    [131] Kuma kada ka miƙar da idanunka zuwa ga abin da Muka jiyar da su daɗi da shi, nau'i-nau'i daga gare su, kamar huren rayuwar duniya yake, domin Mu fitine su a cikinsa, alhali kuwa arzikin Ubangijinka, ne mafi alheri kuma mafi wanzuwa

    [132] Kuma ka umurci iyalanka da salla, kuma ka yi haƙuri a kanta. Ba Mu tambayar ka wani arziki Mu ne Muke azurta ka. Kuma aƙiba mai kyau tana ga taƙawa

    [133] Kuma suka ce: "Don me ba ya zo mana da wata aya daga Ubangijinsa?" Shin, kuwa hujjar abin da ke a cikin littattafan farko, ba ta je musu ba

    [134] Kuma da dai Mun halaka su da wata azaba daga gabaninsa, lalle ne da sun ce: "Ya Ubangijinmu! Da Ka aiko da wani Manzo zuwa gare mu har mu bibiyi ayoyinKa daga gabanin mu ƙasƙanta, kuma mu wulakantu

    [135] Ka ce: "Kowa mai tsumaye ne. Sai ku yi tsumaye. Sa'an nan za ku san su wa ne ma'abuta tafarki madaidaici, kuma wane ne ya nemi shiryuwa

    Anbiyã'u (Annabãwa)

    Surah 21

    [1] Hisabin mutane ya kusanta gare su, ahali kuwa suna a cikin gafala, suna masu bijirewa

    [2] Wani ambato daga Ubangijinsu sabo, ba ya zuwa gare su face sun saurare shi, alhali kuwa suna masu yin wasa

    [3] Sana masu shagaltacin zukatansu, kuma su asirta ganawa: Waɗanda suka yi zalunce (suna cewa) "Wannan ba Kowa ba ne face mutum misalinku. Shin, to, kuna je wa sihiri, ahali kuwa ku, kuna fahimta

    [4] Ya ce: "Ubangijina Yana sanin magana a cikin sama da ƙasa kuma Shi ne Mai ji, Masani

    [5] A'a, suka ce: "Yaye-yayen mafarki ne. A'a, ya ƙirƙira shi ne. A'a, shi mawaƙi ne. Sai ya zo mana da wata aya kamar yadda aka aiko manzanni na farko

    [6] Wata alƙarya da Muka halaka ta a gabaninsu, ba ta yi imani ba. Shin, to, su, suna yin imani

    [7] Kuma ba Mu aika ba a gabaninka face mazaje, Muna yin wahayi zuwa gare su. Ku tambayi ma'abuta ambato idan kun kasance ba ku sani ba

    [8] Kuma ba Mu sanya su jiki, ba su cin abin ci ba, kuma ba su kasance madawwama ba

    [9] Sa'an nan kuma Muka gaskata musu alkawari; sai Muka tserar da su da wanda Muke so, kuma Muka halakar da masu yawaitawa

    [10] Lalle haƙiƙa Mun saukar da wani littafi zuwa gare ku, a cikinsa akwai ambatonku. Shin, to, ba ku hankalta

    [11] Kuma da yawa Muka karya wata alƙarya ta kasance mai zalunci, kuma Muka ƙaga halittar waɗansu mutane na dabam a bayanta

    [12] Sai a lokacin da suka hangi azabarMu, sai ga su suna gudu daga gare ta

    [13] Kada ku yi gudu. Ku komo zuwa ga abin da aka ni'imtar da ku a cikinsa da gidajenku tsammaninku ana tambayar ku

    [14] Suka ce: "Kaitonmu! Lalle mu ne muka kasance masu zalunci

    [15] Sa'an nan waccan ba ta gushe ba, ita ce da'awarsu har Muka mayar da su girbabbu, bitattu

    [16] Kuma ba Mu halitta sama da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu Muna Masu wasa ba

    [17] Da Mun yi nufin Mu riƙi wani abin wasa da Mun riƙe shi daga gunMu, idan Mun kasance masu aikatawa

    [18] A'a, Muna jifa da gaskiya a kan ƙarya, sai ta darkake ta, sai ga ta halakakka. Kuma bone ya tabbata a gare ku saboda abin da kuke siffantawa

    [19] Kuma shi ne da mallakar wanda yake a cikin sammai da ƙasa. Kuma waɗanda suke wurinSa (watau mala'iku), ba su yin girman kai ga ibadarSa. kuma ba su gajiya

    [20] Suna tasbihi dare da rana, ba su yin rauni

    [21] Ko (kafirai) sun riƙi waɗansu abubuwan bautawa ne ga ƙasa, su ne masu tayarwa (gare su)

    [22] Da waɗansu abubuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) face Allah, haƙiƙa da su biyun sun ɓaci. Saboda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al'arshi daga abin da suke siffantawa

    [23] Ba a tambayar Sa ga abin da Yake aikatawa, alhali kuwa suana tambayar su

    [24] Ko sun riƙi waɗansu abubuwan bautawa baicinSa? Ka ce: "Ku kawo hujjarku, wannan shi ne ambaton wanda yake tare da ni, kuma shi ne ambaton wanda yake a gabanina. A'a, mafi yawansuba su sanin gaskiya, saboda haka su masu bijirewa ne

    [25] Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabaninka face Muna yin wahayi zuwa gare shi, cewa "Lalle ne Shi, babu abin bautawa face Ni, sai ku bauta Mini

    [26] Kuma suka ce: "Mai rahama ya riƙi ɗa." Tsarkinsa, ya tabbata! A'a, (mala'iku) bayi ne masu daraja

    [27] Ba su gabatarSa da magana, kuma su da umurninSa suke aiki

    [28] Yana sanin abin da yake gaba gare su da abin da yake a bayansu, kuma ba su yin ceto face ga wanda Ya yarda, kuma sumasu sauna ne saboda tsoronSa

    [29] Kuma wanda ya ce daga gare su, "Lalle ni abin bautawa ne baicinSa," to, wannan Muna saka masa da, Jahannama. Kamar haka Muke saka wa azzalumai

    [30] Shin kuma waɗanda suka kafirta ba, su gani da cewa lalle sammai da ƙasa sun kasance ɗinke, sai Muka buɗe su, kuma Muka sanya dukan kome mai rai daga ruwa? Shin, ba za su yi imani ba

    [31] Kuma Mun sanya tabbatattun duwatsu a cikin ƙasa domin kada ta karkata da su kuma Mun sanya ranguna, hanyoyi, a cikinsu (duwatsun), tsammaninsu suna shiryuwa

    [32] Kuma Mun sanya sama rufi tsararre, alhali kuwa su daga ayoyinta masu bijirewa ne

    [33] Kuma shi ne wanda Ya halitta dare da yini da rana da wata dukansu a cikin wani sarari suKe iyo

    [34] Kuma ba Mu sanya dawwama ga wani mutum ba, a gabaninka. Shin to idan ka mutu to su ne madawwama

    [35] Kowane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne. Kuma Muna jarraba ku da sharri da alheri domin fitina. Kuma zuwa gare Mu ake mayar da ku

    [36] Kuma idan waɗanda suka kafirta suka gan ka, ba su riƙon ka face da izgili (suna cewa), "Shin, wannan ne ke ambatar gumakanku?" Alhali kuwa su, ga ambatar Mai rahama, masu kafirta ne

    [37] An halitta mutum daga gaggawa, zan nuna muku ayoyiNa. Saboda haka kada ku nemiyin gaggawa

    [38] Kuma suna cewa, "A yaushe wannan wa'adi zai tabbata, idan kun kasance masu gaskiya

    [39] Da waɗanda suka kafirta suna sanin lokacin da ba su kange wuta daga fuskokinsu, kuma haka daga bayayyakinsu, alhali kuwa ba su zama ana taimakon su ba

    [40] A'a, tana je musu bisa ga auke sai ta ɗimautar da su, sa'an nan ba su iya mayar da ita, kuma ba su zama ana yi musu jinkiri ba

    [41] Kuma lalle ne, haƙiƙa, an yi izgili ga waɗansu Manzanni daga gabaninka, sai abin da suka kasance suna izgili da shi ya auku ga waɗanda suka yi izgilin daga gare su

    [42] Ka ce: "Wane ne yake tsare ku a dare da yini daga Mai rahama?" A'a, su masu bijirewa ne daga ambaton Ubangijinsu

    [43] Ko kuwa suna da waɗansu abubuwan bautawa waɗanda ke tsare su, daga gare Mu? Ba su iya taimakon kansu kuma ba su kasance ana abutar su ba daga gareMu

    [44] A'a, Mun yalwata wa waɗannan da ubanninsu ni'imarMu, har rayuwa ta yi tsawo a kansu. Shin, to, ba su ganin cewa lalle Mu, Muna je wa ƙasarsu, Muna rage ta daga sasanninta? Shin, to, su ne marinjaya

    [45] Ka ce: "Abin sani, ina yi muku gargaɗi kawai da wahayi," kuma kurma ba ya jin kira a lokacin da ake yi musu gargaɗi

    [46] Kuma haƙiƙa idan wata iska daga azabar Ubangiji ta shafe su, haƙiƙa suna cewa, "Ya kaitonmu! Lalle mu ne muka kasance masu zalunci

    [47] Kuma Muna aza ma'aunan adalci ga Ranar ¡iyama, saboda haka ba a zaluntar rai da kome. Kuma ko da ya kasance nauyin ƙwaya daga komayya ne Mun zo da ita. Kuma Mun isa zama Masu hisabi

    [48] Kuma lalle, haƙiƙa, Mun kawo wa Musa da Haruna Rarrabewa da haske da ambato ga masu aiki da taƙawa

    [49] Waɗanda suke tsaron Ubangijinsu a fake, alhali kuwa su, masu sauna ne daga Sa'a

    [50] Kuma wannan ambato ne mai albarka Mun saukar da shi. Shin, to, ku masu musu ne gare shi

    [51] Kuma lalle haƙiƙa Mun kawo wa Ibrahim shiryuwarsa daga gabani, kuma Mun kasance Masana gare shi

    [52] Ya ce wa ubansa da mutanensa, "Mene ne waɗannan mutummutumai waɗanda kuke masu lazimta a kansu

    [53] Suka ce: "Mun sami Ubanninmu masu lazimta a kansu

    [54] Ya ce: "Lalle, haƙiƙa, kun kasance ku da Ubanninku a cikin ɓata bayyananna

    [55] Suka ce: "Shin ka zo mana da gaskiya ne, Ko kuwa kai kana daga maSu wasa ne

    [56] Ya ce: "A'a, Ubangijinku Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa, wanda Ya ƙaga halittarsu. Kuma Ni ina daga masu shaida a kan haka

    [57] Kuma ina rantsuwa da Allah, lalle zan yi wani shiri ga gumakanku a bayan kun juya kuna masu bayar da baya

    [58] Sai ya sanya su guntu-guntu face wani babba gare su, tsammaninsu suna Komawa zuwa gare shi

    [59] Suka ce: "Wane ne ya aikata wannan ga gumakanmu? Lalle shi, haƙiƙa, yana daga azzalumai

    [60] Suka ce: "Mun ji wani saurayi yana ambatar su. Ana ce masa Ibrahim

    [61] Suka ce: "To, ku zo da shi a kan idanun mutane, tsammanin su za su bayar da shaida

    [62] Suka ce: "Shin kai ne ka aikata wannan ga gumakanmu? Ya Ibrahim

    [63] Ya ce: "A'a, babbansu, wannan, shi ya aikata, shi. Sai ku tambaye su idan sun kasance suna yin magana

    [64] Sai suka koma wa junansu suka ce: "Lalle ne ku, ku ne azzalumai

    [65] Sa'an nan kuma aka sunkuyar da su a kan kawunansu (sukace,) "Lalle, haƙiƙa, ka sani waɗannan ba su yin magana

    [66] Ya ce: "Shin to, kuna bauta wa abin da, ba ya, amfanin ku da Kome kuma ba ya cutar da ku baicin Allah

    [67] Tir da ku, kuma da abin da kuke bauta wa, baicin Allah! Shin to, ba ku hankalta

    [68] Suka ce: "Ku ƙone shi kuma ku taimaki gumakanku, idan kun kasance masu aikatawa

    [69] Muka ce: "Ya wuta! Ki kasance sanyi da aminci ga Ibrahim

    [70] Kuma suka yi nufin wani mugun shiri da shi, sai Mukasanya su mafiya hasara

    [71] Kuma Muka tserar da shi da Luɗu zuwa ga ƙasar nan wadda Muka sanya albarka a cikinta ga talikai

    [72] Kuma Muka ba shi Is'haka da Ya'aƙuba a kan daɗi alhali kuwa dukansu Mun sanya su salihai

    [73] Kuma Muka sanya su shugabanni, suna shiryarwa da umurninMu. Kuma Muka yi wahayi zuwa gare su da ayyukan alheri da tsayar da salla da bayar da zakka. Kuma sun kasance masu bauta gare Mu

    [74] Kuma Luɗu Mun ba shi hukunci da ilmi. Kuma Mun tsirar da shi daga alƙaryar nan wadda ke aikata munanan ayyuka. Lallesu, sun kasance mutanen mugun aiki, fasiƙai

    [75] Kuma Muka shigar da shi a cikin rahamarMu. Lalle ne shi, yana daga salihai

    [76] Kuma Nuhu, a sa'ad da ya yi kira a gabani, sai Muka karɓa masa, sa'an nan Muka tsirar da shi da mutanensa daga baƙin ciki mai girma

    [77] Kuma Muka taimake shi daga mutanen nan waɗanda suka ƙaryata da ayoyinMu. Lalle ne su, sun kasance mutanen mugun aiki. Sai Muka nutsar da su gaba ɗaya

    [78] Kuma Dawuda da Sulaiman sa'ad da suke yin hukunci a cikin sha'anin shuka a lokacin da tumakin mutane suka yi kiiwon dare a cikinsa. Kuma Mun kasance Masu halarta ga hukuncinsu

    [79] Sai Muka fahimtar da ita (mats'alar) ga Sulaiman. Kuma dukansu Mun ba su hukunci da ilmi kuma Muka hore duwatsu tare da Dawuda, suna tasbihi, da tsuntsaye. Kuma Mun kasance Masu aikatawa

    [80] Kuma Muka sanar da shi sana'ar wata tufa saboda ku domin ya tsare ku daga makaminku. To, shin, ku masu godewa ne

    [81] Kuma (Muka hore) wa Sulaiman iska mai tsananin bugawa, tana gudana da umuruinsa zuwa ga ƙasar nan wadda Muka sanya albarka a cikinta. Kuma Mun kasance Masana ga dukkan Kome

    [82] Kuma daga Shaiɗannu (Mun hore) wanda ke nutso saboda shi. Kuma suna yin wani aiki baicin wancan. Kuma Mun kasance Masu tsaro a gare su

    [83] Kuma da Ayyuba a sa'ad da ya yi kiran Ubangijinsa, (ya ce:) "Lalle ni, cuta ta shafe ni, alhali kuwa Kai ne Mafi rahamar masu rahama

    [84] Sai Muka karɓa masa, sa'an nan Muka kuranye abin da ke a gare shi na cuta, kuma Muka kawo masa mutanesa da kwatank wacinsu tare da su, saboda rahama daga wurinMu da tunatarwa ga masu ibada

    [85] Kuma da Ismaila da Idrisa da Zulkifli, dukansu suna daga masu haƙuri

    [86] Kuma Muka shigar da su a cikin rahamarMu. Lalle ne, suna daga salihai

    [87] Kuma mai kifi a sa'ad da ya tafi yana mai hushi, sai ya yi zaton cewa ba za Mu ƙuƙunta masa ba. Sai ya yi kira a cikin duffai cewa, "Babu abin bautawa face Kai. Tsarki ya tabbata a gare Ka. Lalle ne ni, na kasance daga azzalumai

    [88] Sai Muka karɓa masa kuma Muka tsirar da shi daga baƙin ciki. Kamar haka ne Muke tsirarda masu imani

    [89] Kuma da Zakariyya a sa'ad da ya kirayi Ubangijinsa cewa, "Ya Ubangiji! Kada Ka bar ni makaɗaici alhali kuwa Kai ne Mafi alherin masu gado

    [90] Sai Muka karɓa masa kuma Muka kyautata masa matarsa. Lalle ne su, sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri. Kuma suna kiran Mu a kan kwaɗayi da fargaba. Kuma sun kasance masu saunar (aikata saɓo) gare Mu

    [91] Kuma da wadda ta tsare farJinta daga alfasha. Sai Muka hura a cikinta daga ruhinMu. Kuma Muka sanya ta ita da ɗanta wata aya ga duniya

    [92] Lalle ne wannan ita ce al'ummarku ta zama al'umma guda, kuma Ni ne Ubangijinku. Sai ku bauta Mini

    [93] Kuma suka kakkatse al'amarinsu a tsakaninsu. Dukan Kowanensu masu Komowa zuwa gare Ni

    [94] Domin wanda ya aikata daga ayyukan kwarai alhali kuwa yana mai imani, to, babu musu ga aikinsa, kuma Mu Masu rubutawa gare shi ne

    [95] Kuma hananne ne a kan wata alƙarya da Muka halakar cewa lalle su, ba su komowa

    [96] Har sa'ad da aka bude Yajuju da Majuju alhali kuwa suna gaggawa daga kowane tudun ƙasa

    [97] Kuma wa'adin nan tabbatacce ya kusanto, sai ga ta idanun waɗanda suka kafirta suna bayyanannu, (suna cewa), "Ya kaitonmu! Haƙiƙa mun kasance a cikin gafala daga wannan! A'a, mun kasance dai masu zalunci

    [98] (A ce musu) "Lalle ne, ku da abin da kuke bautawa, baicin Allah makamashin Jahannama ne. Ku masu tusgawa gare ta ne

    [99] Da waɗannan (abubuwanbautawar) sun kasance abubuwan bautawar gaskiya ne, da ba su tusga mata ba, alhali kuwa dukansu madawwama a cikinta ne

    [100] Suna da wata hargowa a cikinta, alhali kuwa su, a cikinta, ba su sauraren kome

    [101] Lalle ne waɗanda kalmar yabo ta gabata a gare su daga gare Mu, waɗannan waɗanda ake nisantarwa daga barinta ne

    [102] Ba su jin sautin motsinta alhali kuwa su madawwamane a cikin abin da rayukansu suka yi marmarinsa

    [103] Firgitar nan mafi girma, ba za ta baƙanta musu rai ba. Kuma mala'iku na yi musu maraba (suna cewa) "Wannan yininku ne wanda kuka kasance ana yi muku wa'adi da shi

    [104] A ranar da Muke naɗe sama kamar neɗewar takarda ga abubuwan rubutawa kamar yadda Muka fara a farKon halitta Muke mayar da ita. Wa'adi ne a Kanmu. Lalle ne Mun kasance Masu aikatawa

    [105] Kuma lalle haƙiƙa Mun rubuta a cikin Littafi baicin Ambato (Lauhul Mahfuz) cewa ƙasa, bayiNa salihai, suna gadonta

    [106] Lalle ne a cikin wannan (Alƙur'ani), haƙiƙa, akwai iyarwa (ga maganar da ta gabata ga waɗansu mutane masu ibada)

    [107] Kuma ba Mu aike ka ba face domin wata rahama ga talikai

    [108] Ka ce: "Abin sani kawai, ana yin wahayi zuwa gare ni ne, cewa, lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa ne Guda. To shin ku masu miƙa wuya ne

    [109] Sa'an nan idan suka juya, to, ka ce: "Na sanar da ku, a kan daidaita, kuma ban sani ba, shin, abin da ake yi muku wa'adi makusanci ne Ko kuwa manisanci

    [110] Lalle ne Shi (Allah) Yana sanin bayyane daga magana, kuma Yana sanin abin da kuke ɓoyewa

    [111] Kuma ban sani ba, tsammaninsa ya zama fitina a gare ku, ko kuma don jin daɗi, zuwa ga wani ɗan lokaci

    [112] Ya ce: "Ya Ubangiji! Ka yi hukunci da gaskiya. Kuma Ubangijinmu Mai rahama ne Wanda ake neman taimakonSa a kan abinda kuke siffantawa

    Hajji

    Surah 22

    [1] Ya ku mutane! Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Lalle ne girgizar ƙasa ta tsayuwar Sa'a wata aba ce mai girma

    [2] A ranar da kuke ganin ta dukan mai shayar da mama tana shagala daga abin da ta shayar, kuma dukan mai ciki tana haihuwar cikinta, kuma kana ganin mutane suna masu maye alhali kuwa su ba masu maye ba, amma azabar Allah ce mai tsanani

    [3] Akwai daga mutane wanda yake yin musu ga sha'anin Allah ba da wani ilmi ba, kuma yana biyar kowane Shaiɗan mai taurin kai

    [4] An wajabta masa cewa wanda ya jiɓince shi, to, lalle ne sai ya ɓatar da shi, kuma ya shiryar da shi zuwa ga azabar sa'ir

    [5] Ya ku mutane! Idan kun kasance a cikin shakka a Tashin ¡iyama, to, lalle ne Mu, Man halittaku daga turɓaya, sa'an nan kuma daga gudajin jini, sa'an nan kuma daga taoka wadda ake halittawa da wadda ba a halittawa domin, Mu bayyana muku. Kuma Muna tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sa'an nan kuma Muna fitar da ku kuna jariri, sa'an nan kuma domin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rayuwa domin kada ya san kome a bayan ya sani. Kuma kana ganin ƙasa shiru, sa'an nan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kowane nau'i mai ban sha'awa

    [6] Wancan ne domin lalle Allah Shi ne Gaskiya, kuma lalle ne shi Yake rayar da matattu, kuma lalle Shi Mai ikon yi ne a kan kome

    [7] Kuma lalle ne Sa'ar Tashin ¡iyama mai zuwa ce, babu shakka a cikinta kuma lalle ne Allah Yana tayar da waɗanda suke a cikin ƙaburbura

    [8] Kuma daga mutane akwai mai yin musu ga Allah ba da wani ilmi ba kuma ba da wata shiriya ba, kuma ba da wani littafi mai haskakawa ba

    [9] Yana mai karkatar da sashensa domin ya ɓatar (da wasu) daga tafarkin Allah! Yana da wani wulakanci a duniya, kuma Muna ɗanɗana masa azabar gobara a Ranar ¡iyama

    [10] (A ce masa): "Wancan azaba saboda abin da hannayenka biyu suka gabatar ne, kuma lalle ne Allah bai zama Mai zalunci ga bayinSa ba

    [11] Kuma daga mutane akwai mai bauta wa Allah a kan wani gefe. Sa'an nan idan wani alheri ya same shi, sai ya natsu da shi, kuma idan wata fitina ta same shi, sai ya juya baya a kan fuskarsa. Ya yi hasarar duniya da Lahira. Waccan ita ce hasara bayyananna

    [12] Yana kiran baicin Allah, abin da ba ya cutarsa da abin da ba ya amfaninsa! waccan ita ce ɓata mai nisa

    [13] Yana kiran wanda yake lalle cutarwarsa ce mafi kusa daga amfaninsa! Lalle ne, tir da shi ya zama majiɓinci, kuma tir da ya zama abokin zama

    [14] Lalle ne Allah Yana shigar da waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai a cikin gidajen Aljanna, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu. Lalle ne Allah Yana aikata abin da Yake nufi

    [15] Wanda ya kasance yana zaton cewa Allah ba zai taimake shi ba a cikin duniya da Lahira to sai ya miƙa wata igiya zuwa sama, sa'an nan kuma ya yanke ta, sa'an nan ya duba. Shin, ko lalle kaidinsa zai gusar da abin da yake ji na takaici

    [16] Kuma kamar haka Muka saukar da shi (Alƙur'ani) yana ayoyi bayyanannu. Kuma lalle ne Allah Yana shiryar da wanda Yake nufi

    [17] Lalle ne waɗanda suka yi imani da waɗanda suka tuba (Yahudu) da waɗanda suka karkace (Saba'awa) da Nasara da Majusawa da waɗanda suka yi shirka, lalle ne Allah Yana yin hukunci a tsakaninsu a Ranar ¡iyama. Lalle ne Allah Mahalarci ne a kan dukkan kome

    [18] Ashe, ba ka gani ba, lalle Allah, wanda yake a cikin sammai da wanda yake a cikin ƙasa yana yin sujada a gare shi, da kuma rana da wata da taurari da duwatsu da itace da dabbobi, da kuma masu yawa daga mutane? Kuma waɗansu masu yawa azaba ta tabbata a kansu. Kuma wanda Allah Ya wulakantar, to, ba ya da wani mai girmamawa. Kuma Lalle ne Allah Yana aikata abin da Yake so

    [19] waɗannan ƙungiyoyi biyu ne masu husuma, sun yi husuma ga sha'anin Ubangijinsu. To, waɗanda suka kafirta an yanka musu waɗansu tufafi daga wata irin wuta, ana zuba tafasasshen ruwa daga bisa kawunansu

    [20] Da shi ake narkar da abin da yake a cikin cikunansu da fatun jikinsu

    [21] Kuma suna da waɗansu gwalmomin duka na baƙin ƙarfe

    [22] A koyaushe suka yi nufin fita daga gare ta, daga baƙin ciki, sai a mayar da su a cikinta, (a ce musu) "Ku ɗanɗani azabar gobara

    [23] Lalle ne, Allah Yana shigar da waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai a cikin gidajen Aljanna, ƙoramu suna gudana daga ƙarƙashinsu, ana ƙawata su, a cikinsu, da waɗansu mundaye na zinari da lu'u-lu'u. Kuma tufafinsu a cikinsu alharini ne

    [24] Kuma an shiryar da su zuwa ga mai kyau na zance kuma an shiryar da su zuwa ga, hanyar wanda ake gode wa

    [25] Lalle ne waɗanda suka kafirta kuma suka taushe (mutane) daga hanyar Allah da masallaci mai alfarma wanda Muka sanya shi ga mutane alhali kuwa mazauni a ciki da baƙauye daidai suke kuma wanda ya yi nufin karkatar da gaskiya a cikinsa da zalunci za Mu ɗanɗana masa daga wata azaba mai raɗadi

    [26] Kuma a lokacin da Muka iyakance wa Ibrahim wurin ¦akin (Muka ce masa), "Kada ka haɗa kome da Ni ga bauta, kuma ka tsarkake ¦akiNa domin masu ɗawafi da masu tsayuwa da masu ruku'u da masu sujada

    [27] Kuma ka yi yekuwa ga mutane da wajabcin Hajji su je maka suna masu tafiya da ƙafafu da kuma a kan kowane maɗankwarin raƙumi masu zuwa daga kowane rango mai zurfi

    [28] Domin su halarci abubuwan amfani a gare su, kuma su ambaci sunan Allah a cikin 'yan kwanuka sanannu saboda abin da Ya azurta su da shi daga dabbobin jin daɗi. Sai ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da matsattse matalauci

    [29] Sa'an nan kuma sai su ƙare ibadarsu da gusar da ƙazanta, knma sai su cika alkawuransu kuma sai su yi ɗawafi (suna gewaya) ga ¦akin nin 'yantacce

    [30] Wancan ne. Kuma wanda ya girmama hukunce-hukuncen Allah to shi ne mafifici a gare shi, a wurin Ubangijinsa. Kuma an halatta muku dabbobin ni'ima face abin da ake karantawa a kanku. Saboda haka ku nisanci ƙazanta daga gumaka kuma ku nisanci ƙazanta daga shaidar zur

    [31] Kuna masu tsayuwa ga gaskiya domin Allah, ba masu yin shirka da Shi ba. Kuma wanda ya yi shirka da Allah, to, yana kamar abin da ya faɗo daga sama, sa'an nan tsuntsaye su cafe shi, ko iska ta faɗa da shi a cikin wani wuri mai nisa

    [32] Wancan ne. Kuma wanda ya girmama ibadodin Allah, to, lalle ne ita (girmamawar) tana daga ayyukan zukata na ibada

    [33] Kuna da waɗansu abubuwan amfani a cikinta (dabbar hadaya) har ya zuwa ga wani ajali ambatacce, sa'an nan kuma wurin halattata zuwa ga ¦akin 'yantacce ne

    [34] Kuma ga kowace al'umma Mun sanya ibadar yanka, domin su ambaci sunan Allah a kan abin da Ya azurta su da shi daga dabbobin ni'ima. Sa'an nan kuma Abin bautawarku Abin bautawa ne Guda, sai ku sallama Masa. Kuma ka yi bushara ga masu ƙanƙantar da kai

    [35] Waɗanda suke idan an ambaci Allah sai zukatansu su firgita, da masu haƙuri a kan abin da ya same su, da masu tsayar da salla, kuma suna ciyarwa daga abin da Muka azurta su

    [36] Kuma raƙuman, Mun sanya su a gare ku, a ibadojin Allah. Kuna da wani alheri babba a cikinsu. Sai ku ambaci sunan Allah a kansu suna tsaye a kan ƙafafu uku. Sa'an nan idan sasanninsu suka faɗi, to, ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da mai wadar zuci da mai bara. Kamar haka Muka hore muku su, tsammaninku kuna godewa

    [37] Namominsu ba za su sami Allah ba haka jinainansu amma taƙawa daga gare ku tana, samun Sa. Kamar haka Ya hore su saboda ku domin ku girmama Allah saboda shiriyar da Ya yi muku. Kuma ka yi bushara ga masu kyautata yi

    [38] Lalle ne, Allah Yana yin faɗa saboda waɗanda suka yi imani. Lalle ne Allah ba Ya son dukkan mayaudari, mai yawan kafirci

    [39] An yi izni ga waɗanda ake yaƙar su da cewa lalle an zalunce su, kuma lalle ne Allah, haƙiƙa, Mai ikon yi ne a kan taimakonsu

    [40] Waɗanda aka fitina daga gidajensu ba da wani hakki ba face suna cewa, Ubangijinmu Allah ne."Kuma ba domin tunkuɗewar Allah ga mutane ba, sashensu da sashe, haƙiƙa, da an rusa sauma'o'in (Ruhbanawa) da majami'o'in Nasara da gidajen ibadar Yahudu da masallatai waɗanda ake ambatar Allah a cikinsu da yawa. Kuma lalle, haƙiƙa, Allah Yana taimakon wanda yake taimakon Sa. Lalle Allah ne haƙiƙa Mai ƙarfi Mabuwayi

    [41] Waɗanda suke idan Muka ba su iko a cikin ƙasa sai su tsai da salla, kuma su baybr da zakka kuma su yi umurni da abin da aka sani, kuma su hana daga abin da ba a sani ba. Kuma aƙibar al'amura ga Allah take

    [42] Kuma idan sun ƙaryata ka, to lalle haƙiƙa, mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa, sun ƙaryata a gabaninsu

    [43] Da mutanen Ibrahim da mutanen Luɗu

    [44] Da masu Madyana, kuma an ƙaryata Musa. Sai Na jinkirtawa kafiran, sa'an nan kuma Na kama su. To, yaya musuNa (gare su) ya kasance

    [45] Sa'an nan da yawa daga alƙarya, Muka halaka ta, alhali kuwa tana mai zalunci sai ta zama faɗaɗɗa a kan rassanta, da yawa daga rijiya wadda aka wofintar, da kuma gidajen sarauta maɗaukaka

    [46] Shin, to, ba su yi tafiya ba a cikin ƙasa domin zukata waɗanda za su yi hankali da su da kunnuwa da za su yi saurare da su su kasance a gare su? Domin lalle ne idanun ba su makanta, amma zukata waɗanda ke a cikin ƙiraza su ke makanta

    [47] Kuma suna neman ka yi gaggawa da azaba, alhali kuwa Allah ba zai saɓa wa'adinSa ba kuma lalle ne, yini ɗaya a wurin Ubangijinka kamar shekara dubu yake daga abin da kuke ƙidayawa

    [48] Kuma da yawa daga alƙarya, Na yi jinkirin azaba gare ta (da laifinta) sa'an nan Na kama ta, kuma zuwa gare Ni makoma take

    [49] Ka ce: "Ya ku mutane! Ni wani mai gargaɗi ne kawai zuwa gare ku, mai bayyanawa

    [50] To, waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyuka na ƙwarai, suna da gafara da arziki na karimci

    [51] Kuma waɗanda suka yi aikin ɓatawa a cikin ayoyinMu, suna masu gajiyarwa, waɗancan 'yan Jahim ne

    [52] Kuma ba Mu aika wani manzo ba a gabaninka, kuma ba Mu umurci wani Annabi ba face idan ya yi buri, sai Shaiɗan ya jefa (wani abu) a cikin burinsa, sa'an nan Allah Ya shafe abin da Shaiɗan ke jefawa. Sa'an nan kuma Allah Ya kyautata ayoyinSa. Kuma Allah Masani ne, Mai hikima

    [53] Domin Ya sanya abin da Shaiɗan ke jefawa ya zama fitina ga waɗanda a cikin zukatansu akwai cuta, da masu ƙeƙasassun zukatansu. Kuma lalle ne azzalumai haƙiƙa, suna a cikin saɓanimai nisa

    [54] Kuma domin waɗanda aka bai wa ilmi su sani lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinka domin su yi imani da shi saboda zukatansu su natsu gare shi. Kuma lalle ne Allah, haƙiƙa, Mai shiryar da waɗanda suka yi imani ne zuwa ga hanya madaidaiciya

    [55] Kuma waɗanda suka kafirta ba za su gushe ba suna a cikin shakka daga gare shi, har Sa'a ta je musu bisa ga abke, ko kuwa azabar wani yini bakarare ta je musu

    [56] Mulki a ranar nan ga Allah yake, Yana hukunci a tsakaninsu. To, waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, suna a cikin gidajen Aljannar ni'ima

    [57] Kuma waɗandra suka kafirta kuma suka ƙaryata, game da ayoyinMu, to, waɗannan suna da azaba mai wulakantarwa

    [58] Kuma waɗanda suka yi hijira a cikin tafarkin Allah sa'an nan kuma aka kashe su, ko suka mutu, lalle ne Allah Yana azurta su da arziki mai kyau. Kuma lalle ne Allah, haƙiƙa, Shi ne Mafi alherin masu azurtawa

    [59] Lalle ne, Yana shigar da su a wata mashiga wadda za su yarda da ita. Kuma lalle ne Allah, haƙiƙa Masani ne, Mai haƙuri

    [60] Wancan! Kuma wanda ya rama azaba da misalin abin da aka yi masa, sa'an nan kuma aka zalunce shi, lalle ne Allah Yana taimakon sa. Lalle ne Allah haƙiƙa Mai yafewa ne, Mai gafara

    [61] Wancan! saboda Allah Yana shigar da dare a cikin yini, kuma Yana shigar da yini a cikin dare, kuma lalle, Allah Mai ji ne, Mai gani

    [62] Wancan! saboda lalle ne Allah, shi ne Gaskiya, kuma lalle ne, abin da suke kira waninSa shi ne ƙarya. Kuma lalle ne Allah, Shi ne Maɗaukaki, Mai girma

    [63] Ashe, ba ka gani ba, lalle ne, Allah Ya saukar da ruwa daga sama, sai ƙasa ta wayi gari koriya? Lalle Allah Mai tausasawa ne, Mai ƙididdigewa

    [64] Abin da ke a cikin sammai, da abin da ke a cikin ƙasa, Nasa ne, kuma lalle ne Allah, haƙiƙa, Shi ne wadatacce, Godadde

    [65] Shin ba ka gani ba, lalle ne Allah Ya hore muku abin da yake a cikin ƙasa, kuma jirage suna gudana a cikin teku, da umurninSa kuma Yana riƙe sama domin kada ta faɗi a kan ƙasa face da izninsa? Lalle ne Allah ga mutane haƙiƙa, Mai tausayi ne, Mai jin ƙai

    [66] Kuma shi ne wanda Ya raya ku, sa'an nan kuma Yana matar da ku, sa'an nan kuma Yana rayar da ku. Lalle mutum, haƙiƙa, mai kafirci ne

    [67] Ga kowace al'umma Mun sanya wurin yanka, su ne masu yin baiko gare Shi, saboda haka, kada su yi maka jayayya a cikin al'amarin (hadaya). Kuma ka yi kira zuwa ga Ubangijinka lalle kai kana a kan shiriya madaidaiciya

    [68] Kuma idan sun yi maka jidali, sai ka ce: "Allah ne Mafi sani game da abin da kuke aikatawa

    [69] Allah ne zai yi hukunci a tsakaninku, a Ranar ¡iyama a cikin abin da kuka kasance a cikinsa kuna saɓawa juna

    [70] Ashe, ba ka sani ba, lalle ne Allah Yana sanin abin da yake a cikin sama da ƙasa? Lalle ne wancan yana cikin Littafi lalle wancan ga Allah mai sauƙi ne

    [71] Kuma suna bautawa baicin Allah, abin da (Allah) bai saukar da wani dalili ba game da shi, kuma abin da ba su da wani ilmi game da shi, kuma babu wani mai taimako ga azzalumai

    [72] Kuma idan ana karanta ayoyinMu bayyanannu a kansu kana sanin abin ƙyama a cikin fuskokin waɗanda suka kafirta suna kusa su yi danƙa ga waɗanda ke karatun ayoyinMu a kansu. Ka ce: "Shin to in gaya muku abin da yake mafi sharri daga wannan? (Ita ce) Wuta." Allah Ya yi alkawarinta ga waɗanda suka kafirta. Kuma makomarsu ta munana

    [73] Ya ku mutane! An buga wani misali, sai ku saurara zuwa gare shi. Lalle ne waɗanda kuke kira baicin Allah, ba za su halitta ƙuda ba, ko da sun taru gare shi, kuma idan ƙudan ya ƙwace musu wani abu, ba za su kuɓutar da shi ba daga gare shi. Mai nema da wanda ake neman gare shi sun raunana

    [74] Ba su ƙaddara wa Allah hakkin girmanSa ba. Lalle ne Allah, haƙiƙa, Mai ƙarfi ne, Mabuwayi

    [75] Allah na zaɓen Manzanni daga mala'iku kuma daga mutane. Lalle Allah, Mai ji ne, Mai gani

    [76] Yana sanin abin da ke gaba gare su da abin da ke bayansu, kuma zuwa ga Allah ake mayar da al'amura

    [77] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yi ruku'i, kuma ku yi sujada, kuma ku bauta wa Ubangijinku, kuma ku aikata alheri, tsammaninku, ku sami babban rabo

    [78] Kuma ku yi jihadi a cikin (al'amarin) Allah, hakkin JihadinSa. shi ne Ya zaɓe ku alhali kuwa bai sanya wani ƙunci ba a kanku a cikin addini. Bisa ƙudurcewar ubanku Ibrahim, shi ne ya yi muku suna Musulmi daga gabanin haka. Kuma a cikin wannan (Littafi ya yi muku suna Musulmi), domin Manzo ya kasance mai shaida a kanku, ku kuma ku kasancemasu shaida a kan mutane. Saboda haka ku tsayar da salla kuma ku bayar da zakka kuma ku amince da Allah, Shi ne Majiɓincinku. Saboda haka madalla da Shi Ya zama Majiɓinci, madalla da Shi ya zama Mai taimako

    Muminina

    Surah 23

    [1] Lalle ne, Muminai sun sami babban rabo

    [2] Waɗanda suke a cikin sallarsu masu tawali'u ne

    [3] Kuma waɗanda suke, sudaga barin yasassar magana, masu kau da kai ne

    [4] Kuma waɗanda suke ga zakka masu aikatawa ne

    [5] Kuma waɗanda suke ga farjojinsu masu tsarewa ne

    [6] Face a kan matan aurensu, ko kuwa abin da hannayen damansu suka mallaka to lalle su ba waɗanda ake zargi, ba, ne

    [7] Saboda haka wanda ya nemi abin da ke bayan wancan, to, waɗancan su ne masu ƙetarewar haddi

    [8] Kuma waɗanda suke, suga amanoninsu da alkawarinsu masu tsarewa ne

    [9] Kuma da waɗanda suke, su a kan sallolinsu suna tsarewa

    [10] Waɗannan, su ne magada

    [11] Waɗanda suke gadon (Aljannar) Firdausi, su a cikinta madawwama ne

    [12] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga laka

    [13] Sa'an nan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya

    [14] Sa'an nan kuma Muka halitta shi gudan jini, sa'an nan Muka halitta gudan jinin tsoka, sa'an nan Muka halitta tsokar ta zama ƙasusuwa, sa'an nan Muka tufatar da ƙasusuwan da wani nama sa'an nan kuma Muka ƙaga shi wata halitta dabam. Saboda haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyaun masu halittawa

    [15] Sa'an nan kuma ku, bayan wannan, lalle ne masu mutuwa ne

    [16] Sa'an nan kuma lalle ne ku a Ranar ¡iyama, za a iayar da ku

    [17] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun halitta, a samanku, hanyoyi bakwai, kuma ba Mu kasance, daga barin halittar, Masu shagala ba

    [18] Muka saukar da ruwa daga sama bisa gwargwado, sa'an nan Muka zaunar da shi a cikin ƙasa alhali, lalle ne Mu, a kan tafiyar da shi, Masu iyawa ne

    [19] Sai Muka ƙaga muku, game da shi (ruwan), gonaki daga dainai da inabobi, kuna da, a cikinsu, 'ya'yan itacen marmari masu yawa, kuma daga gare su kuke ci

    [20] Da wata itaciya, tana fita daga dutsin Saina'a, tana tsira da man shafawa, da man miya domin masu ci

    [21] Kuma lalle ne kuna da abin lura a cikin dabbobin ni'imomi Muna shayar da ku daga abin da yake a cikinsu, kuma kuna da a cikinsu abubuwan amfani masu yawa, kuma daga gare su kuke ci

    [22] Kuma a kansu da a kan jirgin ruwa ake ɗaukar ku

    [23] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautawa waninsa. Shin, to, ba za ku yi taƙawa ba

    [24] Sai mashawarta waɗanda suka kafirta daga mutanensa, suka ce: "Wannan ba kowa ba ne, face mutum misalinku, yana nufin ya ɗaukaka a kanku. Da Allah Ya so, lalle ne da Ya saukar da Mala'iku, Ba muji (kome) ba, game da wannan, a cikin ubanninmu na farko

    [25] Shi bai zamo kowa ba face wani namiji ne, a gare shi akwai hauka, sai ku yi jinkiri da shi har wani lokaci

    [26] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka taimakeni saboda sun ƙaryatani

    [27] Sai Muka yi wahayi zuwa gare shi. "Ka sana'anta jirgin bisa ga idonMu, da wahayinMu. To, idan umuminMu ya je, kuma tanda ta ɓuɓɓuga da ruwa, to, ka shigar a cikinta daga kome, ma'aura biyu, da iyalanka, sai wanda Magana ta gabata a kansa, daga gare su, kuma kada ka roƙe Ni (saboda wani) a cikin waɗanda suka yi zalunci, lalle ne su waɗanda ake nutsarwa ne

    [28] Sa'an nan idan ka daidaitu kai da waɗanda ke tare da kai a kan jirgin, sai ka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya tsirar damu daga mutane azzalumai

    [29] Kuma ka ce: 'Ya Ubangijina! Ka saukar da ni, saukarwa mai albarka. Kuma Kai ne Mafi alherin masu saukarwa

    [30] Lalle ne a cikin wancan akwai ayoyi, ko da yake Mun kasance, haƙeƙa' Masu jarrabawa

    [31] Sa'an nan kuma Muka ƙaga wani ƙarni na waɗansu dabam daga bayansu

    [32] Sai Muka aika a cikinsu Manzo daga gare su. "Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautawa, sai Shi. Shin to, ba za ku yi taƙawa ba

    [33] Mashawarta daga mutanensa, waɗanda suka kafirta kuma suka ƙaryata game da haɗuwa da Lahira, kuma Muka ni'imtar da su a cikin rayuwar duniya, suka ce: "Wannan ba kowa ba face wani mutum ne kamarku, yana ci daga abin da kuke ci daga gare shi, kuma yana sha daga abin da kuke sha

    [34] Kuma lalle ne idan kun yi ɗa' a ga mutum misalinku, lalle ne, a lokacin nan, haƙiƙa, ku masu hasara ne

    [35] Shin, yana yi muku wa'adin (cewa) lalle ku, idan kun mutu kuma kuka kasance turɓaya da ɓasusuwa lalle ne ku waɗanda ake fitarwa ne

    [36] Faufau faufau ga abin da ake yi muku wa'adi da shi

    [37] Rayuwa ba ta zama ba face rayuwarmu ta duniya, muna mutuwa kuma muna rayuwa, kuma ba mu zama waɗanda ake tayarwa ba

    [38] Bai zama kowa ba face namiji, ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma ba mu zama, saboda shi, masu imani ba

    [39] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka taimake ni saboda sun ƙaryata ni

    [40] Ya ce: "Daga abu kaɗan, lalle ne za su wayi gari suna masu nadama

    [41] Sai tsawa ta kama su da gaskiya, sai Muka sanya su tunkuɓa. Saboda haka nisa ya tabbataga mutane azzalumai

    [42] Sa'an kuma Muka ƙaga halittar wasu ƙarnoni dabam daga bayansu

    [43] Wata al'umma ba ta gabatar ajalinta, kuma ba za su jinkirta ba

    [44] Sa'an nan kuma Muka aika da ManzanninMu jere a koda yaushe Manzon wata al'umma ya je mata, sai su ƙaryata shi, saboda haka Muka biyar da sashensu ga sashe, kuma Muka sanya su labarun hira. To, nisa ya tabbata ga mutane (waɗanda) ba su yin imani

    [45] Sa'an nan kuma Muka aika Musa da ɗan'uwansa Haruna, game da ayoyinMu da, dalili bayyananne

    [46] Zuwa ga Fir'auna da majalisarsa, sai suka kangara, alhali sun kasance mutane ne marinjaya

    [47] Sai suka ce: "Shin, za Mu yi imani saboda wasu mutane biyu misalinmu, alhali kuwa mutanensu a gare mu, masu bauta ne

    [48] Sai suka ƙaryata su saboda haka suka kasance halakakku

    [49] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun bai wa Musa littafi tsammaninsu za su shiryu

    [50] Kuma Mun sanya ¦an Maryama, shi da uwarsa wata aya Kuma Muka tattara su zuwa ga wani tsauni ma'abucin natsuwa da maremari

    [51] Ya ku Manzanni! Ku ci daga abubuwa masu daɗi kuma ku aikata aikin ƙwarai. Lalle Niga abin da kuke aikatawa, Masani ne

    [52] Kuma lalle ne, wannan al'ummarku ce, al'umma guda, kuma Ni, Ubangijinku ne, sai ku bi Ni da taƙawa

    [53] Sai (al'ummar) suka yanyanke al'amarinsu a tsakaninsu guntu-guntu, kowace ƙungiya suna masu farin ciki da abin da yake a gare su

    [54] To, ka bar su a cikin ɓatarsu har a wani lokaci

    [55] Shin, suna zaton cewa abin da Muke taimakon su da shi daga dukiya da ɗiya

    [56] Muna yi musu gaggawa ne a cikin alherori

    [57] Lalle ne waɗanda suke masu sauna sabo da tsoron Ubangijinsu

    [58] Da waɗanda suke, game da ayoyin Ubangijinsu suna imani

    [59] Da waɗanda suke game da Ubangijinsu ba su yin shirki

    [60] Da waɗanda ke bayar da abin da suka bayar, alhali kuwa zukatansu suna tsorace domin suna komawa zuwa ga Ubangijinsu

    [61] Waɗancan suna gaggawar tsere a cikin ayyukan alheri, alhali kuwa suna masu tserewa zuwa gare su (ayyukan alheri)

    [62] Kuma ba Mu kallafa wa rai face abin iyawarsa, kuma a wurinMu akwai wani Littafi wanda yake magana da gakiya, kuma su ba a zaluntar su

    [63] A'a, zukatansu suna cikin jahilci daga wannan (magana), kuma suna da waɗansu ayyuka, baicin wancan, su a gare su, masu aikatawa ne

    [64] Har idan Mun kama mani'imtansu da azaba, sai ga su suna hargowa

    [65] Kada ku yi hargowa a yau, lalle ne ku, daga gare Mu ba a taimakon ku

    [66] Lalle ne, ayoyiNa sun kasance ana karatun su a kanku, sai kuka kasance, a kan dugaduganku, kuna komawa baya

    [67] Kuna masu girman kai gare shi (Annabi), da hira kuna alfasha

    [68] Shin fa, ba su yi ta'ammalin maganar (Alƙur'ani) ba, ko abin da bai je wa ubanninsu na farko ba ne ya je musu

    [69] Ko ba su san Manzonsu ba ne domin haka suke masu musu a gare shi

    [70] Ko suna cewa, "Akwai hauka gare shi?" A'a, ya zo musu da gaskiya, alhali kuwa mafi yawansu, ga gaskiya, masu ƙi ne

    [71] Kuma da gaskiya (Alƙur'ani) ya bi son zuciyoyinsu, haƙiƙa da sammai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sun ɓaci. A'a, Mun tafo musu da ambaton (darajar) su, sa'an nan su daga barin ambaton su masu bijirewa ne, bijirewa

    [72] Ko kana tambayar su wani haraji ne (a kan iyar da Manzanci a gare su)? To, harajin Ubangijinka ne mafi alheri kuma Shi ne Mafi alherin masu ciyarwa

    [73] Kuma lalle ne kai haƙiƙa kana kiran su zuwa ga hanya madaidaiciya

    [74] Kuma lalle waɗanda ba su yi imani da Lahira ba masu karkacewa daga hanya ne

    [75] Kuma da Mun ji tausayinsu, kuma Muka kuranye musu abin da yake tare da su na cuta, lalle ne da sun yi zurfi a cikin ɓatarsu, suna ɗimuwa

    [76] Kuma lalle ne haƙiƙa Muna kama su da azaba sai dai ba su saukar da kai ba, ga Ubangijinsu, kama ba su yin tawali'u

    [77] Har idan Mun buɗe, akansu, wata ƙofa mai azaba mai tsanani sai ga su a cikinta suna masu mugi

    [78] Kuma Shi ne Wanda Ya ƙaga halittar ji da gani da zukata dominku. Kaɗan ƙwarai kuke godewa

    [79] Kuma Shi ne Ya halitta ku a cikin ƙasa, kuma zuwa gare Shi ake tayar da ku

    [80] Kuma Shi ne Wanda Yake rayarwa, kuma Yana matarwa, kuma a gare Shi ne saɓawar dare da yini take. Shin, to, ba za ku hankalta ba

    [81] A'a, sun faɗi misalin abin da na farko suka faɗa

    [82] Suka ce: "Shin idan mun mutu kuma muka kasance turɓaya da ƙasusuwa shin lal1e ne mu haƙiƙa waɗanda ake tayarwa ne

    [83] Lalle ne, haƙiƙa, an yi mana wa'adi, mu da ubanninmu ga wannan a gabani, wannan abu bai zama kome ba, face tatsuniyoyin na farko

    [84] Ka ce: "Wane ne da mulkin ƙasa da wanda ke a cikinta, idan kun kasance kuna sani

    [85] Za su ce: "Ta Allah ne." Ka ce, "Shin, to, ba za ku yi tunani ba

    [86] Ka ce: "Wane ne Ubangijin sammai bakwai kuma Ubangijin Al'arshi mai girma

    [87] Za su ce: "Na Allah ne." Ka ce, "Shin, to, ba za ku bi Shi da taƙawa ba

    [88] Ka ce: "Wane ne ga hannunsa mallakar kowane abu take alhali kuwa shi yana tsarewar wani, kuma ba a tsare kowa daga gare shi, idan kun kasance kuna sani

    [89] Za su ce: "Ga Allah yake." Ka ce: "To, yaya ake sihirce ku

    [90] A'a, Mun zo musu da gaskiya, kuma lalle ne su, haƙiƙa, maƙaryata ne

    [91] Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma babu wani abin bautawa tare da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne da kowane abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, da waɗansu sun rinjaya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantawa

    [92] Masanin ɓoye da bayyane. sa'an nan Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka

    [93] Ka ce: "Ya Ubangijina! Ko dai Ka nuna mini abin da ake yi musu wa'adi da shi

    [94] Ya Ubangijina, to, kada Ka sanya ni a cikin mutane azzalumai

    [95] Kuma lalle ne Mu haƙiƙa Masu iyawa ne a kan Mu nuna maka abin da Muke yi musu wa'adi da shi

    [96] Ka tunkuɗe cuta da wadda take ita ce mafi kyau. Mu neMafi sani game da abin da suke siffantawa

    [97] Ka ce: "Ya Ubangijina, ina neman tsari da Kai daga fizge-fizgen Shaiɗanu

    [98] Kuma ina neman tsari da Kai, ya Ubangijina! Domin kada su halarto ni

    [99] Har idan mutuwa ta je wa ɗayansu, sai ya ce: "Ya Ubangijina, Ku mayar da ni (duniya)

    [100] Tsammanina in aikata aiki na ƙwarai cikin abin da na bari." Kayya! Lalle ne ita kalma ce, shi ne mafaɗinta, alhali kuwa a baya gare su akwai wani shamaki har ranar da za a tayar da su

    [101] Sa'an nan idan an yi busa a cikin ƙaho, to, babu dangantakoki a tsakaninsu a ranar nan kuma ba za su tambayi junansu ba

    [102] To, wadanda sikelinsu ya yi nauyi, to, waɗannan su ne masu babban rabo

    [103] Kuma waɗanda sikelinsu ya yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu suna madawwama a cikin Jahannama

    [104] Fuskokinsu suna balbalar wuta, kuma su a cikinta masu yagaggun leɓɓa daga haƙora ne

    [105] Shin, ayoyiNa ba su kasance ana karanta su a kanku ba sai kuka kasance game da su kuna ƙaryatawa

    [106] Suka ce: "Ya Ubangijinmu, shaƙawamiu ce ta rinjaya a kanmu, kuma mun kasance mutane ɓatattu

    [107] Ya Ubangjinmu! Ka fitar da mu daga gare ta, sa'an nan idan mun koma, to, lalle ne, mu ne masu zalunci

    [108] Ya ce: "Ku tafi (da wulakanci) a cikinta. Kada ku yi Mini magana

    [109] Lalle ne waɗansu ƙungiyoyi daga bayiNa sun kasance suna cewa, "Ya Ubangijinmu! Mun yi imani, sai Ka gafarta mana, kuma Ka yi mana rahama, kuma Kai ne Mafi alherin masu tausayi

    [110] Sai kuka riƙe su leburori har suka mantar da ku ambatoNa kuma kun kasance, daga gare su kuke yin dariya

    [111] Lalle ne Ni Ina saka musu a yau, saboda abin da suka yi wa haƙuri. Domin lalle ne su su ne masu samun babban rabo

    [112] Ya ce: "Nawa kuka zauna a cikin ƙasa na ƙidayar shekaru

    [113] Suka ce: "Mun zauna a yini ɗaya ko rabin yini, sai ka tambayi masu ƙidayawa

    [114] Ya ce: "Ba ku zauna ba face kaɗan, da dai kun kasance kuna sani

    [115] Shin, to, kun yi zaton cewa Mun halitta ku ne da wasa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, ba za ku komo ba

    [116] Allah Mamallaki gaskiya, Ya ɗaukaka. Babu abin bautawa, face Shi. Shi ne Ubangijin Al'arshi, mai daraja

    [117] Kuma wanda ya kira, tare da Allah, waɗansu abubuwan bautawa na dabam, ba yana da wani dalili game da shi (kiran) ba, to hisabinsa yana wurin Ubangijinsa kawai. Lalle ne, kafirai ba su cin nasara

    [118] Kuma ka ce: "Ya Ubangijina! Ka yi gafara, Ka yi rahama, kuma Kai ne Mafi alherin masu rahama

    Nũr

    Surah 24

    [1] (Wannan) sura ce. Mun saukar da ita, kuma Mun wajabta ta, kuma Mun saukar da ayoyi bayyanannu a cikinta, domin ku riƙa tunawa

    [2] Mazinaciya da mazinaci, to, ku yi bulala ga kowane ɗaya daga gare su, bulala ɗari. Kuma kada tausayi ya kama ku game da su a cikin addinin Allah idan kun kasance kuna yin imani da Allah da Ranar Lahira. Kuma wani yankin jama, a daga muminai, su halarci azabarsu

    [3] Mazinaci ba ya aure face da mazinaciya ko mushirika, kuma mazinaciya babu mai aurenta face mazinaci ko mushiriki. Kuma an haramta wannan a kan muminai

    [4] Kuma waɗanda ke jifar mata masu kamun kai, sa'an nan kuma ba su je da shaidu huɗu ba to, ku yi musu bulala, bulala tamanin, kuma kada ku karɓi wata shaida tasu, har abada. Waɗancan su ne fasiƙai

    [5] Face waɗanda suka tubadaga bayan wannan, kuma suka gyaru, to lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [6] Kuma waɗanda ke jifar matan aurensu kuma waɗansu shaidu ba su kasance a gare su ba, face dai kansu, to, shaidar ɗayansu, shaida huɗu ce da Allah, 'Lalle shi, haƙiƙa, yana daga magasganta

    [7] Kuma ta biyar cewa 'La'anar Allah ta tabbata a kansa, idan ya kasance daga maƙaryata

    [8] Kuma yana tunkuɗe mata azaba ta yi shaida, shaida huɗu da Allah, 'Lalle shi haƙiƙa, yana daga maƙaryata

    [9] Kuma ta biyar cewa 'Hushin Allah ya tabbata a kanta idan ya kasance daga magasganta

    [10] Kuma ba domin falalar Allah ba a kanku, da rahamarSa, kuma cewa Allah Mai karɓar tuba ne, Mai hikima

    [11] Lalle ne waɗanda suka zo da ƙiren ƙarya waɗansu jama'a ne daga gare ku, kada ku yi zatonsa sharri ne a gare ku. A'a, alheri ne gare ku. Kowane mutum daga gare su na da sakamakon abin da ya sana'anta na zunubi, kuma wanda ya jiɓinci girmansa, daga gare su, yana da azaba mai girma

    [12] Don me a lokacin da kuka ji shi muminai maza da muminai mata ba su yi zaton alheri game da kansu ba kuma su ce: "Wannan ƙiren ƙarya ne bayyananne

    [13] Don me ba su zo da shaidu huɗu a kansa ba? To idan ba su kawo shaidun nan ba to, waɗannan, a wurin Allah, su ne maƙaryata

    [14] Kuma ba domin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa a cikin duniya da Lahira. Lalle ne, da azaba mai girma ta shafe ku a cikin abin da kuka kutsa da magana a cikinsa

    [15] A lokacin da kuke marabarsa da harsunanku kuma kuna cewa da bakunanku abin da ba ku da wani ilmi game da shi, kuma kuna zaton sa mai sauƙi alhali kuwa, shi a wurin Allah, babba ne

    [16] Kuma don me a lokacin da kuka ji shi, ba ku ce ba, "Ba ya yiwuwa a gare mu, mu yi magana a game da wannan. Tsarki ya tabbata a gare Ka, wannan ƙiren ƙarya ne mai girma

    [17] Allah Yana yi muku wa'azi, kada ku koma ga irinsa, har abada, idan kun kasance muminai

    [18] Kuma Allah Yana bayyana muku ayoyinSa, kuma Allah Masani ne, Mai hikima

    [19] Lalle ne waɗanda ke son alfasha ta watsu ga waɗanda suka yi imani suna da azaba mai raɗaɗi a cikin duniya da Lahira. KumaAllah, Shi ne Ya sani, alhali kuwa, ku ba ku sani ba

    [20] Kuma ba domin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa. Kuma lalle ne Allah Mai tausayi ne, Mai jin ƙai

    [21] Ya ku waɗanda suka yi imani, kada ku bi hanyoyin Shaiɗan. Kuma wanda ke bin hanyoyin Shaiɗan, to, lalle ne shi, yana umurni da yin alfasha da abin da ba a sani ba, kuma ba domin falalar Allah ba a kanku da rahamarSa, babu wani mutum daga gare ku da zai tsarkaka har abada, kuma amma Allah Yana tsarkake wanda Yake so kuma Allah Mai ji ne, Masani

    [22] Kuma kada ma'abuta falala daga gare ku da mawadata su rantse ga rashin su bayar da alheri ga ma'abuta zumunta da miskinai da muhajirai, a cikin hanyar Allah. Kuma su yafe, kuma su kau da kai. shin, ba ku son Allah Ya gafarta muku, alhali Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [23] Lalle ne waɗannan da suke jifar mata masu kamun kai gafilai muminai, an la'ane su, a cikin duniya da Lahira, kuma sunada azaba mai girma

    [24] A ranar da harsunansu da hannayensu, da ƙafafunsu suke bayar da shaida a kansu, game da abin da suka kasance suna aikatawa

    [25] a ranar dl Allah Yake cika musu sakamakonsu tabbatacce kuma suna sanin (cewa) lalle Allah, Shi ne Gaskiya bayyananna

    [26] Miyagun mata domin miyagun maza suke, kuma miyagun maza domin miyagun mata suke kuma tsarkakan mata domin tsarkakan maza suke kuma tsarkakan maza domin tsarkakan mata suke. waɗancan su ne waɗanda ake barrantawa daga abin da (masu ƙazafi) suke faɗa kuma suna da gafara da arziki na karimci

    [27] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku shiga gidaje waɗanda ba gidajenku ba sai kun sami izni, kuma kun yi sallama a kan ma'abutansu. Wannan ne mafi alheri gare ku, tsammaninku, za ku tuna

    [28] To, idan ba ku sami kowa a cikinsu ba, to, kada ku shige su, sai an yi muku izni. Kuma idan an ce muku, "Ku koma." Sai ku koma, shi ne mafi tsarkaka a gare ku. Kuma Allah game da abin da kuke aikatawa, Masani ne

    [29] Babu laifi a kanku, ga ku shiga gidaje waɗanda ba zaunannu ba, a cikinsu akwai waɗansu kaya naku. Kuma Allah Yana sanin abin da kuke nunawa, da abin dakuke ɓayewa

    [30] Ka ce wa muminai maza su runtse daga ganinsu, kuma su tsare farjojinsu. wannan shi ne mafi tsarki a gare su. Lalle ne, Allah, Mai ƙididdigewa ne ga abin da suke sana'antawa

    [31] Kuma ka ce wa muminai mata su runtse daga gannansu, kuma su tsare farjojinsu kuma kada su bayyana ƙawarsu face abin da ya bayyana daga gare ta, kuma su doka da mayafansu a kan wuyan rigunansu, kuma kada su nuna ƙawarsu face ga mazansu ko ubanninsu ko ubannin mazansu, ko ɗiyansu, ko ɗiyan mazansu, ko 'yan'uwansu, ko ɗiyan 'yan'uwansu mata, ko matan ƙungiyarsu, ko abin da hannayensu na dama suka mallaka, ko mabiya wasun masu bukatar mata daga maza, ko jarirai waɗanda. ba su tsinkaya a kan al'aurar mata. Kuma kada su yi duka da ƙafafunsu domin a san abin da suke ɓoyewa daga ƙawarsu. Kuma ku tuba zuwa ga Allah gaba ɗaya, ya ku muminai! Tsammaninku, ku sami babban rabo

    [32] Kuma ku aurar da gwauraye daga gare ku, da salihai daga bayinku, da kuyanginku. Idan sun kasance matalauta Allah zai wadatar da su daga falalarSa. Kuma Allah Mawadaci ne, Masani

    [33] Kuma waɗannan da ba su sami aure ba su kame kansu har Allah Ya wadatar da su daga, falalarsa. Kuma waɗanda ke neman fansa daga abin da hannuwanku na dama suka mallaka, to, ku ɗaura musu fansa idan kun san akwai wani alheri a cikinsu kuma ku ba su wani abu daga dukiyar Allah wannan da Ya ba ku. Kuma kada ku tilasta kuyanginku a kan yin zina, idan sun yi nufin tsaron kansu, domin ku nemi rayuwar duniya, kuma wanda ya tilasta su to, lalle Allah, a bayan tilasta su, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [34] Kuma lalle ne Mun saukar zuwa gare ku, ayoyi masu bayyanawa, da misali daga waɗanda suka shige daga gabaninku, da wa'azi ga masu taƙawa

    [35] Allah ne Hasken sammai da ƙasa, misalin HaskenSa, kamar taga, a cikinta akwai fitila, fitilar a cikin ƙarau, ƙarau ɗin kamar shi tauraro ne mai tsananin haske, ana kunna shi daga wata itaciya mai albarka, ta zaituni, ba bagabashiya ba kuma ba bayammaciya ba, manta na kusa ya yi haske, kuma ko wuta ba ta shafe shi ba, haske a kan haske, Allah na shiryar da wanda Yake so zuwa ga HaskenSa. Kuma Allah na buga misalai ga mutane, kuma Allah game da dukan kome, Masani ne

    [36] A cikin waɗansu gidaje waɗanda Allah Ya yi umurnin a ɗaukaka kuma a ambaci sunansa a cikinsu, suna yin tasbihi a gare Shi a cikinsu, safe da maraice

    [37] Waɗansu maza, waɗanda wani fatauci ba ya shagaltar da su, kuma sayarwa ba ta shagaltar da su daga ambaton Allah, da tsai da salla da bayar da zakka, suna tsoron wani yini wanda zukata suna bibbirkita a cikinsa, da gannai

    [38] Domin Allah Ya saka musu da mafi kyaun abin da suka aikata, kuma Ya ƙara musu daga falalarsa. Kuma Allah Yana azurta wanda Yake so, ba da lissafi ba

    [39] Kuma waɗanda suka ƙafirta ayyukansu suna kamar ƙawalwalniya ga faƙo, mai ƙishirwa yana zaton sa ruwa, har idan ya je masa bai iske shi kome ba, kuma ya sami Allah a wurinsa, sai Ya cika masa hisabinsa. Kuma Allah Mai gaggawar sakamako ne

    [40] Ko kuwa kamar duffai a cikin teku mai zurfi, taguwar ruwa tana rufe da shi, daga bisansa akwai wata taguwa, daga bisansa akwai wani girgije, duffai sashensu a bisa sashe, idan ya fitar da tafinsa ba ya kusa ya gan shi. Kuma wanda Allah bai sanya masa haske ba, to, ba ya da wani haske

    [41] Shin, ba ka gani ba (cewa) lalle ne Allah, Wanda yake a cikin sammai da ƙasa suna yi Masa tasbihi, kuma tsuntsaye suna masu sanwa, kowane lalle ya san sallarsa da tasbihinsa kuma Allah Masani ne ga abin da suke aikatawa

    [42] Mulkin sammai da ƙasa ga Allah kawai yake, kuma zuwa ga Allah makoma take

    [43] Ashe, ba ka gani ba, lalle ne Allah Yana kora girgije, sa'an nan kuma Ya haɗa a tsakaninsa sa'an nan kuma Ya sanya shi mai hauhawar juna? Sai ka ga ruwa yana fita daga tsattsakinsa, kuma Ya saukar daga waɗansu duwatsu a cikinsa na ƙanƙara daga sama, sai ya samu wanda Yake so da shi, kuma Ya karkatar da shi daga barin wanda Yake so. Hasken walƙiyarsa Yana kusa ya tafi da gannai

    [44] Allah Yana juyar da dare da yini. Lalle ne a cikin wannan akwai abin kula ga ma'abuta gannai

    [45] Kuma Allah ne Ya halitta kowace dabba daga ruwa. To, daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya a kan cikinsu, kuma daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya a kan ƙafafu biyu, kuma daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya akan huɗu. Allah Yana halitta abin da Yake so, lalle Allah, a kan kowane abu, Mai ikon yi ne

    [46] Lalle ne haƙiƙa Mun saukar da ayoyi, masu bayyanawa. Kuma Allah Yana shiryar da wanda Yake so zuwa ga hanya madaidaiciya

    [47] Kuma suna cewa, "Mun yi imani da Allah da kuma Manzo, kuma mun yi ɗa'a." Sa'an nan kuma wata ƙungiya daga gare su, su juya daga bayan wancan. Kuma waɗancan ba muminai ba ne

    [48] Kuma idan aka kira su zuwa ga Allah da ManzonSa, domin Ya yi hukunci a tsakaninsu, sai ga wata ƙnngiya daga gare su suna masu bijirewa

    [49] Kuma idan hakki ya kasance a gare su, za su je zuwa gare shi, snna masu miƙa wuya

    [50] Shin, a cikin zukatansu akwai cuta ne, ko kuwa suna tsoron Allah Ya yi zalunci a kansu da ManzonSa? A'a, waɗancan su ne azzalumai

    [51] Maganar muminai, idan aka kira su zuwa ga Allah da ManzonSa domin Ya yi hukunci a tsakaninsu takan kasance kawai su ce "Mun ji, kuma mun yi ɗa'a, Kuma waɗannan su ne masu cin nasara

    [52] Kuma wanda ya yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, kuma ya ji tsoron Allah, ya kuma bi Shi da taƙawa to waɗannan su ne masu babban rabo

    [53] Kuma suka rantse da Allah iyakar rantsuwarsu, 'Lalle ne idan ka umurce su haƙiƙa suna fita.' Ka ce, "Kada ku rantse, ɗa'a sananna ce! Lalle ne, Allah Mai ƙididdigewa ne ga abin da kuke aikatawa

    [54] Ka ce: "Ku yi ɗa'a ga Allah kuma ku yi ɗa'a ga Manzo. To, idan kun juya, to, a kansa akwai abin da aka aza masa kawai, kuma a kanku akwai abin da aka aza muku kawai, Kuma idan kun yi masa ɗa'a za ku shiryu. Kuma babu abin da yake a kan Manzo face iyarwa bayyananna

    [55] Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi imani daga gare. Ku, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle zai shugabantar da su a cikin ƙasa kamar yadda Ya shugabantar da waɗanda suke daga gabaninsu, kuma lalle ne zai tabbatar musu da addininsu wanda Ya yardar musu, kuma lalle ne Yana musanya musu daga bayan tsoronsu da aminci, suna bauta Mini ba su haɗa kome da Ni. Kuma wanda ya kafirta a bayan wannan, to, waɗancan, su ne fasiƙai

    [56] Kuma ku tsayar da salla, kuma ku bayar da zakka, kuma ku yi ɗa'a ga Manzo, tsammaninku a yi muku rahama

    [57] Kada lalle ka yi zaton waɗanda suka kafirta za su buwaya a cikin ƙasa, kuma makomarsu wuta ce, kuma lalle ne makomar ta munana

    [58] Ya ku waɗanda suka yi imani! Waɗannan da hannuwanku na dama suka mallaka da waɗanda ba su isa mafarki ba daga cikinku, su nemi izni sau uku; daga gabanin sallar alfijir da lokacin da kuke ajiye tufafinku saboda zafin rana, kuma daga bayan sallar isha'i. Su ne al'aurori uku a gare ku. Babu laifi a kanku kuma babu a kansu a bayansu. Su masu kewaya ne a kanku sashenku a kan sashe. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana ayoyinSa a gare ku. Kuma Allah Masani ne, Mai hikima

    [59] Kuma idan yara daga cikinku suka isa mafarki to su nemi izni, kamar yadda waɗanda suke a gabaninsu suka nemi iznin. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana ayoyinSa a gare ku, kuma Allah Masani ne, Mai hikima

    [60] Kuma tsofaffi daga mata, waɗanda ba su fatan wani aure to, babu laifi a kansu su ajiye tufafinsu, ba suna masu fitar da ƙawa ba, kuma su tsare mutuncinsu shi ne mafi alheri a gare su. Kuma Allah Mai ji ne, Masani

    [61] Babu laifi a kan makaho, kuma babu laifi a kan gurgu, kuma babu laifi a kan majiyyaci, kuma babu laifi a kan kowanenku, ga ku ci (abinci) daga gidajenku, ko daga gidajen ubanninku, ko daga gidajen uwayenku, ko daga gidajen 'yan'uwanku maza, ko daga gidajen 'yan'uwanku mata, ko daga gidajen baffanninku, ko daga gidajen gwaggwanninku, ko daga gidajen kawunnanku, ko daga gidajen innoninku ko abin da kuka mallaki mabuɗansa ko abokinku babu laifi a gare ku ku ci gaba ɗaya, ko dabam- dabam. To, idan kun shiga wasu gidaje, ku yi sallama a kan kawunanku, gaisuwa ta daga wurin Allah mai albarka, mai daɗi. Kamar wancan ne Allah Yake bayyana muku ayoyinSa, tsammaninku ku yi hankali

    [62] Waɗanda ke muminai sosai, su ne waɗanda suka yi imani da Allah da ManzonSa, kuma idan sun kasance tare da shi, a kan wani al'amari na aikin gayya, ba su tafiya sai sun neme shi izni. Lalle ne, waɗanda suke biɗar ka izni waɗancan su ne suke yin imani da Allah da ManzonSa. To, idan sun neme ka izni saboda wani sha'aninsu, to, ka yi izni ga wanda ka so daga gare su, kuma ka nema musu gafara daga Allah. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [63] Kada ku sanya kiran Manzo a tsakaninku kamar kiran sashenku ga sashe. Lalle ne Allah Yana sanin waɗanda ke sancewa daga cikinku da saɗaɗe. To, waɗanda suke saɓawa daga umurninSa, su yi saunar wata fitina ta same su, ko kuwa wata azaba mai raɗaɗi ta same su

    [64] To! Lalle Allah ne Yake da mulkin abin da ke a cikin sammai da ƙasa, haƙiƙa, Yana sanin abin da kuke a kansa kuma a ranar da ake mayar da su zuwa gare shi, sai Yana ba su labari game da abin da suka aikata. Kuma Allah, ga dukkan kome, Masani ne

    Rarrabẽwa

    Surah 25

    [1] Albarka ta tabbata ga wanda Ya saukar da (Littafi) mai rarrabewa a kan bawanSa, domin ya kasance mai gargaɗi ga halitta

    [2] wanda Yake da mulkin sammai da ƙasa kuma bai riƙi abin haihuwa ba, kuma abokin tarayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa kuma Ya halitta dukan kowane abu, sa'an nan Ya ƙaddara shi ƙaddarawa

    [3] Kuma suka riƙi abubuwan bautawa, baicin Shi, ba su yin halittar kome alhali su ne ake halittawa kuma ba su mallakar wa kansu wata cuta ko wani amfani, kuma ba su mallakar mutuwa kuma ba su mallakar rayarwa, kuma ba su mallakar tayarwa

    [4] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: "Wannan ba kome ba ne face ƙiron ƙarya da (Muhammadu) ya ƙirƙira shi, kuma waɗansu mutane na dabam suka taimake shi a kansa." To, lalle ne sun je wa zalunci da karkacewar magana

    [5] Kuma suka ce: "Tatsuniyoyi ne na farko ya rurrbuta, sai su ake shibtarsu a gare shi safe da yamma

    [6] Ka ce: "wanda Yake sanin asiri a cikin, sammai da ƙasane Ya saukar da shi. Lalle ne shi Ya kasance Mai gafara, Mai, jin ƙai

    [7] Kuma suka ce: "Mene ne ga wannan Manzo, yana cin abinci, kuma yana tafiya a cikin kasuwanni! Don me ba a saukar da mala'ika zuwa gare shi ba, domin ya kasance mai gargaɗi tare da shi

    [8] Ko kuwa a jefo wata taska zuwa gare shi, ko kuwa wata gona ta kasance a gare shi, yana ci daga gare ta?" Kuma azzalumai suka ce: "Ba ku bin kowa, face mutum sihirtacce

    [9] Ka duba yadda suka buga maka misalai sai suka ɓace, domin haka ba su iya bin tafarki

    [10] Albarka ta tabbata ga wanda idan Ya so, Ya sanya maka mafi alheri daga wannan (abu): gonaki, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu, kuma Ya sanya maka manyan gidaje

    [11] A'a, sun ƙaryata game da Sa'a, alhali kuwa Mun yi tattalin wuta mai tsanani ga wanda ya ƙaryata (manzanni) game da Sa'a

    [12] Idan ta gan su daga wani wuri mai nisa, sai su ji sautin fushi da wani ruri nata

    [13] Kuma idan an jefa su a wani wuri mai ƙunci daga gare ta, suna waɗanda aka ɗaure ciki daidai, sai su kirayi halaka a can

    [14] Kada ku kirayi halaka guda, kuma ku kirayi halaka mai yawa

    [15] Ka ce: "Shin, wancan ne mafi alheri, ko kuwa Aljannar dawwama wadda aka yi wa'adi ga masu taƙawa? Ta zama, a gare su, sakamako da makoma

    [16] Suna da abin da suke so, a cikinta suna madawwama. Wannan ya kasance wa'adi abin tambaya a kan Ubangijinka

    [17] Kuma ranar da Yake tara su da abin da suke bauta wa, baicin Allah sai Ya ce: "Shin ku nekuka ɓatar, da bayiNa, waɗannan, ko kuwa su ne suka ɓata daga hanya

    [18] suka ce: "Tsarki ya tabbata a gare Ka, ba ya kasancewa agare mu, mu riƙi waɗansu majiɓinta, baicin Kai, kuma amma Ka jiyar da su daɗi su da ubanninsu har suka manta da Tunatarwa, kuma sun kasance mutane ne halakakku

    [19] To, lalle ne, sun ƙaryata game da abin da kuke cewa, saboda haka ba ku iya karkatarwa ga (maganarsu), kuma ba ku iya taimako (ga hana azaba), kuma wanda ya yi zalunci a cikinku za Mu ɗanɗana masa azaba mai girma

    [20] Kuma ba Mu aika ba, a gabaninka daga Manzanni, face lalle su haƙiƙa suna cin abinci kuma suna tafiya a cikin kasuwoyi. Kuma Mun sanya sashen mutane fitina ga sashe. Shin kuna yin haƙuri? Kuma Ubangijia Ya kasance Mai gani

    [21] Kuma waɗanda ba su fatan haɗuwa da Mu suka ce: "Don me ba a saukar da mala'iku ba a kanmu, ko kuwa mu ga Ubangijinmu?" Lalle ne sun kangara a cikin rayukansu, kuma suka yi tsaurin kai, tsaurin kai mai girma

    [22] A ranar da suke ganin mala'iku babu bushara a yinin nan ga masu laifi kuma suna cewa,"Allah Ya kiyashe mu

    [23] Kuma Muka gabata zuwa ga abin da suka aikata daga aiki, sai Muka sanya shi ƙura watsattsiya

    [24] Ma'abuta Aljanna a ranar nan su ne mafi alheri ga matabbata kuma mafi kyaun wurin ƙailula

    [25] Kuma a ranar da sama take tsattsagewa tare da gizagizai, kuma a saukar da mala'iku, saukarwa

    [26] Mulki a ranar nan, na gaskiya, yana ga Mai rahama, kuma ya zama yini, a kan kafirai, mai tsanani

    [27] Kuma ranar da azzalumi yake cizo a kan hannayensa, yana cewa "Ya kaitona! (A ce dai) na riƙi hanya tare da Manzo

    [28] Ya kaitona! (A ce dai) ban riƙi wane masoyi ba

    [29] Lalle ne, haƙiƙa ya ɓatar da ni daga Tunawa a bayan (Tunawar) ta je mini."Kuma Shaiɗan ya zama mai zumɓulewa ga mutum

    [30] Kuma Manzo ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle mutanena sun riƙi wannan Alƙur'ani abin ƙauracewa

    [31] Kuma kamar haka ne, Muka sanya maƙiyi daga masu laifi ga kowane Annabi. Kuma Ubangijinka Ya isa ga zama Mai Shiryarwa, kuma Mai taimako

    [32] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: "Don me ba a saukar da Alƙur'ani a kansa ba, jimla guda?" kamar wancan! Domin Mu ƙarfafa zuciyarka game da shi, kuma Mun jeranta karanta shi da hankali jerantawa

    [33] Kuma ba za su zo maka da wani misali ba, face Mun je maka da gaskiya da mafi kyau ga fassara

    [34] Waɗanda ake tayarwa a kan fuskokinsu, zuwa ga Jahannama, waɗancan su ne mafi sharri ga wuri, kuma mafi ɓacewa ga hanya

    [35] Kuma lalle ne, Mun bai wa Musa Littafi, kuma Mun sanya ɗan'uwansa, Haruna, mataimaki tare da shi

    [36] Sai Muka ce: "Ku tafi, ku biyu, zuwa ga mutanen nan waɗanda suka ƙaryata game da ayo yinMu." sai Muka darkake su, darkakewa

    [37] Kuma mutanen Nuhu, a lokacin da suka ƙaryata Manzanni, Muka nutsar da su, kuma Muka sanya su wata aya ga mutane, kuma Muka yi tattalin azaba mai raɗaɗi ga azzalumai

    [38] Da Adawa da Samudawa, da mutanen Rassi, da waɗansu al'ummomi, a tsakanin wannan, masu yawa

    [39] Kuma kowannensu Mun buga masa misalai, kuma kowanne Mun halakar da (shi), halakarwa

    [40] Kuma lalle ne, haƙiƙa, (¡uraishi) sun je a kan alƙaryar nan wadda aka yi wa ruwa, ruwan azaba. Shin, ba su kasance sun gan ta ba? A'a, sun kasance ba su ƙaunar tayarwa (a ¡iyama)

    [41] Kuma idan sun gan ka, ba su rikon ka face da izgili, (suna cewa) "Shin, wannan ne wanda Allah Ya aiko, Manzo

    [42] Lalle ne, ya yi kusa ya ɓatar da mu daga Ubangijinmu, in ba domin da muka yi haƙuri a kansu ba."Kuma za su sani a lokacin da suke ganin azaba, wane ne mafi ɓacewa ga hanya

    [43] Shin, ka ga wanda ya riƙi UbangiJinsa son zuciyarsa? shin, to, kai ne ke kasancewa mai tsaro a kansa

    [44] Ko kana zaton cewa mafi yawansu suna ji, ko kuwa suna hankali? su ba su zama ba face dabbobin gida suke. A'a, su ne mafi ɓacewa ga hanya

    [45] Ashe, ba ka duba ba zuwa ga Ubangijinka, yadda Ya miƙe inuwa? Kuma da Ya so da Ya bar ta tsaye cif, sa'an nan Muka sanya rana mai nuni a kanta

    [46] Sa'an nan Muka karɓe ta (inuwa) zuwa gare Mu, karɓa mai sauƙi

    [47] Kuma shi ne wanda Ya sanya muku dare ya zama tufa da barci ya zama hutawa, da yini ya zama lokacin tashi (kamar Tashin ¡iyama)

    [48] Kuma Shi ne Ya aika iskokin bushara gaba ga rahamarSa, kuma Muka saukar da ruwa mai tsarkakewa daga sama

    [49] Domin Mu rayar, game da shi, gari matacce, kuma Mu shayar da shi dabbobi da mutane masu yawa daga abin da Muka halitta

    [50] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun sarrafa shi (Alƙur'ani) a tsakaninsu, domin su yi tunani, sai dai mafi yawan mutanen sun ƙi face kafirci

    [51] Kuma da Mun so, haƙiƙa da Mun aika da mai gargaɗi a ciƙin kowace alƙarya

    [52] Saboda haka kada ka yi ɗa'a ga kafirai, ka yake su, da shi, yaƙi mai girma

    [53] Kuma shi ne Ya garwaya tekuna biyu, wannan mai dadi, mai sauƙin haɗiya, kuma wannan gishiri gurɓatacce, kuma Ya sanya wani shamaki a tsakaninsu da kariya mai shamakacewa

    [54] Kuma Shi ne Ya halitta mutum daga ruwa, sai Ya sanya shi nasaba da surukuta, kuma Ubangijinka Ya kasance Mai ikon yi

    [55] Kuma suna bauta wa, baicin Allah, abin da ba ya amfanin su, kuma ba ya cutar su, kuma kafiri ya kasance mai taimakon (Shaiɗan) a kan Ubangijinsa

    [56] Ba Mu aika ka ba sai kana mai bayar da bushara, kuma mai gargaɗi

    [57] Ka ce: "Ba ni tambayar ku wata ijara a kansa face wanda ya so ya riƙi wata hanya zuwa ga Ubangijinsa

    [58] Kuma ka dogara a kan Rayayye wanda ba Ya mutuwa, kuma ka yi tasbihi game da gode Masa. Kuma Ya isa zama Mai ƙididdigewa ga laifuffukan bayinSa

    [59] Wanda Ya halitta sammai da ƙasa da abin da yake a tsakaninsu, a cikin kwanuka shida sa'an nan Ya daidaitu a kan Al'arshi Mai rahama, sai ka tambayi mai bayar da labari game da Shi

    [60] Idan aka ce musu, "Ku yi sujada ga Mai rahama." Sai su ce: "Mene ne Mai rahama? Ashe za mu yi sujada ga abin da kuke umurnin mu?"Kuma wannan (magana ta ƙara musu gudu)

    [61] Albarka ta tabbata ga Wanda Ya sanya masaukai (na tafiyar wata) a cikin sama kuma Ya sanya fitila da wata mai haskakewa a cikinta

    [62] Kuma Shi ne wanda Ya sanya dare da yini a kan mayewa, ga wanda yake son ya yi tunani, ko kuwa ya yi nufin ya gode

    [63] Kuma bayin Mai rahama su ne waɗanda ke yin tafiya a kan ƙasa da sauƙi, kuma idan jahilai sun yi musu magana, sai su ce: "Salama" (a zama lafiya)

    [64] Kuma waɗanda suke kwana suna masu sujada da tsayi a wurin Ubangijinsu

    [65] Kuma waɗanda suke cewa "Ya Ubangijinmu! Ka karkatar da azabar Jahannama daga gare mu. Lalle ne, azabarta ta zama tara

    [66] Lalle ne ita ta munana ta zama wurin tabbata da mazauni

    [67] Kuma waɗanda suke idan sun ciyar, ba su yin ɓarna, kuma ba su yin ƙwauro, kuma (ciyarwarsu) sai ta kasance a tsakanin wancan da tsakaitawa

    [68] Kuma waɗanda ba su kiran wani ubangiji tare da Allah, kuma ba su kashe rai wanda Allah Ya haramta face da hakki kuma ba su yin zina. Kuma wanda ya aikata wancan, zai gamu da laifuffuka

    [69] A riɓanya masa azaba a Ranar ¡iyama. Kuma ya tabbata a cikinta yana wulakantacce

    [70] Sai wanda ya tuba, kuma ya yi imani, kuma ya aikata aiki na ƙwarai to, waɗancan Allah Yana musanya miyagun ayyukansu da masu kyau. Allah Ya kasance Mai gafara Mai jin ƙai

    [71] Kuma wanda ya tuba, kuma ya aikata aiki mai kyau, to, lalle ne sai ya tuba zuwa gaAllah

    [72] Kuma waɗanda suke ba su yin shaidar zur, kuma idan sun shuɗe ga yasassar magana sai su shuɗe suna masu mutumci

    [73] Kuma waɗanda suke idan an tunatar da su da ayoyin Allah, ba su saukar da kai, suna kurame da makafi

    [74] Kuma waɗanda suke cewa "Ya Ubangijinmu! Ka ba mu sanyin idanu daga matanmu da zuriyarmu, kuma Ka sanya mu shugabanni ga masu taƙawa

    [75] Waɗannan ana saka musu da bene, saboda haƙurin da suka yi, kuma a haɗa su, a cikinsa, da gaisuwa da aminci

    [76] Suna madawwama a cikinsa. Ya yi kyau ga zama matabbaci da mazauni

    [77] Ka ce: "Ubangijina ba Ya kula da ku in ba domin addu'arku ba. To, lalle ne, kun ƙaryata, saboda haka al'amarin za ya zama malizimci

    Shu'arã'u (Mawaƙa)

    Surah 26

    [1] ¦. S. M

    [2] Waɗancan ayoyin Littafi ne bayyananne

    [3] Tsammaninka kai mai halakar da ranka ne, domin ba su kasance muminai ba

    [4] Idan Mun so za Mu saukar, a kansu, da wata aya daga sama, sai wuyoyinsu su yini saboda ita suna masu ƙasƙantar da kai

    [5] Kuma wata tunatarwa ba ta je musu ba, daga Mai rahama, sabuwa, face sun kasance daga barinta suna masu bijirewa

    [6] To, lalle ne, sun ƙaryata, to, labaran abin da suka kasance suna yi na izgili da shi za ya je musu

    [7] Shin, ba su duba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau

    [8] Lalle ne, a cikin wancan akwai aya, kuma mafi yawansu ba su kasance muminai ba

    [9] Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙiƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai rahama

    [10] Kuma a lokacin da Ubangijinka Ya kirayi Musa, "Ka je wa mutanen nan azzalumai

    [11] Mutanen Fir'auna ba za su yi taƙawa ba

    [12] Ya ce: "Ya Ubangijina, ni ina tsoron su ƙaryata ni

    [13] Kuma ƙirjina ya yi ƙunci kuma harshena ba zai saku ba saboda haka ka aika zuwa ga Haruna

    [14] Kuma suna da wani laifi a kaina, saboda haka ina tsoron kada su kashe ni

    [15] Ya ce: "Kayya! Ku tafi, ku biyu, da AyoyinMu. Lalle ne, Muna tare da ku Muna Masu saurare

    [16] Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne

    [17] Ka saki Bani Isra'ila tare da mu

    [18] Ya ce: "Shin, ba mu yi renonka ba a cikinmu kana jariri, kuma ka zauna a cikinmu shekarudaga lokacin rayuwarka

    [19] Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhali kai kana daga butulai

    [20] Ya ce: "Na aikata shi a lokacin ina daga masu jahilcin hushi

    [21] Saboda haka na gudu daga gare ku a lokacin da na ji tsoronku, sai Ubangijina Ya ba ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni

    [22] Kuma waccan ni'ima ce, kana gorint a kaina, domin ka bautar da Bani Isra'ila

    [23] Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu

    [24] Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakaninsu, idan kun kasance masu ƙarfin imani

    [25] Ya ce wa waɗanda suke a gefensa, "Ba za ku saurara ba

    [26] Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko

    [27] Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne

    [28] Ya ce: "Ubangijin mafitar rana da maɓuyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kuna hankalta

    [29] Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautawa wanina haƙiƙa, ina sanya ka daga ɗaurarru

    [30] Ya ce: "Ashe, kuma ko da na zo maka da wani, abu mai bayyanawa

    [31] Ya ce: "To, ka zo da shi idan ka kasance daga, masu gaskiya

    [32] Sai ya jefa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne

    [33] Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga masu kallo

    [34] (Fir'auna) ya ce ga mashawarta a gefensa, "Lalle ne, wannan haƙiƙa, masihirci ne, mai ilmi

    [35] Yana son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mene ne kuke shawartawa

    [36] Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shi da ɗan'uwansa, kuma ka aika masu gayya a cikin birane

    [37] Za su zo maka da dukkan mai yawan sihiri masani

    [38] Sai aka tara masihirta domin ajalin yini sananne

    [39] Kuma aka ce wa mutane "Ko ku masu taruwa ne

    [40] Tsammaninmu mu bi masihirta, idan sun kasance su ne marinjaya

    [41] To, a lokacin da masihirta suka je suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙiƙa muna da ijara idan mun kasance mu ne marinjaya

    [42] Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, ku ne a lokacin haƙiƙa muƙarrabai

    [43] Musa ya ce musu, "Ku jefa abin da kuke masu jefawa

    [44] Sai suka jefa igiyoyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mu, haƙiƙa, mu ne marinjaya

    [45] Sai Musa ya jefa sandarsa, sai ga ta tana harhaɗe abin da suke yi na ƙarya

    [46] Sai aka jefar da masihirta suna masu sujada

    [47] Suka ce: "Mun yi imani da Ubangijin halitta

    [48] Ubangijin Musa da Haruna

    [49] Ya ce: "Ashe, kun yi imani saboda shi, a gabanin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙiƙa babbanku ne wanda ya koya muku sihirin, to, za ku sani. Lalle ne haƙiƙa, zan kakkatse hannuwanku da kafafunku a tarnaƙi, kuma haƙiƙa, zan tsire ku gaba ɗaya

    [50] Suka ce: "Babu wata cuta! Lalle ne mu masu juyawa ne zuwa ga Ubangijinmu

    [51] Lalle ne mu muna kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gafarta mana kurakuranmu domin mun kasance farkon masu imani

    [52] Kuma Muka aika zuwa ga Musa cewa ka yi tafiyar dare da bayiNa, lalle ne ku waɗanda ake biya ne

    [53] Sai Fir'auna ya aika masu gayya a cikin birane

    [54] Lalle ne, waɗannan, haƙiƙa, ƙungiya ce kaɗan

    [55] Kuma lalle ne su, a gare Mu, Masu fusatarwa ne

    [56] Kuma lalle ne mu haƙiƙa gaba ɗaya masu sauna ne

    [57] Sai Muka fitar da su daga gonaki da maremari

    [58] Da taskoki da mazauni mai kyau

    [59] Kamar haka! Kuma Muka gadar da su ga Bani Israila

    [60] Sai suka bi su suna masu fita a lokacin hudowar rana

    [61] Sa'an nan a lokacin da jama'a biyu suka ga juna, sai abokan Musa suka ce: "Lalle ne mu haƙi ƙa, waɗanda ake riska ne

    [62] Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yana tare da ni, zai shiryar da ni

    [63] Sai Muka yi wahayi zuwa ga Musa cewa "Ka doki teku da sandarka." Sai teku ta tsage, kowane tsagi ya kasance kamar falalen dutse mai girma

    [64] Kuma Muka kusantar da waɗansu mutane a can

    [65] Kuma Muka tsirar da Musa da waɗanda suke tare da shi gaba ɗaya

    [66] Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutanen

    [67] Lalle ne a cikin wannan akwai aya, kuma mafi yawansu ba su kasance masu imani ba

    [68] Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙiƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [69] Kuma ka karanta, a kansu, labarin Ibrahim

    [70] A sa'ilin da ya ce wa ubansa da mutanensa, "Mene ne kuke bauta wa

    [71] Suka ce: "Muna bauta wa gumaka, saboda haka muna yini masu lazimta a gare su

    [72] Ya ce: "Shin, suna jin ku, a lokacin da kuke kira

    [73] Ko kuwa suna amfanin ku, ko suna cutar ku

    [74] Suka ce: "A'a mun sami ubanninmu, kamar haka ne suke aikatawa

    [75] Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kuna bauta wa

    [76] Ku da ubanninku mafi daɗewa

    [77] To lalle ne, su maƙiya ne a gare ni, face Ubangijin halittu

    [78] Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yana shiryar da ni

    [79] Kuma Wanda Yake Shi ne Yake ciyar da ni, kuma Yana shayar da ni

    [80] Kuma idan na yi jiyya, to, Shi ne Yake warkar da ni

    [81] Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rayar da ni

    [82] Kuma wanda Yake ina kwaɗayin Ya gafarta mini kurakuraina, a ranar sakamako

    [83] Ya Ubangijina! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga salihai

    [84] Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutanen ƙarshe

    [85] Kuma Ka sanya ni daga magadan Aljannar ni'ima

    [86] Kuma Ka gafarta wa ubana, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu

    [87] Kuma kada Ka kunyata ni a ranar da ake tayar da su

    [88] A ranar da dukiya ba ta amfani, kuma ɗiya ba su yi

    [89] Face wanda ya je wa Allah da zuciya mai tsarki

    [90] Kuma aka kusantar da Aljanna ga masu taƙawa

    [91] Kuma aka fitar da wuta babba domin halakakku

    [92] Kuma aka ce musu, "Ina abin da kuka kasance kuna bautawa

    [93] Baicin Allah? Shin suna tamakon ku ko kuwa suna tsare kansu

    [94] Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun

    [95] Da rundunar Ibilisa gaba ɗaya

    [96] Suka ce: alhali suna a cikinta suna yin husuma

    [97] Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙiƙa, a cikin ɓata bayyananna

    [98] A lokacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu

    [99] Kuma babu abin da ya ɓatar da mu face masu laifi

    [100] Saboda haka ba mu da waɗansu maceta

    [101] Kuma ba mu da aboki, masoyi

    [102] Saboda haka da lalle muna da (damar) komawa, domin mu kasance daga muminai

    [103] Lalle ne, a cikin wancan akwai aya, kuma mafi yawansu, ba su kasance muminai ba

    [104] Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [105] Mutanen Nuhu sun ƙaryata Manzanni

    [106] A lokacin da ɗan'uwansu, Nuhu, ya ce musu, "Shin, ba za ku yi taƙawa ba

    [107] Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce

    [108] To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [109] Kuma ba ni tambayar ku wata ijara a kansa. Ijarata ba ta zama ba face daga Ubangijin halittu

    [110] Saboda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [111] Suka ce: "Ashe, za mu yi imani saboda kai alhali kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka

    [112] Ya ce: "Kuma ba ni da sani ga abin da suka kasance sana aikatawa

    [113] Hisabinsu bai zama ba face ga Ubangijina, da kuna sansancewa

    [114] Ban zama mai kore muminai ba

    [115] Ni ba kowa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanawa

    [116] Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, ya Nuhu, (daga maganarka,) haƙiƙa, kana kasancewa daga waɗanda ake jefewa

    [117] Ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne mutanena sun ƙaryata ni

    [118] Sai ka yi hukunci, a tsakanina da tsakaninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsirar da ni, da waɗanda suke tare da ni daga muminai

    [119] Sai Muka tsirar da shi, shi da waɗanda suke tare da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lodi

    [120] Sa'an nan Muka nutsar a bayan haka, da sauran

    [121] Lalle ne a cikin wannan akwai aya, kuma mafi yawansu, ba su kasance masu imani ba

    [122] Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙiƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai Rahama

    [123] Adawa sun ƙaryata Manzanni

    [124] A lokacin da ɗan'uwansu, Hudu ya ce musu, "Ba za ku yi taƙawa ba

    [125] Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙiƙa, Manzo ne, amintacce

    [126] Saboda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [127] Kuma ba ni tambayar wata ijara a kansa. Ijarata ba ta zama ba, face daga Ubangijin halittu

    [128] Shin, kuna yin ginin sitadiyo a kowane tsauni ne, kuna yin wasa

    [129] Kuma kuna riƙon matsarar ruwa, tsammaninku, ku dawwama

    [130] Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kuna masu tanƙwasawa

    [131] To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [132] Ku ji tsoron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani

    [133] Ya taimake ku da dabbobin ni'ima da ɗiya

    [134] Da gonaki da maremari

    [135] Lalle ne ni, ina ji muku tsoron azabar wani yini mai girma

    [136] Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Ka yi wa'azi ko ba ka kasance daga masu wa'azi ba

    [137] Wannan abu bai zamo ba face halayen mutanen farko

    [138] Kuma mu ba mu zama waɗanda ake yi wa azaba ba

    [139] Saboda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da su. Lalle ne a cikin wannan akwai aya, kuma mafi yawansu ba su kasance masu imani ba

    [140] Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙiƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [141] Samudawa sun ƙaryata Manzanni

    [142] A lokacin da ɗan'uwansu Salihu ya ce: "Shin, ba za ku bi Allah da taƙawa ba

    [143] Lalle ne ni zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce

    [144] Saboda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [145] Kuma ba ni tambayar ku wata ijara a kansa. Ijarata ba ta zama ba face da a Ubangijin halittu

    [146] Shin, ana barin ku a cikin abin da yake a nan, kuna amintattu

    [147] A cikin gonaki da maremari

    [148] Da shuke-shuke da dabi nai, 'ya'yan itacensu hirtsi masu narkewa a ciki

    [149] Kuma kuna sassaƙa gidaje daga duwatsu, kuna masu alfahari

    [150] Saboda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [151] Kada ku yi ɗa'a ga umurnin maɓarnata

    [152] Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma ba su kyautatawa

    [153] Suka ce: "Kai daga masu sihiri kurum kake

    [154] Ba kowa kake ba, face mutum kamarmu. To, ka zo da wata aya idan ka kasance daga masu gaskiya

    [155] Ya ce: "Wannan rakuma ce tana da shan yini, kuma kuna da shan yini sasanne

    [156] Kada ku shafe ta da cuta har azabar yini mai girma ta shafe ku

    [157] Sai suka soke ta sa'an nan suka wayi gari suna masu nadama

    [158] Saboda haka azaba ta kama su. Lalle ne a cikin wannan akwai aya, kuma mafi yawansu, ba su kasance masu imani ba

    [159] Lalle ne Ubangijinka, haƙi ƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [160] Mutanen Luɗu sun ƙaryata Manzanni

    [161] A lokacin da ɗan'uwansu, Luɗu ya ce musu, "Ba za ku yi taƙawa ba

    [162] Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce

    [163] Saboda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [164] Kuma ba ni tambayar ku wata ijara, Ijarata ba ta zama ba face daga Ubangijin halittu

    [165] Shin kuna je wa maza daga cikin talikai

    [166] Kuma kuna barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga matanku? A'a, ku mutane ne masu ƙetarewa

    [167] Suka ce: "Lalle ne haƙiƙa idan ba ka hanu ba, ya Luɗu! Tilas ne kana kasancewa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)

    [168] Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙiƙa, ina daga masu ƙinsa

    [169] Ya Ubangijina! Ka tsirar da ni da iyalina daga abin da suke aikatawa

    [170] Saboda haka Muka tsirar da shi, Shi da mutanensa gaba ɗaya

    [171] Face wata tsohuwa a cikin masu wanzuwa

    [172] Sa'an nan kuma Muka darkake wasu

    [173] Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya munana

    [174] Lalle ne ga wannan, akwai aya, kuma mafi yawansu ba su kasance masu imani ba

    [175] Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙiƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [176] Ma'abuta ƙunci sun ƙaryata Manzanni

    [177] A lokacin da Shu'aibu ya ce musu, "Ba za ku yi taƙawa ba

    [178] Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce

    [179] Saboda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗa'a

    [180] Kuma ba ni tambayar ku wata ijara a kansa. Ijarata ba ta zama ba face daga Ubangijin halittu

    [181] Ku cika mudu, kuma kada ku kasance daga masu sanyawar hasara (ga mutane)

    [182] Kuma ku yi awo da sikeli daidaitacce

    [183] Kuma kada ku nakasa wa mutane abubuwansu kuma kada ku yi fasadi a cikin ƙasa kuna masu ɓarna

    [184] Kuma ku ji tsoron Allah wanda Ya halitta ku, ku da jama'ar farko

    [185] Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne

    [186] Kuma ba kowa kake ba, face mutum kamarmu kuma lalle ne muna zaton ka, haƙiƙa, daga maƙaryata

    [187] To ka jefo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga masu gaskiya

    [188] Ya ce: "Ubangijina ne Mafi sani ga abin da kuke aikatawa

    [189] Sai suka ƙaiyata shi, saboda haka, azabar ranar girgije ta kama su. Lalle ne ita, ta kasance azabar yini mai girma

    [190] Lalle a cikin wancan haƙika akwai aya, amma mafi yawansu ba su kasance masu imani ba

    [191] Kuma lalle Ubangijinka, haƙiƙa, Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [192] Kuma lalle shi (Alƙur'ani), haƙiƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne

    [193] Ruhi amintacce ne ya sauka da shi

    [194] A kan zuciyarka, domin ka kasance daga masu gargaɗi

    [195] Da harshe na Larabci mai bayani

    [196] Kuma lalle shin, haƙiƙa, yana a cikin litattafan (Manzannin) farko

    [197] Ashe, bai kasance aya ba a gare su, ya zama Malaman Bani Isra'ila sun san shi

    [198] Kuma da mun saukar da shi a kan sashen Ajamawa

    [199] Ya karanta shi a kansu, ba su kasance saboda shi masu imani ba

    [200] Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukatan masu laifi

    [201] Ba za su yi imani da shi ba sai sun ga azabar nan mai raɗadi

    [202] Sai ta taho musu kwatsam, alhali kuwa su, ba su sansance ba

    [203] Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne

    [204] Ashe, to, da azabarMu suke neman gaggawa

    [205] Ashe, to, ka gani, idan Muka jishe su daɗi a shekaru

    [206] Sa'an nan abin da suka kasance ana yi musu wa'adi (da shi) ya je musu

    [207] Abin da suka kasance ana jishe su daɗin ba zai tunkuɗe azaba ba daga gare su

    [208] Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba face tana da masu gargaɗi

    [209] Domin tunatarwa, kuma ba Mu kasance Masu zalunci ba

    [210] Kuma (Alƙur'ani) Shaiɗanu ba su ɗora sauka da shiba

    [211] Kuma ba ya kamata a gare su (su Shaiɗanu su sauka da shi), kuma ba su iyawa

    [212] Lalle ne su, daga saurare, haƙiƙa, waɗanda aka nisantar ne

    [213] Saboda haka, kada ka kira wani abin bautawa na dabam tare da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azaba

    [214] Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci

    [215] Kuma ka sassauta fikafikanka ga wanda ya bi ka daga muminai

    [216] Sa'an nan idan suka saɓa maka to ka ce: "Lalle ni, barrantacce ne daga abin da kuko aikatawa

    [217] Kuma ka dogara ga Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [218] Wanda Yake ganin ka a lokacin da kake tashi tsaye

    [219] Da jujjuyawarka a cikin masu yin sujada

    [220] Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani

    [221] Shin, (kuna so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗannu kan sauka

    [222] Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi

    [223] Suna jefa (abin da suka) ji, alhali kuwa mafi yawansu maƙaryata ne

    [224] Kuma mawaƙa halakakku ne ke bin su

    [225] Shin, ba ku cewa, lalle ne su, cikin kowane rango suna yin ɗimuwa (su ƙetare haddi) ba

    [226] Kuma lalle ne, su, suna faɗin abin da ba su aikatawa

    [227] Face waɗanda suka yi imani suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rama zalunci, daga bayan an zalunce su. Kuma waɗanda suka yi zalunci, za su sani a wace majuya suke juyawa

    Namla

    Surah 27

    [1] ¦. S. Waɗancan ayoyinAlƙur'ani ne da Littafi mai bayyanawa

    [2] Shiriya ce da bushara ga muminai

    [3] Waɗanda suke tsayar da salla kuma su bayar da zakka, alhali kuwa su, game da Lahira, to, su, suna yin yaƙini

    [4] Lalle ne waɗanda suke ba su yin imani da Lahira, Mun ƙawata musu ayyukansu, saboda haka suna ɗimuwa

    [5] Waɗannan ne waɗanda suke suna da mugunyar azaba (a duniya), kuma su, a Lahira, su ne mafiya hasara

    [6] Kuma lalle ne haƙiƙa, ana haɗa ka da Alƙur'ani daga gun Mai hikima, Masani

    [7] A lokacin da Musa ya ce wa iyalinsa "Lalle ni, na tsinkayi wata wuta, ni mai zo muku daga gare ta ne, da wani labari, ko kuwa mai zo muku ne da Yula, makamashi, tsammaninku, ku ji ɗimi

    [8] To, a lokacin da ya je mata, sai aka kira shi cewa, "An tsarkake wanda yake cikin (wurin) wutar da yanda yake a gefenta kuma tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin halittu

    [9] Ya Musa lalle ne shi, Ni ne Allah, Mabuwayi, Mai hikima

    [10] Kuma ka jefa sandarka." To, a lokacin da ya gan ta tana girgiza kamar dai ita ƙaramin maciji ne, sai ya juya yana mai bayar da baya, kuma bai koma ba, "Ya Musa! Kada ka ji tsoro lalle Ni, Manzanni ba sujin tsoro a wuriNa

    [11] Sai wanda ya yi zalunci, sa'an nan ya musanya kyau a bayan cuta, to, lalle Ni, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [12] Kuma ka shigar da hannunka a cikin wuyan rigarka, ya fita fari, babu wata cuta, a cikinwasu ayoyi tara zuwa ga Fir'auna da mutanensa. Lalle ne su, sun kasance mutane ne fasiƙai

    [13] To, a lokacin da ayoyinMu suka je musu, suna masu wayar da kai suka ce wannan sihiri ne bayyananne

    [14] Kuma suka yi musunsu, alhali zukatansu sun natsu da su domin zalunci da girman kai. To, ka dubi yadda aƙibar maɓarnata ta kasance

    [15] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun bai wa Dawuda da Sulaiman ilmi kuma suka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah, Wanda Ya fifita mu a kan masu yawa daga bayinSa muminai

    [16] Kuma sulaiman ya gaji Dawuda ya ce: "Ya ku mutane! An sanar da mu maganar tsuntsaye, kuma an ba mu daga kowane abu. Lalle ne wannan haƙiƙa shi ne falalar (Allah) bayyananna

    [17] Kuma aka tattara, domin Sulaiman, rundunoninsa, daga aljannu da mutane da tsuntsaye, to, su ana kange su (ga tafiya)

    [18] Har a lokacin da suka je a kan rafin tururuwa wata tururuwa ta ce, "Ya ku jama'ar tururuwa! Ku shiga gidajenku, kada Sulaiman da rundunoninsa su kakkarya ku, alhali kuwa su, ba su sani ba

    [19] Sai ya yi murmushi yana mai dariya daga maganarta, kuma ya ce, "Ya Ubangijina! Ka cusa mini in gode wa ni'imarKa wadda Ka ni'imta ta a gare ni da kuma ga mahaifana biyu, kuma in aikata aiki na ƙwarai, wanda Kake yarda da shi, kuma Ka shigar da ni, saboda rahamarKa, a cikin bayinKa salihai

    [20] Kuma ya binciki tsuntsaye, sai ya ce: "Me ya kare ni ba ni ganin hudhudu, ko ya kasance daga masu fakuwa ne

    [21] Lalle ne za ni azabta shi azaba mai tsanani ko kuwa lalle in yanka shi, ko kuwa lalle ya zo mini da dalili bayyananne

    [22] Sai ya zauna ba nesa ba, sa'an nan ya ce: "Na san abin da ba ka sani ba, kuma na zo maka daga Saba da wani labari tabbatacce

    [23] Lalle ni na sami wata mace wadda tana mulkinsu kuma an ba ta daga dukkan kome, kuma tana da gadon sarauta mai girma

    [24] Na same ta ita da mutanenta, suna yin sujada ga rana, baicin Allah, kuma Shaiɗan ya ƙawace musu ayyukansu, saboda haka ya karkatar da su daga hanya, sa'an nan su, ba su shiryuwa

    [25] Ga su yi sujada ga Allah Wanda Yake fitar da abin da yake a ɓoye, a cikin sammai da ƙasa, kuma Ya san abin da kuke ɓoyewada abin da kuke bayyanawa

    [26] Allah babu abin bautawa face shi Ubangijin Al'arshi, mai girma

    [27] Ya ce: "Za mu duba shin ka yi gaskiya ne, ko kuwa ka kasance daga maƙaryata

    [28] Ka tafi da takardata wannan, sa'an nan ka jefa ta zuwa gare su, sa'an nan kuma ka juya daga barinsu, sa'an nan ka ga mene ne suke mayarwa

    [29] Ta ce: "Ya ku mashawarta! Lalle ne, an jefo, zuwa gareni, wata takarda mai girma

    [30] Lalle ita daga Sulaiman take, kuma lalle ita da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai ne

    [31] Kada ku yi girman kai a gare ni, kuma ku zo mini kuna masu sallamawa

    [32] Ta ce: "Ya ku mashawarta! Ku yi Mini fatawa ga al'amarina, ban kasance mai yanke wani al'amari ba, sai kun halarta

    [33] Suka ce: "Mu ma'abuta ƙarfi ne, kuma ma'abbuta yaƙi mai tsanani ne, kuma al'amari ya koma zuwa gare ki, saboda haka ki dubamene ne za ki yi umurui (da shi)

    [34] Ta ce: "Lalle sarakuna idan sun shiga wata alƙarya, sai su ɓata ta, kuma su sanya masu darajar mutanenta ƙasƙantattu. Kuma kamar wancan ne suke likatawa

    [35] Kuma lalle ni mai aikawa ce zuwa gare su da kyauta, sa'an nan mai dubawa ce: Da me manzannin za su komo

    [36] To, a lokacin da ya je wa Sulaiman ya ce: "Shin, za ku ƙara ni da dukiya ne? To, abin daAllah Ya ba ni, shi ne mafi alheridaga abin da Ya ba ku. A'a, ku nekuke yin farin ciki da kyautarku

    [37] Ka koma zuwa gare su. Sa'an nan lalle muna je musu da rundunoni, babu wata taɓukawa gare su game da su, kuma lalle muna fitar da su daga gare ta, suna mafi wulakantuwa, kuma suna ƙasƙantattu

    [38] Ya ce: "Ya ku mashawarta! Wannenku zai zo mini da gadonta a gabanin su zo, suna masu sallamawa

    [39] Wani mai ƙarfi daga aljannu ya ce: "Ni ina zo maka da shi a gabanin ka tashi daga matsayinka. Kuma llale ni a gare shi, haƙiƙa, mai ƙarfi ne amintacce

    [40] Wanda yake a wurinsa akwai wani ilmi daga Littafin ya ce: "Ni ina zo maka da shi a gabanin ƙyaftawar ganinka ta koma gare ka." To, a lokacin da ya gan shi matabbaci a wurinsa, ya ce: "Wannan daga falalar Ubangijina yake, domin Ya jarraba ni: Shin, zan gode ne, ko kuwa zan butulce! Kuma wanda ya gode, to, yana godewa ne domin kansa, kuma wanda ya kafirta, to, lalle Ubangijina Wadatacce ne, Karimi

    [41] Ya ce: "Ku canza kamar gadonta gare ta, mu gani, shin za ta shiryu, ko kuwa tana kasancewa daga waɗanda ba su shiryuwa

    [42] To a lokacin da ta je aka ce "Shin, kamar wannan gadon sarautarki yake?" Ta ce: "Kamar dai shine. Kuma an ba mu ilmi daga gabaninta kuma mun kasance masu sallamawar (al'amari ga Allah)

    [43] Kuma abin da ta kasance tana bautawa, baicin Allah, ya kange ta. Lalle ita, ta kasance daga mutane kafirai

    [44] Aka ce mata, "Ki shiga a gidan sarauta." To, a lokacin da ta gan shi, ta yi zatona wai gurbi ne, kuma ta kuranye daga ƙwaurinta. Ya ce: "Lalle ne shi, gidan sarauta ne mai santsi daga madubai." Ta ce: "Ya Ubangijina! Ba a roƙon Allah sai da sunayensa masu kyau, tis'in da taran nan, sai dai a dunƙule kamar a ce, "Ina roƙon Allah da sunayenSa da na sani da waɗanda ban sani ba." Lalle ni, na zalunci kaina, kuma na sallama al'amari tare da Sulaiman ga Allah, Ubangijin halittu

    [45] Kuma lalle ne, haƙiƙa, mun aika zuwa Samudawa da ɗan'uwansu, Salihu (ya ce), "Ku bauta wa Allah." Sai ga su ƙungiyoyi biyu suna ta husuma

    [46] Ya ce: "Ya mutanena! Don me kuke neman gaggawa game da munanawa, a gabanin kyautatawa. Don me ba ku neman Allah gafara, tsammaninku, za a yi muku rahama

    [47] Suka ce: "Muna shu'umci da kai, kuma da wanda ke tare da kai." Ya ce: "Shu'umcinku a wurin Allah yake. A'a, ku mutane ne, ana fitinar ku

    [48] Kuma waɗansu jama'a tara sun kasance a cikin birnin, suna yin ɓarna, kuma ba su kyautatawa. Suka ce: "Ku yi rantsuwa da Allah, lalle za mu kwanan masa, shi da mutanensa sa'an nan mu ce wa waliyyinsa. 'Ba mu halarci halakar mutanensa ba kuma mu, haƙi ƙa, masu gaskiya ne

    [49] Kuma suka ƙulla makirci, kuma Muka ƙulla sakamakon makirci, alhali su ba su sani ba

    [50] Ka duba yadda aƙibar makircinsu ta kasance lalle Mu Mun darkake su da mutanensu, gaba ɗaya

    [51] Waɗancan, gidajensu ne, wofintattu saboda zaluncin da suka yi, lalle ne a wancan akwai aya ga mutane waɗanda suke sani

    [52] Muka tsirar da waɗanda suka yi imani, kuma sun kasance suna taƙawa

    [53] Da Ludu, a lokacin da ya ce wa mutanensa, "Shin kuna je wa alfasha ne, alhali, kuwa kuna gani

    [54] Shin lalle ku haƙiƙa kuna je wa maza da sha'awa baicin mata? A'a, ku wasu irin mutane ne kuna aikin jahilci

    [55] Lalle ne ku, haƙiƙa kuna je wa maza da sha'awa, baicin mata; A'a, ku mutane ne maɓarnata

    [56] Babu abin da ya kasance jawabin mutanensa face suka ce "Ku fitar da mutanen Luɗu daga alƙaryarku, lalle su, wasu irin mutane ne masu da'awar suna da tsarki

    [57] Sai Muka tsirar da shi, shi da mutanensa, face matarsa, Mun ƙaddara ta a cikin masu wanzuwa

    [58] Kuma Muka yi ruwa a kansu da wani irin ruwa. To, ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya munana

    [59] Ka ce: "Godiya ta tabbata ga A1lah, kuma aminci ya tabbata bisa ga bayinSa, waɗanda Ya zaɓa." Shin Allah ne Mafi alheri koabin da suke yin shirki da Shi

    [60] Ko wane ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma Ya saukar muku, daga, sama, wani ruwa, Muka tsirar, game da shi, gonaki masu sha'awa, ba ya kasancewa gare ku, ku tsirar da itacensu? Shin, akwai abin bautawa tare da Allah? A'a, su mutane ne suna daidaitawa (Allah da wani)

    [61] Ko kuwa wane ne Ya sanya ƙasa tabbatacciya, kuma Ya sanya koguna a tsakaninta kuma Ya sanya mata manyan duwatsu tabatattu, kuma Ya sanya wani shamaki a tsakanin tekuna biyu? Shin akwai wani abin bautawa tare da Allah. A'a, mafi yawansu ba su sani ba

    [62] Ko wane ne yake karɓa, kuma ya sanya ku mamayan ƙasa? Shin akwai wani abin bautawa tare da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunani

    [63] Ko wane ne yake shiryarwa a cikin duffan ƙasa da teku, kuma wane ne Yake aikowar iskoki domin bayar da bushara a gaba ga rahamarSa? Ashe akwai wani abin bautawa tare da Allah? tsarki ya tabbata ga Allah daga barin abin da suke shirki da Shi

    [64] Ko wane ne yake fa ra halitta sa'an nan kuma ya mayar da ita, kuma Wane ne Ya azurta ku daga sama da ƙasa? Ashe, akwai wani abin bautawa tare da Allah? Ka ce: "Ku kawo dalilinku idan kun kasance masu gaskiya

    [65] Ka ce: "Babu wanda ya san gaibi a cikin sammai da ƙasa face Allah. Kuma ba su sansancewar a yaushe ne za a tayar da su

    [66] A'a, saninsu ya kai a cikin Lahira A'a, suna cikin shakka daga gare ta. A'a, su da gare ta makafin zuci ne

    [67] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: "Shin idan mun kasance turɓaya, mu da ubanninmu, shin, haƙiƙa, waɗanda ake fitarwa ne

    [68] Lalle ne, haƙiƙa, an yi mana wa'adi ga wannan, mu da ubanninmu, daga gabanin haka. Wannan ba kome ba ne face tatsuniyoyin farko

    [69] Ka ce: "Ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa'an nan ku duba, yaya aƙibar masu laifi take

    [70] Kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma kada ka kasance a cikin ƙuncin rai daga abin da suke ƙullawa na makirci

    [71] Kuma suna cewa, "A yaushe wannan wa'adi (zai auku), idan kun kasance masu gaskiya

    [72] Ka ce: "Akwai fatan sashen abin da kuke, neman gaggawarsa, ya kasance ya kuturta a gare ku

    [73] Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙiƙa Mai falala ne a kanmutane kuma amma mafi yawansu, ba su godewa

    [74] Kuma lalle Ubangijinka, haƙiƙa Yana sanin abin da ƙirazansu suke, ɓoyewa, da abin da suke hayyanawa

    [75] Kuma babu wata (mas'ala) mai boyuwa, a cikin sama da ƙasa face tana a cikin littafi bayyananne

    [76] Lalle ne wannan Alƙur'ani yana gaya wa Bani Israila mafi yawan abin da su suke saɓa wa junansu a ciki

    [77] Kuma lalle shi haƙiƙa shiriya ce da rahama ga muminai

    [78] Lalle Ubangijinka Yana yin hukunci a tsakaninsu da hukuncinsa, kuma Shi ne Mabuwayi, Masani

    [79] Saboda haka, ka dogara ga Allah, lalle ne, kai ne a kan gaskiya bayyananniya

    [80] Lalle ne kai, ba ka jiyar da matattu, kuma ba ka sa kurame su ji kiranka, idan sun juya suna masu bayar da baya

    [81] Kuma kai ba ka zama mai shiryar da ɗimammu daga ɓata ba. Ba ka jiyarwa face wanda yake yin imani da ayoyinMu. To, su ne masu sallamawa (al'amari zuwa ga Allah)

    [82] Kuma idan magana ta auku a kansu, Muna fitar musu da wata dabba daga ƙasa, tana yi musu magana, cewa "Lalle mutane sun kasance game da ayoyinMu, ba su yin imanin yaƙini

    [83] Kuma a ranar da Muke tarawa daga kowace al'umma, wata ƙungiya daga waɗanda suke ƙaryata ayoyinMu, sai ga su ana kangesu. (ga kora)

    [84] Har idan sun zo, (Allah) zai ce, "Ashe kun ƙaryata ayoyinNa, kuma ba ku kewaye su da sani ba? To, mene ne kuka kasance kuna aikatawa

    [85] Kuma magana ta auku a kansu, saboda zaluncin da suka yi. To, su ba su da ta cewa

    [86] Shin, ba su gani ba, cewa, lalle Mu, Mun sanya dare domin su natsu a cikinsa, kuma da yini mai sanya gani? Lalle a cikin wancan akwai ayoyi! Domin mutane waɗanda suka yi imani

    [87] Kuma da ranar da ake husa a cikin ƙaho, sai wandayake a cikin sammai da waɗanda suke a cikin ƙasa su firgita, face wanda Allah Ya so, kuma dukansu, su je Masa suna ƙasƙantattu

    [88] Kuma kana ganin duwatsu, kana zaton su sandararru, alhali kuwa su suna shuɗewa shuɗewar girgije, bisa sana'ar Allah wanda Ya kyautata kowane abu. Lalle Shi, Mai labartawa ne game da abin da kuke aikatawa

    [89] Wanda ya zo da kyakkyawan aiki guda, to, yana da mafi alheri daga gare shi. Kuma su daga wata firgita, a yinin nan, amintattu ne

    [90] Kuma wanda ya zo da mugun aiki, to, an kife fuskokinsu a cikin wuta. Ko za a saka muku face da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [91] (Ka ce): "An umurce ni, in bauta wa Ubangijin wannan Gari, Wanda Ya mayar da shi Hurumi, kuma Yana da dukan kome. Kuma an umurce ni da in kasance daga masu sallamawa

    [92] Kuma ina karanta Alƙur'ani." To, wanda ya shiryu, ya shiryu ne domin kansa kawai. Kuma wanda ya ɓace, to, ka ce: "Ni daga masu gargaɗi kawai nake

    [93] Kuma ka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah. Zai nuna muku ayoyinSa, har ku sansu." Kuma Ubangijinka bai zama Mai shagala daga barin abin da kuke aikatawa ba

    Kissõshi

    Surah 28

    [1] ¦. S. M

    [2] Waɗancan ayoyin Littafi ne bayyananne

    [3] Muna karantawa a kanka daga labarin Musa da Fir'auna da gaskiya domin mutane waɗanda suke yin imani

    [4] Lalle ne Fir'auna ya ɗaukaka a cikin ƙasa, kuma ya sanya mutanenta ƙungiya-ƙungiya, yana raunanar da wata jama'a daga gare su; yana yanyanka ɗiyansu maza kuma yana rayar da matan. Lalle shi ya kasance daga masu ɓarna

    [5] Kuma Muna nufin Mu yi falala ga waɗanda aka raunanar a cikin ƙasar, kuma Mu sanya su shugabanni, kuma Mu sanya su magada

    [6] Kuma Mu tabbatar da su a cikin ƙasar, kuma Mu nuna wa Fir'auna da Hamana da rundunoninsu abin da suka kasance suna sauna daga gare su

    [7] Kuma Muka yi wahayi zuwa ga uwar Musa, cewa ki shayar da shi, sai idan kin ji tsoro game da shi, to, ki jefa shi a cikin kogi, kuma kada ki ji tsoro, kuma kada ki yi baƙin ciki. Lalle ne Mu, Masu mayar da shi ne zuwa gare ki, kuma Masu sanya shi ne a cikin Manzanni

    [8] Sai mutanen Fir'auna suka tsince shi, domin ya kasance maƙiyi da baƙin ciki a gare su. Lalle ne Fir'auna da Hamana da rundunoninsu, sun kasance masu aikin ganganci

    [9] Kuma matar Fir'auna ta ce ("Ka bar shi yana) sanyin ido a gare ni da gare ka! Kada ka kashe shi, akwai fatan ya amfane mu, ko mu riƙe Shi ɗa," alhali kuwa su ba su sansance ba

    [10] Kuma zuciyar uwar Musa ta wayi gari yofintatta. Lalle ne, haƙiƙa, ta yi kusa ta bayyanar da shi, ba domin Mun ɗaure zuciyarta ba, domin ta kasance daga muminai

    [11] Kuma ta ce wa 'yar'uwarsa, "Ki bi shi." Saboda haka sai ta leƙe shi daga gefe, alhali su ba Su sani ba

    [12] Kuma Muka hana masa masu shayai da mama, a gabanin haka sai ta ce: "Ko in nunamuku mutanen wani gida, su yi muku renonsa alhali kuwa su masu nasiha ne a, gare shi

    [13] Sai Muka mayar da shi zuwa ga uwarsa domin idanunta su yi sanyi, kuma ba za ta yi baƙin ciki ba, kuma domin ta san cewa lalle wa'adin Allah gaskiya ne, amma kuma mafi yawansu ba su sani ba

    [14] Kuma a lokacin da ya kai ƙarfinsa, kuma ya daidaita, Mun ba shi hukunci da ilmi kuma kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa

    [15] Kuma sai ya shiga garin a lokacin da mutanen garin suka shagala, sai ya samu, a cikin garin, waɗansu maza biyu suna faɗa, wannan daga ƙungiyarsa, kuma ɗayan daga maƙiyansa, sai wannann da yake daga ƙungiyarsa ya nemi agajinsa, sai Musa ya yi masa ƙulli, ya kashe shi. Ya ce: "Wannan aikin Shaiɗan ne, domin shi maƙiyi ne mai ɓatarwa, bayyananne

    [16] Ya ce: "Ya Uhangijina! Lalle na zalunci kaina, sai Ka yi mini gafara." Sai Ya gafarta masa, domin Shi ne Mai yawan gafara, Mai jin ƙai

    [17] Ya ce: "Ya Ubangijina! Domin abin da Ka ni'imta shi a kaina, sahoda haka ba zan kasance mai taimako ga masu laifi ba

    [18] Sai ya wayi gari a cikin birnin yana mai tsoro, yana sauna. Sai ga wanda ya nemi taimako daga gare shi a jiya, yana neman agajinsa. Musa ya ce masa, "Lalle kai ɓatacce ne, bayyananne

    [19] To, a lokacin da Musa ya yi nufin ya damƙi wanda yake maƙiyi ne a gare su, (mai neman agajin) ya ce, "Ya Musa! Shin kananufin ka kashe ni ne kamar yadda ka kashe wani rai jiya? Ba ka son kome face ka kasance mai tanƙwasawa a cikin ƙasa kuma ba ka nufin ka kasance daga masu kyautatawa

    [20] Kuma wani mutum ya zo daga mafi nisan birnin yana taliya da gaggawa, ya ce: "Ya Musa! Lalle mashawarta suna shawara game da kai domin su kashe ka saboda haka ka fita. Lalle ni, mai nasiha ne a gare ka

    [21] Sai ya fita daga gare ta, yana mai jin tsoro yana sauna. Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka tserar da ni daga mutane azzalumai

    [22] Kuma a lokacin da ya fuskanci wajen Madyana, ya ce: "Ina fatan Ubangijina Ya shiryar da ni a kan madaidaiciyar hanya

    [23] Kuma a lokacin da ya isa mashayar Madyana, ya sami wata jam'ar mutane suna shayarwa, kuma a bayansu ya sami waɗansu mata biyu suna korar (tumakinsu). Ya ce: "Mene ne sha'aninku?" Suka ce, "Ba za mu iya shayarwa ba sai makiyaya sun fita, kuma ubanmu tsoho ne mai daraja

    [24] Sai ya shayar musu, sa'an nan kuma ya juya zuwa ga inuwa, sa'an nan ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne, ga abin da Ka saukar zuwa gare ni na alheri ni mai bukata ne

    [25] Sai ɗayansu ta je masa, tana tafiya a kan jin kunya, ta ce, "Ubana yana kiran ka, domin ya saka maka ijarar abin da ka shayar saboda mu." To, a lokacin da ya je masa, ya gaya masa labarinsa, ya ce: "Kada ka ji tsoro, ka tsira daga mutane azzalumai

    [26] ¦ayarsu ta ce, "Ya Baba! Ka ba shi aikin ijara, lalle ne mafi alherin wanda ka bai wa aikin ijara shi ne mai ƙarfi amintacce

    [27] Ya ce: "Lalle ne ina nufin in aurar da kai ɗayan 'ya'yana biyu, waɗannan, a kan ka yi mini aikin ijara shekara takwas to, idan ka cika goma, to, daga, gare ka yake. Ba ni so in tsananta maka, za ka same ni, in Allah Ya so, daga salihai

    [28] Ya ce: "Wannan yana a tsakanina da tsakaninka kowane ɗayan adadin biyun na ƙare, to, babu wani zalunci a kaina. Kuma Allah ne Wakili ga abin da muke faɗa

    [29] To, a lokacin da Musa ya ƙare adadin kuma yana tafiya da iyalinsa, sai ya tsinkayi wata Wuta daga gefen dutse (¦ur). Ya cewa iyalinsa, "Ku dakata, lalle ne ni, na tsinkayi wata wuta, tsammanina ni, mai zo muku ne daga gare ta da wani labari, ko kuwa da guntun makamashi daga Wutar don ko ku ji ɗimi

    [30] To, a lokacin da ya je wurinta (Wutar) aka kira shi, daga gefen rafin na dama, a cikin wurin nan mai albarka, daga itaciyar (cewa) "Ya Musa! Lalle Ni ne Allah Ubangijin halittu

    [31] Kuma ka jefa sandarka." To, a lokacin da ya gan ta, tana girgiza kamar ƙaramar macijiya, ya juya yana mai bayar da baya, bai koma ba. "Ya Musa! Ka fuskanto, kuma kada ka ji tsoro lalle ne kana daga waɗanda ke amintattu

    [32] Ka shigar da hannunka a cikin wuyan rigarka, ya fita fari, ba da wata cuta ba, kuma ka haɗa hannuwanka ga kafaɗunka, domin tsoro (ya gushe daga gare ka). To, waɗannan abubuwa dalilai biyu ne daga Ubangijinka zuwa ga Fir'auna da 'yan Majalisarsa. Lalle sun kasance mutane ne fasiƙai

    [33] Ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle na kashe wani rai daga gare su, domin haka ina tsoron kada su kashe ni

    [34] Kuma ɗan'uwana Haruna shi ne mafi fasaha daga gareni, ga harshe, saboda haka Ka aika shi tare da ni, yana mai taimako, yana gaskata ni, lalle ne ina tsoron su ƙaryata ni

    [35] Ya ce: "Za Mu ƙarfafa damtsenka game da ɗan'uwanka kuma Mu sanya muku wani dalili, saboda haka ba za su sadu zuwa gareku ba, tare da ayoyinMu, ku da waɗanda suka bi ku ne marinjaya

    [36] To, a lokacin da Musa ya je musu da ayoyinMu bayyanannu, suka ce: "Wannan ba kome ba sai sihiri, wanda aka ƙaga, kuma ba mu ji wannan ba daga wajen ubanninmu na farko

    [37] Kuma Musa ya ce: "Ubangijina ne Mafi sanin wanda ya zo da shiriya daga gare Shi, da wanda aƙibar gida take kasancewa agare shi. Lalle ne masu zalunci ba su cin nasara

    [38] Kuma Fir'auna ya ce: "Ya ku mashawarta! Ban san kuna da wani abin bautawa baicina ba, saboda haka ka hura mini wuta, ya Hamanu! a kan laka (domin a yi tubali), sa'an nan ka sanya mini bene tsammanina zan ninƙaya zuwa ga Ubangijin Musa kuma lalle ne ni, haƙiƙa, ina zaton sa daga maƙaryata

    [39] Kuma ya kangare, shi da rundunoninsa a cikin ƙasa, ba da haƙƙi ba kuma suka zaci cewa su, ba za a mayar da su zuwa gare Mu ba

    [40] Sai Muka kama shi, shi da rundunoninsa sai Muka jefa su a cikin kogi. Sai ka dubi yaddaaƙibar azzalumai ta kasance

    [41] Kuma Muka sanya su shugabanni, suna kira zuwa ga wuta, kuma a Ranar ¡iyama ba za a taimake su ba

    [42] Kuma Muka biyar musu da la'ana a cikin wannan duniyakuma a Ranar ¡iyama suna daga waɗanda aka munana halittarsu

    [43] Kuma lalle ne haƙiƙa, Mun bai wa Musa Littafi daga bayan Mun halakar da ƙarnonin farko, domin su zama abubuwan kula ga mutane, da shiriya da rahama, tsammaninsu suna tunawa

    [44] Kuma ba ka kasance ba ga gefen rafi na yamma a lokacin da Muka hukunta al'amaru zuwa ga Musa, kuma ba ka kasance daga halartattu ba

    [45] Kuma amma Mu, Mun ƙaga halittawar wasu ƙarnoni har lokatan rayuwa suka yi tsawo a kansu. Kuma ba ka kasance mazauni ba a cikin mutanen Madyana, kana karanta musu ayoyinMu, amma Mu Mun kasance masu aikawa (da kai game da waɗancan labarai)

    [46] Kuma ba ka kasance ga gefen dutse ba a lokacin da Muka yi kira, kuma amma domin rahama daga Ubangijinka, domin ka yi gargaɗi ga mutane waɗanda suke wani mai gargaɗi a gabaninka bai je musu ba, tsammaninsu suna tunawa

    [47] Kuma ba domin wata masifa ta same su ba saboda abin da hannayensu suka gabatar, su ce: "Ya Ubangijinmu! Don me ba Ka aiko wani Manzo zuwa gare mu ba, har mu dinga bin ayoyinKa, kuma mu kasance daga muminai

    [48] Sa'an nan a lokacin da gaskiya ta je musu daga wurinMu, suka ce: "Don me ba a ba shi kamar abin da aka bai wa Musa ba?" Shin kuma ba su kafirta ba da abin da aka bai wa Musa a gabanin (wannan)? suka ce: "Sihirori biyu ne suka taimaki juna," kuma suka ce: "Lalle ne mu, masu kafirta ne ga dukansu

    [49] Ka ce: "To ku zo da wani littafi daga, wurin Allah, wanda yake shi ne mafi shiryarwa daga gare su, in bi shi, idan kunkasance masu gaskiya

    [50] To, idan ba su karɓa maka ba to sai ka sani suna bin son zuciyarsu ne kawai, kuma wane ne mafi ɓata daga wanda ya bi son zuciyarsa, ba tare da wata shiriya daga Allah ba? Lalle ne, Allah ba ya shiryar da mutane azzalumai

    [51] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun sadar da magana saboda su, tsammaninsu, suna tunani

    [52] Waɗanda Muka ba su littafi daga gabaninsa (Alƙur'ani), su masu imani ne da shi

    [53] Kuma idan ana karanta shi a kansu, sai su ce: "Mun yi imani da shi, lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinmu. Lalle mu, mun kasance a gabaninsa masu sallamawa

    [54] Waɗancan ana ba su ladarsu sau biyu, saboda haƙurin da suka yi, kuma da kyautatawa suna tunkuɗewar munanawa kuma daga abin da Muka azurta susuna ciyarwa

    [55] Kuma idan sun ji yasassar magana sukan kau da kai daga barinta, kuma sukan ce, "Ayyukanmu suna a gare mu, kuma ayyukanku suna a gare ku, aminci ya tabbata a kanmu ba mu neman jahilai (da husuma)

    [56] Lalle ne kai ba ka shiryar da wanda ka so, amma kuma Allah Yana shiryar da wanda Yake so, kuma Shi ne Mafi sani daga masu shiryuwa

    [57] Kuma suka ce: "Idan mun bi shiriya tare da kai ana fizge mu daga ƙasamiu." Shin, ba Mu tabbatar musu da mallakar Hurumi ba, ya zama amintacce, ana jawowa zuwa gare shi, 'ya'yan itacen kowane iri, bisa ga azurtawa daga gare Mu? Amma kuma mafi yawansu ba su sani ba

    [58] Kuma da yawa Muka halakar da wata alƙarya wadda ta yi butulci ga rayuwarta. To, waɗancan gidajensu ne, ba a zaune su ba, a bayansu, face kaɗan. Kuma mun kasance Mu ne Magada

    [59] Kuma Ubangijinka bai kasance Mai halaka alƙaryu ba, sai Ya aika a cikin hedkwatarsu da wani Manzo yana karanta ayoyinMu a kansu. Kuma ba Mu kasance Masu halaka alƙaryu ba, face mutanensu sun kasance masu zalunci

    [60] Kuma abin da aka ba su daga kome, to, jin daɗin rayuwar duniya ne da ƙawarta. Kuma abin da ke wurin Allah, shi ne mafi alheri, knma mafi wanzuwa. Shin ba ku hankalta

    [61] Shin fa, wanda Muka yi wa wa'adi, wa'adi mai kyau, sa'an nan shi mai haɗuwa da shi ne, yana zama kamar wanda Muka jiyar da shi ɗan daɗi, daɗin rayuwar duniya, sa'an nan shi a Ranar ¡iyama yana daga masu shiga wuta

    [62] Kuma ranar da (Allah) Yake kiran su sa'an nan Ya ce: "Ina abokan tarayyaTa, waɗanda kuka kasance kuna riyawa

    [63] Waɗanda magana ta wajaba a kansu, su ce: "Ya Ubangijinmu! Waɗannan su ne waɗanda muka halakar mun halakar da su kamar yadda muka halaka. Mun barranta zuwa gare Ka, ba su kasance mu suke bauta wa ba

    [64] Kuma a ce ku kirawo abokan tarayyar ɗinku, sai su kira su, sai ba su amsa ba, kuma su ga azabar. Da dai lalle su sun kasance snna shiryuwa

    [65] Kuma ranar da Yake kiran su, sa'an nan Ya ce: "Mene nekuka karɓa wa Mananni

    [66] Sai labaru su ɓace musu a ranar nan sa'an nan ba za su tambayi junaosu ba

    [67] To, amma wanda ya tuba, kuma ya yi imani' ya aikata aiki na ƙwarai, to, akwai fatan su kasance daga masu cin nasara

    [68] Kuma Ubangijinka Yana halitta abin da Yake so kuma Yake zaɓi. Zaɓi bai kasance a gare su ba. Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma (Allah) Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka

    [69] Kuma Ubangijinka Yana sanin abin da zukatansu ke ɓoyewa, da abin da suke bayyanawa

    [70] Kuma Shi ne Allah, babu abin bautawa face Shi. Kuma Shi ne abin godiya a cikin ta farko (duniya), da ta ƙarshe (Lahira). Kuma Shi ne da hukunci, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [71] Ka ce: "Shin, kun gani, idan Allah Ya sanya dare tutur a kanku har zuwa Ranar ¡iyama, wane abin bautawa wanin Allah zai zo muku da haske? Shin, ba ku ji

    [72] Ka ce: "Shin, kun gani, idan Allah Ya sanya yini a kanku tutur zuwa Ranar ¡iyama, wane abin bautawa, wanin Allah, zai zo muku da dare wanda kuna natsuwa a cikinsa? Shin fa, ba ku gani

    [73] Kuma daga rahamarSa Ya sanya muku dare da yini domin ku natsu a cikinsa, kuma domin ku nema daga falalarSa, kuma tsammaninku za ku gode

    [74] Kuma a ranar da Yake kiran su ya ce: "Ina abokan tarayya Ta, waɗanda kuka kasance kuna riyawa

    [75] Kuma Muka zare mai shaida daga kowace al'umma, sa'an nan Muka ce: "Ku kawo dalilinku." Sai suka san cewa lalle gaskiya ga Allah take. Kuma abin da suka kasance suna ƙirƙirawa na ƙarya ya ɓace daga barinsu

    [76] Lalle ne ¡aruna ya kasance daga mutanen Musa, sai ya fita daga tsarinsu alhali Mun ba shi taskokin abin da yake mabuɗansa suna nauyi ga jama'a ma'abuta ƙarfi a lokacin da mutanensa suka ce masa, "Kada ka yi annashuwa, lalle ne Allah ba Ya son masu annashuwa

    [77] Kuma ka biɗa a cikin abin da Allah Ya ba ka, gidan Lahira, kuma kada ka manta da rabonka daga duniya. Kuma ka kyautata, kamar yadda Allah Ya kyautata zuwa gare ka, kuma kada ka nemi ɓarna a cikin ƙasa, lalle ne Allah ba Ya son masu barna

    [78] Ya ce: "An ba ni shi a kan wani ilmi wanda yake gare ni ne kawai." Shin, kuma bai sani ba cewa lalle Allah haƙiƙa Ya halakar a gabaninsa, daga ƙarnoni, wanda yake Shi ne mafi tsananin ƙarfi daga gare shi, kuma mafi yawan tarawar dukiya, kuma ba za a tambayi masu laifi daga zunubansu ba

    [79] Sai (¡aruna) ya fita a kan mutanensa a cikin adonsa. Waɗanda suke nufin rayuwar duniya suka ce: "Ina dai muna da kwatancin abin da aka bai wa ¡aruna! Lalle shi haƙiƙa ma'abucin rabo babba ne

    [80] Kuma waɗanda aka bai wa ilmi suka ce: "Kaitonku! sakamakon Allah ne mafi alheri a wanda ya yi tunani, kuma ya aikata aikin ƙwarai, kuma babu wanda ake haɗawa da ita face mai ha ƙuri

    [81] Sai Muka shafe ƙasa da shi da kuma gidansa. To, waɗansu jama'a ba su kasance gare shi ba, waɗanda suke taimakon sa, baicin Allah, kuma shi bai kasance daga masu taimakon kansu ba

    [82] Kuma waɗanda suka yi burin matsayinsa a jiya suka wayi gari suna cewa, "Wai! Allah Yana shimfiɗa arziki, ga wanda Yake so daga bayinsa, kuma Yana ƙuntatawa. Ba domin Allah Ya yi mana falala ba da Ya shafe ƙasa da mu. Wai! lalle ne shi, kafirai ba su cin nasara

    [83] Wancan gidan Lahira Muna sanya shi ga waɗanda suke ba su nufin ɗaukaka a cikin rayuwar duniya kuma ba su son ɓarna. Kuma akiba ga masu taƙawa take

    [84] Wanda ya zo da abu mai kyau, to, yana da mafi alheri daga gare shi, kuma wanda ya zo da mugun abu, to, ba za a sakawa waɗanda suka aikata miyagun ayyuka ba, face da abin da suka kasance suna aikatawa

    [85] Lalle ne wanda Ya faralta Alƙur'ani a kanka, haƙiƙa, Mai Mayar da kai ne zuwa ga makoma. ka ce: "Ubangijina ne Mafi sani ga wanda ya zo da shiriya, da kuma wanda yake a cikin ɓata bayyananna

    [86] Kuma ba ka kasance kana fatan a jefa Littafin nan zuwa gare ka ba, face dai domin rahama daga Ubangijinka. Saboda haka kada ka zama mai taimako ga kafirai

    [87] Kuma kada lalle su karkatar da kai daga barin ayoyin Allah, a bayan har an saukar da su uwa gare ka. Ka yi kira zuwa ga Ubangijinka, kuma kada lalle ka kasance daga masu shirka

    [88] Kada ka kira wani abin bautawa na dabam tare da Allah. Babu abin bautawa face Shi. Kowane abu mai halaka ne face fuskarSa. Shi ne da hukunci kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku

    Ankabut

    Surah 29

    [1] L. M

    [2] Ashe, mutane sun yi zaton a bar su su ce: "Mun yi imani," alhali kuwa ba za a fitine su ba

    [3] Kuma lalle Mun fitini waɗanda ke a gabaninsu, domin lalle Allah Ya san waɗanda suka yi gaskiya, kuma lalle Ya san maƙaryata

    [4] Ko waɗanda ke aikata miyagun ayyuka sun yi zaton su tsere Mana? Abin da suke hukuntawa ya munana

    [5] Wanda ya kasance yana fatan gamuwa da Al1ah to lalle ajalin Allah mai zuwa ne, kuma (Allah) Shi ne Mai ji, Masani

    [6] Kuma wanda ya yi jihadi, to, yana yin jihadin ne domin kansa. lalle Allah haƙiƙa waɗatacce ne daga barin talikai

    [7] Kuma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle Muna kankare musu miyagun ayyukansu, kuma lalle Muna saka musu da mafi kyaun abin da suka kasance suna aikatawa

    [8] Kuma Mun yi wa mutum wasiyyar kyautatawa ga uwayensa, kuma idan sun tsananta maka domin ka yi shirki da Ni game da abin da ba ka da ilmi gare shi, to, kada ka yi musu ɗa'a. Zuwa gare Ni makomarku take sa'an nan In ba ku labari ga abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [9] Kuma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle Muna shigar da su a cikin mutanen kirki

    [10] Kuma daga cikin mutane akwai mai cewa, 'Mun yi imani da Allah" sa'an nan idan aka cuce shi wajen aikin Allah, sai ya sanya fitinar mutane kamar azabar Allah kuma lalle idan taimakon Ubangijinka ya zo, haƙiƙa, ya kan ce: "Lalle mu mun kasance tare da ku." shin, Allah bai zama Mafi sani ba ga abin da ke a cikin ƙirazan halittunSa

    [11] Kuma lalle Allah na sanin waɗanda suka yi imani kuma lalle Yana sanin munfukai

    [12] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce wa waɗanda suka yi imani, "Ku bi hanyarmu, kuma Mu ɗauki laifuffukanku," alhali kowa ba su zamo masu ɗauka da a kome ba daga laifuffukansu. Lalle su maƙaryata ne

    [13] Kuma lalle suna ɗaukar kayan nauyinsu da waɗansu nauyayan kaya tare da kayan nauyinsu, kuma lalle za a tambaye su a Ranar ¡iyama game da abin da suka kasance suna ƙirƙirawa na ƙarya

    [14] Kuma lalle Mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya zauna a cikinsu shekara dubu face shekara hamsin, sa'an nan cikowar (¦ufana) ta kama su, alhali kuwa su ne masu zalunci

    [15] Sa'an nan Muka tsirar da shi da mutanen jirgin, kuma Muka sanya jirgin ya zama wata aya ga talikai

    [16] Da Ibrahim a lokacin da ya ce wa mutanensa, "Ku bauta wa Allah ku bi Shi da taƙawa. Wannan Shi ne alheri a gare ku idan kun kasance kuna sani

    [17] Abin da dai kuke bautawa, baiein Allah, gumaka ne, kuma kun ƙirƙira ƙarya. Lalle waɗannan da kuke bauta wa baicin Allah, ba su mallaka muku arziki. Saboda haka ku nemi arziki a wurin Allah kawai, kuma ku bauta Masa, kuma ku yi godiya zuwa gare Shi. Zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [18] Kuma idan kun ƙaryata, to, lalle waɗansu al'ummomi a gabaninku sun ƙaryata, kuma babu abin da ke kan Manzo, face iyar da manzanci, iyarwa bayyananna

    [19] Shin, ba su ga yadda Allah ke fara yin halitta ba, sa'an nan kuma Ya mayar da ita? Lalle wannan abu ne mai sauƙi ga Allah

    [20] Ka ce: "Ku yi tafiya cikin ƙasa, sa'an nan ku duba yadda (Allah) Ya fara yin halitta, sa'an nan kuma Allah Yana ƙaga wata halittar mayarwa. Lalle Allah Mai ikon yi ne a kan kome

    [21] Yana azabta wanda Ya so, kuma Yana jin ƙan wanda Ya so. Kuma zuwa gare shi ake juyaku

    [22] Kuma ba ku zamo masu buwaya ba a cikin ƙasa, kuma haka a cikin sama kuma ba ku da wani majiɓinci wanda ba Allah ba, kuma ha ku da wani mataimaki

    [23] Kuma waɗanda suka kafirta da ayoyin Allah da gamuwa da shi, waɗannan sun yanke ƙauna daga rahamaTa kuma waɗannan suna da wata azaba mai raɗaɗi

    [24] Sa'an nan babu abin da ya kasance jawabin mutanensa (Ibrahim) face dai suka ce: "Ku kashe shi ko, ku ƙona shi," Sai Allah Ya tsirar da shi daga wuta. Lallea cikin wannan akwai ayoyi ga mutanen da ke yin imani

    [25] Kuma Ibrahim ya ce "Babu abin da kuka yi sai dai kub bar Allah kun riƙi gumaka saboda soyayyar tsakaninku a cikin rayuwar duniya, a'an nan a Ranar ¡iyama sashinku zai kafirce wa sashi, kuma makomarku ita ce wuta kuma ba ku da waɗansu mataimaka

    [26] Sai Luɗu ya yi imani da shi. Kuma Ibrahim ya ce: "Lalleni mai ƙaura ne zuwa ga Ubangijina. Lalle Shi Shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [27] Kuma Muka ba shi Ishaƙa da Ya'aƙuba, kuma Muka sanya Annabci da littafi a cikin zuriyarsa. Kuma Mun ba shi sakamakonsa a duniya, kuma lalle shi a Lahira, tabbas, yana a cikin salihai

    [28] Da Luɗu, a lokacin daya ce wa mutanensa, "Lalle ku, haƙiƙa kuna je wa alfasha wadda wani mahaluƙi daga cikin duniya bai riga ku gare ta ba

    [29] Ashe, lalle ku kuna je wa maza, kuma ku yi fashin hanya kuma ku je, a cikin majalisarku da abin da ba shi da kyau? To, jawabin mutanensa bai kasance ba face dai sun ce: 'Ka zo mana da azabar Allah, idan ka kasance daga masu gaskiya

    [30] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka taimake ni a kan mutanen nan maɓarnata

    [31] Kuma a lokacin da ManzanninMu suka je wa Ibrahim da bushara suka ce: "Lalle mu masu halaka mutanen, wannan alƙarya ne. Lalle mutanenta sun kasance masu zalunci

    [32] Ya ce: "Lalle akwai Luɗu a cikinta!" Suka ce: "Mu ne mafiya sani ga waɗanda suke a cikinta, lalle muna tsirar da shi da mutanensa, face fa matarsa ta kasance a cikin masu wanzuwa

    [33] Kuma a lokacin da ManzanninMu suka je wa Luɗu ya ɓata rai saboda su, kuma ya ƙuntata ga kirji saboda su. Kuma suka ce: "Kada ka ji tsoro kuma kada ka yi baƙin ciki lalle mu masu tsirar da kai ne da iyalanka, face dai matarka ta kasance daga masu wanzuwa

    [34] Lalle mu, masu saukar da azaba ne daga sama a kan mutanen wannan alƙarya saboda abin da suka kasance suna yi na fasiƙanci

    [35] Kuma lalle Mun bar wata aya bayyananna daga gare ta ga mutane masu hankalta

    [36] Kuma zuwa ga Madyana, Mun aika ɗan'uwansu shu'aibu, sai ya ce: "Ya mutanena! Ku bauta wa Allah kuma ku yi fatan (rahamar) Ranar Lahira, kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa, alhali kuwa kuna masu lalatarwa

    [37] Sai suka ƙaryata shi, saboda haka tsawa ta kama su, domin haka suka wayi gari suna guggurfane

    [38] Da Adawa da Samudawa alhali kuwa lalle alamun azaba sun bayyana a gare su daga gidajensu kuma Shaiɗan ya ƙawata musu ayyukansu, saboda haka ya kange su daga hanyar Allah, kuma sun kasance masu basira

    [39] Kuma ¡aruna da Fir'auna da Hamana, kuma lalle Musaya je musu da hujjoji, sai suka yi girman kai a cikin ƙasa kuma ba su kasance masu tserewa ba

    [40] Saboda haka kowanensu Mun kama shi da laifinsa. Watau daga cikinsu akwai wanda Muka aika iskar tsakuwa a kansa kuma daga cikinsu akwai wanda tsawa ta kama, kuma daga cikinsu akwai wanda Muka birkice ƙasa da shi kuma daga cikinsu akwai wanda Muka nutsar. Ba ya yiwuwa ga Allah Ya zalunce su, amma sun kasance kansu suke zalunta

    [41] Misalin waɗanda suka riƙi waɗansu masoya waɗanda ba Allah ba, kamar misalin gizogizo ne wanda ya riƙi wani ɗan gida, alhali kuwa lalle mafi raunin gidaje, shi ne gidan gizogizo, da sun kasance suna sane

    [42] Lalle Allah Yana sane da abin da suke kira wanda ba Shi ba na wani abu duka kuma shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [43] Kuma waɗancan misalan Muna bayyana su ga mutane kuma babu mai hankalta da su sai masu ilmi

    [44] Allah Ya halitta sammai da ƙasa da gaskiya. Lalle cikin wancan akwai aya ga muminai

    [45] Ka karanta abin da ake yin wahayi zuwa gare ka daga Littafi, kuma ka tsayar da salla. Lalle salla tana hanawa daga alfasha da abni ƙyama, kuma lalle ambaton Allah ya fi girma, kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa

    [46] Kada ku yi jayayya da mazowa Littafi sai fa da magana wadda ta fi kyau, sai fa waɗanda suka yi zalunci daga gare su, kuma ku ce, "Mun yi imani da abin da aka saukar a gare mu kuma aka saukar a gare ku, kuma Abin bautawarmu da Abin bautawarku Guda ne, kama mu masu sallamawa ne a gare shi

    [47] Kuma kamar haka Muka saukar da Littafi a gare ka, to, waɗannan da Muka bai wa Littafi sana imani da shi, daga cikin waɗannan akwai mai imani da shi, kuma babu mai musun ayoyinMu, face kafirai

    [48] Kuma ba ka kasance kana karatun wani littafi ba a gabaninsa, kuma ba ka rubutunsa da damanka da haka ya auku, da masu ɓarna sun yi shakka

    [49] A'a, shi ayoyi ne bayyanannu a cikin ƙirazan waɗanda aka bai wa ilmi. Kuma babu mai musun ayoyinMu face azzalumai

    [50] Kuma suka ce: "Don me ba a saukar masa da ayoi ba daga Ubangijinsa? "Ka ce: "Su ayoyi a wurin Allah kawai suke, kuma lalle ni mai gargaɗi kawai ne, mai bayyanawa

    [51] Shin bai ishe su ba cewa lalle Mu, Mun saukar da Littafin akanka, ana karanta shi a kansu? Lalle a cikin wancan haƙiƙa akwai rahama da tunatawa ga mutanen da ke yin imani

    [52] Ka ce: "Allah Ya isa shaida a tsakanina da tsakaninku Yana sane da abin da ke a cikin sammai da ƙasa, kuma waɗanda suka yi imani da ɗarya kuma suka kafirta da Allah, waɗannan su nemasu hasara

    [53] Kuma suna neman ka da gaggauta azaba, to, ba domin ajali ƙayyadadde ba, da azaba ta je musu kuma lalle da tana iske su bisa ia abke, alhali kuwa su ba su sani ba

    [54] Suna neman ka da gaggauta azaba, kuma lalle Jahannama, tabbas, mai kewayewa ce gakafirai

    [55] Ranar da azaba ke rufe su daga samansu da kuma ƙasan ƙafafunsu kuma Ya ce: "Ku ɗanɗani abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [56] Ya bayiNa, waɗanda suka yi imani! Lalle fa ƙasaTa mai yalwa ce, sabada haka ku bauta Mini

    [57] Kowane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne, sa'an nan zuwa gare Mu ake mayar da ku

    [58] Kuma waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, lalle za Mu zaunar da su daga cikin Aljanna a gidajen bene, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu. To, madalla da sakamakon masu aikin ƙwarai

    [59] Waɗanda suka yi haƙuri, kuma suna dogara ga Ubangijinsu kawai

    [60] Kuma da yawa dabba wadda ba ta ɗaukar abincinta Allah Yana ciyar da ita tare da ku, kuma Shi ne Mai ji, Mai ilmi

    [61] Lalle idan ka tambaye su: "Wane ne ya halitta sammai da ƙasa kuma ya hore rana da wata?" Lalle suna cewa Allah ne. TO, yaya ake karkatar da su

    [62] A1lah ne ke shimfiɗa arziki ga wanda Yake so daga cikin bayinsa kuma Yana ƙuntatawa ga (wanda, Yake so). Lalle Allah, Masani ne ga dukan kome

    [63] Kuma lalle idan ka tambaye su. "Wane ne ya saukar da ruwa daga sama, har ya rayar da ƙasa game da shi a bayan mutuwarta?" Lalle suna cewa, "Allah ne." Ka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah." A'a, mafi yawansu ba su hankalta

    [64] Kuma wannan rayuwa ta duniya ba ta zamo ba, face abar shagala da wasa kuma lalle Lahira tabbas, ita ce rayuwa, da sun kasance suna sani

    [65] To, a lokacin da suka shiga cikin jirgin ruwa, sun kirayi Allah suna masu tsarkake addini a gare shi, to, a lokacin da Ya tsirar da su zuwa ga tudun ƙasa, sai ga su suna shirki

    [66] Domin su kafirce wa abin da Muka ba su kuma domin su ji daɗi sa'an nan kuma za su sani

    [67] Shin, ba su ga cewa, lalle Mun sanya Hurumi amintacce ba alhali kuwa ana fisge mutane a gefensu? Shin, da ɓataccen abu suke imani kuma da ni'imarAllah suka kafirta

    [68] Kuma wane ne ya fi zalunci bisa ga wanda ya ƙirƙira ƙarya ya jingina ta ga Allah, ko kuma ya ƙaryata gaskiya a lokacin da ta je masa? Ashe a cikin Jahannama babu mazauna ga kafirai

    [69] Kuma wadannan da suka yi ƙoƙari ga neman yardarMu, lalle Muna shiryar da su ga hanyoyinMu, kuma lalle Allah, tabbas, Yana tare da masu kyautatawa (ga addininsu)

    Rum

    Surah 30

    [1] L. M

    [2] An rinjayi Rumawa

    [3] A cikin mafi kusantar ƙasarsu, kuma su, a bayan rinjayarsu, za sn rinjaya

    [4] A cikin'yan shekaru. Al'amari na Allah ne a gabanin kome da bayansa, kuma a ranar nan muminai za su yi farin ciki

    [5] Da taimakon Allah Yana taimakon wanda Yake so. Kuma Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [6] Wa'adin Allah, Allah ba ya saɓawa ga wa'adinsa, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [7] Suna sanin bayyanannar rayuwar duniya, alhali kuwa su shagalallu ne daga rayuwar Lahira

    [8] Shin, ba su yi tunani ba a cikin zukatansu cewa Allah bai halitta sammai da ƙasa ba da abin da ke tsakaninsu, face da gaskiya da ajali ambatacce? Kuma lalle masu yawa daga mutane kafirai ne ga gamuwa da Ubangijinsu

    [9] Shin, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasa domin su gani yadda aƙibar waɗanda ke a gabaninsu ta kasance? Sun kasance mafiya ƙarfi daga gare su kuma suka nomi ƙasa suka raya ta fiye da yadda suka raya ta, kuma manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu. Sabo da haka Allah ba Ya yiwuwa Ya zalunce su, amma kansu suka kasance suna zalunta

    [10] Sa'an nan aƙibar waɗannan da suka aikata mugun aiki ta kasance mafi muni, watau sun ƙaryata game da ayoyin Allah, kuma suka kasance suna izgili da su

    [11] Allah ne ke fara yin halitta, sa'an nan Ya sake ta sa'an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [12] Kuma a ranar da sa'a ke tsayuwa, masu laifi za su kasa magana

    [13] Kuma ba su da masu ceto daga abubuwan shirkinsu, kuma snn kasance masu kafircewadaga abubuwan shirkinsu

    [14] Kuma a ranar da Sa'a ke tsayuwa, a ranar nan mutane ke farraba

    [15] To, amma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai to su ana faranta musu rayuka, a cikin wani lambu

    [16] Kuma waɗanda suka kafirta, kuma suka ƙaryata, game da ayoyinMu da kuma haɗuwa da Ranar Lahira, to, waɗancan ana halartar da su a cikin azaba

    [17] Saboda haka tsarkakewa ta tabbata ga Allah a lokacin da kuke shiga maraice, da lokacin da kuke shiga safiya

    [18] Kuma Shi ne da godiya, a cikin sammai da ƙasa kuma da lokacin yamma da lokacin zawali

    [19] Yana fitar da mai rai daga matacce kuma Yana fitar da matacce daga mai rai, kuma Yana rayar da ƙasa a bayan mutuwarta. Kuma haka ake fitar da ku

    [20] Kuma akwai daga ayoyinSa, Ya halitta ku daga turɓaya, sai ga ku kun zama mutum, kuna watsuwa

    [21] Kuma akwai daga ayoyinsa, Ya halitta muku matan aure daga kanku, domin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya sanya soyayya da rahama a tsakaninku. Lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga mutane masu yin tunani

    [22] Kuma akwai daga ayoyinSa halittar sammai da ƙasa da saɓa, war harsunanku, da launukanku. Lalle a cikin wannan akwai ayoyi ga masu ilmi

    [23] Kuma akwai daga cikin ayoyinSa, barcinku a cikin dare da rana, da nemanku ga falalarsa. Lalle a cikin wannan akwai ayoyi ga mutane masu saurarawa

    [24] Kuma akwai daga cikin ayoyinSa, Ya nuna muku walƙiya a kan tsoro da ɗammani kuma Ya dinga saukar da ruwa daga sama Sa'an nan Ya rayar da ƙasa game da shi a bayan mutuwarta. Lalle a cikin wannan akwai ayoyi ga mutane masu hankaltawa

    [25] Kuma akwai daga ayoyinsa, tsayuwar sama da asƙa bisa umurninsa, sa'an nan idan Ya kira ku, kira ɗaya, daga ƙasa, sai ga ku kuna fita

    [26] Kuma wanda ke cikin sammai da ƙasa Nasa ne shi kaɗai. Dukansu masu tawali'u ne a gare Shi

    [27] Kuma Shi ne Wanda Ya fara halitta, sa'an nan Ya sake ta kuma sakewarta ta fi sauƙi a gare shi. Kuma Yana da misali wanda ya fi ɗaukaka a cikin sammai da ƙasa kuma Shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [28] Ya buga muku wani misali daga kanku. Ko kuna da abokan tarewa, daga cikin bayin da hannayenku na dama suka mallaka, a cikin arzikinku, watau ku zama daidai a ciki kuna tsoron su kamar tSoronku ga kanku? Haka dai Muke bayyana ayoyi, daki-daki, ga mutane masu hankaltawa

    [29] A'aha! waɗanda suka yi za1unci sun bi son zuciyoyinsu, ba tare da wani ilmi ba. To wane ne zai shiryar da wanda Allah Ya ɓatar, kuma ba su da waɗansu mataimaka

    [30] Saboda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini, kana mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutane a kanta. Babu musanyawa ga halittar Allah, wannan shi ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [31] Kuna masu mai da al'amari gare Shi, kuma ku bi Shi dataƙawa, kuma ku tsayar da salla, kuma kada ku kasance daga mushirikai

    [32] Watau waɗanda suka rarrabe addininsu kuma suka kasance ƙungiya-ƙungiya, kowace ƙungiya tana mai farin ciki da abin da ke a gare ta kawai

    [33] Kuma idan cuta ta shafi mutane, sai su kirayi Ubangijinsu, suna masu mai da al'amari gare Shi, sa'an nan idan Ya ɗanɗana musu wata rahama daga gare Shi, sai ga wani ɓangare daga gare su suna shirki da Ubangijinsu

    [34] Domin su kafirta dl abin da Muka ba su. To ku ji daɗi kaɗan Sa'an nan za ku, sani

    [35] Ko Mun saukar da wani dali li a gare su? Shi kuwa yana magana da abin da suka kasance suna shirkin da shi

    [36] Kuma idan Muka ɗanɗana wa mutane wata rahama, sai su yi farin ciki da ita kuma idan cuta ta same su, saboda abin da hannayensu suka gabatar, sai ga su suna yanke ƙauna

    [37] Shin, kuma ba su gani ba cewa Allah na shimfida arziki ga wanda Yake so kuma Yana ƙuntatawa? Lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga mutane masu yin imani

    [38] Saboda haka ka bai wa zumu hakkinsa da miskinai da ɗan hanya, wannan shi ne alheri ga waɗanda ke nufin yardar Allah kuma waɗancan su ne masu samun babban rabo

    [39] Kuma abin da kuka bayar na riba domin ya ƙaru a cikin dukiyar mutane to, ba zai ƙaru ba, a wurin Allah. Kuma abin da kuka bayar na zakka, kana nufin yardar Allah to (masu yin haka) waɗancan su ne masu ninkawa (ga dukiyarsu)

    [40] Allah ne Wanda Ya halitta ku, sa'an nan Ya azurta ku, sa'an nan Ya matar da ku, sa'an nan Ya rayar da ku. Ashe, daga cikin abubuwan shirkinku akwai wanda ke aikata wani abu daga waɗannan ahubuwa? Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma Ya ɗaukaka bisa ga abin da suke yi na shirki

    [41] ¥arna ta bayyana a cikin ƙasa da teku, saboda abin da hannayen mutane suka aikata. Domin Allah Ya ɗanɗana musu sashin abin da suka aikata, ɗammaninsu za su komo

    [42] Ka ce: "Ku tafi a cikin ƙasa sa'an nan ku dubi yadda aƙibar waɗanda suka kasance a gabaninku ta kasance. Mafi yawansu sun kasance masu yin shirki

    [43] Saboda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini madaidaici a gabanin wani yini ya zo, babu makawa gare Shi daga Allah, a ranar nan mutane suna tsagewa (su rabu biyu)

    [44] Wanda ya kafirta, to, kafircinsa na kansa, kuma wanda ya aikata aikin ƙwarai, to, saboda kansu suke yin shimfiɗa

    [45] Domin Ya saka wa waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga falalarSa. Lalle Allah ba Ya son kafirai

    [46] Kuma akwai daga ayoyinSa, ya aika iskoki masu bayar da bushara kuma domin Ya ɗanɗana muku daga rahamarSa, kuma domin jiragen ruwa su gudana da umurninSa, kuma domin ku nema daga falalarSa, fatanku za ku gode

    [47] Kuma lalle Mun aiki waɗansu Manzanni a gabaninka, zuwa ga mutanensu sai suka je musu da hujjoji, bayyanannu, sa'an nan Muka azabtar da waɗanda suka yi laifi, kuma ya kasance tabbatacce taimakon muminai wajibi ne a kan mu

    [48] Allah ne Wanda ke aika iskoki, sai su motsar da girgije, sa'an nan Ya shimfiɗa shi a cikin sama yadda Yake so, kuma Ya sanya shi wani ɓaɓɓake, sa'an nan ka ga ruwa na fita daga tsakaninsa. Sa'an nan idan Allah Ya sami waɗanda Ya so daga bayinsa, Sai ga su suna bushara da shi

    [49] Kuma ko da sun kasance a gabanin a saukar da shi a kansu, kusa-kusa, suna baƙin ciki hai ba su iya magana

    [50] Sai ka dubi alamomin rahamar Allah yadda Yake rayar da ƙasa a bayan mutuwarta. Lalle wannan (Mai wannan aiki), tabbas, Mai rayar da halitta ne, kuma Shi Mai ikon yi ne a kan kome

    [51] Kuma lalle idan Mun aika wata iska, suka ganta fatsifatsi, lalle za su yini a bayansa suna kafirta

    [52] Saboda haka, kai, ba ka jiyar da matattu kira, kuma ba ka jiyar da kurame kira idan sun juya baya suna gudu

    [53] Kuma ba ka zamo mai shiryar da makafi ba daga ɓatarsu, ba ka jiyarwa face wanda ke yin imani da ayoyinMu, watau su ne masu miƙa wuya, su sallama

    [54] Allah ne Ya halitta ku daga rauni, sa'an nan Ya sanya wani ƙarfi a bayan wani rauni, sa'an nan Ya sanya wani rauni da furfura a bayan wani ƙarfi, Allah na halitta abin da Ya so, kuma Shi ne Mai ilmi, Mai ikon yi

    [55] Kuma a ranar da Sa'a ke tsayuwa, masu laifi na rantsuwa: Ba su zauna a cikin kabari ba face sa'a guda. Kamar haka suka kasance ana karkatar da su

    [56] Kuma waɗanda aka bai wa ilmi da imani suka ce: "Lalle, haƙiƙa kun zauna a cikin Littafin Allah, har zuwa ranar tayarwa, to, kuma wannan ita ce ranar tayarwar, kuma amma ku, kun kasance ba ku sani ba

    [57] To, a ranar da uzurin waɗanda suka yi zalunci ba ya amfaninsu, kuma ba a neman yardarsu

    [58] Kuma lalle tabbas Mun buga kowane irin misali ga mutane a cikin wannan Alƙur'ani, kuma lalle idan ka je musu da kowace aya, lalle, waɗanda suka kafirta za su ce "Ku, ba kome kuke ba face masu barua

    [59] Kamar haka Allah Yake shafe haske a kan zukatan waɗanda ba su sani ba

    [60] Saboda haka ka yi haƙuri lalle wa'adin Allah gaskiya ne, kuma kada waɗanda ba su da yaƙini su sassabce maka hankali

    Luqmãnu

    Surah 31

    [1] L. M

    [2] Waɗancan ayoyin Littafin ne mai hikima

    [3] Shiriya da rahama ne ga masu kyautatawa

    [4] Waɗanda ke tsai da salla kuma suna ɓayar da zakka kuma su, suna yin imanin yaƙini, ga lahira

    [5] Waɗannan suna a kan shiriya ta daga Ubangijinsu kuma waɗannan su ne masu babban rabo

    [6] Kuma akwai daga cikin mutane wanda ke sayen tatsuniyoyi domin ya ɓatar da mutane daga hanyar Allah, ba da wani ilmi ba, kuma ya riƙe ta abin izgili! Waɗancan suna da wata azaba mai wulakantawa

    [7] Kuma idan an karanta ayoyinMu a gare shi, sai ya juya baya, yana mai girman kai, kamar dai bai saurare su ba kamar dai akwai wani danni a kan kunnuwansa! To, ka yi masa bushara da azaba mai raɗaɗi

    [8] Lalle, waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, suna da gidajen Aljannar ni'ima

    [9] Suna dawwama a cikinsu Allah Ya yi alkawarin, Ya tabbatar da shi. Kuma shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [10] (Allah) Ya halitta sammai, ba da ginshiƙi wanda kuke gani ba, kuma Ya jefa duwatsu masu kafuwa a cikin ƙasa, domin kada ta karkata da ku kuma Ya watsa daga kowanc irin dabba a cikinta, kuma Mun saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka tsirar a cikinta, daga kowane nau'i biyu (nami; i da mace) mai ban sha'awa

    [11] Wannan shi ne halittar Allah. To ku nuna mini, "Mene ne waɗanan da ba Shi ba suka halitta? A'a, azzalumai suna a cikin ɓata bayyananna

    [12] Kuma lalle haƙiƙa Mun bai wa Luƙman hikima. (Muka ce masa) Ka gode wa Allah, kuma wanda ya gode, to yana godewa ne domin kansa kawai kuma wanda ya kafirta, to, lalle, Allah Mawadaci ne, Godadde

    [13] Kuma a lokacin da Luƙman ya ce wa ɗansa, alhali kuwa yana yi masa wa'azi, "Ya ƙaramin ɗana! Kada ka yi shirki game da Allah. Lalle shirki wani zalunci ne mai girma

    [14] Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu; uwarsa ta ɗauke shi a cikin rauni a kan wani rauni, kuma yayensa a cikin shekaru biyu (Muka ce masa) "Ka gode Mini da kuma mahaifanka biyu. Makoma zuwa gare Ni kawai take

    [15] Kuma idan mahaifanka suka tsananta maka ga ka yi shirki game da Ni, ga abin da ba ka da ilmi gare shi, to, kada ka yi musu ɗa'a. Kuma ka abuce su a cikin duniya gwargwadon shari'a, kuma ka bi hanyar wanda ya mayar da al'amari zuwa gare Ni, sa'an nan zuwa gare Ni makomarku take sa'an nan In ba ku labari game da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [16] Ya ƙaramin ɗana! Lalle ita idan gwargwadon ƙwayar komayya ce ta kasance, to, ta kasance a cikin wani falalen dutse, ko a cikin sammai, ko a cikin ƙasa, Allah zai kawo ta Lalle Allah Mai tausasawa ne, Masani

    [17] Ya ƙaramin ɗana! Ka tsai da salla, kuma ka yi umurni da abin da aka sani, kuma ka yi hani daga abin da ba a sani ba, kuma ka yi haƙuri a kan abin da ya same ka. Lalle, wancan yana daga muhimman al'amura

    [18] Kada ka karkatar da kundukukinka ga mutane, kada ka yi tafiya a cikin ƙasa kana mai nuna faɗin rai. Lalle, Allah ba Ya son dukan mai taƙama, mai alfahari

    [19] Kuma ka tsakaita a tafiyarka, kuma ka runtse ga sautinka. Lalle mafi munin sautuka haƙiƙa shi ne sautin jakuna

    [20] Ashe, ba ku gani ba, cewa Allah Ya hore muku abin da ke a cikin sammai da abin da ke a cikin ƙasa, kuma Ya zuba ni'imominsa a kanku, bayyanannu da ɓoyayyu? Kuma akwai daga mutane wanda ke yin jidali ga al'amarin Allah, ba da wani ilmi ba, kuma ba da wata shiriya ba, kuma ba da wani littafi mai haskakawa ba

    [21] Kuma idan aka ce musu, "Ku bi abin da Allah ya saukar," sai su ce: "A'a, muna bin abin da muka sami ubanninmu a kansa." shin ko da Shaiɗan na kiran su ne zuwa ga azabar sa'ir

    [22] kuma wanda ya mika fuskarsa zuwa ga Allah, alhali kuma yana mai kyautatawa, to, lalle ya yi riƙo ga igiya amintacciya. Kuma zuwa ga Allah aƙibar al'amura take

    [23] Kuma wanda ya kafirta, to, kada kafircinsa ya baƙanta maka rai, zuwa gare Mu makomarsu take, sa'an nan Mu ba su labari game da abin da suka aikata. Lalle Allah, Masani ne ga abin da ke a cikin ƙiraza

    [24] Muna jishe su dadi kaɗan sa'an nan Mu tilasta su ga shiga zuwa azaba kakkaura

    [25] Kuma lalle, idan ka tambaye su, "Wane ne ya halitta sammai da kasa?" Lalle za su ce: "Allah ne." Ka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah" A'a, mafi yawansu ba su sani ba

    [26] Abin da yake a cikin sammai da ƙasa duka na Allah kawai ne. Lalle, Allah Shi ne Mawadaci, Godadde

    [27] Kuma da dai abin da ke a cikin ƙasa duka, na itace, ya zama alƙalumma, kuma teku tana yi masa tawada, a bayansa da waɗansu tekuna bakwai kalmomin Allah ba za su ƙare ba. Lalle, Allah Mabuwayi ne, Mai hikima

    [28] Halittarku ba ta zama ba, kuma tayar da ku bai zama ba, face kamar rai guda. Lalle, Allah Mai ji ne, Mai gani

    [29] Ashe, ba ku ga, lalle, Allah Yana shigar da dare a cikin rana ba, kuma Yana shigar da rana a cikin dare kuma Ya hore rana da wata kowane yana gudana zuwa a ajali ambatacce kuma lalle Allah Masani ne ga abin da kuke aikatawa

    [30] Wannan fa domin Allah Shi ne Gaskiya, kuma abin da suke kira wanda ba Shi ba, shi ne ƙarya, kuma lalle, A1lah shi ne Maɗaukaki, Mai girma

    [31] Ashe, ba ka ga lalle jirgin ruwa na gudana ba a cikin teku da ni'imar Allah domin Ya nuna muku daga ayoyinSa? Lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga dukan mai haƙuri, mai godiya

    [32] Kuma idan taguwar ruwa, kamar duwatsu, ta rufe su, sai su kira Allah suna tsarkakewar addini a gare shi. To, a lokacin da Ya tsirar da su zuwa ga tudu, sai daga cikinsu akwai mai taƙaitawa kuma babu mai musun ayoyinMu face dukkan mayaudari mai yawan kafirci

    [33] Ya ku mutane! Ku bauta wa Ubangijinku da taƙawa, kuma ku ji tsoron wani yini, ranar da wani mahaifi ba ya saka wa abin haifuwarsa da kome kuma wani abin haifuwa ba ya saka wa mahaifinsa da kome. Lalle wa'adin Allah gaskiya ne. Saboda haka, kada wata rayuwa ta kusa ta rude ku, kuma kada maruɗin nan ya ruɗe ku game da Allah

    [34] Lalle, Allah a wurinsa kawai sanin sa'a yake, kuma Yana saukar da girgije, kuma Yana sanin abin da yake a cikin mahaiffannai kuma wani rai bai san abin da yake aikatawa a gobe ba, kuma wani rai bai san a wace ƙasa yake mutuwa ba. Lalle Allah Masani ne Mai ƙididdidigewa

    Sajada

    Surah 32

    [1] L. M

    [2] Saukar da Littafin babu shakka a gare shi, daga Ubangijin talikai yake

    [3] Ko suna cewa (Muhammadu ne) ya ƙirƙira shi? A'a, shi ne gaskiya daga Ubangijinka, domin ka yi gargaɗi ga mutane waɗanda wani mai gargaɗi bai je musu ba a gabaninka, fatan za su shiryu

    [4] Allah ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa da abin da yake a tsakaninsu a cikin kwanuka shida, sa'an nan Ya daidaita a kan Al'arshi. Ba ku da, baicin Shi, wani majiɓinci kuma babu wani maceci. Shin, ba za ku yi tunani ba

    [5] Yana shirya al'amari daga sama zuwa ga ƙasa, sa'an nan ya taka zuwa gare Shi a cikin yini, wanda gwargwadonsa shekaru dubu ne ga abin da kuke lissafawa

    [6] Wannan shi ne Masanin fake da bayyane, Mabuwayi, Mai jinƙai

    [7] Wanda Ya kyautata kome, Wanda Ya halitta shi. Shi ne kuma Ya fara halittar mutum daga laka

    [8] Sa'an nan Ya sanya ɗiyansa daga wani asali na wani ruwa wulakantacce

    [9] Sa'an nan Ya daidaita shi, kuma Ya hura a cikinsa, daga ruhinSa kuma Ya sanya muku ji, da ganunuwa da zukata. Godiyarku kaɗan ce ƙwarai

    [10] Kuma suka ce: "Shin, idan mun ɓace a cikin ƙasa, shin, lalle mu, tabbas ne muna zama a cikin wata halitta sabuwa?" A'a, su game da gamuwa da Ubangijinsu kafirai

    [11] Ka ce: "Mala, ikin mutuwa ne. wanda aka wakkala a gare ku, shi ne ke karɓar rayukanku. Sa'an nan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku

    [12] Kuma da ka gani a lokacin da masu laifi suke masu sunkuyar da kawunansu a wurin Ubangijinsu, "Ya Ubangijinmu! Mun gani, kuma mun ji, to, Ka mayar da mu mu aikata aiki na ƙwarai. Lalle mu masu yaƙini ne

    [13] Kuma da Mun so da Mun bai wa kowane rai shiriyarsa to, amma magana ta tabbata daga gare Ni! Lalle ne Ina cika Jahannama daga aljannu da mutane gaba ɗaya

    [14] To, ku ɗanɗana saboda abin da kuka manta na haɗuwa da ranarku wannan. Lalle Mu ma Mun manta da ku, kuma ku danɗani azabar dawwama saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [15] Waɗanda ke imani da ayoyinMu kawai, su ne waɗanda idan aka karanta musu ayoyinMu sai su faɗi suna masu sujada kuma su yi tasbihi game da gode wa Ubangijinsu, alhali kuwa su ba su yin girman kai

    [16] Sasanninsu na nisanta daga wuraren kwanciya, suna kiran Ubangijinsu bisa ga tsoro da ɗammani, kuma suna ciryawa daga abin da Muka azurta su

    [17] Saboda haka wani rai bai san abin da aka ɓoye musu ba, na sanyin idanu, domin sakamako ga abin da suka kasance suna aikatawa

    [18] Shin, wanda ya zama mumini yana kamar wanda ya zama fasiƙi? Ba za su yi daidai ba

    [19] Amma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwafai, to, suna da gidajen Aljannar makoma, a kan liyafa saboda abin da suka kasance suna aikatawa

    [20] Kuma waɗanda suka yi fasiƙanci to makomarsu ita ce wuta, ko da yaushe suka yi nufin su fita daga gare ta, sai a mayar da su a cikinta, kuma a ce musu: "Ku ɗanɗana azabai wuta, wadda kuka kasance kuna ƙaryatawa game da ita

    [21] Kuma lalle Muna ɗanɗana musu daga azaba, mafi ƙasƙanci, kafin a kai ga azaba mafi girma, domin fatan za su komo

    [22] Kuma wane ne ya fi zalunci bisa ga wanda aka tunatar da ayoyin Ubangijinsa, sa'an na ya bijire daga barinsu? Lalle Mu, Masu yin azabar ramuwa ne ga masu laifi

    [23] Kuma lalle haƙiƙa, Mun bai wa Musa Littafi, saboda haka kada ka kasance a cikin shakka daga haɗuwa da shi. Kuma Mun sanya shi ya zama shiriya ga Bani Isra'ila

    [24] Kuma Mun sanya shugabanni daga cikinsu, suna shiryarwa da umurninMu, a lokacin da suka yi haƙuri, kuma sun kasance suna yin yaƙini da ayoyinMu

    [25] Lalle Ubangijinka shi ne zai rarrabe a tsakaninsu a Ranar ¡iyama a cikin abin da suka kasance suna saɓa wa juna a cikinsa

    [26] Shin, ba ya shiryar da su cewa da yawa Muka halakara gabaninsu, daga al'ummomi suna tafiya a cikin masaukansu? Lalle a cikin wancan akwai ayoyi. Shin, ba su ji ne

    [27] Shin, kuma ba su gani ba cewa lalle Mu, Muna kora ruwa zuwa ga ƙasa ƙeƙasasshiya, sa'an nan Mu fitar, game da shi, wata shuka wadda dabbobinsu, da su kansu ke ci daga gare ta? Ashe fa ba su gani ba

    [28] Kuma suna cewa, "Yaushe wannan hukunci yake, aukuwa idan kun kasance masu gaskiya

    [29] Ka ce: "Ranar hukuncin nan, imanin waɗanda suka kafirta ba zai amfane su ba (a cikinta) kuma ba za a yi musu jinkiri ba

    [30] Saboda haka ka kau da kai daga barinsu, kuma, ka yi jira lalle, su ma masu jira ne

    Ahzab

    Surah 33

    [1] Ya kai Annabi! Ka bi Allah da taƙawa, kuma kada ka yi ɗa'a ga kafirai da munafukai. Lalle, Allah Ya kasance Mai ilmi, Mai hikima

    [2] Kuma ka bi abin da aka yi wahayi da shi zuwa gare ka daga Ubangijinka. Lalle, Allah Ya kasance Mai labartawa ga abin da kuke aikatawa

    [3] Ka dogara ga Allah. Kuma Allah Ya isa Ya zama wakili

    [4] Allah bai sanya zuciya biyu ba ga wani namiji a cikinsa, kuma bai sanya matanku waɗanda kuke yin zihari daga gare su, su zama uwayenku ba, kuma bai sanya ɗiyan hankakarku su zama ɗiyanku ba. wannan abu naku, maganarku ce da bakunanku alhali kuwa Allah na faɗar gaskiya, kuma Shi ne ke shiryarwa ga hanyar ƙwarai

    [5] Ku kira su ga ubanninsu, shi ne mafi adalci a wurin Allah. To, idan ba ku san ubanninsu ba, to, 'yan'uwanku ga addini da dimajojinku. Kuma babu laifi a gare ku ga abin da kuka yi kuskure da shi, kuma amma (akwai laifi) ga abin da zukatanku suka ganganta, kuma Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai

    [6] Annabi ne mafi cancanta ga muminai bisa ga su kansu, kuma matansa uwayensu ne. Kuma ma'abuta zumunta waɗansunsu sun fi waɗansu a cikin Littafin Allah bisa ga muminai da Muhajirai, face fa idan kun aikata wani alheri zuwa ga majiɓintanku. Wancan ya kasance a cikin Littafi, rubutacce

    [7] Kuma a lokacin da Muka riƙi alkawarin Annabawa daga gare su, kuma daga gare ka, kuma daga Nuhu da Ibrahim da Musa da kuma Isa ɗan Maryama, kuma Muka riƙi wani alkawari mai kauri daga gare su

    [8] Domin Ya tambayi masu gaskiya a kan gaskiyarsu, kuma Ya yi tattalin wata azaba mai raɗaɗi ga kafirai

    [9] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku tuna ni'imar Allah a kanku a lokacin da waɗansu rundunoni suka zo muku, sai Muka aika wata iska a kansu da waɗansu rundunoni waɗanda ba ku gani ba, Kuma Allah Ya kasance Mai gani ga abin da kuke aikatawa

    [10] A lokacin da suka zo muku daga samanku da kuma ƙasa daga gare ku, kuma a lokacin da gannai suka karkata kuma zukata suka kai ga maƙosai, kuma kuka yi zaton zace-zace, game da Allah

    [11] A can aka jarrabi muminai, kuma aka yi girgiza da su, girgiza mai tsanani

    [12] Kuma a lokacin da munafukai da waɗanda akwai cuta a cikin zukatansu ke cewa, Allah da ManzonSa, "Ba su yi mana wa'adin kome ba, face ruɗi

    [13] Kuma a lokacin da wata ƙungiya daga gare su, ta ce, "Ya mutanen Yasriba! Ba ku da wani matsayi, saboda haka ku koma." Kuma wata ƙungiya daga gare su na neman izni ga Annabi sunacewa, "Lalle gidajenmu kuranye suke," alhali kuwa ba kuranye suke ba, ba su da nufin kome face gudu

    [14] Kuma da an shige ta (Madina) a kansu, daga sasanninta, sa'an nan aka tambaye su fitina (kafirci), lalle da sun je mata, kuma da ba su zauna a cikinta (Madina) ba face kaɗan

    [15] Kuma lalle haƙiƙa, sun kasance suna yi wa Allah alkawari, a gabanin wannan; Ba za su juya domin gudu ba, kuma alkawarin Allah ya kasance abin tambaya

    [16] Ka ce: "Gudun nan ba zai amfane ku ba daga mutuwa ko kisa. Kuma har in kun gudu, ba za a jishe ku daɗi ba face kaɗan

    [17] Ka ce: "Wane ne wanda yake tsare ku daga Allah, idan Ya yi nufin wata cuta game da ku?" Kuma ba za su samar wa kansu wani majiɓinci ba, banda Allah, kuma ba za su samar wa kansu wani mataimaki ba

    [18] Lalle Allah Ya san masu hana mutane fita daga cikinku, da masu cewa ga 'yan'uwansu,"Ku zo nan a wurinmu." Kuma ba za su shiga yaƙi ba face kaɗan

    [19] Suna masu rowa gare ku, sa'an nan idan tsoro ya zo, sai ka gan su suna kallo zuwa gare ka, idanunsu suna kewaya, kamar wanda ake rufe hankalinsa saboda mutuwa. Sa'an nan idan tsoron ya tafi, sai su yi muku miyagun maganganu da harussa masu kaifi, suna masu rowa a kan dukiya. Waɗannan, ba su yi imani ba, saboda hakaAllah Ya ɓata ayyukansu. Kuma wannan ya kasance mai sauƙi ga Allah

    [20] Suna zaton ƙungiyoyin kafirai ba su tafi ba. Kuma idan ƙungiyoyin kafirai sun zo, suna gurin da dai sun zama a karkara a cikin ƙauyawa, suna tambayar labaranku. Kuma ko da sun kasance a cikinku, ba za su yi yaƙi ba, face kaɗan

    [21] Lalle, abin koyi mai kyau ya kasance gare ku daga Manzon Allah, ga wanda ya kasanee yana fatan rahamar Allah da Ranar Lahira, kuma ya ambaci Allah da yawa

    [22] Kuma a lokacin da muminai suka ga ƙungiyoyin kafirai, sai suka ce, "Wannan ne abin da Allah da ManzonSa suka yi mana wa'adi, Allah da ManzonSa sunyi gaskiya." Kuma wannan bai ƙara musu kome ba face imani da sallamawa

    [23] Daga muminai akwai waɗansu mazaje da suka gaskata abin da suka yi wa Allah alkwari a kansa, sa'an nan a cikinsu, akwai wanda ya biya bukatarsa, kuma daga cikinsu akwai wanda ke jira. Kuma ba su musanya ba, musanyawa

    [24] Domin Allah Ya saka wa masu gaskiya da gakiyarsu, kuma Ya azabtar da munafukai idan Ya so, ko Ya karɓi tuba a kansu. Lalle, Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai

    [25] Kuma Allah Ya mayar da waɗanda suka kafirta da fushinsu, ba su sami wani alheri ba. Allah Ya isar wa muminai daga barin yaƙi. Kuma Allah Ya kasance Mai ƙarfi, Mabuwayi

    [26] Kuma Ya saukar da waɗannan da suka taimake su daga mazowa Littafi, daga biranensu, kuma Ya jefa tsoro a cikin zukatansu; wata ƙungiya kuna kashewa, kuma kuna kama wata ƙungiyar

    [27] Kuma Ya gadar da ku gonakinsu da gidajensu da dukiyoyinsu, da wata ƙasa wadda ba ku taɓa takarta ba. Kuma Allah ya kasance Mai ikon yi ne a kan kome

    [28] Ya kai Annabi! Ka ce wa matanka, "Idan kun kasance kuna nufin rayuwar duniya da ƙawarta, to, ku zo in yi muku kyautar ban kwana kuma in sake ku, saki mai kyau

    [29] Kuma idan kun kasance kuna nufin Allah da Manzonsa da gidan Lahria, to, lalle, Allah Ya yi tattalin wani sakamako mai girma ga masu kyautatawa daga gare ku

    [30] Ya matan Annabi! Wadda ta zo da alfasha bayyananna daga cikinku za a ninka mata azaba ninki biyu. Kuma wancan ya kasance mai sauƙi ga Allah

    [31] Kuma wadda ta yi tawali'u daga cikinku ga Allah da ManzonSa, kuma ta aikata aiki na ƙwarai, za Mu ba ta sakamakonta ninki biyu, kuma Mun yi mata tattalin arziki ma karimci

    [32] Ya matan Annabi! Ba ku zama kamar kowa ba daga mata, idan kun yi taƙawa, saboda haka, kada ku sassautar da magana, har wanda ke da cuta a cikin zuciyarsa ya yi ɗammani, kuma ku faɗi magana ta alheri

    [33] Kuma ku tabbata a cikin gidajenku, kuma kada ku yi fitar gaye-gaye irin fitar gaye-gaye ta jahiliyyar farko. Kuma ku tsai da salla, kuma ku bayar da zakka, ku yi ɗa, a ga Allah da ManzonSa. Allah na nufin Ya tafiyar da ƙazamta kawai daga gare ku, ya mutanen Babban Gida! Kuma Ya tsarkake ku, tsarkakewa

    [34] Kuma ku tuna abin da ake karantawa a cikin ɗakunanku daga ayoyin Allah da hukunci. Lalle Allah Ya kasance Mai tausasawa Mai labartawa

    [35] Lalle, Musulmi maza da Musulmi mata da muminai maza da muminai mata, da masu tawali'u maza da masu tawaliu matada masu gaskiya maza da masu gaskiya mata, da masu haƙuri maza da masu haƙuri mata, da masu tsoron Allah maza da masu tsoron Allah mata, da masu sadaka maza da masu sadaka mata, da masu azumi maza da masu azumi mata da masu tsare farjojinsu maza da masu tsare farjojinsu mata, da masu ambaton Allah da yawa maza da masu ambatonsa mata, Allah Ya yi musu tattalin wata gafara da wani sakamako mai girma

    [36] Kuma ba ya halatta ga mumini kuma haka ga mumina, a lokacin da Allah da Manzonsa Ya hukunta wani umurni, wani zaɓi daga al'amarinsu ya kasance a gare su. Kuma wanda ya saɓa wa Allah da ManzonSa, to, ya ɓace, ɓacewa bayyananna

    [37] Kuma a lokacin da kake cewa ga wanda Allah Ya yi ni'ima a gare shi kai kuma ka yi ni'ima a gare shi, "Ka riƙe matarka, kuma ka bi Allah da taƙawa," kuma kana ɓoyewa a cikin ranka abin da Allah zai bayyana shi, kana tsoron mutane, alhali kuwa Allah ne Mafi cancantar ka ji tsoronSa. to a lokacin da zaidu ya ƙare bukatarsa daga gare ta, Mun aurar da kai ita, domin kada wani ƙunci ya kasance a kan muminai a cikin (auren matan) ɗiyan hankakarsu, idan sun ƙare bukata daga gare su. Kuma umurnin Allah ya kasance abin aikatawa

    [38] Wani ƙunci bai kasance a kan Annabi ba ga abin da Allah Ya faralta a kansa, a kan ƙa'idar, Allah a cikin (Annabawa) waɗanda suka shige daga gabaninsa. Kuma umurnin Allah ya kasance abin ƙaddarawa tabbatacce

    [39] Waɗanda ke iyar da Manzancin Allah, kuma suna tsoronSa, kuma ba su tsoron kowa face Allah, Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai hisabi

    [40] Muhammadu bai kasance uban kowa ba daga mazanku, kuma amma shi ya kasance Manzon Allah kuma cikon Annabawa. Kuma Allah Ya kasance Masani ga kome

    [41] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ambaci Allah, ambata mai yawa

    [42] Kuma ku tsarkake shi, a safiya da maraice

    [43] (Allah) Shi ne Wanda ke tsarkake ku, da mala'ikunSa (suna yi muku addu'a), domin Ya fitar da ku daga duffai zuwa ga haske. Kuma (Allah) Ya kasance Mai Jin ƙai ga muminai

    [44] Gaisuwarsu a ranar da suke haɗuwa da shi "Salam", kuma Ya yi musu tattalin wani sakamako na karimci

    [45] Ya kai Annabi! Lalle Mu Mun aike ka kana mai shaida, kuma mai bayar da bushara kuma mai gargaɗi

    [46] Kuma mai kira zuwa ga Allah da izninSa, kuma fitila mai haskakawa

    [47] Kuma ka yi bushara ga muminai cewa, suna da falalamai girma daga Allah

    [48] Kuma kada ka yi ɗa'a ga kafirai da munafukai, kuma ka ƙya1e cutarsu (gare ka), kuma ka dogara ga Allah. Allah Ya isa zama wakili

    [49] Ya ku waɗanda suka yi imani! idan kun auri muminai mata, sa'an nan kuka sake su a gabanin ku shafe su, to, ba ku da wata idda da za ku lissafa a kansu, kuma ku yi musu kyautar jin daɗi kuma ku sake su saki mai kyau

    [50] Ya kai Annabi! Lalle Mu, Mun halatta maka matanka waɗanda ka bai wa sadakokinsu da abin da hannun damanka ya mallaka daga abin da Allah Ya ba ka na ganima, da 'ya'yan baffanka, da 'ya'yan goggonninka da 'ya'yan kawunka da 'ya'yan innoninka waɗanda suka yi hijira tare da kai, da wata mace mumina idan ta bayar da kanta ga Annabi, idan shi Annabi yana nufin ya aure ta (halin wannan hukunci) keɓe yake gare ka, banda gamuminai. Lalle Mun san abin da Muka faralta a kansu (smuminai) game da matansuda abin da hannayensu suka mallaka. Do min kada wani ƙunci ya kasance a kanka, kuma Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai

    [51] Kana iya jinkirtar da wadda ka ga dama daga gare su, kuma kana taro wadda kake so zuwa gare ka. Kuma wadda ka nema daga waɗanda ka nisantar, to, babu laifi agare ka. Wannan ya fi kusantar da sanyaya idanunsu, kuma ba za su yi baƙin ciki ba, kuma su yarda da abin da ka ba su, su duka. Kuma Allah Yana sane da abin da yake a cikin zukatanku. Kuma Allah Ya kasance Masani, Mai haƙuri

    [52] Waɗansu mata ba su halatta a gare ka a bayan haka, kuma ba za ka musanya su da matan aure ba, kuma ko kyaunsu ya ba ka sha'awa, face dai abin da hannun damanka ya mallaka. Kuma Allah Ya kasance Mai tsaro ga dukan kome

    [53] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku shiga gidajen Annabi, face fa idan an yi izni a gare ku zuwa ga wani abinci, ba da kun tsaya jiran nunarsa ba, kuma amma idan an kira ku, to, ku shiga, sa'an nan idan kun ci, to ku watse, kuma ba da kun tsaya kuna masu hira da wani Iabari ba. Lalle wannan yana cutar da Annabi, to, yana jin kunyarku, alhali kuwa Allah ba Ya jin kunya daga gaskiya. Kuma idan za ku tambaye su waɗansu kaya, to, ku tambaye su daga bayan shamaki. Wannan ya fi muku tsarki ga zukatanku da zukatansu. Kuma ba ya halatta a gare ku, ku cuci Manzon Allah, kuma ba ya halatta ku auri matansa a bayansa har abada. lalle wannan a gare ku ya kasance babban abu a wurin Allah

    [54] Idan kun bayyana wani abu, ko kuma kuka ɓoye shi, to, lalle Allah Ya kasance Masani ga kome

    [55] Babu laifi a kansu game da ubanninsu, kuma babu game da ɗiyansu, kuma babu game da 'yan'uwansu maza, kuma babu game da ɗiyan 'yan'uwansu maza, kuma babu game da ɗiyan 'yan'uwansu mata, kuma babu game da matan muminai, kuma babu game da abin da hannayensu suka mallaka, kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Ya kasance Mahalarci a kan kome

    [56] Lalle, Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi. Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi

    [57] Lalle waɗanda ke cutar Allah da MauzonSa Allah Ya la'ane su, a cikin duniya da Lahira, kuma Ya yi musu tattalin azaba mai wulakantarwa

    [58] Kuma waɗanda suke cutar muminai maza da muminai mata, ba da wani abu da suka aikata ba to, lalle sun ɗauki ƙiren ƙarya da zunubi bayyananne

    [59] Ya kai Annabi! Ka ce wa matan aurenka da 'ya'yanka da matan muminai su kusantar da ƙasa daga manyan tufafin da ke a kansu. Wancan ya fi sauƙi ga a gane su domin kada a cuce su. Kuma Allah Ya kasance Mai gafara, Mai Jin ƙai

    [60] Lalle, idan munafukai da waɗanda yake akwai wata cuta a cikin zukatansu, da masu tsegumi a cikin Madina, ba su hanu ba (daga halayensu), lalle, za Mu shushuta ka a gare su, sa'an nan ba za su yi maƙwabtaka da kai ba, a cikinta, face kaɗan

    [61] Suna la'anannu, inda duka aka same su a kama su, kuma a karkashe su karkashewa

    [62] A kan hanyar Allah (ta gyaran jama'a) a cikin waɗanda suka shuɗe gabaninka, kuma ba za ka sami musanyawa ba ga hanyar Allah

    [63] Suna tambayar ka ga Sa'a. Ka ce: "Saninta yana wurin Allah kawai." Kuma me ya sanar da kai cewa ana tsammanin sa'a ta kasance kusa

    [64] Lalle Allah Ya la'ani kafirai, kuma Ya yi musu tattalin wata wuta mai ƙuna

    [65] Suna madawwama a cikinta har abada, ba su samun majiɓinci, kuma ba su samun mataimaki

    [66] Ranar da ake juya fuskokinsu a cikin wuta suna cewa, "Kaitonmu, saboda, rashin biyarmu ga Allah da rashin biyarmu ga Manzo

    [67] Kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Lalle mu mun bi shugabanninmu da manyanmu! Sai suka ɓatar da mu daga hanya

    [68] Ya Ubangijinmu! Ka ba su ninki biyu na azaba, kuma ka la'ane su, la'ana mai girma

    [69] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku kasance kamar waɗanda suka cuci Musa sa'an nan Allah Ya barrantar da shi daga abin da suka ce. Kuma ya kasance mai daraja a wurin Allah

    [70] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku faɗi magana madaidaiciya

    [71] Ya kyautata muku ayyukanku, kuma Ya gafarta zunubanku. Kuma wanda ya yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, to, lalle, ya rabbanta, babban rabo mai girma

    [72] Lalle Mu, Mun gitta amana ga sammai da ƙasa da duwatsu, sai suka ƙi ɗaukarta kuma sukaji tsoro daga gare ta, kuma mutum ya ɗauke ta, lalle shi (mutum) ya kasance mai yawan zalunci, mai yawan jahilci

    [73] Domin Allah Ya azabta munafukai maza da munafukai mata, da mushirikai maza da mushirikai mata, kuma Allah Ya karɓi tuba ga muminai maza da muminai mata. Kuma Allah Ya kasance Mai gafara, Mai jin ƙai

    Saba'u

    Surah 34

    [1] Godiya ta tabbata ga Allah, wanda Yake abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa Nasa ne, kuma shi ne Mai hikima, Mai labartawa

    [2] Ya san abin da yake shiga a cikin ƙasa da abin da yake fita daga gare ta, da abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa a cikinta, kuma Shi ne Mai jin ƙai, Mai gafara

    [3] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: "Sa'a ba za ta zo mana ba." Ka ce: "Kayya! Na rantse da Ubangijina, lalle, za ta zo muku." Masanin gaibi, gwargwadon zarra ba ta nisanta daga gare Shi a cikin sammai kuma ba ta nisanta a cikin ƙasa, kuma babu mafi ƙaranci daga wancan kuma babu mafi girma face yana a cikin Littafi bayyananne

    [4] Domin Ya saka wa waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Waɗancan suna da wata gafara da wani arziki mai karimci

    [5] Kuma waɗanda suka yi makirci ga ayoyinMu, suna masu gajiyarwa, waɗannan suna da wata azaba daga azaba mai raɗaɗi

    [6] Kuma waɗanda aka bai wa ilmi suna ganin abin nan da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka, shi ne gaskiya, kuma yana shiryarwa zuwa ga hanyar Mabuwayi, Godadde

    [7] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: "Shin za mu nuna muku wani namiji wanda yake gaya muku wai idan an tsattsage ku, kowace irin tsattsagewa, lalle ku, tabbas, kuna a cikin wata halitta sabuwa

    [8] Ya ƙaga ƙarya ga Allah ne ko kuwa akwai wata hauka a gare shi?" A'a, waɗanda ba su yi imani da Lahira ba, suna a cikin azaba da ɓata mai nisa

    [9] Ashe fa, ba su yi dubi ba zuwa ga abin da ke a gaba gare su da abin da ke a bayansu daga sama da ƙasa? idan Mun so, sai Mu shafe ƙasa da su, ko kuma Mu kayar da wani ɓaɓɓake daga sama a kansu. Lalle, a cikin wancan akwai aya ga dukan bawa mai maida al'amarinsa ga Allah

    [10] Kuma lalle, haƙiƙa, Mun bai wa Dawuda wata falala dagagare Mu. Ya duwatsu, ku konkoma sautin tasbihi tare da shi kuma da tsuntsaye. Kuma Muka tausasa masa baƙin ƙarfe

    [11] Ka aikata sulkuna kuma ka ƙaddara lissafi ga tsarawa, kuma ka aikata aikin ƙwarai. Lalle NiMai gani ne ga abin da kuke aikatawa

    [12] Kuma ga Sulaiman, Mun hore masa iska, tafiyarta ta safiya daidai da wata, kuma ta maraice daidai da wata. Kuma Muka gudanar masa da marmaron gaci, kuma daga aljannu (Muka hore masa) waɗanda ke aiki a gaba gare shi, da iznin Ubangijinsa. Wanda ya karkata daga cikinsu, daga umurninMu, sai Mu ɗanɗana masa daga azabar sa'ir

    [13] Suna aikata masa abin da yake so, na masallatai da mutummutumai da akussa kamar kududdufai, da tukwane kafaffu. Ku aikata godiya, ya ɗiyan Dawuda, kuma kaɗan ne mai godiya daga bayiNa

    [14] Sa'an nan a lokacin da Muka hukunta mutuwa a kansa babu abin da ya ja hankalinsu, a kan mutuwarsa, face dabbar ƙasa (gara) wadda take cin sandarsa. To a lokacin da ya faɗi, sai aljannu suka bayyana (ga mutane) cewa da sun kasance sun san gaibi, da ba su zauna ba a cikin azaba mai wulakantarwa

    [15] Lalle, haƙiƙa, akwai aya ga saba'awa a cikin mazauninsu: gonakin lambu biyu, dama da hagu. "Ku ci daga arzikin Ubangijinku, kuma ku yi godiya gare shi. Gari mai daɗin zama, da Ubangiji Mai gafara

    [16] Sai suka bijire saboda haka Muka saki Malalin Arimi (dam) a kansu, kuma Muka musanya musu gonakinsu biyu da waɗansu gonaki biyu masu 'ya'yan itace kaɗan: talakiya da goriba da wani abu na magarya kaɗan

    [17] Wancan, da shi Muka yi musu sakamako saboda kafircinsu. Kuma lalle, ba Mu yi wa kowa irin wannan sakamako, face kafirai

    [18] Kuma Muka sanya, a tsakaninsu da tsakanin garuruwan da Muka Sanya albarka a cikinsu, waɗansu garuruwa masuganin juna kuma Muka ƙaddara tafiya a cikinsu, "Ku yi tafiya a cikinsu, daruruwa da ranaiku, kuna amintattu

    [19] Sai suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka nisantar da tsakanin tafiyoyinmu," kuma suka zalunci kansu, saboda haka Muka sanya su labaran hira kuma Muka kekkece su kowace, irin kekkecewa. Lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga dukan mai yawan haƙuri, mai yawan godiya

    [20] Kuma lalle, haƙiƙa, Iblis ya gaskata zatonsa a kansu, sai suka bi shi face wani ɓangare na muminai

    [21] Kuma ba ya da wani dalili a kansu face dai domin Mu san wanda yake yin imani da Lahira daga wanda yake a cikin shakka daga gare ta. Kuma Ubangijinka, a kan kome, Mai tsaro ne

    [22] Ka ce: "Ku kirayi waɗanda kuka riya (cewa abubuwan bautawa ne) baicin Allah, ba su Mallakar ma'aunin zarra a cikin sammai, kuma ba su Mallakarsa a cikin ƙasa kuma ba su da wani rabon tarewa a cikinsu (sammai da ƙasa), kuma ba Shi da wani mataimaki daga gare su

    [23] Kuma wani ceto ba ya amfani a wurinSa face fa ga wanda Ya yi izni a gare shi. Har a lokacin da aka kuranye tsoro daga zukatansu, sai su ce, 'Mene ne Ubangijinku Ya ce?' Suka ce: 'Gaskiya', kuma shi ne Maɗaukaki, Mai girma

    [24] Ka ce: "Wane ne yake azurta ku daga sama da ƙasa?" Ka ce: "Allah kuma lalle mu ko ku, wani yana a kan shiriya, ko yana a cikin ɓata bayyananniya

    [25] Ka ce: "Ba za a tambaye ku ba ga abin da muka aikata daga laifi, kuma ba za a tambaye mu daga abin da kuke aikatawa ba

    [26] Ka ce: "Ubangijinmu zai tara tsakaninmu, sa'an nan Ya yi hukunci a tsakaninmu da gaskiya. Kuma Shi ne Mahukunci, Masani

    [27] Ka ce: "Ku nuna mini waɗanda kuka riskar da Shi, su zama abokan tarayya. A'a, Shi ne Allah, Mabuwayi, Mai hikima

    [28] Kuma ba Mu aika ka ba face zuwa ga mutane gaba ɗaya, kana mai bayar da bushara kuma mai gargaɗi, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [29] Suna cewa, "Yaushe ne wannan wa'adi zai auku idan kun kasance masu gaskiya

    [30] Ka ce: "Kuna da mi'adin wani yini wanda ba ku jinkirta daga gare shi ko da sa'a ɗaya, kuma ba ku gabata

    [31] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: "Ba za mu yi imanida wannan Alƙur'ani ba, kuma ba za mu yi imani da abin da yakea gabaninsa ba (na waɗansu littattafan sama)." Kuma da ka gani a lokacin da azzalumai suke abin tsayarwa wurin Ubangijinka, sashensu na mayar wa sashe maganar maraunana (mabiya) suke cewa makangara (shugabanni) "Ba dominku ba, lalle, da mun kasance muminai

    [32] Makangara suka ce wa maraunana, "Ashe, mu ne muka kange ku daga shiriya a bayan ya zo muku? A, a' kun dai kasance masu laifi

    [33] Kuma maraunana suka ce wa makangara. "A'a, (ku tuna) makircin dare da na rana a lokacin da kuke umurnin mu da mu kafirta da Allah, kuma mu sanya Masa abokan tarayya." Kuma suka assirtar da nadama a lokacin da suka ga azaba. Kuma Muka sanya ƙuƙumma a cikin wuyoyin waɗanda suka kafirta. Lalle, ba za a yi musu sakamako ba face da abin da suka kasance suna aikatawa

    [34] Kuma ba mu aika wani mai gargaɗi ba a cikin wata alƙarya face mani'imtanta (shugabanni) sunce, "Lalle mu, masu kafirta ne da abin da aka aiko ku da shi

    [35] Kuma suka ce: "Mu ne mafiya yawa ga dukiya da ɗiya, kuma mu ba mu zama waɗanda ake yi wa azaba ba

    [36] Ka ce: "Lalle, Ubangijina Yana shimfiɗa arziki ga wanda Ya so, kuma Yana ƙuntatawa, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [37] Kuma dukiyarku ba ta zamo ba, haka ɗiyanku ba su zamo abin da yake kusantar da ku ba a wurinMu, kusantarwar muƙami face wanda, ya yi imani kuma ya aikata aikin ƙwarai. To, waɗannan suna da sakamakon ninkawa saboda abin da suka aikata. Kuma su amintattu ne a cikin benaye

    [38] Kuma waɗanda suke makirci a cikin ayoyinMu, suna neman gajiyarwa, waɗannan abin halartawa ne a cikin azaba

    [39] Ka ce: "Lalle, Ubangijina Yana shimfida arziki ga wanda Ya so daga bayinSa, kuma Yana ƙuntatawa a gare shi, kuma abin da kuka ciyar daga wani abu, to, Shi ne zai musanya shi, kuma Shi ne Mafi ficin masu azurtawa

    [40] Kuma ranar da Allah Ya ke tara su gaba ɗaya, sa'an nan Ya ce wa Mala'iku, "Shin, waɗannan ku ne suka kasance suna bauta wa

    [41] Sukace: "Tsarki ya tabbata a gare Ka. Kai ne Majiɓincinmu, ba su ba. A'a, sun kasance suna bauta wa aljannu. Mafi yawansu, da su suka yi imani

    [42] Saboda haka, a yau sashenku ba ya mallakar wani amfani ga wani sashen, kuma ba ya mallakar wata cuta, kuma Muna cewa ga waɗanda suka yi zalunci, Ku ɗanɗani azabar wuta wadda "kuka kasance game da ita, kuna ƙaryatawa

    [43] Kuma idan an karanta ayoyinMu bayyanannu a kansu, sai su ce: "Wannan bai zama ba face namiji ne yana son ya kange ku daga abin da ubanninku suka kasance suna bauta wa." Kuma su ce: "Wannan bai zama ba face ƙiren ƙarya da aka ƙaga." Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: ga gaskiya a lokacin da ta je musu: "Wannan ba kome ba face sihiri ne bayyananne

    [44] Kuma ba Mu ba su waɗansu littattafai ba waɗanda suke karatun su, kuma ba Mu aika wani mai gargaɗi ba zuwa gare su a gabaninka

    [45] Kuma waɗanda suke a gabaninsu, sun ƙaryata, alhali kuwa ba su kai ushurin-ushurin abin da Muka ba su ba, sai suka ƙaryata ManzanniNa! To, yaya musuNa (ga maƙaryata) ya kasance

    [46] Ka ce: "Ina yi muku wa'azi ne kawai da kalma guda! watau ku tsayu domin Allah, bibbiyu da ɗaiɗai, sa'an nan ku yi tunani, babu wata hauka ga ma'abucinku. Shi bai zama ba face mai gargaɗi ne a gare ku a gaba ga wata azaba mai tsanani

    [47] Ka ce: "Abin da na roƙe ku na wani sakamako, to, amfaninsa naku ne. Ijarata ba ta zama ba face daga Allah, kuma shi Mahalarci ne a kan dukan kome

    [48] Ka ce: "Lalle Ubangijina Yana jefa gaskiya. (Shi) Masanin abubuwan fake ne

    [49] Ka ce: "Gaskiya ta zo, kuma ƙarya ba ta iya fara (kome) kuma ba ta iya mayarwa

    [50] Ka ce: "Idan na ɓace, to, ina ɓacewa ne kawai a kan kaina. Kuma idan na shiryu, to, saboda abin da Ubangijina Yake yowar wahayi ne zuwa a gare ni. Lalle Shi Mai ji ne, Makusanci

    [51] Kuma da ka gani, a lokacin da suka firgita, to, babu kuɓuta, kuma aka kama su daga wuri makusanci

    [52] Kuma suka ce: "Mun yi imani da Shi." To ina za su samu kamawa daga wuri mai nisa

    [53] Kuma lalle sun kafirta da Shi a gabanin haka, kuma suna jifa da jahilci daga wuri mai nisa

    [54] Kuma an shamakance a tsakaninsu da tsakanin abin da suke marmari, kamar yadda aka aikata da irin ƙungiyoyinsu a gabaninsu. Lalle su sun kasance a cikin shakka mai sanya kokanto

    Fatir

    Surah 35

    [1] Godiya ta tabbata ga Allah, Mai fara halittar sammai da ƙasa, Mai sanya mala'iku manzanni masu fukafukai, bibbiyu, da uku-uku da hurhuɗu. Yana ƙarawar abin da Ya ke so a cikin halittar. Lalle Allah Mai ikon yi ne a kan kome

    [2] Abin da Allah Ya buɗa wa mutane daga rahama, to, babu mai riƙewa a gare shi, kuma abin da Ya riƙe, to, babu mai saki a gare shi, waninSa, kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [3] Ya ku mutane! Ku tuna ni'imar Allah a kanku. Shin, akwai wani mai halitta wanin Allah da zai azurta ku daga sama da, ƙasa? Babu wani abin bautawa, face Shi. To, yaya ake karkatar da ku

    [4] Kuma idan sun ƙaryata ka, to, lalle, an ƙaryata waɗansu Manzanni a gabaninka, kuma zuwa ga Allah ake mayar da al'amura

    [5] Ya ku mutane! Lalle wa'adin Allah gaskiya ne, saboda haka kada rayuwar duniya ta ruɗar da ku, kuma kada maruɗi ya ruɗe ku game da Allah

    [6] Lalle Shaiɗan maƙiyi ne a gare ku, sai ku riƙe shi maƙiyi. Yana kiran ƙungiyarsa kawai ne, domin su kasance 'yan sa'ir

    [7] Waɗanda suka kafirta suna da azaba mai tsanani kuma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, suna da wata gafara da sakamako mai girma

    [8] Shin to, wanda aka ƙawata masa aikinsa, har ya gan shi mai kyau (yana daidai da waninsa)? Saboda haka, lalle, Allah Yana ɓatar da wanda Yake so, kuma Yana shiryar da wanda Yake so, saboda haka kada ranka ya halaka a kansu domin baƙin ciki. Lalle Allah Masani ne ga abin da suke sana'antawa

    [9] Kuma Allah ne Ya aika da iskoki har su motsar da girgije, sa'an nan Mu kora shi zuwa ga gari matacce, sa'an nan Mu rayar da ƙasa game da shi a bayan mutuwarta. Kamar wancan ne Tashin ¡iyama yake

    [10] Wanda ya kasance yana neman wata izza, to, Allah ne da izza gaba ɗaya. zuwa gare Shi magana mai daɗi ke hawa, kuma aiki na ƙwarai Yana ɗaukar ta Kuma waɗanda ke yin makircin munanan ayyuka, suna da wata azaba mai tsanani, kuma makircin waɗannan yana yin tasgaro

    [11] Kuma Allah ne Ya halitta ku daga turɓaya, sa'an nan daga ɗigon maniyyi, sa'an nan Ya sanya ku surkin maza da mata. Kuma wata mace ba ta yin ciki, kuma ba ta haihuwa, face da saninSa, kuma ba za a rayar da wanda ake rayarwa ba, kuma ba za a rage tsawon ransa ba face yana a cikin Littafi. Lalle, wancan mai sauki ne ga Allah

    [12] Kuma koguna biyu ba su daidaita: Wannan mai ruwan daɗi, mai zaƙi, mai sauƙin haɗiya kuma wannan mai ruwan gishiri mai zartsi, kuma daga kowane, kuna cin wani nama sabo, kuma kuna fitar da kawa wadda kuke tufantarta, kuma kana ganin jirage a cikinsa suna masu gudana, domin ku nemo daga falalarSa, kuma ɗammaninku za ku dinga godewa

    [13] Yana shigar da dare a cikin rana, kuma Yana shigar da rana a cikin dare. Kuma Ya hore rana da wata kowannensu yana gudana zuwa ga ajali ambatacce Wannan Shi ne Allah, Ubangijinku, gare Shi mulki yake, kuma waɗanda kuke kira waninSa ba su mallakar ko fatar gurtsun dabino

    [14] Idan kun kira su, ba za su ji kiranku ba, kuma ko sun jiya, ba za su karɓa muku ba, kuma a Ranar ¡iyama za su kafirce wa shirkinku, kuma babu mai ba ka labari, kamar wanda ya sani

    [15] Ya ku mutane! Ku ne masu bukata zuwa ga Allah, kuma Allah, Shi ne Mawadaci, Godadde

    [16] Idan Ya so, zai tafi da ku, kuma Ya zo da wata halitta sabuwa

    [17] Kuma wancan bai zama mabuwayi ba ga Allah

    [18] Kuma wani rai mai ɗaukar nauyi, bai ɗaukar nauyin wani rai. Kuma idan ran da aka nauyaya wa kaya ya yi kira (ga wani mataimaki) zuwa ga kayansa, ba za a dauki kome ba daga gare shi, kuma ko da (wanda ake kiran) ya kasance makusancin zumunta ne. Kana gargaɗi kawai ne ga waɗanda ke tsoron Ubangijinsu a fake, kuma suka tsayar da salla. Kuma wanda ya tsarkake, to, yana tsarkaka ne domin kansa. Kuma zuwa ga Allah kawai makoma take

    [19] Kuma makaho ba ya daidaita da mai gani

    [20] Kuma duffai ba su daidaita, kuma haske ba ya daidaita

    [21] Kuma inuwa ba ta daidaita, kuma iskar zafi ba ta daidaita

    [22] Kuma rayayyu ba su daidaita kuma matattu ba su daidaita. Lalle Allah Yana jiyar da wa'azi ga wanda Ya so, kuma ba ka jiyar da waɗanda suke a cikin kaburbura

    [23] Ba ka zama ba face mai gargaɗi kawai

    [24] Lalle Mu Mun aike ka da gaskiya, kana mai bayar da bushara kuma mai gargaɗi. Kuma babu wata al'umma face wani mai gargaɗi ya shuɗe a cikinta

    [25] Kuma idan suna ƙaryata ka, to, haƙiƙa, waɗanda suke a gabaninsu sun ƙaryata. Manzanninsu sun je musu da hujjoji, kuma da takardu, kuma da Littafi mai haske

    [26] Sa'an nan Na kama waɗanda suka kafirta. To, yaya musuNa yake

    [27] Ba ka gani ba, lalle Allah Ya saukar da ruwa daga sama? Sai Muka fitar, game da shi,'ya'yan itace masu saɓanin launuka kuma daga duwatsu akwai zane-zane, farfaru da jajaye, masu saɓanin launin, da masu launin baƙin ƙarfe, baƙaƙe

    [28] Kuma daga mutane da dabbobi da bisashen gida, masu saɓanin launinsu kamar wancan. Malamai kawai ke tsoron Allah daga cikin bayinSa. Lalle, Allah, Mabuwayi ne, Mai gafara

    [29] Lalle waɗanda ke karatun Littafin Allah kuma suka tsayar da salla, kuma suka ciyar daga abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane, suna fatan (samun) wani fatauci ne wanda ba ya yin tasgaro

    [30] Domin (Allah) zai cika musu sakamakonsu, kuma Ya ƙara musu daga falalarSa. Lalle Shi Mai gafara ne, Mai godiya

    [31] Kuma abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, daga Littafi

    [32] Sa'an nan Mun gadar da Littafin, ga waɗanda Muka zaɓa daga bayinMu, sa'an nan daga cikinsu, akwai mai zalunci ga kansa, kuma daga cikinsu akwai mai tsakaitawa, kuma daga cikinsu akwai mai tserewa da ayyukan alheri da iznin Allah. Waccan ita ce falalar (Allah) mai girma

    [33] Gidajen Aljannar zama suna shigar su. Ana ƙawace su a cikinsu, da ƙawa ta mundaye daga zinariya da lu'ulu'u, kuma tufafinsu, a cikinsu alharini ne

    [34] Kuma suka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya tafiyar da baƙin ciki daga gare mu. Lalle Ubangijinmu, haƙiƙa Mai gafarane, Mai godiya

    [35] Wanda Ya saukar da mu a gidan zama, daga falalarSa, wata wahala ba ta shafar mu a cikinsa, kuma wata kasawa ba ta shafar mu a cikinsa

    [36] Kuma waɗanda suka kafirta suna da wutar Jahannama, ba a yin hukunci a kansu balle su mutu kuma ba a sauƙaƙa musu daga azabarta. Kamar haka Muke saka wa kowane mai yawan kafirci

    [37] Kuma su, suna hargowar neman agaji a cikinta. (Suna cewa) "Ya Ubangijinmu! Ka fitar da mu, mu aikata aiki mai kyau, wanin wanda muka kasance muna aikatawa." Ashe, kuma, ba Mu rayar da ku ba, abin da mai tunani zai iya yin tunani a ciki, kuma mai gargaɗi ya je muku? To, ku ɗanɗana, saboda haka babu wani mataimaki, ga azzalumai

    [38] Lalle Allah ne Masanin gaibin sammai da ƙasa. Lalle Shi ne Masani ga abin da yake ainihin zukata

    [39] Shi ne Wanda Ya sanya ku masu maye wa juna, a cikin ƙasa. To, wanda ya kafirta, to, kafircinsa yana a kansa. Kuma kafircin kafirai ba ya kara musu kome face baƙin jini, kuma kafircin kafirai ba ya kara musu kome face hasara

    [40] Ka ce: "Shin, kun ga abubuwan shirkinku, waɗanda kuke kira, wasun Allah? Ku nuna mini, mene ne suka halitta daga ƙasa? Ko suna da tarayya ne a cikin sammai? Ko kuma Mun ba su wani littafi ne saboda haka suna a kan wata hujja ce daga gare shi? A'a, azzalumai ba su yin wani wa'adi, sashensu zuwa ga sashe, face ruɗi

    [41] Lalle Allah Yana riƙe sammai da ƙasa domin kada su gushe. Kuma haƙiƙa, idan sun gushe, babu wani baicinSa da zai riƙe su. Lalle Shi Ya kasance Mai haƙuri, Mai gafara

    [42] Kuma suka yi rantsuwa da Allah, mafi nauyin rantsuwarsu, "Lalle, idan wani mai gargaɗi ya zo musu tabbas za su kasance mafi shiryuwa, daga ɗayan al'ummomi." To, a lokacin da mai gargaɗi ya je musu, bai ƙara su da kome ba face gudu

    [43] Domin nuna girman kai a cikin ƙasa da makircin cuta. Kuma makirci na cuta ba ya fadawa face a kan mutanensa. To shin suna jiran (wani abu ne) face dai hanyar (kafiran) farko. To, ba za ka sami musanya ba ga hanyar Allah. Kuma ba za ka sami juyarwa ba ga hanyar Allah

    [44] Ashe, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasa, domin su duba yadda aƙibar waɗannan da suke a gabaninsu ta kasance? Alhali kuwa sun kasance mafifita ƙarfi daga gare su? Kuma Allah bai kasance wani abu na iya rinjayarSa ba, a cikin sammai, kuma haka a cikin kaƙa. Lalle Shi ne Ya kasance Masani, Mai ikon yi

    [45] Kuma da Allah Yana kama mutane saboda abin da suka aikata, da bai bar wata dabba ba a kanta (kasa). Amma Yana jinkirta musu zuwa ga ajalin da aka ambata. Sa'an nan idan ajalinsu ya zo, to, lalle Allah ya kasance Mai gani ga bayinSa

    Ya Sin

    Surah 36

    [1] S

    [2] Ina rantsuwa da Al-ƙur'ani Mai hikima

    [3] Lalle kai, haƙiƙa kana cikinManzanni

    [4] A kan hanya madaidaiciya

    [5] (Allah Ya saukar da Al-kur'ani) saukarwar Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [6] Domin ka yi gargaɗi ga waɗansu mutane da ba a yi gargaɗi ga ubanninsu ba, saboda haka sumasu rafkana ne

    [7] Lalle, haƙiƙa, kalma ta wajaba a kan mafi yawansu, domin su, ba za su yi imani ba

    [8] Lalle Mu, Mun sanya ƙuƙumma a cikin wuyoyinsu, sa'an nan su (ƙuƙumman sun kai) har zuwa ga haɓoɓinsu, saboda haka, su banƙararru ne

    [9] Kuma Muka sanya wata toshiya a gaba gare su, da wata toshiya a bayansu, saboda haka Muka rufe su, sai suka zama ba su gani

    [10] Kuma daidai yake a gare su, shin, ka yi musu gargaɗi ko ba ka yi musu gargaɗi ba, su ba za su yi imani ba

    [11] Kana yin gargaɗi kawai ga wanda ya bi Alƙur'ani ne, kuma ya ji tsoron mai rahama a fake. To, ka yi masa bushara da gafara da wani sakamako na karimci

    [12] Lalle Mu, Mu ne ke rayar da matattu kuma Mu rubuta abin da suka gabatar, da gurabunsu, kuma kowane abu Mun ƙididdige shi, a cikin babban Littafi Mabayyani

    [13] Kuma ka buga musu misali: Waɗansu ma'abuta alƙarya, a lokacin da Manzanni suka je mata

    [14] A lokacin da Muka aika (Manzannin) biyu zuwa gare su, sai suka ƙaryata su, sa'an nan Muka ƙarfafa (su) da na uku, sai suka ce: "Lalle mu, Manzanni ne zuwa gare ku

    [15] Suka ce: "Ku ba ku zamo baface mutane ne kamarmu kuma Mai rahama bai saukar da kome ba, ba ku zamo ba face ƙarya kuke yi

    [16] Suka ce: "Ubangijinmu Ya sani, lalle mu, haƙiƙa Manzanni nezuwa gare ku

    [17] Kuma babu abin da ke kanmu, face iyar da manzanci bayyananne

    [18] Suka ce: "Lalle mu muna shu'umci da ku! Haƙiƙa idan ba ku, hanu ba, haƙiƙa, za mu jefe ku, kuma haƙiƙa wata azaba mai raɗaɗi daga gare mu za ta shafe ku

    [19] Suka ce: "Shu'umcinku, yana tare da ku. Ashe, domin an tunatar da ku? A'a, ku dai mutane ne masu ƙetare haddi

    [20] Kuma wani mutum daga mafi nisan birnin ya je, yana tafiya da gaggawa, ya ce: "Ya mutanena! Ku bi Manzannin nan

    [21] Ku bi waɗanda ba su tambayar ku wata ijara kuma su shiryayyu ne

    [22] Kuma mene ne a gare ni, ba zan bauta wa Wanda Ya ƙaga halittata ba, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [23] Shin, zan riƙi waninSa abubuwan bautawa? Idan Mai rahama Ya nufe ni da wata cuta, to cetonsu ba ya amfanina da kome, kuma ba za su iya tsamar da ni ba

    [24] Lalle ni, a lokacin nan, tabbas, ina a cikin ɓata bayyananna

    [25] Lalle ni, na yi imani da Ubangijinku, saboda haka ku saurare ni

    [26] Aka ce (masa), "Ka shiga Aljanna." Ya ce, "Da dai a ce mutanena suna iya sani

    [27] Game da gafarar da Ubangijjina ya yi mini, kuma Ya sanya ni a cikin waɗanda aka girmama

    [28] Kuma ba Mu saukar da waɗansu runduna ba daga sama a kan (halaka) mutanensa, daga bayansa, kuma ba za Mu kasance. Masu saukarwa ba

    [29] Ba ta kasance ba face tsawa guda, sa'an nan sai ga su somammu

    [30] Ya nadama a kan bayiNa! Wani Manzo ba ya zuwa gare su face sun kasance suna masu yi masa izgili

    [31] Ba su gani ba, da yawa Muka halakar da (mutanen) ƙarnoni a gabaninsu kuma cewa su ba za su komo ba

    [32] Kuma lalle babu kowa face waɗanda ake halartarwa ne a wurinMu

    [33] Kuma aya ce a gare su: ¡asa matacciya, Mu rayar da ita, Mu fitar da ƙwaya daga gare ta, sai ga shi daga gare ta suke ci

    [34] Kuma Muka sanya, a cikinta (ƙasa), waɗansu gonaki na dabino da inabobi, kuma Muka ɓuɓɓugar da ruwa daga maremari a cikinta

    [35] Domin su ci 'ya'yan itacensa, alhali kuwa hannayensu ba su aikata shi ba. Shin, to, ba za su gode ba

    [36] Tsarki ya tabbata ga Wanda Ya halitta nau'uka, namiji da mace, dukansu, daga abin da ƙasa ke tsirarwa, kuma daga kansu, kuma daga abin da ba su sani ba

    [37] Kuma aya ce a gare su: Dare Muna feɗe rana daga gare shi, sai ga su suna masu shiga duhu

    [38] Kuma rana tana gudana zuwa ga wani matabbaci nata. Wannan ƙaddarawar Mabuwayi ne, Masani

    [39] Kuma da wata Mun ƙaddara masa manziloli, har ya koma kamar tsumagiyar murlin dabino wadda ta tsufa

    [40] Rana ba ya kamata a gare ta, ta riski wata. Kuma dare ba ya kamata a gare shi ya zama mai tsere wa yini, kuma dukansua cikin sarari guda suke yin iyo

    [41] Kuma aya ce a gare su. Lalle Mu, Mun ɗauki zuriyarsu a cikin jirgin, wanda aka yi wa lodi

    [42] Kuma Muka halitta musu, daga irinsa, abin da suke hawa

    [43] Kuma idan Mun so, za Mu nutsar da su, har babu kururuwar neman agaji, a gare su, kuma ba su zama ana tsirar da su ba

    [44] Sai fa bisa ga wata rahama daga gare Mu, da jiyarwa daɗi zuwa ga wani ɗan lokaci

    [45] Kuma idan aka ce musu, "Ku kare abin da ke a gaba gare ku da abin da yake a bayanku, domin tsammaninku a ji tausayinku

    [46] Kuma wata aya daga ayoyin Ubangijinsu ba ta zuwa a gare su, sai sun kasance suna masu bijirewa daga gare ta

    [47] Kuma idan aka ce musu, "Ku ciyar daga abin da Allah Ya azurta ku," sai waɗanda suka kafirta su ce ga waɗanda suka yi imani, "Ashe, za mu ciyar da wanda idan Allah Ya so Yana ciyar da shi? Ba ku zama ba face a cikin ɓata bayyananniya

    [48] Kuma suna cewa, "A yaushe wannan wa'adi yake (aukuwa) idan kun kasance masu gaskiya

    [49] Ba su jiran (kome) face wata tsawa guda, za ta kama su, alhali kuwa suna yin husuma

    [50] Ba za su iya yin wasiyya ba, kuma ba za su iya komawa zuwa ga iyalansu ba

    [51] Kuma aka yi busa a cikin ƙaho, to, sai ga su, daga kaburbura zuwa ga Ubangijinsu, suna ta gudu

    [52] Suka ce: "Ya bonenmu! Wane ne ya tayar da mu daga barcinmu?" "Wannan shi ne abin da Mai rahama ya yi wa'adi da shi, kuma Manzanni sun yi gaskiya

    [53] Ba ta kasance ba face wata tsawa ce guda, sai ga su duka, suna abin halartarwa a gare Mu

    [54] To, a yau, ba za a zalunci wani rai da kome ba. Kuma ba za a saka muku ba face da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [55] Lalle, 'yan Aljanna, a yau, suna cikin shagali, suna masu nishaɗi

    [56] Su da matan aurensu suna cikin inuwowi, a kan karagai, suna masu gincira

    [57] Suna da, 'ya'yan itacen marmari a cikinta kuma suna samun abin da suke kiran a kawo

    [58] Aminci," da magana, daga Ubangiji Mai jin ƙai

    [59] Ku rarrabe dabam, a yau, ya ku masu laifi

    [60] Ashe, ban yi muku umurni na alkawari ba, ya ɗiyan Adamu? Cewa kada ku bauta wa Shaiɗan, lalle shi, maƙiyi ne a gareku bayyananne

    [61] Kuma ku bauta Mini. Wannan ita ce hanya madaidaciya

    [62] Kuma lalle haƙiƙa, (Shaiɗan) ya ɓatar da jama'a masu yawa daga gare ku. Ashe to ba ku kasance kuna yin hankali ba

    [63] Wannan ita ce Jahannama wadda kuka kasance ana yi muku wa'adi da ita

    [64] Ku shige ta a yau, saboda abin da kuka kasance kuna yi na kafirci

    [65] A yau, Muna sanya hatimin rufi a kan bakunansu, kuma hannayensu su yi Mana magana, kuma ƙafafunsu su yi shaidu da abin da suka kasance suna aikatawa

    [66] Da Mun so, da Mun shafe gani daga idanunsu, sai su yi tsere ga hanya, to, yaya za su yi gani

    [67] Kuma da Mun so, da Mun juyar da halittarsu a kan halinsu, saboda haka ba za su iya shuɗewa ba, kuma ba za su komo ba

    [68] Kuma wanda Muka raya shi, Mana sunkuyar da shi ga halittarsa. Ashe, ba su hankalta

    [69] Ba Mu sanar da shi (Annabi) waka ba, kuma waka ba ta kamata da shi (Annabi) ba. Shi (Al-ƙur'ani) bai zama ba face tunatarwa ce, da abin karatu bayyananne

    [70] Domin ya yi gargaɗi ga wanda ya kasance mai rai, kuma magana ta wajaba a kan kafirai

    [71] Shin, ba su gani ba (cewa) lalle Mun halitta musu dabbobi daga abin da HannayenMu suka aikata, sai suna mallakar su

    [72] Kuma Muka hore su, saboda su, saboda haka daga gare su abin hawansu yake, kuma daga gare su suke ci

    [73] Kuma suna da waɗansu amfanoni a cikinsu, da abubuwan sha. Ashe fa, ba za; su gode ba

    [74] Kuma suka riƙi waɗansu abubuwan bautawa wanin Allah, ɗammaninsu za su taimake su

    [75] Ba za su iya taimakonsu ba, alhali kuwa su runduna ce wadda ake halartarwa (a cikin wuta)

    [76] Saboda haka, kada maganarsu ta ɓata maka rai. Lalle Mu, Muna sanin abin da suke asirtawa da abin da suke bayyanawa

    [77] Ashe, kuma mutum bai ga (cewa) lalle Mu, Mun halitta shi daga maniyyi ba, sai ga shi mai yawan husuma, mai bayyanawar husumar

    [78] Kuma ya buga Mana wani misali, kuma ya manta da halittarsa, ya ce: "Wane ne ke rayar da ƙasusuwa alhali kuwa suna rududdugaggu

    [79] Ka ce: "Wanda ya ƙaga halittarsu a farkon lokaci Shi ke rayar da su, kuma Shi, game da kowace halitta, Mai ilmi ne

    [80] Wanda ya sanya muku wuta daga itace kore, sai ga ku kuna kunnawa daga gare shi

    [81] Shin, kuma Wanda Ya halitta sammai da ƙasa bai zama Mai ikon yi ba ga Ya halitta kwatankwacinsu? Na'am, zai iya! Kuma Shi Mai yawan halittawa ne, Mai ilmi

    [82] UmurninSa idan Ya yi nufin wani abu sai Ya ce masa kawai, "Ka kasance," sai yana kasancewa (kamar yadda Yake nufi)

    [83] Saboda haka, tsarki ya tabbata ga Wanda mallakar kowane abu take ga HannayenSa, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku

    Saffat

    Surah 37

    [1] Ina rantsuwa da masu yin sahu-sahu (a cikin salla ko yaƙi)

    [2] Sa'an nan masu yin tsawa domin gargaɗi

    [3] Sa'an nan da masu karatun abin tunatarwa

    [4] Lalle Abin bautawarku haƙiƙa ¦aya ne

    [5] Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke tsakaninsu, kuma Ubangijin wuraren fitar rana

    [6] Lalle Mu, Mun ƙawatar da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurari

    [7] Kuma suna tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai

    [8] Ba za su iya saurare zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Mala'iku) ba, kuma ana jifar su daga kowane gefe

    [9] Domin tunkuɗewa kuma suna da wata azaba tabbatacciya

    [10] Face wanda ya fizgi wata kalma, sai yula mai haske ta bi shi

    [11] Ka tambaye su: "Shin su ne mafi wuya ga halittawa, ko, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mu, Mun halitta su daga laka mai ɗauri

    [12] A'a, ka yi mamaki, alhali kuwa suna ta yin izgili

    [13] Kuma idan aka tunatar da su, ba su tunawa

    [14] Idan suka ga wata aya, sai su dinga yin izgili

    [15] Kuma su ce, "Wannnan ba kome ba, face sihiri, ne bayyananne

    [16] Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasusuwa, ashe, lalle mu tabbas waɗandaake tayarwa ne

    [17] Ashe ko da ubanninmu na farko

    [18] Ka ce: "Na'am alhali kuwa kuna ƙasƙantattu

    [19] Tsawa guda kawai ce, sai ga su, suna dubi

    [20] Kuma su ce: "Ya bonenmu! Wannan ita ce ranar sakamako

    [21] Wannan ita ce ranar rarrabewa wadda kuka kasance kuna ƙaryatawa

    [22] Ku tara waɗanda suka yi zalunci, da abokan haɗinsu, da abin da suka kasance suna bautawa

    [23] Wanin Allah, saboda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahim

    [24] Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne

    [25] Me ya same ku, ba ku taimakon juna

    [26] A'a, su a yau, masu sallamawa ne

    [27] Kuma sashensu ya fuskanta ga sashe, suna tambayar juna

    [28] Suka ce: "Lalle ku, kun kasance kuna je mana daga wajen dama (inda muka amince)

    [29] Suka ce: "A'a, ba ku kasance muminai ba

    [30] Kuma wani dalili bai kasance ba gare mu a kanku. A'a, kun kasance mutane ne masu ketare iyaka

    [31] Saboda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mu, masu ɗanɗanawa ne

    [32] Saboda haka muka ɓatar da ku. Lalle mu, mun kasance ɓatattu

    [33] To lalle su a ranar nan, masu tarayya ne a cikin azabar

    [34] Lalle Mu, kamar haka Muke aikatawa game, da masu laifi

    [35] Lalle su, sun kasance idan an ce musu: "Babu abin bautawa, face Allah," sai su dora girman kai

    [36] Kuma suna cewa, "Shin, mu lalle masu barin gumakanmu ne, saboda maganar wani mawaƙi mahaukaci

    [37] A'a, ya zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni

    [38] Lalle ku, haƙiƙa masu ɗanɗana azaba mai raɗaɗi ne

    [39] Kuma ba za a saka muku ba face da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [40] Face bayin Allah waɗanda aka tsarkake

    [41] Waɗannan suna da abinci sananne

    [42] Ya'yan itacen marmari, kuma suna waɗanda ake girmamawa

    [43] A cikin gidajen Aljannar ni'ima

    [44] A kan karagu, suna masu fuskantar juna

    [45] Ana kewayawa a kansu da hinjalan giya, ta daga waɗansu maremari

    [46] Fara mai daɗi ga mashayan

    [47] A cikinta babu jiri kuma ba su zama masu maye daga gare ta ba

    [48] Kuma a wurinsu, akwai matan aure masu taƙaita kallonsu, masu manyan idanu

    [49] Kamar dai su ƙwai ne ɓoyayye

    [50] Sai sashensu ya fuskanta a kan sashe, suna tambayar juna

    [51] Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani aboki ya kasance a gare ni (a duniya)

    [52] Yana cewa, "Shin, kai lalle, kana daga masu gaskatawa ne

    [53] Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasusuwa, ashe, lalle, mu tabbas waɗanda ake saka wa ne

    [54] (Mai maganar) ya ce: "Shin, ko ku, masu tsinkaya ne (mu gan shi)

    [55] Sai ya tsinkaya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim

    [56] Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, ka yi kusa, haƙiƙa, ka halakani

    [57] Kuma ba domin ni'imar Ubangijina ba, lalle, da na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tare da kai a cikin wuta)

    [58] Shin fa, ba mu zama masu mutuwa ba

    [59] Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba

    [60] Lalle, wannan shi ne babban rabo mai girma

    [61] Saboda irin wannan, sai masu aiki su yi ta aikatawa

    [62] Shin wancan shi ne mafi zama alheri ga liyafa ko itaciyar zaƙƙum

    [63] Lalle, Mu, Mun sanya ta fitina ga. azzalumai

    [64] Lalle ita wata itaciya ce wadda take fita daga asalin Jahim

    [65] Gundarta, kamar dai shi kanun Shaiɗan ne

    [66] To, lalle su haƙiƙa masu ci ne daga gare ta. Sa'an nan masu cika cikuna ne daga gare ta

    [67] Sa'an nan lalle suna da wani garwaye a kanta, daga ruwan zafi

    [68] Sa'an nan lalle makomarsu, haƙiƙa, zuwa ga Jahim take

    [69] Lalle su, sun iske ubanninsu batattu

    [70] Saboda haka su, a kan gurabunsu, suke gaggawa

    [71] Kuma tabbas haƙiƙa mafi yawan mutanen farko sun ɓace a gabaninsu

    [72] Kuma tabbas haƙiƙa, Mun aika masu gargaɗi a cikinsu

    [73] Sai ka duba yadda aƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance

    [74] Face bayin Allah waɗanda aka tsarkake

    [75] Kuma lalle, haƙiƙa' Nuhu ya kira Mu. To, madalla da masu karɓawa, Mu

    [76] Kuma Mun tsirar da shi da mutanensa daga bakin ciki babba

    [77] Muka sanya zurriyarsa suna masu wanzuwa

    [78] Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe

    [79] Aminci ya tabbata ga Nuhu, a cikin halittu

    [80] Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa

    [81] Lalle shi, yana daga bayinMu muminai

    [82] Sa'an nan Muka nutsar da waɗansunsu

    [83] Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙiƙa, Ibrahim yake

    [84] A lokacin da ya je wa dangijinsa da zuciya kuɓutacciya

    [85] A lokacin da ya ce wa ubansa da mutanensa, "Mene ne kuke bautawa

    [86] Shin, ƙiren ƙarya (watau) gumaka, wanin Allah, kuke bautawa

    [87] To, mene ne zatonku game da Ubangijin halittu

    [88] Sai ya yi dubi, duba ta sosai, a cikin taurari

    [89] Sa'an nan ya ce: "Ni mai rashin lafiya ne

    [90] Sai suka juya ga barinsa, suna masu juyawa da baya

    [91] Sai ya karkata zuwa ga gumakansu, sa'an nan ya ce: "Ashe ba za ku ci ba

    [92] Me ya same ku, ba ku magana

    [93] Sai ya zuba duka a kansu da hannun dama

    [94] Sai suka fuskanto zuwa gare shi, suna gaggawa

    [95] Ya ce, "Kuna bauta wa abin da kuke sassaƙawa

    [96] Alhali, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatawa

    [97] Suka ce: "Ku gina wani gini saboda shi, sa'an nan ku jefa shi a cikin Jahim

    [98] Saboda haka suka yi nufin makida game da shi. Sai Muka sanya su, su ne mafi ƙasƙanci

    [99] Kuma (Ibrahim] ya ce: "Lalle, ni mai tafiya ne zuwa ga Ubangijina, zai shiryar da ni

    [100] Ya Ubangijina! Ka ba ni (abokin zama) daga salihan mutane

    [101] Sai Muka yi masa bushara da wani yaro mai haƙuri

    [102] To, a lokacin da ya isa aiki tare da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗana! Lalle ne ina gani, a ciki barci, lalle ina yanka ka. To, ka duba me ka gani?" (Yaron) ya ce: "Ya, Babana! Ka aikata abin da aka umurce ka, za ka same ni, in Allah Ya so, daga masu haƙuri

    [103] To, a lokacin da suka yi sallama, (Ibrahim) ya kayar da shi ga gefen goshinsa

    [104] Kuma Muka kira shi cewa "Ya Ibrahim

    [105] Haƙiƙa ka gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa

    [106] Lalle wannan ita ce jarrabawa bayyananna

    [107] Kuma Muka yi fansar yaron da wani abin yanka, mai girma

    [108] Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutanen ƙarshe

    [109] Aminci ya tabbata ga Ibrahim

    [110] Kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa

    [111] Lalle shi, yana daga bayinMu muminai

    [112] Kuma Muka yi masa bushara Da Is'haƙa ya zama Annabi daga salihan mutane

    [113] Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'haka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatawa da kuma maizalunci domin kansa, mai bayyanawa (ga zaluncin)

    [114] Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Musa da Haruna

    [115] Kuma Muka tsirar da su da mutanensu daga bakin ciki mai girma

    [116] Kuma Muka taimake su, saboda haka suka kasance masu rinjaya

    [117] Kuma Muka ba su Littafi mai iyakar bayani

    [118] Kuma Muka shiryar da su ga hanya miƙaƙƙiya

    [119] Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutanen karshe

    [120] Aminci ya tabbata ga Musa da Haruna

    [121] Lalle kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa

    [122] Lalle, suna daga bayinMu muminai

    [123] Kuma lalle Ilyas, haƙiƙa, yana daga Manzanni

    [124] A lokacin da yake ce wa mutanensa, "Ashe, ba za ku yi taƙawa ba

    [125] Shin, kuna bauta wa Ba'al ne, kuma kuna barin Mafi kyautatawar masu halitta

    [126] Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko

    [127] Sai suka ƙaryata shi. Saboda haka su lalle waɗanda za a halartawa ne (a wuta)

    [128] Sai bayin Allah waɗanda aka tsarkake

    [129] Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutanen ƙarshe

    [130] Aminci ya tabbata ga Ilyas

    [131] Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa

    [132] Lalle shi, yana daga bayinMu muminai

    [133] Kuma lalle Ludu, haƙiƙa, yana daga Manzanni

    [134] A lokacin da Muka tsirar da shi, da mutanensa gaba ɗaya

    [135] Sai wata tsohuwa tana a cikin masu wanzuwa (a cikin azaba)

    [136] Sa'an nan Muka darkake waɗansu mutanen

    [137] Kuma lalle ku, haƙiƙa, kuna shuɗewa a kansu, kuna masu asubanci

    [138] Kuma da dare. Shin fa, ba za ku hankalta ba

    [139] Kuma lalle Yunusa, haƙiƙa, yana daga Manzanni

    [140] A lokacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lodi

    [141] Sa'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya

    [142] Sai kifi ya yi loma da shi, alhali kuwa yana wanda ake zargi

    [143] To, ba domin lalle shi ya kasance daga masu tasbihi ba

    [144] Lalle da ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa ranar da za a tayar da su

    [145] Sai Muka jefa shi ga wani fili alhali kuwa yana mai raunin rashin lafiya

    [146] Kuma Muka tsirar da wata itaciya ta kankana a kusa da shi

    [147] Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutane dubuɗari, ko suna ƙaruwa (a kan haka)

    [148] Sai suka yi imani saboda haka Muka jiyar da su dadi har wani lokaci

    [149] Saboda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mata, kuma su da ɗiya maza

    [150] Ko kuma Mun halitta mala'iku mata ne, alhali kuwa su sunahalarce

    [151] To! Lalle su, daga ƙiren ƙaryarsu suna cewa

    [152] Allah Ya haihu," alhali kuwa lalle su, haƙiƙa maƙaryata ne

    [153] Shin, Ya zaɓi 'ya'ya mata ne a kan ɗiya maza

    [154] Me ya same ku? Yaya kuke hukuntawa (wannanhukunci)

    [155] Shin, ba ku tunani

    [156] Ko kuma kuna da wani dalili bayyananne ne

    [157] To, ku zo da littafinku idan kun kasance masu gaskiya

    [158] Kuma suka sanya nasaba a tsakaninSa da tsakanin aljannu. Alhali kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle su, haƙiƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wuta)

    [159] Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantawa

    [160] Sai bayin Allah waɗanda aka tsarkake

    [161] To, lalle, ku da abin da kuke bautawa

    [162] Ba ku zama masu buwaya ba a gare Shi

    [163] Sai wanda yake mai shiga babbar wuta Jahim

    [164] Kuma babu kowa daga cikinmu, face yana da matsayi sananne

    [165] Kuma lalle mu, haƙiƙa, mu ne masu yin sahu-sahu (domin ibada)

    [166] Kuma lalle mu haƙiƙa, mu ne masu yin tasbihi

    [167] Kuma lalle su, sun kasance suna cewa

    [168] Da lalle muna da wani littafi irin na mutanen farko

    [169] Lalle da mun kasance bayin Allah waɗanda aka tsarkake

    [170] Sai suka kafirta da shi. Saboda haka za su sani

    [171] Kuma lalle, haƙiƙa kalmarMu ta gabata ga bayinMu, Manzanni

    [172] Lalle su, haƙiƙa, su ne waɗanda ake taimako

    [173] Kuma lalle rundunarMu, haƙiƙa, su ne marinjaya

    [174] Saboda haka juya daga barinsu, har a wani lokaci

    [175] Ka nuna musu (gaskiya), da haka za su dinga gani

    [176] Shin fa, da azabarMu suke neman gaggawa

    [177] To, idan ta sauka ga farfajiyarsu, to, safiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta munana

    [178] Kuma ka juya daga barinsu har a wani lokaci

    [179] Ka nuna (musu gaskiya), da haka za su dinga nunawa

    [180] Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjaye, daga barin abin da suke siffantawa

    [181] Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni

    [182] Kuma godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu

    Sad

    Surah 38

    [1] S, Ina rantsuwa da Al-ƙur'ani mai hukunce-hukunce

    [2] A'a, waɗanda suka kafirta suna cikin girman kai (ga rikon al'adunsu) da saɓani (tsakanin junansu)

    [3] Da yawa Muka halakar da wani ƙarni, a gabaninsu, suka yi kira (neman ceto), babu lokacin kuɓucewa

    [4] Kuma suka yi mamaki domin Mai gargaɗi, daga cikinsu, ya je musu. Kuma kafirai sukace, "Wannan mai sihiri ne, maƙaryaci

    [5] Shin, ya sanya gumaka duka su zama abin bautawa guda? Lalle wannan, haƙiƙa, abu ne mai ban mamaki

    [6] Shugabanni daga cikinsu, suka tafi (suka ce),"Ku yi tafiyarku, ku yi haƙuri a kan abubuwan bautawarku. Lalle wannan, haƙiƙa, wani abu ne ake nufi

    [7] Ba mu taɓa ji ba, game da wannan a cikin addinin ƙarshe. Wannan bai zama ba face ƙiren ƙarya

    [8] Shin, an saukar da Alƙur'ani ne a kansa, a tsakaninmu (mu kuma ba mu gani ba)?" A'a, su dai suna cikin shakka daga hukunciNa A'a, ba su i da ɗanɗanar azaba ba

    [9] Ko kuma a wurinsu ne ake ajiye taskokin rahamar Ubangijinka, Mabuwayi, Mai yawan kyauta

    [10] Ko kuma su ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu? To sai su hau a cikin sammai (domin, su hana saukar Alƙur'ani ga Muhammadu)

    [11] Rundunoni ne abin da ke can, rusassu, na ƙungiyoyinsu

    [12] Mutanen Nuhu sun ƙaryata, a gabaninsu, da Adawa da Fir'auna mai turakun (da suka kafe mulkinsa)

    [13] Da Samudawa da mutanen Luɗu da ma'abuta ƙunci, waɗancan ne ƙungiyoyin

    [14] Babu kowa a cikinsu face ya ƙaryata Manzanni, saboda haka azabaTa ta wajaba

    [15] Kuma waɗannan ba su jiran kome face tsawa guda, wadda ba ta da hani

    [16] Kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka gaggauta mana da rabonmu, a gabanin ranar bincike

    [17] Ka yi haƙuri bisa ga abin da suke faɗa (na izgili), kuma ka ambaci bawanMu Dawuda ma'abucin ƙarfin ibada. Lalle, shi, mai mayar da al'amari ga Allah ne

    [18] Lalle Mu, Mun hore duwatsu tare da shi, suna yin tasbihi maraice da fitowar rana

    [19] Da tsuntsaye waɗanda ake tattarawa, kowannensu mai komawa ne a gare shi

    [20] Kuma Muka ƙarfafa mulkinsa, kuma Muka ba shi hikima da rarrabewar magana

    [21] Kuma shin, labarin masu husuma ya zo maka, a lokacin da suka haura garun masallaci

    [22] A lokacin da suka shiga ga Dawuda, sai ya firgita daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsoro, masu husuma biyu ne; sashenmu ya zalunci sashe. Saboda haka, ka yi hakunci a tsakaninmu da gaskiya. Kada ka ƙetare haddi kuma ka shiryar da mu zuwa, ga tsakar hanya

    [23] Lalle wannan dan'uwana ne, yana da tunkiya casa'in da tara, kuma ina da tunkiya guda, sai ya ce: 'Ka lamunce mini ita. Kuma ya buwaye ni ga magana

    [24] (Dawuda) ya ce: "Lalle, haƙiƙa ya zalunce ka game da tambayar tunkiyarka zuwa ga tumakinsa. Kuma lalle ne masu yawa daga abokan tarayya, haƙiƙa, sashensu na zambatar sashe face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai." Kuma Dawuda ya tabbata cewa Mun fitine shi ne, saboda haka, ya nemi Ubangijinsa gafara, kuma ya faɗi yana mai sujada, kuma ya mayar da al'amari ga Allah

    [25] Saboda haka Muka gafarta masa wancan, kuma lalle yana da wata kusantar daraja a wurinMu, da kyaun makoma

    [26] Ya Dawuda! Lalle Mu Mun sanya ka Halifa a cikin ƙasa. To, ka yi hukunci tsakanin mutane da gaskiya, kuma kada ka biye wa son zuciyar, har ya ɓatar dakai daga hanyar Allah. Lalle waɗanda ke ɓacewa daga hanyar Allah suna da wata azaba mai tsanani domin abin da suka manta, a ranar hisabi

    [27] Kuma ba Mu halitta sama da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu ba a kan ƙarya. Wannan shi ne zaton waɗanda suka kafirta. To, bone ya tabbata ga waɗanda suka kafirta daga wuta

    [28] Ko za Mu sanya waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai kamar waɗanda suke masu barna ne a cikin ƙasa? Ko kuma za Mu sanya masu bin Allah da taƙawa kamar fajirai makarkata

    [29] (Wannan) Littafi ne, Mun saukar da shi zuwa gare ka, yana, mai albarka, domin su lura da ayoyinsa, kuma don masu hankali su riƙa yin tunani

    [30] Kuma Muka bai wa Dawuda Sulaiman. Madalla da bawanMu, shi. Lalle shi (Sulaiman) mai mayar da al'amari ne ga Allah

    [31] A lokacin da aka gitta masa dawaki masu asali, a lokacin maraice

    [32] Sai ya ce: "Lalle ni, na fifita son dukiya daga tunawar Ubangijina, har (rana) ta faku da shamaki

    [33] Ku mayar da su a gare ni." Sai ya shiga yankansu da takobi ga ƙwabrukansu da wuyoyinsu

    [34] Kuma lalle haƙiƙa, Mun fitini Sulaiman kuma Muka jefa wani jikin mutum a kan karagarsa. Sa'an nan ya mayar da al'amari zuwa gare Mu

    [35] Ya ce: "Ya Ubangijina! Ka gafarta mini, kuma Ka ba ni mulki wanda ba ya kamata da kowa daga bayana. Lalle Kai, Kai ne Mai yawan kyauta

    [36] Saboda haka Muka hore masa iska tana gudu da umurninsa, tana tashi da sauƙi, inda ya nufa

    [37] Da shaiɗanu dukan mai gini, da mai nutsa (a cikin koguna)

    [38] Waɗansu, ɗaɗɗaure a cikin maruruwa

    [39] Wannan kyautarMu ce. Sai ka yi kyauta ga wanda kake so, ko kuma ka riƙe, babu wani bincike

    [40] Kuma lalle, haƙiƙa yana da kusantar daraja a wurinMu da kyaun makoma

    [41] Kuma ka ambaci bawanMu Ayyuba a lokacin da ya kirayi Ubangijinsa, ya ce: "Lalle ni, Shaiɗan ya shafe ni da wahala da kuma wata azaba

    [42] Ka shura da ƙafarka. Wannan abin wanka ne mai sanyi da abin sha

    [43] Kuma Muka ba shi iyalansa da kwatankwacinsu tare da su saboda rahama daga gare Mu, da tunatarwa ga masu hankali

    [44] Kuma ka riƙi wata ƙulla da hannunka, ka yi duka da ita kuma kada ka karya rantsuwarka. Lalle Mu, Mun same shi mai haƙuri. Madalla da bawa, shi Lalle shi mai mayar da al'amari ga Allah ne

    [45] Kuma ka ambaci bayinMu: Ibrahim da ls'haƙa da Ya'aƙuba, ma'abuta ƙarfin (ɗaukar umurninMu) da basira

    [46] Lalle Mu, Mun keɓance su game da wata, tsattsarkar aba: Hukunce-hukuncen gidan duniya (mai tunatar da su Lahira)

    [47] Kuma lalle su a wurinMu, tabbas, suna daga zaɓaɓɓu, mafifita

    [48] Kuma ka ambaci Isma'ila da llyas da Zulkifli, kuma dukansu suna daga zaɓaɓɓu

    [49] Wannan tunatarwa ce, kuma lalle masu bin Allah da taƙawa, suna da kyakkyawar makoma

    [50] Gidajen Aljannar zama, alhali kuwa tana abar buɗe wa kofofi saboda su

    [51] Suna gingincire a cikinsu, suna kira a cikinsu, ga 'ya'yan itacen marmari masu yawa, da abin sha

    [52] Kuma a wurinsu akwai matan aure masu gajarta ganinsu ga mazansu, tsarar juna

    [53] Wannan shi ne abin da ake yi muku wa'adi ga ranar hisabi

    [54] Lalle wannan, haƙiƙa, azurtarwarMu ce, ba ta ƙarewa

    [55] Wannan shi ne kuma lalle makangara, haƙiƙa, suna da mafi sharrin makoma

    [56] Jahannama, suna shigarta. To, shimfiɗar ta munana, ita

    [57] Wannan shi ne! To, su ɗanɗane shi: ruwan zafi ne da ruɓaɓɓen jini

    [58] Da wani daga siffarsa nau'i-nau'i

    [59] Wannan wani yanki ne mai kutsawa tare da ku, babu maraba a gare su, lalle su, masu shiga Wuta ne

    [60] Suka ce: "A'a, ku ne babu maraba a gare ku, ku ne kuka gabatar da shi a gare mu." To, matabbatar ta munana (ita wutar)

    [61] Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Wanda ya gabatar da wannan a gare mu, to, Ka ƙara masa azaba, ninki, a cikin wuta

    [62] Kuma suka ce: "Me ya same mu, ba mu ganin waɗansu mazaje, mun kasance muna ƙidaya su daga ashararai

    [63] Shin, mun riƙe su abin izgili ne ko idanunmu sun karkata daga gare su ne

    [64] Lalle wannan, haƙiƙa, gaskiya ne, husumar mutanen wuta

    [65] Ka ce: "Ni mai gargaɗikawai ne, kuma babu wani abin bautawa sai Allah, Makaɗaici, Mai tilastawa

    [66] Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu Mabuwayi, Mai gafara

    [67] Ka ce: "Shi (Alkur'ani) babban labari ne mai girma

    [68] Ku, masu bijirewa ne daga gare shi

    [69] Wani ilmi bai kasance a gare ni ba game da jama'a (mala'iku) mafi ɗaukaka a lokacin da suke yin husuma

    [70] Ba a yi mini wahayin kome ba face cewa ni mai gargaɗi kawai ne, mai bayyanawa

    [71] A lokacin da Ubangijinka Ya ce wa mala'iku, "Lalle Ni Mai halitta mutum ne daga laka

    [72] Sa'an nan idan Na daidaita shi, kuma Na hura (wani abu) daga RuhiNa a cikinsa to ku faɗi kuna masu sujada a gare; shi

    [73] Sai mala'ikun suka yi sujada dukansu, gaba ɗaya

    [74] Face Iblis, ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kafirai

    [75] (Allah) Ya ce, "Ya Ibilis! Me ya hana ka, ka yi sujada ga abin da Na halitta da HannayeNa biyu? Shin, ka yi girman kai ne, ko kuwa ka kasance daga maɗaukaka ne

    [76] Ya ce, "Ni, mafifici ne daga gare shi: Ka halitta ni daga wuta, kuma Ka halitta shi daga laka

    [77] Ya ce, "To, ka fita daga gare ta, domin lalle kai la'ananne ne

    [78] Kuma lalle a kanka akwai la'anaTa har zuwa ranar sakamako

    [79] Ya ce, "Ya Ubangijina! To, Ka yi mini jinkiri zuwa ga ranar da ake tayar da su

    [80] Ya ce, "To, lalle kana daga waɗanda aka yi wa jinkiri

    [81] Zuwa ga yinin lokaci sananne

    [82] Ya ce, "To, ina rantsuwa da buwayarKa, lalle, ina ɓatar da su gaba ɗaya

    [83] Face bayinKa tsarkakakku daga gare su

    [84] (Allah) Ya ce, "To, (wannan magana ita ce) gaskiya. Kuma gaskiya Nake faɗa

    [85] Lalle za Ni cika Jahannama daga gare ka, kuma daga wanda ya bi ka daga gare su, gaba ɗaya

    [86] Ka ce: "Ba ni tambayar ku wata ijara, a kansa kuma ba ni daga masu ƙaƙalen faɗarsa

    [87] Shi (Alkur'an) bai zama ba face ambato ne ga dukan halitta

    [88] Kuma lalle za ku san babban labarinsa a bayan ɗan lokaci

    Zumar

    Surah 39

    [1] Saukar da Littafin daga Allah ne, Mabuwayi, Mai hikima

    [2] Lalle Mu Mun saukar da Littafi zuwa gare ka, da gaskiya. Saboda haka, ka bauta wa Allah kana mai tsarkake addini a gare Shi

    [3] To, addini tsarkakakke na Allah ne, kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, ba Shi ba, (suna cewa) "Ba mu bauta musu ba face domin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja." Lalle Allah na yin hukunci a tsakaninsu ga abin da suka zama suna saɓawa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kafirci

    [4] Da Allah Ya yi nufin Ya riƙi ɗa, to, lalle sai Ya zaɓa daga abin da Yake halittawa abin da Yake so. Tsarki ya tabbata a gare Shi. Shi ne Allah, Makaɗaici, Mai tilastawa

    [5] Ya halitta sammai da ƙasa da gaskiya. Yana shigar da dare a kan rana, kuma Yana shigar da rana a kan dare kuma Ya hore rana da wata, kowannensu yana gudana zuwa ga ajali ambatacce. To, Shi ne Mabuwayi, Mai gafara

    [6] Ya halitta ku daga rai guda, sa'an nan Ya sanya ma'auranta daga gare shi. Kuma ya saukar muku daga dabbobin gida nau'i takwas Yana halitta ku a cikin cikunnan uwayenku, halitta a bayan wata halitta, a cikin duffai uku. Wannan shi ne Allah Ubangijinku. Mulki a gare shi yake. Babu abin bautawa face Shi. To, yaya ake karkatar da ku

    [7] Idan kun kafirta to, lalle Allah Wadatacce ne daga barinku, kuma ba Shi yarda da kafirci ga bayinSa, kuma idan kun gode, Zai yarda da ita (godiyar) a gare ku, kuma wani rai mai ɗaukar nauyi, ba ya ɗaukar nauyin wani. Sa'an nan kuma makomarku zuwa ga Ubangijinku take, domin Ya ba ku labari game da abin da kuka kasance kuna aikatawa. Lalle Shi, Masani ne ga abin da yake a ainihin zukata

    [8] Kuma idan wata cuta ta shafi mutum, sai ya kira Ubangijinsa, yana mai mai da al'amari zuwa gare Shi, sa'an nan idan Ya juyar da cutar da ni'ima ta daga gare Shi, sai ya manta da abin da ya kasance yana kira zuwa gare shi a gabanin haka, kuma ya sanya wa Allah waɗansu abokan tarewa domin ya ɓatar (da su) daga hanyarSa. Ka ce (masa), "Ka ji daɗi da kafircinka, a ɗan lokaci, lalle kai daga 'yan wuta ne

    [9] Shin, wanda yake mai tawali'u sa'o'in dare, yana mai sujada kuma yana mai tsayi ga salla, yana tsoron Lahira, kuma yana fatan rahamar Ubangijinsa, (yana daidai da waninsa?) Ka ce: "Ashe, waɗanda suka sani, suna daidaita da waɗanda ba su sani ba?" Masu hankali kawai ke yin tunani

    [10] Ka ce: (Allah Ya ce): "Ya bayiNa waɗanda suka yi imani! Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Waɗanda suka kyautata a cikin wannan duniya suna da sakamako mai kyau, kuma ƙasar Allah mai faɗi ce. Masu haƙuri kawai ake cika wa ijararsu, ba da wani lissafi ba

    [11] Ka ce: "Lalle ni, an umurce ni da in bauta wa Allah, ina tsarkake addini a gare Shi

    [12] Kuma an umurce ni da in kasance farkon masu miƙa wuya (ga umurnin Allah)

    [13] Ka ce: "Lalle ni ina tsoro, idan na saɓa wa Ubangijina, ga azabar yini mai girma

    [14] Ka ce: "Allah nake bauta wa, ina mai tsarkake addinina a gare Shi

    [15] To, ku bauta wa abin da kuke so, waninSa." Ka ce: "Lalle masu hasara, su ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu da iyalansu, a Ranar ¡iyama. To, waccan fa, ita ce hasara bayyananna

    [16] Suna da waɗansu inuwowi na wuta daga samansu, kuma daga ƙasansu akwai waɗansu inuwowi. Wancan Shi ne Allah ke tsoratar da bayinSa da shi. Ya bayiNa! To, ku bi Ni da taƙawa

    [17] Kuma waɗanda suka nisanci Shaiɗannu ga bauta musu, kuma suka mai da al'amari ga Allah, suna da bushara. To, ka bayar da bushara ga bayiNa

    [18] Waɗanda ke sauraren magana, sa'an nan su bi mafi kyaunta. waɗancan su ne Allah Ya shiryar da su, kuma waɗancan su ne masu hankali

    [19] Shin fa, wanda kalmar azaba ta wajaba a kansa? Shin fa, kana iya tsamar da wanda ke a cikin wuta

    [20] Amma waɗanda suka bi Ubangijinsu da taƙawa, suna da benaye, daga samansu akwai waɗansu benaye ginannu, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu. Alkawarin Allah. Allah ba Ya saɓa wa alkawarinSa

    [21] Shin, ba ka gani ba cewa lalle Allah Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya gudanar da shi yana maremari a cikin ƙasa sa'an nan Ya fitar da shuka game da shi, launukan shukar masu saɓanin juna sa'annan shukar ta ƙeƙashe har ka gan ta fatsifatsi, sa'an nan Allah Ya sanya ta dandaƙaƙƙiya? Lalle ne ga wancan akwai tunatarwa ga masu hankali (ga iyawar gudanar da ruwa a cikin gidajen Aljanna)

    [22] Shin fa, wanda Allah Ya buɗa ƙirjinsa, domin Musulunci sa'an nan shi yana a kan haske daga Ubangijinsa, (zai zama kamar waninsa)? To, bone ya tabbata ga maƙeƙasa zukatansu daga ambaton Allah. Waɗancan suna a cikin wata ɓata bayyananna

    [23] Allah Ya sassaukar da mafi kyaun labari, Littafi mai kama da juna, wanda ake konkoma karatunsa fatun waɗanda ke tsoron Ubangijinsu, suna taƙura saboda Shi, sa'an nan fatunsu da zukatansu su yi laushi zuwa ga ambaton Allah. Waccan ita ce shiryarwar Allah, Yana shiryar da wanda Ya so game da ita. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, ba shi da wani mai shiryarwa

    [24] Shin fa, wanda ke kare muguwar azaba da fuskarsa (yana zama kamar waninsa) a Ranar ƙiyama? Kuma a ce wa azzalumai, "Ku ɗanɗani abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [25] Waɗanda ke a gabaninsu, sun ƙaryata, sai azaba ta je musu daga inda ba su sani ba

    [26] Sai Allah Ya ɗanɗana musu azabar wulakanci a cikin rayuwar duniya, kuma lalle azabar Lahira ita ce mafi girma, da sun kasance suna da sani

    [27] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun buga wa mutane a, cikin wannan Alƙur'ani, daga kowane misali, ɗammaninsu su yi tunani

    [28] Abin karantawa ne na Larabci, ba mai wata karkata ba, ɗammaninsu, su yi taƙawa

    [29] Allah Ya buga misali; wani mutum (bawa) a cikinsa akwai masu tarayya, masu mugun halin jayayya, da wani mutum (bawa) dukansa ga wani mutum. Shin, za su daidaita ga misali? Godiya ta tabbata ga Allah (a kan bayani). A'a, mafi yawan mutane ba su sani ba

    [30] Lalle kai mai mutuwa ne, kuma su ma lalle masu mutuwa ne

    [31] Sa'an nan, lalle ku, a Ranar ¡iyama, a wurin Ubangijinku, za ku yi ta yin husuma

    [32] To, wane ne mafi zalunci daga wanda ya yi ƙarya ga Allah, kuma ya ƙaryata gaskiya a lokacin da ta je masa? Shin babu mazauni a cikin Jahannama ga kafirai

    [33] Kuma wanda ya zo da gaskiya, kuma ya gaskata a game da ita, waɗancan su ne masu taƙawa

    [34] Suna da abin da suke so wajen Ubangijinsu. Wancan shi ne sakamakon masu kyautatawa

    [35] Domin Allah Ya kankare musu mafi munin abin da suka aikata, kuma Ya saka musu ijararsu da mafi kyaun abin da suka kasance suna aikatawa

    [36] Ashe Allah bai zama Mai isa ga BawanSa ba? Kuma suna tsoratar da kai ga waɗanda suke waninSa, kuma wanda Allah Ya ɓatar to, ba, shi da mai shiryarwa

    [37] Kuma wanda Allah Ya shiryar, to, ba shi da mai ɓatarwa. Ashe, Allah bai zama Mabuwayi ba, Mai azabar ramuwa

    [38] Kuma lalle idan ka tambaye su: "Wane ne ya halitta sammai da ƙasa?" Haƙiƙa, za su ce, "Allah ne." Ka ce: "Ashe, to, kun gani abin da kuke kira, waɗanda suke wanin Allah ne, idan Allah Ya nufe ni da wata cuta, shin su abubuwan nan masu kuranye, cutarsa ne? Ko kuma Ya nufe ni da wata rahama, shin, su abubuwan nan masu kame rahamarSa ne?" Ka ce: "Mai isata Allah ne, gare Shi masu tawakkali ke dogara

    [39] Ka ce: "Ya mutanena! Ku yi aiki a kan halinku, lalle ni, ina aiki a kan halina. Sa'an nan za ku sani

    [40] Wanda azaba ta je masa, za ta wulakanta shi, kuma wata azaba mai dawwama za ta sauka a kansa

    [41] Lalle Mu Mun saukar da littafi a gare ka domin mutane da gaskiya. Sa'an nan wanda ya nemi shiriya, to, domin kansa, kuma wanda ya ɓace, to, yana ɓacewa ne a kanta. Kuma ba ka zama wakili a kansu ba

    [42] Allah ne ke karɓar rayuka a lokacin mutuwarsu, da waɗannan da ba su mutu ba, a cikin barcinsu. Sa'an nan Ya riƙe wanda Ya hukunta mutuwa a kansa kuma Ya saki gudar, har zuwa ga ajali ambatacce. Lalle a cikin wancan, haƙiƙa, akwai ayoyi ga mutane waɗanda ke yin tunani

    [43] Ko kuma sun riƙi masu ceto ne, waɗansun Allah? Ka ce: "Shin, kuma ko da sun kasance ba su da mallakar kome, kuma ba su hankalta

    [44] Ka ce: "Ceto gaba ɗaya ga Allah yake. Mulkin sammai da ƙasa Nasa ne. Sa'an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [45] Kuma idan aka ambaci Allah Shi kaɗai zukatan waɗanda ba su yi imani ba da Lahira, su yi ƙiyama, kuma idan an ambaci waɗanda suke kiran, wasunSa, sai gasu suna yin busharar farin ciki

    [46] Ka ce: "Ya Allah, Mai ƙaga halittar sammai da ƙasa, Masanin gaibi da bayyane! Kai ne ke yin hukunci a tsakanin bayinKa a cikin abin da suka kasance suna saɓa wa juna a cikinsa

    [47] Kuma da waɗanda suka yi zalunci suna da abin da ke cikin ƙasa gaba ɗaya, da misalinsa a tare da shi lalle da sun yi fansa da shi daga mummunar azaba, a Ranar ¡iyama. Kuma abin da ba su kasance suna zato ba, daga Allah, ya bayyana a gare su

    [48] Munanan ayyuka da suka aikata, suka bayyana a gare su, kuma abin da suka kasance suna yi, na izgili, ya wajaba a kansu

    [49] To, idan wata cuta ta shafi mutum, sai ya kiraye Mu, sa'an nan idan Muka canza masa ita, ya sami ni'ima daga gare Mu, sai ya ce: "An ba ni ita ne a kan wani ilmi nawa kawai." A'a ita wannan (magana) fitina ce, kuma amma mafi yawansu ba su sani ba

    [50] Lalle waɗanda ke a gabaninsu, sun faɗe ta, saboda haka abin da suka kasance suna aikatawa bai wadatar da su da kome ba

    [51] Sai (sakamakon) munanan abin da suka aikata ya same su. Kuma waɗanda suka yi zalunci daga waɗannan, (sakamakon) munanan abin da suka aikata zai same su, kuma ba su zama mabuwaya ba

    [52] Ashe kuma ba su sani ba cewa Allah, na shimfiɗa arziƙi ga wanda Yake so, kuma Yana ƙuƙuntawa? Lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga mutane waɗanda ke yin imani

    [53] Ka ce: (Allah Ya ce): "Ya bayiNa waɗanda suka yi barna a kan rayukansu! Kada ku yanke ƙauna daga rahamar Allah. Lalle Allah na gafarta zunubai gaba ɗaya. Lalle Shi, Shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [54] Kuma ku mayar da al'amari zuwa ga Ubangijinku, kuma ku sallama Masa, a gabanin azaba ta zo muku, sa'an nan kuwa ba za a taimake ku ba

    [55] Kuma ku bi mafi kyaun abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku, a gabanin azaba ta zo muku, bisa auke, kuma ku ba ku sani ba

    [56] Kada wani rai ya ce: 'Ya nadamata a kan abin da na yi sakaci a cikin sashen Allah' kuma lalle na kasance, haƙiƙa, daga masu izgili

    [57] Ko kuma (kada) ya ce: 'Da Allah Ya shiryar da ni, da na kasance daga masu taƙawa

    [58] Ko kuma (kada (ya ce: a lokacin da yake ganin azaba, 'Da lalle a ce ina da wata komawa (zuwa duniya) domin in kasance daga masu kyautatawa

    [59] Na'am! Lalle ne ayoyiNa sun je maka, sai ka ƙaryata a game da su, kuma ka yi girman kai, kuma ka kasance daga kafirai

    [60] Kuma a Ranar ¡iyama kana ganin waɗanda suka yi ƙarya ga Allah fuskokinsu suna masu yin baƙi. Ashe babu mazauni a cikin Jahannama ga masu girman kai

    [61] Kuma Allah na tsirar da waɗanda suka yi taƙawa a game da wurin samun babban rabonsu, cuta ba za tashafe su ba, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba

    [62] Allah ne Mai halitta dukan kome, kuma Shi ne Wakili a kan kome

    [63] Shi ke da mabuɗan sammai da ƙasa. Kuma waɗanda suka kafirta da ayoyin Allah, waɗannan su nemasu hasara

    [64] Ka ce: "Shin, wanin Allah kuke umurni na da in bauta wa? Ya ku jahilai

    [65] Kuma an yi wahayi zuwa gare ka da kuma zuwa ga waɗanda suke a gabaninka, "Lalle idan ka yi shirki haƙiƙa aikinka zai ɓaci, kuma lalle za ka kasance daga masu hasara

    [66] A'aha! Ka bauta wa Allah kaɗai, kuma ka kasance daga masu godiya

    [67] Kuma ba su ƙaddara Allah a kan haƙiƙanin ikon yinsa ba: ¡asa duka damƙarSa ce, a Ranar ¡iyama, kuma sammai abubuwan naɗewa ne ga damanSa. Tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Ya ɗaukaka daga barin abin da suke shirki da shi

    [68] Kuma aka busa a cikin ƙaho, sai waɗanda ke a cikin sammai da ƙasa suka suma sai wanda Allah Ya so (rashin sumansa) sa'an nan aka hura a cikinsa, wata hurawa, sai ga su tsaitsaye, suna kallo

    [69] Kuma ƙasa ta yi haske da hasken Ubangijinta, kuma aka aza littafi, kuma aka zo da Annabawa da masu shaida, kuma aka yi hukunci a tsakaninsu, da gaskiya, alhali kuwa, su, ba za a zalunce su ba

    [70] Kuma aka cika wa kowane rai abin da ya aikata. Kuma (Allah) Shi ne Mafi sani game da abin da suke aikatawa

    [71] Kuma aka kora waɗanda suka kafirta zuwa Jahannama, jama'a-jama'a har a lokacin da suka je mata, sai aka buɗe ƙofofinta, kuma matsaranta suka ce musu, "Ashe, waɗansu Manzanni, daga cikinku ba su je muku ba, suna karanta ayoyin Ubangijinku a kanku, kuma suna yi muku gargaɗin gamuwa da yininku wannan?" Suka ce, "Na'am, "kuma amma kalmar azaba ita ce ta wajaba a kan kafirai

    [72] Aka ce, "Ku shiga ƙofofin Jahannama, kauna madawwama a cikinta. Sa'an nan mazaunin makangara ya munana

    [73] Kuma aka kora waɗanda suka bi Ubangijinsu da taƙawa zuwa Aljanna jama'a-jama'a har a lokacin da suka je mata, alhali kuwa an buɗe kofofinta, kuma matsaranta suka ce musu, "Aminci ya tabbata a gare ku, kun ji daɗi, saboda haka ku shige ta, kuna madawwama (a cikinta)

    [74] Kuma suka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya yi mana gaskiya ga wa'adinSa, kuma Ya gadar da mu ƙasa, muna zama a cikin Aljanna a inda muke so." To, madalla da ijarar ma'aikata

    [75] Kuma kana ganin mala'iku suna masu tsayawa da haƙƙoƙin da aka ɗora musu daga kewayen Al'arshi, suna tasbihi game da gode wa Ubangijinsu. Kuma aka yi hukunci a tsakaninsu da gaskiya. Kuma aka ce, "Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu

    Gafir

    Surah 40

    [1] H. M

    [2] Saukar da Littafi daga Allah ne, Mabuwayi, Masani

    [3] Mai gafarta zunubi kuma Mai karɓar tuba Mai tsananin azaba, Mai wadatarwa babu abin bautawa face Shi, zuwa gare Shi makoma take

    [4] Babu mai jayayya a cikin ayoyin Allah, face waɗanda suka kafirta. Saboda haka kada juyawarsu a cikin garuruwa ta ruɗe ka

    [5] Mutanen Nuhu sun ƙaryata a gabaninsu, da ƙungiyoyin da suke a bayansu, kuma kowace al'umma ta yi nufi game da Manzonsu, domin su kama shi. Kuma suka yi jayayya da ƙarya domin su gusar da gaskiya da ita. Sai Na kama su. To, yaya azabaTa take

    [6] Kuma kamar haka kalmar Ubangijinka ta wajaba a kan waɗanda suka kafirta, domin su 'yan wuta ne

    [7] Waɗanda ke ɗaukar Al'arshi da waɗanda ke kewayenta, suna tasbihi game da gode wa Ubangijinsu, kuma suna yin imani da Shi, kuma suna yin istigfari domin waɗanda suka yi imani, (suna cewa), "Ya Ubangijinmu! Ka yalwaci dukan kome da rahama da ilmi to Ka yi gafara ga waɗanda suka tuba kuma suka bi hanyarKa, kuma Ka tsare musu azabar Jahim

    [8] Ya Ubangijinmu! Kuma Ka shigar da su a gidajen Aljannar zama, wannan da Ka yi musu wa'adi, su da wanda ya kyautatu daga ubanninsu da matan aurensu da zurriyarsu. Lalle Kai, Kai ne Mabuwayi, Mai hikima

    [9] Kuma Ka tsare su daga munanan ayyuka, kuma wanda Ka tsare shi daga munanan ayyuka a ranarnan, to, lalle, Ka yi masa rahama kuma wancan shi ne babban rabo mai girma

    [10] Lalle waɗanda suka kafirta, ana kiran su, "Haƙiƙa, ƙin Allah (a gare ku) shi ne mafi girma daga ƙinku ga kanku a lokacin da ake kiran ku zuwa ga imani, sai kuna ta kafircewa

    [11] Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka matar da mu sau biyu, kuma Ka rayar da mu sau biyu, saboda haka mun yarda da laifuffukan mu. To, shin, akwai wata hanya zuwa ga fita

    [12] Wancan sababinsa, lalle (shi ne) idan an kirayi Allah Shi kaɗai, sai ku kafirta, kuma idan aka yi shirki game da Shi, sai ku yi imani. To, hukuncin fa, na Allah Maɗaukaki, Mai girma ne

    [13] Shi ne Wanda ke nuna muku ayoyinSa, kuma Ya saukar da arziki daga sama saboda ku, kuma babu mai yin tunani face mai mayar da al'amari ga Allah

    [14] Saboda haka ku kirayi Allah, kuna masu tsarkake addini a gare Shi, kuma ko da kafirai sun ƙi

    [15] Mai ɗaukaka darajoji (domin muminai), Mai Al'arshi, Yana jefa ruhi daga al'amarinSa a kan wanda Ya so daga bayinSa, domin ya yi gargaɗi kan ranar gamuwa

    [16] Ranar da suke bayyanannu, babu wani abu daga gare su wanda yake iya boyuwa ga Allah. "Mulki ga wa ya ke a yau?" Yana ga Allah, Makaɗaici, Mai tilastawa

    [17] Yau ana saka wa kowane rai a game da abin da ya aikata, babu zalunci a yau. Lalle Allah Mai gaggawar hisabi ne

    [18] Kuma ka yi musu gargaɗi kan ranar (Sa'a) makusanciya, a lokacin da zukata suke masu cika da bakin ciki, ga maƙosansu. Babu wani masoyi ga azzalumai, kuma babu wani mai ceto da za a yi wa da'a (ga cetonsu)

    [19] (Allah) Ya san yaudarar idanu da abin da ƙiraza ke ɓoyewa

    [20] Kuma Allah Shi ke yin hukunci da gaskiya, waɗannan da kuke kira, waninSa, ba su yin hukunci da kome. Lalle Allah, Shi ne Mai ji, Mai gani

    [21] Ashe, ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasa, domin su duba ga yadda aƙibar waɗanda suka kasance a gabaninsu ta zama? Sun kasance su ne mafi tsananin ƙarfi daga gare su, da kufaifan aiki a cikin ƙasa, sai Allah Ya kama su da laifuffukansu. Kuma ba su da wani mai tsarewa daga Allah

    [22] Wancan sababinsa, domin su Manzanninsu sun kasance suna zuwa gare su da hujjoji bayyanannu, sai suka kafirta, sai Allah Ya kama su. Lalle Shi Mai ƙarfi ne, Mai tsananin azaba

    [23] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun aika Musa a game da ayoyinMu da wani dalili bayyananne

    [24] Zuwa ga Fir'auna da Hamana da Karuna, sai suka ce: "Mai sihiri ne, maƙaryaci

    [25] Sa'an nan, a lokacin da ya je musu da gaskiya daga wurinMu, suka ce: "Ku kashe ɗiyan waɗanda suka yi imani tare da shi, kuma ku rayar da matansu." Kuma mugun shirin kafirai, bai zama ba face a cikin bata

    [26] Kuma Fir'auna ya ce: "Ku bar ni in kashe Musa, kuma shi, ya kirayi Ubangijinsa. Lalle ne ni, ina tsoron ya musanya addininku, ko kuwa ya bayyana ɓarna a cikin kasa

    [27] Kuma Musa ya ce: "Lalle ni, na nemi tsari da Ubangijina kuma Ubangijinku, daga dukan makangari, wanda ba ya imani da ranar Hisabi

    [28] Kuma wani namiji mumini daga dangin Fir'auna, yana boye imaninsa, ya ce: "Ashe, za ku kashe mutum domin ya ce Ubangijina Allah ne, alhali kuwa haƙiƙa ya zo muku da hujjoji bayyanannu daga Ubangijinku? Idan ya kasance maƙaryaci ne, to, ƙaryarsa na kansa, kuma idan ya kasance mai gaskiya ne, sashen abin da yake yi muku wa'adi zai same ku. Lalle ne Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai barna, mai yawan ƙarya

    [29] Ya ku mutanena! Kuna da mulki a yau, kuma ku ne marinjaya a cikin kasa to wane ne zai taimake mu daga azabar Allah idan ta zo mana?" Fir'auna ya ce: "Ba ni nunamuku kome face abin da na gani, kuma ba ni shiryar da ku, sai ga hanyar shiryuwa

    [30] Kuma wannan da ya yi imani ya ce: "Ya mutanena! Lallene, ni, ina yi muku tsoron kwatankwacin ranar ƙungiyoyi

    [31] Kwatankwacin al'adar mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa da waɗanda ke a bayansu. Kuma Allah ba Ya nufin zalunci ga bayinSa

    [32] Kuma ya mutanena! Lalleni, ina yi muku tsoron ranar kiran juna

    [33] A ranar da za ku juya, kuna masu bayar da baya (gudane) ba ku da wani mai tsaro daga Allah. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, ba shi da wani mai shiryarwa

    [34] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Yusufu ya zo muku daga gabani, da hujjoji bayyanannu, ba ku gushe ba kuna a cikin shakka daga abin da ya zo muku da shi, har a lokacin da ya halaka kuka ce, 'Allah ba zai aiko wani Manzo ba, a bayansa.' Kamar haka Allah ke ɓatar da wanda yake mai ɓarna, mai shakka

    [35] Waɗanda kejayayya a cikin ayoyin Allah, ba da wani dalili da ya zo musu ba. Jidalin ya girma ga zamansa abin ki a wurin Allah da wurin waɗanda suka yi imani. Kamar haka Allah ke bicewar haske a kan zuciyar dukan makangari, mai tilastawa

    [36] Kuma Fir'auna ye ce, "Ya Hamana! Ka gina mini bene, dammanina za ni isa ga ƙofofi

    [37] ¡ofofin sammai domin in yi ninƙaya zuwa ga abin bautawar Musa. Kuma lalle ni haƙiƙa ina zaton sa maƙaryaci." Kuma haka dai aka ƙawace wa Fir'auna munanan aikinsakuma aka danne shi daga barin tafarki. Kuma mugun nufin Fir'auna bai zama ba face yana a cikin hasara

    [38] Kuma wannan da ya yi imani ya ce: "Ya mutanena! Ku bi ni, in shiryar da ku tafarkin shiryuwa

    [39] Kuma ya mutanena! Wannan rayuwa ta duniya dan jin daɗi ne kawai, kuma lalle Lahira ita ce gidan tabbata

    [40] Wanda ya aikata mummunan aiki to, ba za a saka masa ba face da misalinsa, kuma wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji ko mace alhali kuwa shi mumini ne, to, waɗannan suna shiga Aljanna, ana ciyar da su a cikinta, ba da lissafi ba

    [41] Kuma ya mutanena! Me ya same ni, ina kiran ku zuwa ga tsira, kuma kuna kira na zuwa ga wuta

    [42] Kuna kira na zuwa ga in kafirta da Allah, kuma in yi shirki, game da Shi, da abin da babu wani ilmi game da shi gare ni, kuma ni ina kiran ku zuwa ga Mabuwayi, Mai gafara

    [43] Haƙƙan ne abin da kawai kuke kira na zuwa gare shi, ba ya da wani kira a cikin duniya, kuma ba shi da shi a Lahira kuma lalle makomarmu zuwa ga Allah take, kuma lalle mabarnata su ne 'yan wuta

    [44] To za ku ambaci abin da nake gaya muku, kuma ina fawwala al'amarina zuwa ga Allah. Lalle Allah Mai gani ne ga bayinSa

    [45] Sai Allah Ya tsare shi daga munanan abubuwa da suka yi na makirci, kuma mummunar azaba ta wajaba ga mutanen Fir'auna

    [46] Wuta, ana gitta su a kanta, safe da maraice, kuma a ranar da Sa'a take tsayuwa, ana cewa, "Ku shigar da mutanen Fir'auna a mafi tsananin azaba

    [47] Kuma a lokacin da suke husuma a cikin wuta, sai raunana (mabiya) su ce wa waɗanda suka kangara (shugabanni), "Lalle mu, mun kasance mabiya gare ku, to, shin ku masu wadatar da mu ne daga barin wani rabo daga wuta

    [48] Waɗanda suka kangara suka ce: "Lalle mu duka muna a cikinta. Lalle ne, Allah Ya yi hukunci a tsakanin bayinSa

    [49] Kuma waɗanda suke a cikin wuta suka ce wa matsaran Jahannama, "Ku roki Ubangijinku Ya sauƙaƙa mana, a yini ɗaya, daga azaba

    [50] Suka ce: "Ashe, Manzanninku ba su je muku da hujjoji bayyanannu ba?" Suka ce: "Na'am, sun je!" Suka ce: "To, ku roƙa." Kuma roƙon kafirai bai zamo ba face a cikin ɓata

    [51] Lalle Mu, hakika, Muna taimakon ManzanninMu da waɗanda suka yi imani, a cikin rayuwar duniya da ranar da shaidu ke tsayawa

    [52] Ranar da uzurin azzalumai ba ya amfaninsu, kuma suna da la'ana, kuma suna da munin gida

    [53] Kuma lalle haƙiƙa, Mun bai wa Musa shiriya, kuma Mun gadar da Bani Isra'ila Littafi

    [54] Shiryarwa da tunawa ga ma'abuta hankali

    [55] Saboda haka, ka yi haƙuri, lalle wa'adin Allah gaskiya ne. Kuma ka nemi gafara ga zunubinka, kuma ka yi tasbihi game da gode wa Ubangijinka, maraice da kuma wayewar safiya

    [56] Lalle waɗanda ke jayayya a cikin ayoyin Allah, ba game da wani dalili wanda ya je musu ba, babu kome a cikin kirazansu, face girman kai, ba su zama masu isa ga gurinsu ba, saboda haka ka nemi tsari daga Allah. Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Mai gani

    [57] Lalle halittar sammai da ƙasa, ita ce mafi girma daga halittar mutane, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [58] Kuma makaho da mai gani ba su daidaita kuma waɗanda suka yi imani suka, aikata ayyukan ƙwarai da mai munanawa ba su daidaita. Kaɗan ƙwarai, kuke yin tunani

    [59] Lalle Sa'a, haƙiƙa mai zuwa ce, babu shakka a gare ta, kuma amma mafi yawan mutane ba su yin imani

    [60] Kuma Ubangijinku ya ce: "Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama suna ƙasƙantattu

    [61] Allah ne Wanda Ya sanya muku dare domin ku natsu a cikinsa, da rana mai ganarwa. Lalle Allah, haƙiƙa, Ma'abucin falala ne a kan mutane, kuma amma mafi yawan mutane ba su godewa

    [62] Wancan shine Allah Ubangijinku, Mahaliccin dukan kome, babu abin bautawa face Shi. To, yaya ake karkatar da ku

    [63] Kamar haka ake karkatar da waɗanda suka kasance suna jayayya game da ayoyin Allah

    [64] Allah ne Ya sanya muku kasa tabbatacciya, da sama ginanniya, kuma Ya suranta ku, sa'an nan Ya kyautata surorinku,, kuma Ya azurta ku daga abubuwa masu daɗi. Wancan Shine Allah Ubangijinku. To, albarkar Allah Ubangijin halittu ta bayyana

    [65] Shi ne Mai rai, babu abin bautawa face Shi. Saboda haka ku kira Shi, kuna masu tsarkake addini a gare Shi. Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu

    [66] Ka ce: "Lalle ni, an hana ni in bauta wa waɗanda kuke kira waɗansun Allah a lokacin da hujjoji bayyanannu suka zo mini daga Ubangijina, kuma an umurce ni in sallama ga Ubangijin halittu

    [67] Shi ne Wanda Ya halitta ku daga turɓaya, sa'an nan daga maniyyi, sa'an nan daga saren jini, sa'an nan Ya fitar da ku kuna jariri, sa'an nan domin ku isa ga cikar ƙarfinku sa'an nan domin ku kasance tsofaffi, kuma daga cikinku, akwai wanda ake karɓar ransa a gabanin haka, kuma domin ku isa ga ajali ambatacce, kuma dammaninku ko za ku hankalta

    [68] Shi ne Wanda ke rayarwa kuma Yana kashewa. To, idan Ya hukunta wani al'amari, to, Yana cewa kawai gare shi, ka kasance sai yana kasancewa (kamar yadda ake bukatar sa)

    [69] Ashe, ba ka gani ba ga waɗanda ke jayayya a cikin ayoyin Allah, yadda ake karkatar da su

    [70] Waɗanda suka ƙaryata, game da Littafin, kuma da abin da Muka aika Manzanninmu da shi. To, za su sani

    [71] A lokacin da ƙuƙumma suke a cikin wuyoyinsu, da sarƙoƙi ana jan su

    [72] A cikin ruwan zafi, sa'an nan a cikin wuta ana babbaka su

    [73] Sa'an nan a ce musu, "Ina abin da kuka kasance kuna shirki da shi

    [74] Wanin Allah?" Suka ce: "Sun ɓace mana. A'a, ba mu kasance muna kiran kome ba a gabani."Kamar wancan ne Allah Yake ɓatar da kafirai

    [75] Wancan domin abin da kuka kasance ne kuna farin ciki da shi, a cikin ƙasa, ba da hakki ba, kuma da abin da kuka kasance kuna yi na nishaɗi

    [76] Ku shiga kofofin Jahannama kuna madawwama a cikinta. To, mazaunin masu girman kai ya munana

    [77] Saboda haka ka yi haƙuri. Lalle wa'adin Allah gaskiya ne. To, ko dai lalle Mu nuna maka sashen abin da Muka yi musu wa'adi da shi ko kuwa lalle Mu karɓi ranka, to, zuwa gare Mu ake mayar da su

    [78] Kuma lalle haƙiƙa, Mun aika wasu Manzanni daga gabaninka, daga cikinsu akwai wanda Muka ƙissanta maka labarinsa kuma daga cikinsu akwai wanda ba Mu ƙissanta labarinsa ba a gare ka. Ba ya yiwuwa ga wani Manzo ya je da wata ayar mu'ujiza face da iznin Allah. Sa'an nan idan umurnin Allah ya je, sai a yi hukunci da gaskiya, masu ɓatawa sun yi hasara a can

    [79] Allah ne Wanda Ya sanya muku dabbobi domin ku hau daga gare su, kuma daga gare su kuke ci

    [80] Kuma kuna da abubuwan amfani a cikinsu, kuma domin ku isar da wata buƙata, a cikin ƙirazanku a kansu kuma a kansu da a kan jirage ake, ɗaukar ku

    [81] Kuma Ya nuna muku ayoyinSa. To, wane ayoyin Allah kuke musu

    [82] Ashe fa, ba su yi tafiya a cikin ƙasa ba, domin su duba yadda aƙibar waɗanda ke a gabaninsu ta kasance? Sun kasance mafi yawa daga gare su. Kuma sun fi tsananin ƙarfi, da (yawan) gurabun sana'o'i a cikin ƙasa. To, abin da suka kasance suna aikatawa bai wadatar da su ba

    [83] A lokacin da Manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu, suka yi farin ciki da abin da ke wurinsu na ilmi kuma abin da suka kasance suna yi na izgili da shi ya wajaba a kansu

    [84] Sa'an nan a lokacin da suka ga azabarMu, suka ce: "Mun yi imani da Allah, Shi kaɗai, kuma mun kafirta da abin da muka kasance muna shirki da shi

    [85] To imaninsu bai kasance yana amfaninsu ba a lokacin da suka ga azabarMu. Hanyar Allah wadda ta gabata a cikin bayinSa. Kuma kafirai sun yi hasara a can

    Fussilat

    Surah 41

    [1] H. M

    [2] Saukarwa (da Alƙur' ani) daga Mai rahama ne, Mai jin ƙai

    [3] Littafi ne, an bayyana ayoyinsa daki-daki, yana abin karantawa na Larabci, domin mutanen dake sani

    [4] Yana mai bayar da bushara kuma mai gargaɗi. Sai mafi yawansu suka bijire. Saboda haka su, ba su saurarawa

    [5] Kuma suka ce: "Zukatanmu na a cikin kwasfa daga abin da kake Kiran mu zuwa gare shi, kuma a cikin kunnuwanmu akwai wani nauyi, kuma daga tsakaninmu da tsakaninka akwai wani shamaki. sahoda haka ka yi aiki, lalle mu masu aiki ne

    [6] Ka ce: "Ni mutum kawai ne kamarku, ana yin wahayi zuwa gare ni cewa abin bautawarku, abin bautawa guda ne. Sai ku daidaitu zuwa gare Shi, kuma ku nemi gafararSa." Kuma bone ya tabbata ga masu yin shirki

    [7] Waɗanda ba su bayar da zakka, kuma su a game da Lahira su kafirai ne

    [8] Lalle wɗdanda suka yi imani, Kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, suna da wani sakamako wanda bai yankewa

    [9] Ka ce: "Ashe lalle ku, haƙiƙa, kuna kafurta a game da wanda Ya halitta kasa a cikin kwanuka biyu, kuma kuna sanya Masa kishiyoyi? Wancan fa, shi ne Ubangijin halittu

    [10] Kuma Ya sanya, a cikinta, duwatsu kafaffu daga samanta, kuma Ya sanya albarka a cikinta, kuma Ya ƙaddara abubuwan cinta a cikinta a cikin kwanuka huɗu masu daidaita, domin matambaya

    [11] Sa'an nan Ya daidaita zuwa ga sama alhali kuwa ita (a lokacin) hayaƙi ce, sai Ya ce mata, ita da ƙasa "Ku zo, bisa ga yarda ko a kan tilas." Suka ce: "Mun zo, muna masu ɗa'a

    [12] Sai Ya hukunta su sammai bakwai a cikin kwanuka biyu. Kuma Ya yi wahayi, a cikin kowace sama da al'amarinta, kuma Muka kawata sama ta kusa da fitilu kuma don tsari. Wancan ƙaddarawar Mabuwayi ne, Masani

    [13] To, idan sun bijire sai ka ce: "Na yi muku gargaɗi ga wata tsawa kamar irin tsawar Adawa da samudawa

    [14] A lokacin da Manzanninsu suka je musu daga gaba gare su kuma daga bayansu, "Kada ku bauta wa kowa face Allah." suka ce: "Da UbangiJinmu Ya so, lalle da Ya saukar da mala' iku, saboda haka lalle mu, masu kafirta ne a game da abin da aka aiko ku da shi

    [15] To, amma Adawa, sai suka yi girman kai a cikin kasa, ba da wani hakki ba, suka ce: "Wane ne mafi tsananin ƙarfi daga gare mu?" Ashe, kuma ba su gani ba cewa Allah, wanda Ya halitta su Shine Mafi ƙarfi daga gare su, kuma sun kasance a game da ayoyinMu suna yin musu

    [16] Sai Muka aika, a kansu, da iska mai tsananin sauti da sanyi, a cikin kwanuka na shu'umci, domin Mu ɗanɗana musu azabar wulaƙanci, a cikin rayuwar duniya, kuma lalle azabar Lahira ita ce mafi wulaƙantarwa, kuma su ba za a taimake su ba

    [17] Kuma amma Samudawa, sai Muka shiryar da su, sai suka fi son makanta a kan shiriya, domin haka tsawar azabar wulakanci, ta kama su saboda abin da suka kasance suna aikatawa (domin neman wata fa'ida)

    [18] Kuma Muka tsirar da waɗanda suka yi imani kuma suka kasance suna yin taƙawa

    [19] Kuma ranar da ake tara maƙiyan Allah zuwa wuta, to, su ana kakkange su

    [20] Har idan sun je mata, sai jinsu da ganinsu da fatunsu, su yi shaida a kansu a game da abin da suka kasance suna aikatawa

    [21] Kuma suka ce wa fatunsu, "Don me kuka yi shaida a kanmu?" Suka ce: "Allah, Wanda ke sanya kowane abu ya yi furuci, Shi ne Ya sanya mu mu yi furuci, kuma Shi ne Ya halitta ku can da farko, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [22] Ba ku kasance kuna sani ba a ɓoye, cewa jinku zai yi shaida a kanku kuma ganinku zai yi, kuma fatunku za su yi. Kuma amma kun yi zaton cewa Allah bai san abubuwa masu yawa daga abin da kuke aikatawa ba

    [23] Kuma wancan zaton naku wanda kuka yi zaton shi, game da Ubangijinku, ya halakar da ku, sai kuka wayi gari a cikin masu hasara

    [24] Saboda haka idan sun yi hakuri, to, wutar, ita ce mazauni a gare su, kuma idan sun nemi yarda, to, ba su zama daga waɗanda ake yardwa ba

    [25] Kuma Muka sallaɗar da mabiya a gare su, sai suka ƙawata musu abin da ke a gabansu da abin da ke a bayansu. Kuma kalmar azaba ta wajaba a kansu, a cikin wasu al'ummomi da suka shuɗe a gabaninsu daga aljannu da mutane. Lalle su, sun kasance masu hasara

    [26] Kuma waɗanda suka kafirta suka cc, "Kada ku saurara ga wannan Alkur' ani, kuma ku yi ta yin kuwwa a ckin (lokacin karatun) sa, ɗammaninku za ku rinjaya

    [27] Saboda haka, lalle za Mu ɗanɗana wa waɗanda suka kafirta wata azaba mai tsanani, kuma lalle za Mu saka musu da mafi munin abin da suka kasance suna aikatawa

    [28] Wancan shi ne sakamakon makiyan Allah, watau wuta. Suna a gidan dawwama a cikinta, domin sakamako ga abin da suka kasance suna yin musu game da ayoyinMu

    [29] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka nuna mana wadannan biyun da suka batar da mu daga aljannu da mutane, mu sanya su a karkashin, ƙafafunmu, domin su kasance daga ƙaskantattu

    [30] Lalle waɗannan da suka ce: "Ubangjinmu, shi ne Allah," sa'an nan suka daidaitu, mala'iku na sassauka a kansu (a lokacin saukar ajalinsu suna ce musu) "Kada ku ji tsoro, kuma kada ku yi baƙin ciki, kuma ku yi bushara da Aljanna, wadda kun kasance ana yi muku wa'adi da ita

    [31] Mu ne majibintanku a cikin rayuwar duniya da kuma a cikin Lahira, kuma a cikinta kuna da abin da rayukanku ke sha'awa, kuma kuna da abin da kuke kira (akawo muku) a cikinta

    [32] A kan liyafa daga Mai gafara, Mai jin ƙai

    [33] Kuma wane ne mafi kyau ga magana daga wanda ya yi kira zuwa ga Allah, kuma ya aikata aiki na ƙwarai kuma ya ce: "Lalle niina daga masu sallamawar al'amari zuwa ga Allah

    [34] Kuma kyautatawa ba ta daidaita kuma haka munanawa. Ka tunkuɗe cuta da abin da yake mafi kyau, sai ga shi wanda akwai ƙiyayya a tsakaninka da tsakaninsa, kamar dai shi majibinci ne, masoyi

    [35] Kuma ba za a cusa wa kowa wannan hali ba face waɗanda suka yi haƙuri, kuma ba za a cusa shi ba face ga mai rabo mai gima

    [36] Kuma idan wata fizga ta fizge ka daga Shaiɗan, to ka nemi tsari ga Allah. Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani

    [37] Kuma akwai daga ayoyinSa, dare da yini, da rana da wata. Kada ku yi sujada ga rana, kuma kada ku yi ga wata. Kuma ku yi sujada ga Allah wanda Ya halitta su, idan kun kasance Shi ne kuke bauta wa

    [38] To, idan sun yi girman kai, to, waɗanda ke a wurin Ubangijinka, suna tasbihi a gare Shi, a dare da rana, alhali kuwa su, ba su ƙosawa

    [39] Kuma akwai daga ayoyinSa cewa lalle kai kana ganin ƙasa ƙeƙasasshiya, to, idan Mun saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura. Lalle wannan da Ya raya ta, haƙiƙa, Mai rayar da matattu ne. Lalle Shi Mai ikon yi ne a kan kowane abu

    [40] Lalle waɗannan da ke karkacewa a cikin ayoyinMu, ba su fakuwa a gare Mu. Ashe fa, wanda ake jefawa a cikin Wuta ne mafifici ko kuwa wanda zai je amintacce a Ranar ¡iyama? Ku aikata abin da kuke so! Lalle Shi Mai gani ne ga abin da kuke aikatawa

    [41] Waɗannan da suka kafirta game da Alkur'ani a lokacin da ya je musu, kuma lalle shi haƙiƙa littafi ne mabuwayi

    [42] ¥arna ba za ta je masa ba daga gaba gare shi. kuma ba za ta zo ba daga baya gare shi. Saukarwa ce daga Mai hikima, Godadde

    [43] Ba za a fada maka ba face abin da aka riga aka faɗa ga Manzannin da suke a gabaninka. Lalle Ubangijinka, haƙiƙa, Ma'abucin gafara ne, kuma Ma'abucin azaba mai raɗaɗi ne

    [44] Kuma da Mun sanya shi abin karatu na ajamanci, lalle da sun ce, "Don me ba a bayyana ayoyinsa ba? Ashe, zai yiwu a sami littafi ba'ajame da Manzo Balarabe?" Ka ce: "Shi, shiriya ne da warkewa ga waɗanda suka yi imani. Kuma wadanda ba su yi imani ba akwai wani nauyi a cikin kunnuwansu, kuma shi wata makanta ne a kansu. Waɗannan ana kiran su daga wuri mai nisa

    [45] Kuma lalle Mun bai wa Musa Littafi, sai aka yi ɗaɓani a cikinsa, Kuma ba domin wata kalma da ta gabata ba daga Ubangijinka, lalle da an yi hukunci a tsakaninsu. Kuma lalle su, haƙiƙa suna a cikin shakka daga, gare shi, mai sanya kokanto

    [46] Wanda ya aikata aiki na ƙwarai to saboda kansa ne, kuma wanda ya munana, to, yana akansa. Kuma Ubangiwinka, ba Mai zalunci ga bayinSa ne ba

    [47] Zuwa gare Shi ake mayar da sanin Sa'a. Kuma waɗansu 'ya'yan itace ba su fita daga kwasfofinsu, kuma wata mace ba ta yin ciki, kuma ba ta haihuwa, face da saninSa, kuma a ranar da Yake kiran su (Ya ce): "Ina abokan tarayyaTa?" Sai su ce, "Mun sanar da Kai babu mai bayar da shaida da haka nan daga gare mu

    [48] Kuma abin da suka kasance suna kira a gabanin haka ya ɓace musu, kuma suka yi zaton cewa ba su da wata mafaka

    [49] Mutum ba ya kosawa daga addu 'ar neman alheri kuma idan sharri ya shafe shi, sai ya zama mai yanke kauna, Mai nuna kasawa

    [50] Kuma lalle idan Mun ɗanɗana masa wata rahama daga gareMu, daga bayan wata cuta ta shafe shi, lalle zai ce, "Wannan (ni'ima) tawa ce kuma ba ni zaton Sa'a mai tsayuwa ce, kuma lalle idan aka mayar da ni zuwa ga Ubangijina, haƙiƙa, ina da makoma mafi kyau, a wurinSa." To, lalle za Mu ba da labari ga waɗanda suka kafirta game da abin da suka aikata, kuma lalle Muna ɗanɗana musu daga azaba, Mai kauri

    [51] Kuma idan Muka yi ni'ima ga mutum, sai ya bijire, kuma ya nisantar da gefensa, kuma idan sharri ya same shi, sai ya zama ma'abucin addu'a mai faɗi

    [52] Ka ce: "Ashe, kun gani! Idan (Alƙur'ani) ya kasance daga Allah ne, sa'an nan kun kafirta a game da Shi, wane ne mafi ɓata daga wanda yake yana a cikin saɓani manisanci (daga gaskiya)

    [53] Za Mu nuna musu ayoyinMu a cikin sasanni da kuma cikin rayukansu, har ya bayyana a gare su cewa lalle (Alƙur'ani), shi ne gaskiya. Ashe, kuma Ubangijinka bai isa ba, ga cewa lalle Shi halartacce ne a kan kowane abu ne

    [54] To lalle su, suna a cikin shakka daga gamuwa da Ubangijinsu. To, lalle Shi, Mai kewayewane ga dukan kome ne

    Shũra

    Surah 42

    [1] H. M

    [2] I. S

    [3] Kamar wancan (asirin) Allah, Mabuwayi, Mai hikima, ke yin wahayi zuwa gare ka da zuwa ga waɗanda ke gabaninka

    [4] (Allah) Shi ne da abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa, kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma

    [5] Sammai na kusan su tsage daga bisansu, kuma mala'iku na yin tasihi game da gode wa Ubangijinsu kuma suna istigfari domin wanda ke cikin ƙasa. To, lalle Allah Shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [6] Kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majiɓinta waɗanda ba Shi ba Allah ne Mai tsaro a kansu, kuma kai, ba wakili ne a kansu ba

    [7] Kuma kamar haka ne Muka yi wahayin abin karantawa (Alƙur'ani) na Larabci zuwa gare ka, domin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu (Makka) da wanda ke a kewayenta, kuma ka yi gargaɗi game da ranar taruwa, babu shakka gare ta, wata ƙungiya tana a cikin Aljanna kuma wata ƙungiya tana a cikin sa'ir

    [8] Kuma da Allah Ya so, da Ya haɗa su al'umma guda, kuma Amma Yana shigar da wanda Ya so a cikin rahamarSa alhali kuwa azzaluMai ba su da, wani majiɓinci, kuma ba su da wani mataimaki

    [9] Ko kuma sun riƙi waninSa majiɓinta? To Allah Shi ne Majiɓinci, kuma Shi ne ke rayar da matattu alhali kuwa Shi, Maiikon yi ne a kan dukan kome

    [10] Kuma abin da kuka saɓa wa juna a cikinsa ko mene ne, to, hukuncinsa (a mayar da shi) zuwa ga Allah. Wancan Shi ne Allah Ubangijina, a gare Shi na dogara, kuma zuwa gare Shi nake mayar da al'amarina

    [11] (Shi ne) Mai ƙaga halittar sammai da ƙasa, Ya sanya muku ma'aura daga jinsinku, kuma (Ya sanya) daga dabbobi maza da mata, Yana halitta ku a cikinsu, wani abu bai zama kamar tamkarSa ba, kuma Shi ne Mai ji, Mai gani

    [12] Shi ne da mabuɗan sammai da ƙasa Yana shimfiɗa arziki ga wanda ya so kuma Yana hukuntawa. Lalle ne, Shi Masani ne ga dukan kome

    [13] Ya shar'anta muku, game da addini, abin da Ya yi wasiyya da shi ga Nuhu da abin da Muka yi wahayi da shi zuwa gare ka, da abin da Muka yi wasiyya da shi ga Ibrahim da Musa da Isa, cewa ku tsayar da addini sosai kuma kada ku rarrabu a cikinsa. Abin da kuke kira zuwa gare shi, ya yi nauyi a kan masu shirki. Allah na zaɓen wanda Yake so zuwa gare Shi, kuma Yana shiryar da wanda ke tawakkali gare Shi, ga hanyarSa

    [14] Kuma ba su rarraba ba face bayan da ilmi ya je musu, domin zalunci a tsakaninsu kuma ba domin wata kalma ta gabata ba daga Ubangijinka, zuwa ga wani ajali ambatacce, da an yi hukunci a tsakaninsu. Kuma lalle ne waɗanda aka gadar wa Littafi daga bayansu, haƙiƙa, suna cikin shakka a gare shi, mai sanya kokanto

    [15] Saboda haka, sai ka yi kira kuma kai ka daidaitu kamar yadda aka umurce ka, kuma kada ka bi son zuciyoyinsu, kumaka ce, "Na yi imani da abin da Allah Ya saukar na littafi, kuma an umurce ni da in yi adalci a tsakaninku. Allah ne Ubangijinmu, kuma Shi ne Ubangijinku, ayyukanmu na gare mu, kuma ayyukanku na gare ku, kuma babu wata hujja a tsakaninmu da tsakaninku. Allah zai tara mu, kuma zuwa gare Shi makoma take

    [16] Kuma waɗannan da ke jayayya a cikin al'amarin Allah daga bayan an karɓa masa, hujjarsu ɓatacciya ce a wurin Ubangijinsu, kuma akwai fushi a kansu, kuma suna da wata azaba mai tsanani

    [17] Allah ne Wanda Ya saukar da Littafi da gaskiya, da sikeli. Kuma me ya sanar da kai (cewa ana) tsammanin Sa'ar kusa take

    [18] Waɗanda ba su yi imanida ita ba, (su) ke neman gaggautowarta. Alhali kuwa waɗanda suka yi imani, masu tsoro ne daga gare ta, kuma sun sani, cewa ita gaskiya ce. To, lalle ne waɗanda ke shakka a cikin Sa'a, haƙiƙa, suna a cikin ɓata Mai nisa

    [19] Allah Mai tausasawa ne ga bayinsa. Yana azurta wanda yake so, alhali kuma Shi ne Maiƙarfi, Mabuwayi

    [20] Wanda ya kasance yana nufin noman Lahira za Mu ƙara masa a cikin nomansa, kuma wanda ya kasance yana nufin noman duniya, za Mu sam masa daga gare ta, alhali kuwa ba shi da wani rabo a cikin Lahira

    [21] Ko suna da waɗansu abokan tarayya (da Allah) waɗanda suka shar'anta musu, game da addini, abin da Allah bai yi izni ba da shi? Kuma ba domin kalmar hukunci ba, da lalle, an yi hukunci a tsakaninsu. Kuma lalle azzalumai suna da azaba mai raɗaɗi

    [22] Kana ganin azzalumai suna masu tsoro daga abin da suka sana'anta alhali kuwa shi abin tsoron, mai aukuwa ne gare su, kuma waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai suna a cikin fadamun Aljanna suna da abin da suke so a wurin Ubangijinsu. Waccan fa ita ce falala mai girma

    [23] Wancan shi ne Allah ke bayar da bushara da shi ga bayinSa waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Ka ce: "Ba ni tambayar ku wata ijara a kansa, face dai soyayya ta cikin zumunta." Kuma wanda ya aikata wani abu mai kyau, za Mu ƙara masa kyau a cikinsa, lalle Allah Mai gafara ne, Mai godiya

    [24] Ko za su ce: "Ya ƙirƙira ƙarya ga Allah ne?" To, idan Allah Ya so, zai yunƙe a kan zuciyarka, kuma Allah Yana shafe ƙarya kuma Yana tabbatar da gaskiya da kalmominSa. Lalle ne Shi Masani ne ga abin da ke cikin zukata

    [25] Kuma Shi ne ke karɓar tuba daga bayinSa, kuma Yana Yafe ƙananan laifuffuka, alhali kuwa Yana sanin abin da kuke aikatawa

    [26] Kuma Yana karɓa wa waɗannan da suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma Yana ƙara musu (sakamako) daga falalarSa. Kuma kafirai suna da wata azaba mai tsanani

    [27] Kuma da Allah Ya shimfiɗa arziki ga bayinSa, da sun yi zaluncin rarraba jama'a a cikin ƙasa, kuma amma Yana sassaukarwa gwargwado ga abin da Yake so. Lalle ne Shi, game da bayinSa, Mai labartawa ne, Mai gani

    [28] Kuma Shi ne ke sassaukar da girgije (ruwa) a bayan sun yanke ƙauna kuma Yana watsa rahamarSa, alhali kuwa Shi ne Majiɓinci, Mai godiya

    [29] Kuma akwai daga ayoyinSa, halittar sammai da ƙasa da abin da Ya watsa a cikinsu na dabba alhali kuwa Shi Mai iko ne ga tara su, a lokacin da Yake so

    [30] Kuma abin da ya same ku na wata masifa, to, game da abin da hannayenku suka sana' anta ne kuma (Alah) Yana Yafewar (waɗansu laifuffuka) masu yawa

    [31] Kuma ba ku zama masu buwaya ba a cikin ƙasa kuma ba ku da wani majiɓinci, wanin Allah, kuma ba ku da wani mataimaki

    [32] Kuma akwai daga ayoyinsa, jirage masu gudana a cikin teku kamar duwatsu

    [33] Idan Ya so, sai Ya kwantar da iskar, sai jiragen su yini suna masu kawaici a kan bayan tekun, Lalle ne ga wancan, haƙiƙa, akwai ayoyi ga dukan mai haƙuri, Mai godiya

    [34] Ko Ya halaka su (su jiragen) saboda abin da masu su suka sana'anta, alhali kuwa Yana yafe (laifuffuka) masu yawa

    [35] Kuma domin waɗanda ke jayayya a cikin ayoyinMu su sani (cewa) ba su da wata mafaka

    [36] Saboda haka abin da aka ba ku, ko mene ne, to, jin daɗin rayuwar duniya ne, kuma abin da ke a wurin Allah Shi ne mafifici, kuma Shi ne mafi wanzuwa ga waɗanda suka yi imani kuma suna dogara a kan Ubangijinsu kawai

    [37] Kuma waɗanda ke nisantar manyan zunubbai da ayyukan alfasha, kuma idan sun yi fushi, su, suna gafartawa

    [38] Da waɗanda suka karɓa kira ga Ubangijinsu, kuma suka tsayar da salla, kuma al'amarinsu shawara ne a tsakaninsu, kuma daga abin da Muka azurta su suna ciyarwa

    [39] Da waɗanda idan zalunci ya same su, suna neman taimako (su rama)

    [40] Kuma sakamakon cuta shi ne wata cuta kamarta, sai dai wanda Ya yafe kuma ya kyautata, to ladarsa na ga Allah. Lalle ne, Shi (Allah) ba Ya son azzalumai

    [41] Kuma Lalle ne, wanda ya nemi taimakon ramawa a bayan an zalunce shi, to waɗannan babu wata hanyar zargi a kansu

    [42] lnda hanyar zargi kawai take, shi ne a kan waɗanda ke zaluntar mutane kuma suna ƙetare haddin shari'a cikin ƙasa ba tare da haƙƙi ba. Waɗannan suna da azaba Mai raɗaɗi

    [43] Kuma Lalle ne, wanda ya yi haƙuri kuma ya gafarta (wa wanda ya zalunce shi), to shi wancan aiki haƙiƙa, yana daga manyan al'amura (da Allah ke so)

    [44] Kuma wanda (Allah Ya ɓatar, to, ba shi da wani majiɓinci bayanSa, kuma za ka ga azzalumai, a lokacin da suka ga azaba, suna cewa, "Shin, akwai hanya zuwa ga komawa)

    [45] Kuma kana ganin su ana gitta su a kanta, suna ƙasƙantattu saboda wulakanci, suna hange daga gefen gani ɓoyayye. Kuma waɗanda suka yi imani sai su ce, "Lalle ne, masu hasara, su ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu da iyalansu a Ranar ¡iyama." To, lalle ne, azzalumai suna a cikin wata azaba zaunanniya

    [46] Kuma waɗansu majiɓinta ba su kasance ba a gare su, waɗanda ke iya taimakonsu, baicin Allah. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, ba shi da wani godabe na tsira

    [47] Ku karɓa wa Ubangijinku tun gabanin wani yini ya zo, babu makawa gare shi daga Allah, ba ku da wata mafaka a ranar nan, kuma ba ku iya yin wani musu

    [48] To, idan sun bijire, to, ba Mu aike ka kana mai tsaro a kansu ba, babu abin da ke a kanka face iyar da Manzanci. Kuma lalle ne, Mu idan Mun ɗanɗana wa mutum wata rahama daga gare Mu, sai ya yi farin ciki da ita, kuma idan wata masifa ta same su saboda abin da hannayensu suka gabatar, to, lalle ne mutum mai tsananin kafirci ne

    [49] Mulkin sammai da ƙasa na Allah kawai ne. Yana halitta abin da Yake so. Yana bayar da 'ya'ya mata ga wanda yake so, kuma Yana bayar da ɗiya maza ga wanda Yake so

    [50] Ko kuma Ya haɗa su maza da mata, kuma Yana sanya wanda Ya so bakarare. Lalle shi, Mai ilmi ne, Mai ikon yi

    [51] Kuma ba ya kasancewa ga wani mutum Allah Ya yi masa magana face da wahayi, ko daga baYan wani shamaki, ko Ya aika wani Manzo, sa'an nan Ya yi wahayi, da izninsa ga abin da Yake so. Lalle Shi, Maɗaukaki ne Mai hikima

    [52] Kuma kamar wancan Mun aika wani ruhi (rai mai haɗa jama'a) zuwa gare ka, daga gare Mu. Ba ka kasance ka san abin da yake littafi ba, ko abin da Yake imani, kuma amma Mun sanya shi (ruhin, watau Alƙur'ani) wani haske ne, Muna shiryar da wanda Muke so daga cikin bayinMu game da shi. Kuma Lalle kai, haƙiƙa, kana shiryarwa zuwa ga hanya, madaidaiciya

    [53] Hanyar Allah wanda ke da mulkin abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa. To, zuwa ga Allah kawai al'amura ke komawa

    Zukhruf

    Surah 43

    [1] H. M

    [2] Ina rantsuwa da Littafi Mabayyani

    [3] Lalle Mu, Mun sanya shi abin karatu na Larabci, tsammaninku, kuna hankalta

    [4] Kuma lalle, shi, a cikin uwar littafi a wurin Mu, haƙiƙa, maɗaukaki ne, bayyananne

    [5] Shin, za Mu kau da kai daga saukar da hukunci daga gare ku ne domin kun kasance mutane masu ɓarna

    [6] Alhali kuwa sau nawa Muka aika wani Annabi a cikin mutanen farko

    [7] Kuma wani Annabi bai je musu ba face sun kasance, game da shi, suna masu yin izgili

    [8] Sai Muka halakar da waɗanda suke su ne mafiya ƙarfin damƙa daga gare su. Kuma abin misalin mutanen farkon ya shuɗe

    [9] Kuma lalle ne, idan ka tambaye su, "Wane ne ya halitta sammai da ƙasa?" Lalle za su ce, "Mabuwayi Mai ilmi ne Ya halitta su

    [10] Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa kuma Ya sanya muku hanyoyi a cikinta, tsammaninku za ku nemi shiryuwa

    [11] Kuma Wanda Ya saukar da ruwa daga sama, a kan wani gwargwado, sai Muka rayar da gari matacce game da shi. Kamar haka nan ake fitar da ku (daga kabari)

    [12] Kuma Wanda Ya halitta ma'aura dukansu, kuma Ya sanya muku, daga jirgi da dabbobin ni'ima, abin da kuke hawa

    [13] Domin ku daidaitu a kan bayansa, sa'an nan ku tuna ni'imar Ubangijinku a lokacin da kuka daidaita a kansa kuma ku ce, "Tsarki ya tabbata ga Wanda Ya hore mana wannan alhali kuwa ba mu kasance masu iya rinjaya gare Shi ba

    [14] Kuma lalle mu haƙiƙa masu juyawa muke, zuwa ga Ubangijinmu

    [15] Kuma suka sanya Masa juz'i daga bayinsa. Lalle ne mutum, haƙiƙa, mai yawan kafirci ne, mai bayyanawar kafircin

    [16] Ko za Ya ɗauki 'ya'ya mata daga abin da Yake halittawa ne, kuma Ya zaɓe ku da ɗiya maza

    [17] Alhali kuwa idan an bayar da bushara ga ɗayansu da abin da ya buga misali da shi ga Mai rahama, sai fuskarsa ta yini tana wadda aka baƙanta launinta, kuma yana cike da baƙin ciki

    [18] Ashe, kuma (Allah zai zaɓi) wanda ake reno a cikin ƙawa alhali kuwa ga shi a husuma ba mai iya bayyanawar magana ba

    [19] Kuma suka mayar da mala'iku ('ya'ya) mata, alhali kuwa su, waɗanda suke bayin (Allah) Mai rahama ne! Shin, sun halarci halittarsu ne? za a rubuta shaidarsu kuma a tambaye su

    [20] Kuma suka ce: "Da Mai rahama ya so, da ba mu bauta musu ba." Ba su da wani ilmi game da wancan! Babu abin da suke yi face yanki-faɗi

    [21] Ko Mun ba su wani littafi ne a gabaninsa (Alƙur'ani) saboda haka da shi suke riƙe

    [22] A'a, sun ce dai, "Lalle mu, mun sami ubanninmu a kan wani addini (na al'ada) kuma lalle mu, a kan gurabunsu muke masu neman shiryuwa

    [23] Kuma kamar haka, ba Mu aika wani mai gargaɗi ba a gabaninka, a cikin wata alƙarya, face mani'imtanta sun ce, "Lalle mu, mun sami ubanninmu a kan wani addini kuma lalle mu, masu koyi nea kan gurabunsu

    [24] (Sai mai gargaɗin) ya ce: "Shin, ban zo muku da abin da ya fi zama shiriya daga abin da kuka sami ubanninku a kansa ba?" Suka ce, "Lalle mu dai masu kafirta ne game da abin da aka aiko ku da shi

    [25] Saboda haka Muka yi musu azabar ramuwa. To, ka dubi yadda aƙibar masu ƙaryatawa take

    [26] Kuma (ka ambaci) lokacin da Ibrahim ya ce wa ubansada mutanensa, "Lalle ni mai barranta ne daga abin da kuke bautawa

    [27] Face wannan da Ya ƙaga halittata, to, lalle Shi ne zai shiryar da ni

    [28] Kuma (Ibrahim) ya sanya (ita wannan magana) kalma mai wanzuwa a cikin zuriyarsa, tsammaninsu su komo daga ɓata

    [29] A'a, Na jiyar da waɗannan mutane daɗi su da ubanninsu har gaskiya, da Manzo mai bayyanawar gaskiyar, ya zo musu

    [30] Kuma a lokacin da gaskiyar ta je musu sai suka ce: "Wannan sihiri ne kuma mu masu kafirta da shi ne

    [31] Kuma suka ce: "Don me ba a saukar da wannan Alƙur'ani a kan wani mutum mai girma daga alƙaryun nan biyu ba

    [32] Shin, su ne ke raba rahamar Ubangijinka? Mu ne, Muka raba musu abincinsu a cikin rayuwar duniya, kuma Muka ɗaukaka waɗansunsu a kan waɗansu da darajoji domin waɗansunsu su riƙi waɗansu leburori kumarahamar Ubangijinka (ta Annabci), ita ce mafificiya daga abin da suke tarawa

    [33] Kuma ba domin mutane su kasance al'umma ɗaya ba, lalle ne, da Mun sanya wa masu kafirce wa Mai Rahama, a gidajensu, rufi na azurfa, kuma da matakalai, ya zama a kanta suke taƙawa

    [34] (Kuma a gidajensu, Mu sanya) ƙyamare da gadaje, a kansu suke kishingiɗa

    [35] Da zinariya. Kuma dukan wancan abu bai zama ba, sai jin daɗin rayuwar duniya nekawai' alhali kuwa Lahira, a wurin Ubangijinka, ta masu taƙawa ce

    [36] Kuma wanda ya makanta daga barin hukuncin Mai rahama, to, za Mu lulluɓe shi da shaiɗan, watau shi ne abokinsa

    [37] Kuma lalle su haƙiƙa suna kange su daga hanya, kuma suna Zaton cewa su masu shiryuwa ne

    [38] Har a lokacin da (abokin Shaiɗan) ya zo Mana (ya mutu) sai ya ce: (wa Shaiɗan) "Da dai a tsakanina da tsakaninka akwai nisan gabas da yamma, saboda haka, tir da kai ga zama abokin mutum

    [39] Kuma (wannan magana) ba za ta amfane ku ba, a yau, domin kun yi zalunci, lalle ku masu tarewa ne a cikin azaba

    [40] Shin to, kai kana jiyar da kurma ne, ko kana shiryar da makaho da wanda ke a cikin ɓata bayyananna

    [41] To, ko dai Mu tafi da kai to, lalle Mu, masu yin azabarramu, wa ne a kansu

    [42] Ko kuma Mu nuna maka abin da Muka yi musu wa'adi, to, lalle Mu, Masu ikon tasarrufi a kansu ne

    [43] Saboda haka, ka yi riƙo ga abin da aka yi wahayi da shi zuwa gaie ka. Lalle ne kai, kana a kan hanya madaidaiciyl

    [44] Kuma shi (abin wahayin) ambato (na ɗaukaka) ne a gare ka da kuma ga mutanenka, kuma za a tambaye ku

    [45] Kuma ka tambayi waɗanda Muka aika a gabaninka daga Manzannin Mu, "Shin, Mun sanya waɗansu gumaka, wasun (Allah), Mai rahama, ana bauta musu

    [46] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun aika Musa, game da ayoyin Mu, zuwa ga Fir'auna da mashawartansa, sai ya ce: "Lalle ni, Manzo ne daga Ubangijin halittu

    [47] To, a lokacin da ya je musu da ayoyinMu, sai ga su suna yi musu dariya

    [48] Kuma ba Mu nuna musu wata aya ba, face ita ce mafi girma daga 'yar'uwarta. Kuma Muka kama su da azaba, tsammaninsu ko suna komowa

    [49] Kuma suka ce: "Ya kai mai sihiri! Ka roƙa mana Ubangijinka da albarkacin abin da yi alkawari a wurinka, lalle mu, haƙiƙa, masu shiryuwa ne

    [50] To, a lokacin da duk Muka kuranye musu azaba, sai ga su suna warware alkawarinsu

    [51] Kuma Fir'auna ya yi kira a cikin mutanensa, ya ce: "Ya mutanena! Ashe mulkin Masar ba a gare ni yake ba, kuma waɗannan koguna suna gudana daga ƙarƙashina? Ashe, ba ku gani ba

    [52] Ko kuma ba ni ne mafifici ba daga wannan wanda yake shi wulakantacce ne kuma ba ya iya bayyanawar magana sai da ƙyar

    [53] To, don me, ba a jefa mundaye na zinariya a kansaba, ko kuma mala'iku su taho tare da shi haɗe

    [54] Sai ya sassabce hankalin mutanensa, saboda haka suka bi shi. Lalle su, sun kasance waɗansu irin mutane ne fasiƙai

    [55] Saboda haka a lokacin da suka husatar da Mu, Muka yi musu azabar ramuwa sai Muka nutsar da su gaba ɗaya

    [56] Sai Muka sanya su magabata kuma abin misali ga mutanen ƙarshe

    [57] Kuma a lokacin da aka buga misali da ¦an Maryama, sai ga mutanenka daga gare shi (shi misalin) suna dariya da izgili

    [58] Kuma suka ce: "Shin, gumakanmu ne mafifita ko shi (¦an Maryama)?" Ba su buga wannan misali ba a gare ka face domin yin jidali. A'a, su mutane nemasu husuma

    [59] Shi (¦an Maryama) bai zama ba face wani bawa ne, Mun yi ni'ima a gare shi, kuma Muka sanya shi abin koyi ga Bani Isra'ila

    [60] Kuma da Muna so lalle ne da Mun sanya mala'iku, daga ci, kinku, a cikin ƙasa, suna mayewa

    [61] Kuma lalle shi, haƙiƙa, wani ilmi ne na Sa'a, saboda haka, kada ku yi shakka a gare ta, kuma ku bi Ni. Wannan ita ce hanya madaidaiciya

    [62] Kuma kada Shaiɗan ya taushe ku (daga hanyar). Lalle shi maƙiyi ne a gare ku, mai bayyanawar ƙiyayya

    [63] Kuma a lokacin da Isa ya je da hujjoji bayyanannu, ya ce: "Lalle ne na zo muku da hikima kuma domin in bayyana muku, sashen abin da kuke saɓa wa juna acikinsa, saboda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗa'a

    [64] Lalle ne, Allah Shi ne Ubangijina kuma Shi ne Ubangijinku saboda haka ku bauta Masa. Wannan ita ce hanya madaidaiciya

    [65] Sai ƙungiyoyi suka saɓa a tsakaninsu. To, bone ya tabbata ga waɗanda suka yi zalunci daga azabar yini mai raɗaɗi

    [66] Shin suna jiran wani abu ne? sai dai Sa'a ta je musu bisaga abke, alhali kuwa ba su sani ba

    [67] Masoya a yinin nan, sashensu zuwa ga sashe maƙiya ne, face masu taƙawa (su kam masu son juna ne)

    [68] Ya bayiNa! Babu tsoro a kanku a yau, kuma ba za ku yi baƙin ciki ba

    [69] Waɗanda suka yi imani da ayoyinMu, kuma suka kasance masu sallamawar al'amari (ga Allah)

    [70] Ku shiga Aljanna, ku da matan aurenku, ana girmama ku

    [71] Ana kewayawa a kansu da akussa na zinariya da kofuna, alhali kuwa a cikinsu akwai abin da rayuka ke marmari kuma idanu su ji daɗi, kuma ku, a cikinta (Aljannar), madawwama ne

    [72] Kuma waccan ita ce Aljannar, wannan da aka gadar da ku ita saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [73] Kuna samu, a cikinta, 'ya'yan itacen marmari masu yawa, daga cikinsu kuke ci

    [74] Lalle masu laifi madawwama ne a cikin azabar Jahannama

    [75] Ba a sauƙaƙar da ita (azabar) daga gare su, alhali kuwa su, a cikinta, masu kasa magana ne

    [76] Kuma ba Mu zalunce su ba, amma su ne suka kasance azzalumai

    [77] Kuma suka yi kira, "Ya Maliku! Ubangijinka Ya kashe mu mana " (Maliku) ya ce: "Lalle ku mazauna ne

    [78] Lalle ne, haƙiƙa, Mun je muku da gaskiya, kuma amma mafi yawanku masu ƙi ga gaskiyar ne

    [79] Ko kuma sun tukka wani al'amari ne? To, lalle Mu, Masu tukkawa ne

    [80] Ko suna zaton lalle Mu, ba Mu jin asirinsu da ganawarsu? Na'am! Kuma manzannin Mu na tare da su suna rubutawa

    [81] Ka ce: "Idan har akwai ɗa ga Mai rahama, to, ni ne farkon masu bauta (wa ɗan)

    [82] Tsarkin Ubangijin sammai da ƙasa, Ubangijin Al'arshi, ya tabbata daga abin da suke sifantawa

    [83] Saboda haka, ka ƙyale su, su kutsa kuma su yi wasa har su haɗu da yininsu, wanda ake yi musu wa'adi da shi

    [84] Kuma Shi ne wanda ke abin bautawa a sama kuma abin bautawa a ƙasa, kuma, Shi ne Mai hikima, Masani

    [85] Kuma albarkar wanda ke da mulkin sammai da ƙasa abin da ke a tsakaninsu ta bayyana, kuma a wurinSa ne ilmin Sa'a yake, kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku

    [86] Kuma waɗanda suke kira baicinSa ba su mallaki ceto ba, face wanda ya yi shaida da gaskiya, kuma su, suna sane (da haka)

    [87] Kuma lalle idan ka tambaye su: "Wane ne ya halitta su?" Lalle ne za su ce Allah ne. To, yaya ake juyar da su

    [88] Kuma da (ilmin) maganarSa (Annabi) "Ya Ubangijina! Lalle waɗannan mutane ne waɗanda ba za su yi imani ba

    [89] To, sai ka kau da kai daga gare su, kuma ka ce, "salama." Sa'an nan kuma za su sani

    Dukhan

    Surah 44

    [1] H. M

    [2] Ina rantsuwa da Littafi Mabayyani

    [3] Lalle ne, Mu, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mu' Mun kasance Masu yin gargaɗi

    [4] A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kowane umurui bayyananne

    [5] Umurni na daga wurinMu. Lalle Mu ne Muka kasanceMasu aikawa

    [6] Saboda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani

    [7] (Shi ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu, idan kun kasance masu yaƙini (za ku gane haka)

    [8] Babu abin bautawa face Shi. Yana rayarwa Kuma Yana kashewa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko

    [9] A'a su, suna wasa a cikin shakka

    [10] Saboda haka, ka dakata ranar da sama za ta zo da hayaƙi bayyananne

    [11] Yana rufe mutane. Wannan wata azaba ce mai raɗaɗi

    [12] Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azaba. Lalle Mu, masu imani ne

    [13] Ina tunawa take a gare su, alhali kuwa, haƙiƙa, Manzo mai bayyanawa Ya je musu (da gargaɗin saukar azabar, ba su karɓa ba)

    [14] Sa'an nan suka juya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayawa ne, mahaukaci

    [15] Lalle Mu, Masu kuranyewar azaba ne, a ɗan lokaci kaɗan, lalle ku, masu komawa ne (ga laifin)

    [16] Ranar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mu masu azabar ramuwa ne

    [17] Kuma lalle ne haƙiƙa a gabaninsu, Mun fitini mutanen Fir'auna, kuma wani Manzo karimi ya je musu

    [18] (Mazon ya ce): "Ku kawo mini (imaninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku

    [19] Kuma kada ku nemi ɗaukaka a kan Allah. Lalle ni mai zo muku ne da dalili bayyananne

    [20] Kuma lalle ni na nemi tsari da Ubangijina, kuma Ubangijinku, domin kada ku jefe ni

    [21] Kuma idan ba ku yi imani saboda ni ba, to, ku nisance ni

    [22] Sai ya kirayi Ubangjinsa cewa waɗannan mutanene masu laifi

    [23] (Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle ku, waɗanda ake bi ne (domin a kama ku)

    [24] Kuma ka bar teku rarrabe. Lalle su, runduna ce abar nutsarwa

    [25] Da yawa suka bar gonaki da maremari

    [26] Da shuke-shuke da matsayi mai kyau

    [27] Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta suna masu hutu

    [28] Kamar haka! Kuma Muka gadar da ita ga waɗansu mutane na dabam

    [29] Sa'an nan sama da ƙasa ba su yi kuka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba

    [30] Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun tsirar da Bani Isra'ila daga, azaba mai wulakantawa

    [31] Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin masu ɓarna

    [32] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun zaɓe su saboda wani ilmi (na Taurata) a kan mutane

    [33] Kuma Muka ba su, daga ayoyin mu'ujizoji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna

    [34] Lalle waɗannan mutane, haƙika, suna cewa

    [35] Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tayarwa ba

    [36] Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance masu gaskiya

    [37] shin, su ne mafifita ko kuwa mutanen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabaninsu? Mun halaka su, lalle su, sun kasance masu laifi

    [38] Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu ba, alhali kuwa Muna masu wasa

    [39] Ba Mu halitta su ba face da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba

    [40] Lalle ranar rarrabewa, ita ce lokacin wa'adinsu gaba ɗaya

    [41] Ranar da wani zumu ba ya amfanin wani zumu da kome kuma ba su zama ana taimakon su ba

    [42] face wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shi ne Mabuwayi, Mai jin ƙai

    [43] Lalle itaciyar zaƙƙum (ɗanyen wuta)

    [44] Ita ce abincin mai laifi

    [45] Kamar narkakken kwalta yana tafasa a cikin cikunna

    [46] Kamar tafasar ruwan zafi

    [47] (A ce wa mala'ikun wuta), "Ku kama shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahim

    [48] Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azabar ruwan zafi

    [49] (A ce masa), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwayi mai girma

    [50] Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kuna shakka game da shi

    [51] Lalle masu taƙawa suna cikin matsayi amintacce

    [52] A cikin gidajen Aljanna da maremari

    [53] Suna tufanta daga tufafin alharini raƙiƙi, da mai kauri, suna masu zaman fuskantar juna

    [54] Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mata masu kyaun idanu, masu girmansu

    [55] Suna kira, a cikinsu (gidejen) ga dukan 'ya'yan itacen marmari, suna amintattu (daga dukan abin tsoro)

    [56] Ba su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, face mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azabar Jahim

    [57] Saboda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma

    [58] Domin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ani) da harshenka, tsammaninsu, su riƙa tunawa

    [59] Sai ka yi jira. Lalle su, masu jira ne

    Jasiya

    Surah 45

    [1] H. M

    [2] Saukar Littafi daga Allah Mabuwayi Mai hikima yake

    [3] Lalle ne a cikin sammai da ƙasa akwai ayoyi ga masu imani

    [4] Kuma a cikin halittarku da abin da ke watsuwa na dabba akwai ayoyi ga mutane masu yaƙini

    [5] Kuma da saɓawar dare da yini da abin da Allah Ya saukar daga sama na arziki, sa'an nan Ya rayar da ƙasa game da shi a bayan mutuwarta, da juyawar iskoki, akwai ayoyi ga mutane masu yin hankali

    [6] Waɗancan ayoyin Allah ne, Muna karanta su gare ka da gaskiya. To, da wane labari bayan Allah da ayoyinSa suke yin imani

    [7] Bone ya tabbata ga dukan mai yawan ƙiren ƙarya, mai laifi

    [8] Yana jin ayoyin Allah ana karanta su a kansa, sa'an nan ya doge yana makangari, kamar bai ji su ba. To, ka yi masa bushara da azaba mai raɗaɗi

    [9] Kuma har idan ya san wani abu daga ayoyinMu, sai ya rika su da izgili. Waɗancan suna da wata azaba mai wulakantawa (a duniya)

    [10] Gaba gare su (a Lahira) akwai Jahannama, kuma abin da suka sana'anta ba ya wadatar da su daga kome, kuma abubuwan da suka riƙa majiɓinta, baicin Allah, ba su wadatar da su daga kome. Kuma suna da wata azaba mai girma

    [11] Wannan (Alƙur'ani) shi ne shiryuwa. Kuma waɗanda suka kafirta game da ayoyin Ubangijinsu, suna da wata azaba ta wulakanci mai raɗaɗi

    [12] Allah ne wanda Ya hore muku teku domin jirgi ya gudana a cikinta da umurninSa, kuma domin ku nema daga falalarSa, kuma tsammaninku za ku gode

    [13] Kuma Ya hore muku abin da ke a cikin sammai da abin da ke a cikin ƙasa, gaba ɗaya daga gare Shi yake. Lalle ne, a cikin wancan, haƙiƙa, akwai ayoyi ga mutane waɗanda ke yin tunani

    [14] Ka ce wa waɗanda suka yi imani, su yi gafara ga waɗanda ba su fatan rahama ga kwanukan Allah, domin (Allah) Ya saka wa mutane da abin da suka kasance suna aikatawa

    [15] Wanda ya aikata aikin ƙwarai, to, domin kansa, kuma wanda ya munana aki, to, a kansa. Sa'an nan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku

    [16] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun bai (wa Bani Isra'ila Littafi da hukunci da Annabci, Kuma Mun azurta su daga abubuwa masudaɗi, Kuma Mun fifta su a kan mutanen duniya (a zamaninsu)

    [17] Kuma Muka ba su hujjoji na umurni. Ba su saɓa ba face bayan ilmi ya je musu, saboda zalunci a tsakaninsu. Lalle ne, Ubangijinka zai yi hukunci a tsakaninsu, a Ranar ƙiyama a cikin abin da suka kasance suna saɓa wa (juna)

    [18] Sa'an nan Muka sanya ka a kan wata shari'a ta al'amarin. Sai ka bi ta, Kuma kada ka bi son zuciyoyin waɗannan daba su sani ba

    [19] Lalle ne su, ba za su wadatar da kai da kome ba daga Allah. Kuma lalle ne azzalumai sashensu majiɓintan sashe ne. Kuma Allah ne Majiɓincin masu taƙawa

    [20] wannan (Alkur'ani) hukunce-hukuncen natsuwa ne ga mutane, da shiryuwa, da rahama, ga mutane waɗanda ke da yaƙini

    [21] Ko waɗanda suka yagi miyagun ayyuka suna zaton Mu sanya su kamar waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, su zama daidai ga rayuwarsu da mutuwarsu? Abin da suke hukuntawa ya munana

    [22] Alhali kuwa Allah ne Ya halitta sammai da ƙasa saboda gaskiya, Kuma domin a saka wa kowane rai da abin da ya sana'anta, kuma su, ba za a zalunce su ba

    [23] Shin, ka ga wanda ya riƙi son zuciyarsa sih ne abin bautawarsa, kuma Allah Ya ɓatar da shi a kan wani ilmi, Kuma Ya sa hatini a kan jinsa, da zuciyarsa, kuma Ya sa wata yana a kan ganinsa? To, wane ne zai shiryar da shi bayan Allah? Shin to, ba za ku yi tunani ba

    [24] Kuma suka ce: "Babu kome face rayuwarmu ta duniya; muna mutuwa kuma muna rayuwa (da haihuwa) kuma babu abin da ke halaka mu sai zamani." Alhali kuwa (ko da suke faɗar maganar) ba su da wani ilmi game da wannan, ba su bin kome face zato

    [25] Kuma idan ana karanta ayoyinMu bayyanannu a kansu, babu abin da ya kasance hujjarsu face suka ce: "Ku zo mana da ubanninmu, idan kun kasance masu gaskiya

    [26] Ka ce: "Allah ne ke rayar da ku kuma Shi ne ke matarda ku, sa'an nan Ya tara ku zuwa ga Ranar ¡iyama, babu shakka a gare ta, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba

    [27] Kuma mulkin sammai da ƙasa na Allah ne, Shi kaɗai. Kuma ranar da Sa'a ke tsayuwa, a ranar nan masu ɓatawa (ga hujjojin Allah domin su ki bin shari'arSa) za su yi hasara

    [28] Kuma za ka ga kowace al'umma tana gurfane, kowace al'umma ana kiran ta zuwa ga littafinta. (A ce musu) "A yau ana saka muku da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [29] Wannan littafinMu ne yana yin magana a kanku da gas, kiya. Lalle Mu, Mun kasanceMuna sauya rubutun tamkar abin dakuka kasance kuna aikatawa

    [30] To, amma waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, to, Ubangijinsu zai sanya su a cikin rahamarsa. Wannan shi ne babban rabo bayyananne

    [31] Kuma amma waɗanda suka kafirta (Allah zai ce musu): "Shin, ayoyiNa ba su kasance ana karanta su a kanku ba sai kuka kangare, Kuma kuka kasance mutane masu laifi

    [32] Kuma idan aka ce, lalle wa'adin Allah gaskiya ne, kuma Sa'a, babu shakka a cikinta sai kuka ce, 'Ba mu san abin da ake cewa Sa'a ba, ba mu zato (game da ita) face zato mai rauni, Kuma ba mu zama masu yaƙni ba

    [33] Kuma munanan abin da suka aikata ya bayyana a gare su, kuma abin da suka kasance suna yi na izgili ya wajaba a kansu

    [34] Kuma aka ce: "A yau za Mu manta da ku, kamar yadda kuka manta da gamuwa da yininku wannan. Kuma makomarku wuta ce, Kuma ba ku da waɗansu masu taimako

    [35] Wancan domin lalle ku, kun riƙi ayoyin Allah da izgili, Kuma rayuwar duniya ta ruɗe ku. To, a yau ba za su fita daga gare ta ba, Kuma ba za su zama waɗanda ake neman yardarsu ba

    [36] Saboda haka, godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin sammai, kuma Ubangijin ƙasa, Ubangijin halittu

    [37] Kuma gare Shi girma yake, a cikin sammai da ƙasa, kuma Shi ne Mabuwayi, Mai Hikima

    Ahqaf

    Surah 46

    [1] H. M

    [2] Saukar da littafi daga Allah, Mabuwayi, Mai hikima yake

    [3] Ba Mu halitta sammai da ƙasa ba, da abin da ke tsakaninsu, face da gaskiya da wani ajali ambatacce, kuma waɗanda suka kafirta, masu bijirewa ne daga abin da aka yi musu gargaɗi (da shi)

    [4] Ka ce: "Shin, kun gani, abin da kuke kira, wanda yake baicin Allah? Ku nuna mini, menene suka halitta daga ƙasa? Ko kuwa suna da tarayya a cikin sammai? Ku zo mini da wani littafi na gabanin wannan (Alƙur'ani) ko wata alama daga wani ilmi, idan kun kasance masu gaskiya

    [5] Kuma wane ne mafi ɓata daga wanda ke kiran wanin Allah wanda da ba zai karɓa masa ba, bar Ranar Kyama, alhali su (waɗanda ake kiran) shagaltattu ne daga kiransu

    [6] Kuma idan aka tara mutane sai su kasance maƙiya a gare su, alhali sun kasance masu ƙi ga ibadarsu

    [7] Kuma idan ana karatun ayooyinMu bayyanannu a kansu, sai waɗanda suka kafirta ga gaskiya a lokacin da ta je musu, su ce, "Wannan sihiri ne bayyananne

    [8] Kokuwa suna cewa: "Ya ƙirƙira shi (Alƙur'ani) ne?" Ka ce: "Idan na ƙirƙira shi ne, to ba ku mallaka mini kome daga Allah. Shi ne Mafi sani ga abin da kuke kutsawa a cikinsa na magana. (Allah) Ya isa Ya zama shaida a tsakaninada tsakaninku. Kuma shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai

    [9] Ka ce: "Ban kasance farau ba daga Manzanni, kuma ban san abin da za a yi game da ni ko game da ku (na gaibi) ba, ba ni bin kome face abin da ake yin wahayi zuwa gare ni, kuma ban zama ba, face mai gargaɗi mai bayyanawa

    [10] Ka ce: "Shin, kun gani, idan (Alƙur'ani) ya kasance daga wurin Allah yake, kuma kuka kafirta da shi, kuma wani mai shaida daga Bani Isra'ila ya bayar da shaida a kan kwatankwacinsa, sa'an nan ya yi imani, kuma kuka kangare? Lalle Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [11] Kuma waɗanda suka kafirta suka ce wa waɗanda suka yi imani: "Da (Alƙur'ani) ya kasance, wani alheri ne," da ba su riga muzuwa gare shi ba. Kuma tun da ba su shiryu game da shi ba, to, za su ce, "Wannan ƙiren ƙarya ne daɗaɗɗe

    [12] Alhali kuwa a gabaninsa akwai littafin Musa, wanda ya kasance abin koyi, kuma rahama. Kuma wannan (Alƙur'ani) littafi ne mai gaskatawa (ga littafin Musa), a harshe na Larabci domin ya gargaɗi waɗanda suka yi zalunci, kuma ya zama bushara ga masu kyautatawa

    [13] Lalle ne waɗanda suka ce: "Ubangijinmu Allah ne," sa'an nan suka daidaitu, to, babu wani tsoro a kansu, kuma ba za su yi baƙin ciki ba

    [14] Waɗannan 'yan Aljanna ne, suna madawwama a cikinta, a kan sakamako ga abin da suka kasance suna aikatawa

    [15] Kuma Mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa biyu da kyautatawa, uwarsa ta yi cikinsa wahala, kuma ta haife shi wahala. cikinsa da yayensa wata talatin. Har a lokacin da ya kai ga mafi ƙarfinsa, kuma ya kai shekara arba'in, ya ce: "Ya Ubangijina! Ka kange nidomin in gode wa ni'imarKa, wadda Ka ni'imta a kaina da kuma a kan mahaifana biyu, kuma domin in aikata aikin ƙwarai wanda Kake yarda da shi, kuma Ka kyautata mini a cikin zuriyata. Lalle ni, na tuba zuwa gare Ka, kuma lalle ni, ina daga masu sallamawa (ga umurninKa)

    [16] Waɗancan ne waɗanda Muke karɓa, daga gare su, mafi kyaun abin da suka aikata, kuma Muke gafarta mafi munanan ayyukansum (suna) a cikin 'yan Aljanna, a kan wa'adin gaskiya wanda suka kasance ana yi musu alkawari (da shi)

    [17] Kuma wanda ya ce wa mahaifansa biyu: "Tir gare ku! shin, kuna tsoratar da ni cewa za a fitar da ni daga (kabari) ne, alhali kuwa ƙarnoni na mutane da yawa sun shuɗe a gabanina (ba su komo ba)?" Kuma su (mahaifan) suna neman Allah taimako (sunace masa) "Kaitonka! Ka yi imani, lalle wa'adin Allah gaskiya ne." Sai shi kuma ya ce. "Wannan ba kome ba ne face tatsuniyoyin mutanen farko

    [18] Waɗancan ne waɗanda kalmar azaba ta wajaba a kansu, a cikin al'ummomi waɗanda suka shuɗe, (ba da daɗewa ba), a gabaninsu, daga aljannu da mutane. Lalle su, sun kasance masu hasara

    [19] Kuma ga kowane nau'i, yana da darajoji daga abinda suka aikata. Kuma domin (Allah) Ya cika musu (sakamakon) ayyukansu, alhali kuwa su, ba za a zalunce su ba

    [20] Kuma ranar da ake gitta waɗanda suka kaflrta a kan wuta (a ce musu): "Kun tafiyar da abubuwanku na jin daɗi a cikin rayuwarku ta duniya, kuma kun nemi jin dadi da su, to, ayau ana saka muka da azabar wulakanci, domin abin da kuka kasance kana yi na gmian kai a cikin ƙasa, ba da wani hakki ba, kuma domin abin da kuka kasance kuna yi na fasiƙansi

    [21] Kuma ka ambaci ɗan'uwan Adawa a lokacin da ya yi gargaɗi ga mutanensa, a Tuddan Rairayi, alhali kuwa waɗansu masu gargaɗi sun shuɗe agaba gare shi da baya gare shi (da cewa) "Kada ku bauta wa kowa face Allah. Lalle ni ina tsorata muku azabar yini mai girma

    [22] Suka ce: "Shin, ka zo mana ne domin ka karkatar da mu daga gumakaumu? To, ka zo mana da abin da kake yi mana wa'adin, idan ka kasance daga masu gaskiya

    [23] Ya ce: "Ilimi a wurin Allah kawai yake, kuma ina iyar maku abin da aka aiko ni da shi, kuma amma ina ganin, ku, wasu mutane ne, kuna jahiltar gaskiya

    [24] To, a lokacin da suka ga azabar, kumar hadari mai fuskantar rafukansu, suka ce: "Wannan hadari ne mai yi mana ruwa. A'a, shi na abin da kuke neman gaggawar saukarsa; Iska ce, a cikinta akwai wata azaba mai raɗaɗi

    [25] Tana darkake kowane abu da umurnin Ubangijinta. Sai suka wayi gari, ba a ganin kome face gidajensu. Kamar wannan ne Muke saka wa mutane masu laifi

    [26] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun ba su iko ga abin da ba Muba ku iko gare shi ba, kuma Muka sanya musu wani irin ji da gani dazukata. Sai dai jnsu bai amfane su ba, kuma zukatansu ba su amfane su ba ga kome, domin sun kasance suna musu game da ayoyin Allah, kuma abin da suka kasance suna aikatawa na izgili game da shi ya wajaba a gare su

    [27] Kuma ne, lalle haƙiƙa, Mun halakar da abin da yake kewayenku na alƙaryu kuma Muka jujjuya ayoyi, tsammaninsu za su komo

    [28] To, don mene ne waɗanda suka riƙa, baicin Allah, abubuwan yi. wa baiko, gumaka, ba su taimake su ba? A'a, sun ɓace musu Kuma wannan shi ne ƙiren ƙaryarsu da abin da suka kasance suna ƙirƙirawa

    [29] Kuma a lokcin da Muka juya waɗansu jama'a na aljamiu zuwa gare ka suna sauraren Alƙur'ani. To, alokacin da suka halarce shi suka ce: "Ku yi shiru." Sa'an nan da aka ƙare, suka juya zuwa ga jama'arsu suna masu gargaɗi

    [30] Suka ce: "Ya mutanenmu! Lalle mu, mun ji wani littafi an saukar da shi a bayan Musa, mai gaskatawa ga abin da ke a gaba da shi, yana shiryarwa ga gaskiya da kuma zuwa ga hanya madaidaiciya

    [31] Ya mutanenmu! Ku karɓa wa mai kiran Allah, kuma ku yi imani da Shi, Ya gafarta muku daga zunubanku, kuma ya tserar da ku daga azaba mai raɗaɗi

    [32] Kuma wanda bai karɓa wa mai kiran Allah ba to bai zama mai buwaya a cikin ƙasa ba, kuma ba ya da waɗansu majiɓinta, baicin Shi. Waɗannnan suna a cikin ɓata bayyananna

    [33] Shin, kuma ba su gani ba cewa: "Lalle Allah, Wanda Ya halitta sammai da ƙasa kuma bai kasa ga halittarsu ba, Mai ikon yi ne a kan rayar da matattu?" Na'am, lalle Shi, Mai ikon yi ne a kan kome

    [34] Kuma ranar da ake gittar da waɗanda suka kafirta a kan wuta, (a ce musu) "Ashe, wannan ba gaskiya ba ne?" Su ce: "Na'am, gaskiya ne, mun rantse da Ubangijinmu!" Sai Ya ce, "To, ku ɗanɗani azabar saboda abin da kuka kasance kuna yi na kafirci

    [35] Saboda haka, ka yi haƙuri kamar yadda masu ƙarfin niyya daga Manzanni suka yi haƙuri. Kuma kada ka yi musu gaggawa. Kamar dai su, a ranar da suke ganin (sakamako) abin da ake yi musu wa'adi ba su zauna ba, face sa'a guda daga yini. Iyarwa dai da Manzanci). Shin, akwai wanda za a halakar? (Babu), face mutane fasiƙai

    Muhammadu

    Surah 47

    [1] Waɗanda suka kafirta kuma suka kange mutane daga tafarkin Allah, (Allah) Ya ɓatar da ayyukansu

    [2] Kuma waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka yi imani da abinda aka sassaukar ga Muhammadu, alhali kuwa shi ne gaskiya daga Ubangijinsu, (Allah) Ya karkare musu miyagun ayyukansu, kuma Ya kyautata halayensu

    [3] Wannan kuwa saboda lalle, waɗanda suka kafirta sun bi ƙarya, kumar lalle waɗanda suka yi imani, sun bi gaskiya daga Ubangijinsu. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana wa mutane misalansu

    [4] Saboda haka idan kun haɗu da waɗanda suka kafirta, sai ku yi ta dukan wuyoyinsu har a lokacin da suka yawaita musu kisa, to, ku tsananta ɗaurinsu sa'an nan imma karimci a bayan' haka ko biyan fansa, har yaƙi ya saukar da kayansa masu nauyi. Wancan, da Allah na so da Ya ci nasara a kansu (ba tare da yaƙin ba) kuma amma (ya wajabta jihadi) domin Ya jarraba sashenku da sashe. Kuma waɗanda zaka kashe a cikin tafarkin Allah, to, ba ai ɓatar da ayyukansu ba

    [5] Zai shiryar da su, kuma Ya kyautata halayensu

    [6] Kuma Ya shigarda su Aljanna (wadda) Ya siffanta ta a gare su

    [7] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan kun taimaki Allah, zai taimake ku, kuma Ya tabbatar da dugaduganku

    [8] Kuma waɗanda suka kafirta, to, ruɓushi ya tabbata a gare su, kuma (Allah) Ya ɓatar da ayyukansu

    [9] Wannan, saboda lalle su, sun ƙi abin da Allah Ya saukar domin haka Ya ɓata ayyukansu

    [10] Shin, ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasa, domin su gani yadda aƙibar waɗanda ke a gabaninsu ta kasance? Allah Ya darkake a kansu. Kuma akwai misalan wannan aƙibar ga kafirai (na kowane zamani)

    [11] Wancan! Saboda lalle Allah ne Majiɓincin waɗanda suka yi imani, kuma lalle, kafirai babu wani majiɓinci a gare su

    [12] Lalle ne, Allah na shigar da waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai a gidajen Aljanna, kogunan ruwa na gudana daga ƙarƙashinsu, kuma waɗanda suka kafirta suna jin ɗan daɗi (aduniya) kuma suna ci, kamar yadda dabbobi ke ci, kuma wuta ita ce mazauni a gare su

    [13] Kuma da yawa akwai alƙarya, ita ce mafi tsanani ga ƙarfi daga alƙaryarka wadda ta fitar da kai, Mun halaka ta, sa'an nan kuwa babu wani mai taimako a gare su

    [14] Shin, wanda ya kasance a kan wata hujja daga Ubangijinsa, zai zama kamar wanda aka ƙawace masa mugun aikinsa, kuma suka bibbiyi son zuciyoyinsu

    [15] Misalin Aljanna, wadda aka yi wa'adinta ga masu taƙawa, a cikinta akwai waɗansu koguna na ruwa ba mai sakewa ba da waɗansu koguna na madara wadda ɗanɗanonta ba ya canjawa, da waɗansu koguna na giya mai daɗi ga mashaya, da waɗansu koguna na zuma tatacce kuma suna samu, a cikinta, daga kowane irin 'ya'yan itace, da wata gafara daga Ubangijinsu. (Shin, masu wannan ni'ima na daidaita) kamar wanda yake madawwami ne a cikin wuta kuma an shayar da su wani ruwa mai zafi har ya kakkatse hanjinsu

    [16] Kuma daga cikinsu akwai wanda ke saurare zuwa gare ka, har idan sun fita daga wurinka, su ce wa waɗanda aka bai wa ilmi "Mene ne (Muhammadu) ya faɗa ɗazu?" Waɗannan ne waɗanda Allah Ya shafe haske daga zukatansu, kuma suka bi son zuciyoyinsu

    [17] Kuma waɗannan da suka nemi shiryuwa (Allah) Ya ƙara musu shiryuwarsu, kuma Ya ba su (sakamakon) taƙawarsu

    [18] To shin suna jiran (wani abu)? Face S'a ta je musu bisa abke, domin lalle sharuɗɗanta sun zo. To, yaya tunawarsu take, idan har ta je musu

    [19] Saboda hakaa ka sani, cewa babu abin bautawa face Allah, kuma ka nemi gafara ga zunubin, ka, (kuma saboda muminai maza da muminai mata kuma Allah Ya san majuyaiku da mazauninku)

    [20] Kuma waɗanda suka yi imani suna cewa: "Don mene ne ba a saukar da wata sura ba? "To idan aka saukar da wata sura, bayyananna, kuma aka ambaci yaƙi a cikinta, za ka ga waɗanda yake akwai wata cuta a cikin zukatansu suna kallo zuwa gare ka, irin kallon wanda aka rufe da magagi saboda mutuwa. To, abin da yake mafifici a gare su

    [21] Yin ɗa'a da magana mai kyau. Sa'an nan idan al'marin ya ƙullu, to, da sun yi wa Allah gaskiya, lalle da ya kasance mafifi ci a gare su

    [22] To, shin, kuna fatan idan kun juya (daga umurnin) za ku yi ɓarna a cikin ƙasa, kuma ku yan yanke zumuntarku

    [23] Waɗannan su ne waɗanda Allah Ya la'ane su, sa'an nan Ya kurumtar da su, kuma Ya makantar da ganinsu

    [24] Shin to, ba za su, kula da Alƙur'ani ba, ko kuwa a bin zuka tansu akwai makullansu

    [25] lalle ne, waɗanda suka koma baya a kan dugadugansu a bayan shiryuwa ta bayyana a gare su, Shaiɗan ne ya ƙawata musu (haka), kuma ya yi musu shibta

    [26] Wancan, domin lalle su sun ce wa waɗanda suka ƙi abin da Allah Ya saukar: "Za mu yi muku ɗa'a ga sashen al'amarin," alhali kuwa Allah Yana sane da ganawarsu ta asiri

    [27] To, yaya halinsu yake a lokacin da mala'iku ke karɓar rayukansu, suna dukan fuskokinsu da ɗuwaiwansu

    [28] Wannan, domin lalle su sun bi abin da ya, fusatar da Allah kuma sun ƙi yardarSa, saboda haka Ya ɓata ayyukansu

    [29] Ko kuwa waɗanda ke da wata cuta a cikin zukatansu suna zaton cewa Allah ba zai fitar da mugun ƙulle-ƙullen su (ga Musulunci) ba

    [30] Kuma da Muna so, da lalle Mun nuna maka su. To, lalle kana sanin su game da alamarsu. Kuma lalle kana sanin su ga shaguɓen magana, alhali kuwa Allah Yana sanin ayyukanku

    [31] Kuma lalle ne, Muna jarraba ku, har Mu san masu jihadi daga cikinku da masu haƙuri kuma Muna jbrraba labaran ku

    [32] Lalle ne, waɗanda suka kafirta, kuma suka kange daga tafarkin Allah, kuma suka saɓa wa Manzon sa a bayan shiriyar ta bayyana a gare su, ba za su cuci Allah da kome ba, kuma za Ya ɓata ayyukansu

    [33] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yi ɗa'a ga Allah, kuma ku yi ɗa'a ga ManzonSa, kuma kada ku ɓata ayyukanku

    [34] Lalle ne waɗanda suka kafirta sa'an nan kuma suka kange (mutane) daga tafarkin Allah, sa'an nan suka mutu, alhali kuwa suna kafirai, to, Allah ba zai yi gafara ba a gare su

    [35] Saboda haka kada ku yi rauni, kuma (kada) ku yi kira zuwaga sulhi alhali kuwa ku ne mafiɗaukaka kuma Allah na tare da ku, kuma ba, zai naƙasa muku ayyukanku ba

    [36] Rayuwar duniya, wasa da abin shagala kawai ce, kuma idan kun yi imani, kuma kun yi taƙawa, Allah zai kawo muku ijarorinku, kuma ba zai tambaye ku dukiyarku ba

    [37] Da Allah zai tambaye ku su (dukiyoyin) har Ya wajabta muku bayarwa, za ku yi rowa kuma Ya fitar da miyagun ƙulle-ƙullenku

    [38] Ga ku, ya ku waɗannan! Ana kiran ku domin ku ciyar ga tafarkin Allah, sa'an nan daga cikinku akwai mai yin rowa. Kuma wanda ke yin rowa, to, yana yin rowar ne ga kansa. Kuma Allah ne wadatacce alhali kuwa ku faƙirai ne. Kuma idan kuka juya (daga yi Masa ɗa'a), zai musanya waɗansu mutane waɗansunku sa'an nan ba za su kasance kwatankwacinku ba

    Fatahu

    Surah 48

    [1] Lalle Mu, Mun yi maka rinjaye (a kan maƙiyanka), rinjaye bayyananne

    [2] Domin Allah Ya shafe abin da ya gabata na laifinka da abin da ya jinkirta, kuma Ya cika ni'imarSa a kanka, kuma Ya shiryar da kai ga hanya madaidaiciya

    [3] Kuma Allah Ya taimake ka, taimako mabuwayi

    [4] Shi ne wanda Ya saukar da natsuwa a cikin zukatan muminai domin su ƙara wani imani tare da imaninsu, alhali kuwa rundunonin sammai da ƙasa, na Allah kawai ne, kuma Allah Ya kasance Masani, Mai hikima

    [5] Domin Ya shigar da muminai maza da muminai mata gidajen Aljanna, kogunan ruwa na gudana daga ƙarƙashin gidajen, suna madawwama a cikinsu kuma Ya kankare musu munanan ayyukansu. wannan abu ya kasance a wurin Allah babban rabo, mai gimia

    [6] Kuma Ya yi azaba ga munafikai maza da munafikai mata da mushirikai maza da musbirikai mata, masu zaton mugun zato game da Allah, mugunyar masifa mai kewayewa ta tabbata a kansu, kuma Allah Ya yi hushi da su, kuma Ya la'ane su, kuma Ya yi musu tattlain Jahannama kuma ta munana ta zama makoma (gare su)

    [7] Rundunonin sammai da ƙasa na Allah kawai ne, kuma Allah Ya kasance Mabuwayi, Mai hikima

    [8] Lalle Mu Mun aike ka, kana mai shaida, kuma mai bayar da bushara kuma mai gargaɗi

    [9] Domin ku yi imani da Allah da ManzonSa, kuma ku ƙarfafa shi, kuma ku girmama Shi, kuma ku tsarkake Shi (Allah) safiya da maraice

    [10] Lalle waɗanda ke yi maka mubaya'a, Allah kawai ne suke yi wa mubaya'a, Hannun Allah na bisa hannayensu, saboda haka wanda ya warware, to, yana warwarewa ne a kan kansa kawai, kuma wanda ya cika ga alkawarin da ya yi wa Allah a kansa, to, (Allah) zai kawo masa ijara mai girma

    [11] Waɗanda aka bari daga ƙauyawa za su ce maka, "Dukiyoyinmu da iyalanmu sun shagaltar da mu, sai ka nema mana gafara." Suna faɗa, da harsunansu, abin da ba shi ne a cikin zukatansu ba. Kace: "To, wane ne ke mallakar wani abu daga Allah saboda ku, idan Ya yi nufin wata cuta agare ku ko kuma (idan) Ya yi nufin wani amfani a gare ku? A'a, Allah Ya kasance Mai labartawa ne ga abin da kuke aikatawa

    [12] A'a kun yi zaton Annabi da muminai, ba za su komo zuwa ga iyalansu ba, har abada. Kuma an ƙawata wannan (tunani) a cikin zukatanku, kuma kun yi zato, zaton mugunta, kuma kun kasance mutane halakakku

    [13] Kuma wanda bai yi imani da Allah da kuma Manzonsa ba, to, lalle Mu, Mun yi tattalin wuta mai tsananin ƙuna, domin kafirai

    [14] Mulkin sammai da ƙasa na Allah kawai ne, Yana gafartawa ga wanda Yake so, kuma Yana azabta wanda Yake so alhali kuwa Allah Ya kasance Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [15] Waɗanda aka bari za su ce idan kun tafi zuwa ga waɗansu ganimomi domin ku karɓo su, "Ku bar mu, mu bi ku." Suna son su musanya maganar Allah ne. Ka ce: "Ba za ku bi mu ba. Kamar wannan ne Allah Ya ce, a gabanin haka." Sa'an nan za su ce: "A'a, kuna dai hassadar mu ne." A'a, sun kasance ba su fahimtar (abubuwa) sai kaɗan

    [16] Ka ce wa waɗanda aka bari daga ƙauyawa: "Za a kira ku zuwa ga waɗansu mutane masu tsananin yaƙi (domin) ku yaƙe su ko kuwa su musulunta. To, idan kun yi ɗa'a, Allah zai kawo muku wata ijara mai kyau, kuma idan kuka juya baya kamar yadda kuka juya a gabanin wancan, zai azabta ku, azaba mai raɗadi

    [17] Babu laifi a kan makaho, kuma babu laifi a kan gurgu, kuma babu laifi a kan majiyyaci. Kuma wanda ya yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, (Allah) zai shigar da shi a gidajen Aljanna, koguna na gudana daga ƙarƙashinsu. Kuma wanda ya juya baya, (Allah) zai azabtashi, azaba mai raɗaɗi

    [18] Lalle ne haƙiƙa, Allah Ya yarda da muminai a lokacin da suke yi maka mubaya, a a ƙarƙashin itaciyar nan domin Ya san abin da ke cikin zukatansu sai Ya saukar da natsuwa a kansu, kuma Ya saka musu da wani cin nasara makusanci

    [19] Da waɗansu ganimomi masu yawa da za su karɓo su. Kuma Allah Ya kasance Mabuwayi, Mai hikima

    [20] Kuma Allah Ya yi muku wa'adin waɗansu ganimomi masu yawa, waɗanda za ku karɓo su, kuma Ya gaggauta muku wannan. Kuma Ya kange hannayen mutane daga gare ku, kuma domin ta kasance wata aya ce ga muminai, kuma Ya shiryar da ku ga hanya madaidaiciya

    [21] Da waɗansu (ganimomin) da ba ku da iko a kansu lalle Allah Ya kewaye su da saninSa, kuma Allah Ya kasance Mai ikon yi ne a kan dukan kome

    [22] Kuma da waɗanda suka kafirta sun yake ku, da sun juyar da ɗuwaiwai (domin gudu) sa'an nan ba za su sami majiɓinci ba, kuma ba za su sami mataimaki ba

    [23] Hanyar Allah wadda ta shuɗe daga gabanin wannan, kuma ba za ka sami musanya ba ga hanyar Allah (ta taimakon muminai akan mai zaluntarsu)

    [24] Kuma Shi ne Ya kange hannayensu daga gare ku, kuma da hannayenku daga gare su, a cikin Makka, bayan Ya rinjayar da ku a kansu. Kuma Allah Ya kasance Mai gani ga abin da kuke aikatawa

    [25] Su ne waɗanda suka kafirta kuma suka kange ku daga Masallacin Harami, da hadaya tana tsare (sun hana ta) ta isa ga wurinta. Kuma ba domin waɗansu maza muminai da waɗansu mata muminai ba ba ku sansu ba ku taka su har wani aibi ya same ku daga gare su, ba da sani ba, (da Allah Ya yi muku iznin yaƙi), domin Allah Ya shigar da wanda Yake so a cikin rahamarSa. Da (muminai) sun tsabbace da Mun azabtar da waɗanda suka kafirta daga gare su da azaba mai raɗiɗi

    [26] A lokacin da waɗanda suka kafirta suka sanya hananar ƙabi lanci a cikin zukatansu hananar ƙabilanci irin na Jahiliyya sai Allah Ya saukar da natsuwarSa a kan ManzonSa, kuma da a kan muminai kuma Ya lazimta musu kalmar taƙawa alhali kuwa sun kasance mafi dacewa da ita kuma ma'abutanta. Kuma Allah ya kasance Masani game da dukan kome

    [27] Lalle ne haƙiƙa Allah Ya gaskata wa ManzonSa mafarkinsa da gaskiya: Lalle za ku shiga Masallacin Harami, in Allah Ya so, kuna masu natsuwa, masu aske kawunanku da masu suisuye, ba ku jin tsoro, domin (Allah) Ya san abin da ba ku sani ba, sa'an nan Ya sanya wani cin nasara makusanci a bayan wannan

    [28] Shi ne wanda Ya aiki ManzonSa da shiriya da addinin gaskiya domin Ya rinjayar da shi a kan addinai dukansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai shaida

    [29] Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, kana ganin su suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda. Wannan shi ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injila ita ce kamar tsiron shuka wanda ya fitar da reshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafafunsa, yana bayar da sha'awa ga masu shukar' domin (Allah) Ya fusatar da kafirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gafara da ijara mai girma

    Hujurat

    Surah 49

    [1] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku gabata (da kome) gaba ga Allah da ManzonSa. Kuma ku yi ɗa'a ga Allah da taƙawa. Lalle Allah Mai ji ne, Masani

    [2] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku ɗaukaka saututtukanku bisa sautin Annabi, kuma kada ku bayyana sauti gare shi a magana, kamar bayyanawar sashenku ga sashe, domin kada ayyukanku su ɓaci, alhali kuwa ku ba ku sani ba

    [3] Lalle waɗanda ke runtsewar saututtukansu a wurin Manzon Allah waɗannan ne waɗanda Allah Ya, jarrabi zukatansu ga taƙawa. Suna da wata irin gafara da ijara mai girma

    [4] Lalle waɗanda ke kiranka daga bayan ɗakuna, mafi Yawansu ba su aiki da hankali

    [5] Kuma da lalle su, sun yi haƙuri har ka fita zuwa gare su, haƙiƙa, da ya kasance mafi alheri gare su, kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [6] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan fasiƙi Ya zo muku da wani babban labari, to, ku nemi bayani, domin kada ku cuci waɗansu mutane a cikin jahilci, saboda haka ku wayi gari a kan abin da kuka aikata kuna masu nadama

    [7] Kuma ku sani (cewa) lalle ne, a cikinku akwai Manzon Allah. Da Yana bin ku ga (halaye) masu Yawa na al'amarin, da kun auku a cikin zunubi, kuma amma Allah Ya soyar da imani a gare ku, kuma Ya ƙawata shi a cikin zukatanku kuma Ya ƙyamantar da kafirci da fasicci da saɓo zuwa gare ku. Waɗannan (da suka lazimci sifofin nan) su ne shiryayyu

    [8] Bisa ga falala daga Allah da ni'ima. Kuma Allah Masani ne, Mai hikima

    [9] Kuma idan jama'a biyu ta muminai suka yi yaki, to, kuyi sulhu, a tsakaninsu. Sai idan ɗayansu ta yi zalunci a kan gudar, to, sai ku yaƙi wadda ke yin zalunci har ta koma, zuwa ga umurnin Allah. To, idan ta koma, sai ku yi sulhu a tsakaninsu da adalci kuma ku daidaita. Lalle Allah na son masu daidaitawa

    [10] Muminai 'yan'uwan juna kawai ne, saboda haka ku yi sulhu a tsakanin 'yan'uwanku biyu, kuma ku bi Allah da taƙawa tsammaninku, a yi muku rahama

    [11] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada waɗansu mutane su yi izgili game da waɗansu mutane, mai yiwuwa ne (abin yi wa izgilin) su kasance mafifita daga gare su (masu izgilin), kuma waɗansu mata kada su yi izgili game da waɗansu mata mai yiwuwa ne su kasancc mafifita daga gare su. Kuma kada ku aibanta kanku, kuma kada ku jefi juna da miyagun sunaye na laƙabobi. Tir da suna na fasicci a bayan imani. Kuma wanda bai tuba ba, to, waɗannan su ne azzalumai

    [12] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku nisanci abu mai yawa na zato. Lalle sashen zato laifi ne. Kuma kada ku yi rahoto, kuma kada sashenku ya yi gulmar sashe. Shin, ɗayanku na son ya ci naman ɗan'uwansa yana matacce? To, kun ƙi shi (cin naman). Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Mai karɓar tuba ne, Mai jin ƙai

    [13] Ya ku mutane! Lalle ne Mu, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangogi da kabiloli, domin ku san juna. Lalle mafificinku daraja a wurin Allah, (shi ne) wanda yake mafificinku a taƙawa. Lalle ne Allah Masani ne, Mai ƙididdigewa

    [14] ¡auyawa suka ce: "Mun yi imani." Ka ce: "Ba ku yi imani ba, amma dai ku ce, 'Mun miƙawuya, imani bai gama shiga a cikinzukatanku ba. Kuma idan kun yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa, to, ba zai rage muku kome daga ayyukanku ba. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [15] Muminan gaskiya kawai, su ne waɗanda suka yi imani da Allah da ManzonSa, sa'an nan ba su yi shakka ba, kuma suka yi jihadi da dukiyarsu da kuma rayukansu, cikin tafarkin Allah. Waɗannan su ne masu gaskiya

    [16] Ka ce: "Kuna sanar da Allah ne game da addininku, alhali kuwa Allah Ya san abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa, kuma Allah Masani ne ga dukan kome

    [17] Suna yin gori a kanka wai sun musulunta. Ka ce: "Kada ku yi gorin kun musulunta a kaina. A'a, Allah ne ke yi muku gori domin Ya shiryar da ku ga imani, idan kun kasance masu gaskiya

    [18] Lalle Allah yana sanin gaibin sammai da ¡asa, kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatawa

    Qafu

    Surah 50

    [1] ¡. Ina rantsuwa da Alƙur'ani Mai girma

    [2] A'a, sun yi mamaki, cewa mai gargaɗi, daga gare su, ya zo musu, sai kafirai suka ce: "Wannan wani abu ne mai ban mamaki

    [3] Shin idan muka mutu kuma muka kasance turɓaya (za a komo da mu)? Waccan komowa ce mai nisa

    [4] Lalle ne Mun san abin da ƙasa ke ragewo daga gare su, kuma wurinMu akwai wani littafi mai tsarewa

    [5] A'a, sun ƙaryata ne game da gaskiyar a lokacin da ta je musu, saboda haka suna a cikin wani al'amari mai raurawa

    [6] Shin, to, ba su yi dubi ba zuwa ga sama a bisa gare su, yadda Muka gina ta, kuma Muka ƙawace ta, kuma ba ta da waɗansu tsagogi

    [7] Da ƙasa, Mun miƙe ta, kuma Mun jefa kafaffun duwatsu a cikinta, kuma Mun tsirar, a cikinta daga kowane ma'auri mai ban sha'awa

    [8] Domin wayar da ido da tunatarwa ga dukan bawa mai tawakkali

    [9] Kuma Mun sassakar, daga sama ruwa mai albarka sa'an nan Muka tsirar game da shi (itacen) lambuna da ƙwaya abin girbewa

    [10] Da itacen dabino dogaye, suna da'ya'yan itace gunda masu hauhawar juna

    [11] Domin arziki ga bayi, kuma Muka rayar da ƙasa matacciya game da shi. Kamar wannan ne fitar daga kabari kake

    [12] Mutanen Nuhu sun ƙaryata, a gabaninsu (mutanen yanzu) da ma'abuta Rassi, da Samudawa

    [13] Da Adawa da Fir'auna da 'yan'uwan Luɗu

    [14] Da ma'abuta ƙunci da mutanen Tubba'u, kowanensu ya ƙaryata Manzanni, sai ƙyacewaTa ta tabbata

    [15] Shin, to, Mun kasa ne game da halittar farko? A'a, su suna a cikin rikici daga halitta sabuwa

    [16] Kuma lalle ne haƙiƙa Mun halitta mutum kuma Mun san abin da ransa ke yin waswasi da shi, kuma Mu ne mafi kusanta zuwa gare shi daga lakar jannayensa

    [17] A lokacin da masu haɗuwa biyu suke haɗuwa daga dama, kuma daga hagu akwai wani (mala'ika) zaunanne

    [18] Ba ya lafazi da wata magana face a liƙe da shi akwai mai tsaro halartacce

    [19] Kuma mayen mutuwa ya je da gaskiya. Wannan shi ne abin da ka kasance daga gare shi kana bijirewa

    [20] Kuma aka hura a cikin ƙaho. Wancan yinin ƙyacewar ne fa

    [21] Kuma kowane rai ya zo, tare da shi akwai mai kora da mai shaida

    [22] (Sai a ce masa): "Lalle ne, haƙiƙa, ka kasance a cikin gafala daga wannan. To, Mun kuranye maka rufinka, saboda haka ganinka a yau, mai kaifi ne

    [23] Kuma abokin haɗinsa ya ce: "Wannan shi ne abin da ke tare da ni halarce

    [24] (A ce wa Mala'iku), "Ku jefa, a cikin Jahannama, dukan mai yawan kafirci, mai tsaurin rai

    [25] Mai yawan hanawa ga alheri, mai zalunci, mai shakka

    [26] Wanda ya sanya, tare da Allah wani abin bautawa na dabam, saboda haka kujefa shi a cikin azaba mai tsanani

    [27] Abokin haɗinsa ya ce: "Ya Ubangijinmu! Ban sanya shi girman kai ba, kuma amma ya kasance a cikin ɓata mai nisa

    [28] Ya ce: "Kada ku yi husuma a wuriNa, alhali Na gabatar da ƙyacewa zuwa gare ku

    [29] Ba a musanya magana a wuriNa, Kuma Ban zama Mai zalunci ba ga bayiNa

    [30] Ranar da Muke cewa ga Jahannama "Shin, kin cika?" Kuma ta ce: "Ashe, akwai wani ƙari

    [31] Kuma a kusantar da Aljanna ga masu taƙawa, ba da nisa ba

    [32] Wannan shi ne abin da ake yi muku wa'adi da shi ga dukan mai yawan komawa ga Allah, mai tsarewar (umurninSa)

    [33] Wanda ya ji tsoron Mai rahama a fake, kuma ya zo da wata irin zuciya mai tawakkali

    [34] (A ce musu) "Ku shige ta da aminci, waccan ita ce ranar dawwama

    [35] Suna da abin da suke so a cikinta, kuma tare da Mu akwai ƙarin ni'ima

    [36] Kuma da yawa Muka halakar, a gabaninsu, (mutanen yanzu) ɗaga waɗansu al'ummomi, (waɗanda suke) su ne mafi ƙarfin damƙa daga gare su, sa'an nan suka yi bincike a cikin ƙasashe: 'Ko akwai wurin tsira'? (Babu)

    [37] Lalle ne, a cikin wancan, akwai tunatarwa ga wanda zuciyarsa ta kasance gare shi, ko kuwa ya jefa sauraro, alhali kuwa yana halarce (da hankalinsa)

    [38] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun halitta sammai da ƙasa da abin da ke a tsakaninsu, a cikin kwanaki shida, alhali wata'yar wahala ba ta shafe Mu ba

    [39] Saboda haka, ka yi haƙuri a kan abin da suke fada, kuma ka yi tasihi game da gode wa Ubangijinka (watau ka yi salla) a gabanin fitowar rana da gabanin ɓacewarta

    [40] Kuma daga dare, sai ka yi tasbihi a gare Shi da bayan sujada

    [41] Kuma ka saurara a ranar da mai kira ke yin kira daga wuri makusanci

    [42] Ranar da suke sauraron tsawa da gaskiya. Wancan shi ne yinin fita (daga kabari)

    [43] Lalle Mu ne haƙiƙa, Mu ne ke rayarwa, kuma Mu ne ke kashewa, kuma zuwa gare Mu kawai ne makomar take

    [44] Ranar da ƙasa ke tsattsagewa daga gare su, suna masu gaggawa. Wancan tarawar mutane ne, mai sauƙi a gare Mu

    [45] Mu ne mafi sani game da abin da suke faɗi, kuma ba za ka zama mai tilasta su ba. Saboda haka ka tunatar game da Alƙur'ani, ga wanda ke tsoron ƙyacewaTa

    Azzariyat

    Surah 51

    [1] Ina rantsuwa da iskoki masu shekar abubuwa, sheƙewa

    [2] Sa'an nan da giragizai masu ɗaukar nauyi (na ruwa)

    [3] Sa'an nan da jirage masu gudana (a kan ruwa) da sauƙi

    [4] Sa'an nan da Mala'iku masu rabon al'amari (bisa umurnin Allah)

    [5] Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙiƙa gaskiya ne

    [6] Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙiƙa, mai aukuwa ne

    [7] Ina rantsuwa da sama ma'abuciyar hanyoyi (na tafiyar taurari da sautin rediyo)

    [8] Lalle ku, haƙiƙa, kuna cikin magana mai saɓa wa juna (game da Alƙur'ani)

    [9] Ana karkatar da wanda aka juyar (daga gaskiya)

    [10] An la'ani masu ƙiri-faɗi

    [11] Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jahilci

    [12] Suna tambaya: "Yaushe ne ranar sakamako za ta auku

    [13] Ranar da suke a kan wuta ana fitinar su

    [14] (A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shi ne abin da kuka kasance kuna neman zuwansa da gaggawa

    [15] Lalle masu taƙawa, suna a cikin lambunan itace da maremari

    [16] Suna masu dibar abin da Ubangijinsu Ya ba su. Lalle su, sun kasance masu kyautatawa a gabanin haka (a duniya)

    [17] Sun kasance a lokaci kaɗan na dare suke yin barci

    [18] Kuma a lokutan asuba suna ta yin istigfari

    [19] Kuma a cikin dukiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai roƙo da wanda aka hana wa roƙo

    [20] Kuma a cikin ƙasa akwai ayoyi ga masu yaƙini

    [21] Kuma a cikin rayukanku (akwai ayoyi). To, ba za ku duba ba

    [22] Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitowa) da abin da ake yi muku alkawari

    [23] To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasa, lalle shi (abin da ake yi muku alkawari), haƙiƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kuna karantawa na magana

    [24] Shin, labarin Baƙin Ibrahim, waɗanda aka girmama, ya zo maka

    [25] A lokacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutane baƙi

    [26] Sai ya juya zuwa ga iyalinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna

    [27] Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Ba za ku ci ba

    [28] Sai ya ji tsoro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsoro." Kuma suka yi masa bushara da (haihuwar) wani yaro mai ilmi

    [29] Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallowa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsohuwa bakarariya (za ta haihu)

    [30] Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shi, Shi ne Mai hikima, Mai ilmi

    [31] (Ibraim) ya ce: "To mene ne babban al'almarinku, ya ku Manzanni

    [32] Suka ce: "Lalle mu, an aike mu zuwa ga waɗansu mutane, masu laifi

    [33] Domin mu saka musu waɗansu duwatsu na wani yumɓu (bom)

    [34] Waɗanda aka yi wa alama daga wajen Ubangijinka, domin masu ɓarna

    [35] Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga muminai

    [36] Sai dai ba mu samu ba, a cikinta, face gida guda na Musulmi

    [37] Kuma Muka bar wata aya, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsoron azaba, mai raɗaɗi

    [38] Kuma ga Musa, a lokacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalili bayyananne

    [39] Sai ya juya baya tare da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne ko kuwa mahaukaci

    [40] Saboda haka, Muka kama shi tare da rundunarsa, sa'an nan Muka jefa su a cikin teku, alhali kuwa yana wanda ake zargi

    [41] Kuma ga Adawa, a lokacin da Muka aika iska ƙeƙasasshiya a kansu

    [42] Ba ta barin kome da ta je a kansa, face ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasusuwa

    [43] Kuma ga Samudawa, a lokacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan daɗi har wani ɗan lokaci

    [44] Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, saboda haka tsawa ta kama su, alhali kuwa suna kallo

    [45] Ba su ko samu damar tsayawa ba, kuma ba su kasance masu neman agaji ba

    [46] Da mutanen Nuhu a gabanin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutane ne fasiƙai

    [47] Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhali kuwa lalle Mu ne Masu yalwatawa

    [48] Kuma ƙasa Mun shimfiɗa ta, To, madalla da masu shimfiɗawa, Mu

    [49] Kuma daga kome Mun halitta nau'i biyu, watakila za ku yi tunani

    [50] Saboda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle ni mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi

    [51] Kuma kada ku sanya, tare da Allah wani abin bautawa na dabam, lalle ni, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi

    [52] Kamar haka dai wani Manzo bai je wa waɗanda ke gabaninsu ba face sun ce: "Mai sihiri ne ko mahaukaci

    [53] shin, suna yi wa juna wasiyya da shi ne? A'a, su dai mutane ne masu girman kai

    [54] Sai ka juya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne

    [55] Kuma ka tunatar, domin tunatarwa tana amfanin muminai

    [56] Kuma Ban halitta aljannu da mutane ba sai domin su bauta Mini

    [57] Ba Ni nufln (samun) wani arziki daga gare su, Ba Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni

    [58] Lalle Allah, Shi ne Mai azurtawa, Mai ikon yi, Mai cikakken ƙarfi

    [59] To, lalle waɗanda suka yi zalunci suna da masaki (na ɗiban zunubi) kamar masakin abokansu, saboda haka kada su yi Mini gaggawa

    [60] Saboda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kafirta, daga ranar su wadda aka yi musu alkawari

    Ɗũr

    Surah 52

    [1] Ina rantsuwa da ¦ur (Dutsen Musa)

    [2] Da wani littafi rubutacce

    [3] A cikin wata takardar fata shimfiɗaɗɗa

    [4] Da Gidan da aka rayar da shi (da ibada)

    [5] Da rufin nan da aka ɗaukaka

    [6] Da tekun nan da aka cika (da ruwa)

    [7] Lalle, azabar Ubangijinka, haƙiƙa, mai aukuwa ce

    [8] Ba ta da mai tunkuɗewa

    [9] Ranar da sama ke yin motsi tana kai kawo

    [10] Kuma duwatsu na tafiya suna shuɗewa

    [11] To, bone ya tabbata a ranar nan ga masu ƙaryatawa

    [12] Waɗanda suke a cikin kududdufi suna wasa

    [13] Ranar da za a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗawa

    [14] (A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kuna ƙaryatawa game da ita

    [15] To, shin wannan sihiri ne ko kuwa ku ne ba ku gani

    [16] Ku shige ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai ana yi muku sakamakon abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [17] Lalle, masu taƙawa, suna a cikin gidajen Aljanna da wata ni'ima

    [18] Suna masu jin daɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsare musu azabar Jahim

    [19] (A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, domin abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [20] Suna kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mata masu farin idanu, masu girmansu

    [21] Kuma waɗanda suka yi imani kuma zuriyarsu suka bi su ga imanin, Mun riskar da zuriyarsu da su, alhali kuwa ba da Mun rage musu kome ba daga aikinsu, kowane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta

    [22] Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itace da nama irin wanda suke marmari

    [23] Suna miƙa wa junansu a cikinta hinjalan giya, wadda babu yasassar magana a cikinta, kuma babu jin nauyin zunubi

    [24] Kuma waɗansu samari na gewayawa a kansu, kamar dai su lu'ulu'u ne wanda ke kulle

    [25] Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, suna tambayar juna

    [26] Suka ce: "Lalle mu mun kasance a gabanin wannan (a duniya) a cikin iyalanmu muna jin tsoro

    [27] To, Allah Ya yi mana kyautar falala, kuma Ya tsare mana azabar iskar zafi

    [28] Lalle mu mun kasance, a gabanin haka, muna kiran sa. Lalle Shi, Shi ne Mai kyautatawa, Mai rahama

    [29] To, ka tunatar kai fa saboda ni'imar Ubangjinka, ba boka kake ba, kuma ba mahaukaci ba

    [30] Shin za su ce: "Mawaƙi ne, muna jiran, masifun mutuwa game da shi

    [31] Ka ce: "Ku yi jira, domin ni ma lalle ina a cikin masu jira tare da ku

    [32] Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, ko kuwa su wasu mutane ne masu ƙetare haddi

    [33] Shin, cewa suke yi: "Shi ne ke ƙaga faɗarsa"? A'a ba su dai yi imani ba

    [34] Sai su zo da wani labari mai misalinsa idan sun kasance sumasu gaskiya ne

    [35] Shin, an halitta su ne ba daga kome ba, ko kuwa su ne masu yin halitta

    [36] Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? A'a ba su dai yi imanin yaƙini ba

    [37] Shin, taskokin Ubangijinka, suna a wurinsu ne? Ko kuwa su ne masu rinjaya

    [38] Shin, suna da wani tsani ne wanda suke (hawa suna) sauraron (labarin sama) a cikinsa? Sai mai sauraronsu ya zo da wani dalili bayyananne

    [39] Shin, Yana da 'ya'ya mata ne kuma ku, kuna da ɗiya maza ne

    [40] Shin, kana tambayar su wata ijara ne, saboda haka suka zama masu jin nauyin biyan tarar

    [41] Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, saboda haka suna rubutawa

    [42] Shin, suna nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kafirta su ne waɗanda ake yi wa kaidi

    [43] Shin, suna da wani abin bautawa ne wanda ba Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki

    [44] Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga sama yana faɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar juna

    [45] To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sumar da su a cikinsa

    [46] Ranar da kaidinsu ba ya wadatar masu da kome, kuma ba a taimakon su

    [47] Kuma lalle, waɗannan da suka yi zaluncin, suna da azaba (a nan duniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba

    [48] Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kana idanunMu, kuma ka tsarkake Ubangijinka da (tasbihi) game da gode Masa a lokacin da kake tashi tsaye (domin salla ko wani abu)

    [49] Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbihin) dalokacin juyawar taurari

    An Najmi

    Surah 53

    [1] Ina rantsuwa da tauraron, a lokacin da ya faku

    [2] Ma'abucinku bai ɓata ba, kuma bai ƙetare haddi ba

    [3] Kuma ba ya yin magana daga son zuciyarsa

    [4] (Maganarsa) ba ta zamo ba, face wahayi ne da ake aikowa

    [5] (Mala'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi

    [6] Ma'abucin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita

    [7] Alhali kuwa yana a sararin sama mafi aukaka

    [8] Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurowa

    [9] Har ya kasance gwargwadon zira'i biyu, ko kuma abin da ya fi kusa

    [10] Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bawan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa)

    [11] Zuciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba

    [12] Shin, za ku yi masa musu a kan abin da yake gani

    [13] Kuma lalle ya gan shi, haƙiƙatan, a wani lokacin saukarsa

    [14] A wurin da magaryar tuƙewa take

    [15] A inda taken, nan Aljannar makoma take

    [16] Lokacin da abin da yake rufe magaryar tuƙewa ya rufe ta

    [17] Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba

    [18] Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ayoyin Ubangijinsa

    [19] Shin, kun ga Lata da uzza

    [20] Da (wani gunki wai shi) Manata, na ukunsu

    [21] Ashe, ku ne da ɗa namiji Shi (Allah) kuma da ɗiya mace

    [22] Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe

    [23] Waɗannan ba kome ba ne face sunaye, waɗanda kuka ambace su da su, ku da uwayenku. Allah bai saukar da wani dalili game da su ba. (Kafirai) ba su biyar kome face zato da abin da rayukansu ke so, Alhali kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta je musu (sai suka bar ta suka koma wa zaton)

    [24] Ko (an fai cewa) mutum zai sami abin da yake guri

    [25] To, Lahira da duniya na Allah kawai ne (wanda ya neme su daga wani, ya yi kuskure)

    [26] Akwai mala'iku da yawa a cikin sammai cetonsu ba ya wadatar da kome face bayan Allah Ya yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda

    [27] Lalle waɗannan da ba su yin imani da Lahira, haƙiƙa suna kiran mala'iku da sunan mace

    [28] Kuma ba su da wani ilmi game da shi, ba su bin kome face zato alhali kuwa lalle zato ba ya amfanar da kome daga gaskiya

    [29] Saboda haka sai ka kau da kai daga wanda ya juya baya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kome ba face rayuwar kusa (duniya)

    [30] Wannan ita ce iyakar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nemi shiriya

    [31] Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa na Allah kawai ne, domin Ya saka wa waɗanda suka munana da abin da suka aikata, kuma Ya saka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau

    [32] Waɗanda ke nisantar manyan zunubai da abubuwan alfasha, face ƙananan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gafara ne, Shi ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lokacin da Ya ƙaga halittarku daga ƙasa, kuma a lokacin da kuke tayuna a cikin cikannan uwayenku. Saboda haka, kada ku tsarkake kanku, Shi ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa

    [33] Shin, ka ga wannan da ya juya baya

    [34] Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa

    [35] Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Saboda haka yana ganin gaibin

    [36] Ko kuwa ba a ba shi labari ba ga abin da yake a cikin Littafan Musa

    [37] Da Ibrahim wanda ya cika alkawari

    [38] Cewa wani rai mai kayan laifi ba ya ɗaukar kayan laifin wani

    [39] Kuma mutum ba shi da kome face abin da ya aikata

    [40] Kuma lalle, aikinsa za a gan shi

    [41] Sa'an nan a saka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni

    [42] Kuma lalle, makomar zuwa Ubangijinka kawai take

    [43] Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kuka

    [44] Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya kashe, kuma Ya rayar

    [45] Kuma lalle Shi ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace

    [46] Daga wani ɗigon ruwa guda a lokacin da ake jefa shi a cikin mahaifa

    [47] Kuma a kansa ne ƙaga halitta ta biyu take

    [48] Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya azurta, kuma Ya wadatar

    [49] Kuma lalle, Shi, Shi ne Ubangijin Shi'ira

    [50] Kuma lalle, Shi, Shi ne Ya halaka Adawa na farko

    [51] Da Samudawa, sa'an nan bai rage su ba

    [52] Da mutanen Nuhu a gabanin haka, lalle su sun kasance mafi zalunci kuma mafi girman kai

    [53] Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kayar da su

    [54] Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su

    [55] To, da wace daga ni'imomin Ubangijinka kake yin shakka

    [56] wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin masu gargaɗi na farko

    [57] Makusanciya fa, ta yi kusa

    [58] Babu wani rai, banda Allah, mai iya bayani gare ta

    [59] Shin, kuma daga wannan labari kuke mamaki

    [60] Kuma kuna yin dariya, kuma ba ku yin kuka

    [61] Alhali kuna masu wasa

    [62] To, ku yi tawali'u ga Allah, kuma ku bauta (masa)

    Al-Qamar

    Surah 54

    [1] Sa'a ta yi kusa, kuma wata ya tsage

    [2] Kuma idan sun ga wata aya, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dogewa

    [3] Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zuciyarsu, alhali kuwa kowane al'amari (wanda suke son su ture daga Annabi) an tabbatar da shi

    [4] Kuma lalle, abin da yake akwai tsawatarwa a cikinsa na labaraiya zo musu

    [5] Hikima cikakka! Sai dai abubuwan gargaɗi ba su amfani

    [6] Saboda haka, ka bar su! Ranar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama

    [7] ¡asƙantattu ga idanunsu za su fito daga kaburburansu, kamar dai su fari ne waɗandasuka watse

    [8] Suna gaggawar tafiya zuwa ga mai kiran, kafirai na cewa, "Wannan yini ne mai wuya

    [9] Mutanen Nuhu sun ƙaryata, a gabaninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsawace shi

    [10] Saboda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle ni, an rinjaye ni, sai Ka yi taimako

    [11] Sai Muka buɗe kofofin sama da ruwa mai zuba

    [12] Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasa ta zama idanun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi

    [13] Kuma Muka ɗauke Nuhu a kan (jirgi) na alluna da ƙusoshi

    [14] Tana gudana, a kan idanunMu, domin sakamako ga wanda aka yi wa kafircin

    [15] Kuma lalle, Mun bar ta ta zama aya. To, Shin, akwai mai tunani

    [16] To, yaya azabaTa take da gargaɗiNa

    [17] Kuma lalle ne, haƙikƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, domin tunawa. To, shin, akwai mai tunawa

    [18] Adawa sun ƙaryata, to, yaya azabaTa take, da gargaɗiNa

    [19] Lalle Mu, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahisa mai dogewa

    [20] Tana fizgar mutane kamar dai su kututturan dabino tumɓukakku ne

    [21] To, yaya azabaTa take da gargaɗiNa

    [22] Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, domin tunawa. To, shin, akwai mai tunawa

    [23] Samudawa sun ƙaryata game da gargaɗin

    [24] Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bi shi! Lalle mu a lokacin, haƙiƙa mun shiga wata ɓata da hauka

    [25] Shin, an jefa masa Manzancin ne, a tsakaninmu? A'a, shi dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai

    [26] Za su sani a gobe, wane ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan

    [27] Lalle Mu, masu aikawa da raƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri

    [28] Kuma ka ba su labari cewa ruwa rababbe ne a tsakaninsu (da raƙumar), kowane sha, mai shi yana halartar sa

    [29] Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya soke ta

    [30] To, yaya azabaTa take da gargaɗiNa

    [31] Lalle Mu, Mun aika tsawa guda a kansu, sai suka kasance kamar yayin mai shinge

    [32] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, domin tunawa. To, shin, akwai mai tunawa

    [33] Mutanen Luɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi

    [34] Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, face mabiyan Luɗu, Mun tsirar da su a lokacin asuba

    [35] Saboda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke saka wa wanda ya gode

    [36] Kuma lalle, haƙiƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin

    [37] Kuma lalle haƙiƙa, su, sun neme shi ta wajen baƙinsa, sai Muka shafe idanunsu. "To, ku ɗanɗani azabaTa da gargaɗiNa

    [38] Kuma lalle, haƙiƙa, wata azaba matabbaciya ta waye musu gari da yaƙi, tun da safe

    [39] To, ku ɗanɗani azabaTa da gargaɗiNa

    [40] Kuma lalle ne, haƙiƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani domin tunawa. To, shin, akwai mai tunawa

    [41] Kuma lalle, haƙiƙa, gargaɗin ya je wa mabiyan Fir'auna

    [42] Sun ƙaryata game da ayoyinMu, dukansu sai Muka kama su, irin kamun Mabuwayi, Mai ikon yi

    [43] Shin, kafiranku ne mafi alheri daga waɗancan, ko kuwa kuna da wata bara'a a cikin littattafai

    [44] Ko za su ce: "Mu duka masu haɗa ƙarfi ne domin cin nasara

    [45] Za a karya taron, kuma su juya baya domin gudu

    [46] A'a, Sa'a ita ce lokacin wa'adinsu, kuma Sa'ar ta fi tsananin masifa, kuma ta fiɗaci

    [47] Lalle ne, masu laifi suna a cikin ɓata da hauka

    [48] Ranar da za a ja su a cikin wuta a kan fuskokinsu. "Ku ɗanɗani shafar wutar Saƙar

    [49] Lalle Mu, kowane irin abu Mun halitta shi a kan tsari

    [50] Kuma umurninMu bai zamo ba face da kalma ɗaya, kamar walƙawar ido

    [51] Kuma lalle ne haƙiƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunani

    [52] Kuma kowane abu, da suka aikata shi, yana a cikin littattafai

    [53] Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne

    [54] Lalle masu taƙawa suna a cikin gidajen Aljanna da koguna

    [55] A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa

    Ar-Rahman

    Surah 55

    [1] (Allah) Mai rahama

    [2] Ya sanar da Alƙur'ani

    [3] Ya halitta mutum

    [4] Ya sanar da shi bayani (magana)

    [5] Rana da wata a kan lissafi suke

    [6] Kuma tsirrai masu yaɗo da itace suna tawalu'i

    [7] Kuma sama Ya ɗaukaka ta, Kuma Ya aza sikeli

    [8] Domin kada ku karkatar da sikelin

    [9] Kuma ku daidaita awo da adalci, kuma kada ku rage sikelin

    [10] Kuma ƙasa Ya aza ta domin talikai

    [11] A cikinta akwai 'ya'yan itacen marmari da dabino mai kwasfa

    [12] Da ƙwaya mai soshiya da ƙamshi

    [13] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangjinku kuke ƙaryatawa

    [14] Ya halitta mutum daga ƙekasasshen yumɓu kumar kasko

    [15] Kuma ya halitta aljani daga bira daga wuta

    [16] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [17] Ubangjin mafita biyu na rana, kuma Ubangijin mafaɗa biyu na rana

    [18] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [19] Ya garwaya teku biyu (ruwan daɗi da na zartsi) suna haɗuwa

    [20] A tsakaninsu akwai shamaki, ba za su ƙetare haddi ba

    [21] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [22] Lu'ulu'u da murjani na fita daga gare su

    [23] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [24] Kuma Yana da manyan jirage, waɗanda ake ƙagawa a cikin teku kamar manyan duwatsu

    [25] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [26] Dukkan wanda ke kanta mai ƙarewa ne

    [27] Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa

    [28] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [29] wanda ke a cikin sammai da ƙasa yana roƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani

    [30] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [31] Za mu ɗauki lokaci saboda ku, ya ku masu nauyin halitta biyu

    [32] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [33] Ya jama'ar aljannu da mutane! Idan kuna iya zarcewa daga sasannin sammai da ƙasa to ku zarce. Ba za ku iya zarcewaba face da wani dalili

    [34] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [35] Ana sako wani harshe daga wata wuta a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, ba za ku nemi taimako ba

    [36] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [37] Sa'an nan idan sama ta tsage kuma ta zama ja kamar jar fata

    [38] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [39] To, a ran nan ba za a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani

    [40] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [41] za a iya sanin masu laifi da alamarsu, saboda haka sai a kama kwarkaɗarsu da sawayensu

    [42] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [43] Wannan Jahannama ce wadda masu laifi ke ƙaryatawa game da ita

    [44] Suna kewaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa

    [45] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [46] Kuma wanda ya ji tsoron tsayawa a gaba ga Ubangijinsa yana da Aljanna biyu

    [47] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [48] Masu rassan itace

    [49] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [50] A cikinsu akwai maremari biyu suna gudana

    [51] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [52] A cikinsu akwai nau'i biyu daga kowane 'ya'yan itacen marmari

    [53] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [54] Suna gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufafin alharini mai kauri ne kuma nunannun 'ya'yan itacen Aljannar biyu kusakusa suke

    [55] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [56] A cikinsu akwai mata masu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani

    [57] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [58] Kamar dai su yaƙutu ne da murjani

    [59] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [60] Shin, kyautatawa na da wani sakamako? (A'aha) face kyautatawa

    [61] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [62] Kuma baicinsu akwai waɗansu gidajen Aljanna biyu

    [63] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [64] Masu duhun inuwa

    [65] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [66] A cikinsu akwai maremari biyu masu kwararar ruwa

    [67] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [68] A cikinsu akwai 'ya'yan itacen marmari da dabino darummani

    [69] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [70] A cikinsu, akwai wasu mata masu kyaun halaye, masu kyaun halitta

    [71] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [72] Masu farin idanu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimomi

    [73] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [74] Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani

    [75] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [76] Suna gincire a kan wasu matasai masu koren launi da katifun Abkara kyawawa

    [77] To, saboda wanne daga ni'imomin Ubangijinku, kuke ƙaryatawa

    [78] Sunan Ubangjinka, Mai girman Jalala da Karimci, ya tsarkaka

    Al-Waqi'a

    Surah 56

    [1] Idan mai aukuwa ta auku

    [2] Babu wani (rai) mai ƙaryatawa ga aukuwarta

    [3] (Ita) mai ƙasƙantawa ce, mai ɗaukakawa

    [4] Idan aka girgiza ƙasa girgizwa

    [5] Kuma aka niƙe duwatsu, niƙewa

    [6] Sai suka kasance ƙura da ake watsarwa

    [7] Kuma kun kasance nau'i uku

    [8] Watau mazowa dama. Mene ne mazowa dama

    [9] Da mazowa hagu. Mene ne mazowa hagu

    [10] Da waɗanda suka tsere. Su wɗanda suka tseren nan

    [11] Waɗancan, su ne waɗanda aka kusantar

    [12] A ckin Aljannar ni'ima

    [13] Jama'a ne daga mutanen farko

    [14] Da kaɗan daga mutanen ƙarshe

    [15] (Suna) a kan wasu gadaje saƙaƙƙuu

    [16] Suna gincire a kansu, suna masu kallon juna

    [17] Wasu yara samari na dindindin gewaya a kansu

    [18] Da wasu kofuna da shantula da hinjalai daga (giya) mai ɓuɓɓuga

    [19] Ba a sanya musu ciwon jiri saboda ita, kuma ba su buguwa

    [20] Da wasu 'ya'yan itacen marmari daga irin waɗanda suke zaɓe

    [21] Da naman tsuntsaye daga wanda suke ganin sha'awa

    [22] Da wasu mata masu fararen idanu da girmansu

    [23] Kamar misalan lu'ulu'u wanda aka ɓoye

    [24] A kan sakamakon, domin abin da suka kasance suna aikatawa

    [25] Ba su jin wata yasassar magana a cikinta, kuma ba su jin sun yi laifi

    [26] Sai dai wata magana (mai daɗi): Salamun, Salamun

    [27] Da mazowa dama. Mene ne mazowa dama

    [28] (Suna) a cikin itacen magarya maras ƙaya

    [29] Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya

    [30] Da wata inuwa miƙaƙƙiya

    [31] Da wani ruwa mai gudana

    [32] Da wasu 'ya'yan itacen marmari masu yawa

    [33] Ba su yankewa kuma ba a hana su

    [34] Da wasu shimfiɗu maɗaukaka

    [35] Lalle Mu, Mun ƙaga halittarsu ƙagawa

    [36] Sa'an nan Muka sanya su budurwai

    [37] Masu son mazansu, a cikin tsara ɗaya

    [38] Ga mazowa dama

    [39] Wata ƙungiya ce daga mutanen farko

    [40] Da wata ƙungiya daga mutanen ƙarshe

    [41] Mazowa hagu, Mene ne mazowa hagu

    [42] Suna a cikin wata iskar zafi da wani ruwan zafi

    [43] Da wata inuwa ta hayaƙi mai baƙi

    [44] Ba mai sanyi ba, kuma ba mai wata ni'ima ba

    [45] Lalle su, sun kasance a gabanin wannan waɗanda aka jiyar daɗi

    [46] Kuma sun kasance suna dogewa a kan mummunan zunubi mai girma

    [47] Kuma sun kasance suna cewa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓaya da ƙasusuwa shin lalle mu waɗanda za a koma rayarwa ne haƙiƙatan

    [48] Shin, kuma da ubanninmu na farko

    [49] Ka ce: "Lalle mutanen farko da na ƙarshe

    [50] Tabbas, waɗanda ake tarawa ne a cikin wani yini sananne

    [51] Sa'an nan lalle ku, ya ku ɓatattu, masu ƙaryatawa

    [52] Lalle masu ci ne daga wata itaciya ta zaƙƙum (ɗanyen wuta)

    [53] Har za ku zama masu cika cikunna daga gare ta

    [54] Sa'an nan kuma masu sha ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zafi

    [55] Ku zama masu sha irin shan raƙuma masu ƙishirwa

    [56] Wannan ita ce liyafarsu a ranar sakamako

    [57] Mu ne Muka halitta ku, to, don me ba za ku gaskata ba

    [58] Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi

    [59] Shin ku ne kuke halitta shi, ko kuwa mu ne Masu halittawa

    [60] Mu ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakaninku, kuma ba Mu zama Masu gajiyawa ba

    [61] A kan Mu musanya waɗansu (mutane) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba

    [62] Kuma lalle, ne haƙiƙa, kun san halittar farko, to, don me ba za ku yi tunani ba

    [63] Shin, kuma kun ga abin da kuke nomawa

    [64] Shin, ku ne ke tsirar da shi ko kuwa Mu ne Masu tsirarwa

    [65] Da Muna so lalle, da Mun sanya shi busasshiyar ciyawa, sai ku yini kuna mamakin baƙin ciki

    [66] (Kuna cewa) "Lalle haƙiƙa an aza mana tara

    [67] A'a, mun dai zama waɗanda aka hana wa

    [68] Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha

    [69] Shin, ku ne kuke saukar da shi daga girgije, ko kuwa Mune Masu saukarwa

    [70] Da Mun so, da Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me ba ku godewa

    [71] Shin, kuma kun ga wuta wannan da kuke ƙyastawa

    [72] Shin, ku ne kuke ƙaga halittar itaciyarta, ko kuwa Mu ne Masu ƙagawa

    [73] Mu ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin daɗi ga matafiya a cikin jeji

    [74] Sai ka tsarkake sunan Ubangijinka Mai girma

    [75] To, ba sai Na yi rantsuwa ba da lokutan faɗuwar taurari

    [76] Kuma lalle ne' haƙiƙa, rantsuwa ce mai girma, da kun sani

    [77] Lalle shi (wannan littafi), haƙiƙa, abin karantawa ne mai daraja

    [78] A cikin wani littafi tsararre

    [79] Babu mai shafa shi face waɗanda aka tsarkake

    [80] Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta

    [81] Shin, to, wannan labarin ne kuke masu wulakantawa

    [82] Kuma kuna sanya arzikinku (game da shi) lalle ku, ku ƙaryata (shi)

    [83] To, don me idan rai ya kai ga maƙoshi? (Kusa da mutuwa)

    [84] Alhali kuwa ku, a loklcin nan, kuna kallo

    [85] Kuma Mu ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma ku ba ku gani

    [86] To, don me in dai kun kasance ba waɗanda za a yi wa sakamako ba

    [87] Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance masu gaskiya

    [88] To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta

    [89] Sai hutawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima

    [90] Kuma amma idan ya kasance daga mazowa dama

    [91] Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazowa dama

    [92] Kuma amma idan ya kasance daga masu ƙaryatawar, ɓatattun

    [93] Sai wata liyafa ta ruwan zafi

    [94] Da ƙonuwa da Jahim

    [95] Lalle wannan, haƙiƙa, ita ce gaskiya ta yaƙini

    [96] Saboda haka, ka tsarkake sunan Ubangijinka, Mai karimci

    Al-Hadid

    Surah 57

    [1] Abin da ke cikin sammai da ƙasa ya yi tasbihi ga Allah. Kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [2] Shi ne da mulkin sammai da ƙasa: Yana rayarwa kuma Yana kashewa, kuma Shi Mai ikon yi ne a kan kome

    [3] Shi ne Na farko, Na ƙarshe, Bayyananne, Boyayye, kuma Shi Masani ne ga dukkan kome

    [4] Shi ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin wasu kwanuka shida, sa'an nan Ya daidaitu a kan Al'arshi, Yana sanin abin da ke shiga cikin ƙasa da abin da ke fita daga gare ta, da abin da ke sauka daga sama da abin da ke hawa cikinta, kuma Shi yana tareda ku duk inda kuka kasance. Kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatawa

    [5] Shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma zuwa gare Shi (Allah) kawai ake mayar da al'amura

    [6] Yana shigar da dare a cikin yini, kuma Yana shigar da yini a cikin dare, kuma Shi Masani ne ga abin da yake a cikin ƙiraza

    [7] Ku yi imani da Allah da ManzonSa, kuma ku ciyar daga abin da Allah Ya wakilta ku a cikinsa (na dukiya). To, waɗannan da suka yi imani daga cikinku, kuma suka ciyar, suna da wani sakamako mai girma

    [8] kuma me ya same ku, ba za ku yi imani ba da Allah, alhali kuwa manzonSa na kiran ku domin ku yi imani da Ubangijinku, kuma lalle Allah Ya karɓi alkawarinku (cewa za ku bauta Masa)? (Ku bauta Masa) idan kun kasance masu imani

    [9] Shi ne wanda ke sassaukar da ayoyi bayyanannu ga BawanSa, domin Ya fitar da ku daga duffai zuwa ga haske, kuma lalle Allah haƙiƙa Mai tausayi ne gare ku, Mai jin ƙai

    [10] Kuma me ya same ku, ba za ku ciyar ba domin ɗaukaka kalmar Allah, alhali kuwa gadon sammai da ƙasa na Allah ne? Wanda ya ciyar a gabanin cin nasara, kuma ya yi yaƙi daga cikinku, ba ya zama daidai (da wanda bai yi haka ba). waɗancan ne mafifita girman daraja bisa ga waɗanda suka ciyar daga baya kuma suka yi yaƙi. Kuma dukansu Allah Ya yi musu wa'adi da (sakamako) mai kyau, kuma Allah Masani ne ga abin da kuke aikatawa

    [11] Wane ne wanda zai ranta wa Allah rance mai kyau domin Allah Ya ninka masa shi (a duniya) kuma Yana da wani sakamako na karimci (a Lahira)

    [12] Ranar da za ka ga muminai maza da muminai mata haskensu na tafiya a gaba gare su, da kuma dama gare su. (Ana ce musu) "Bushararku a yau, ita ce gidajen Aljanna." Ruwa na gudana daga ƙarƙashinsu suna masu dawwama a cikinsu. Wannan, shi ne babban rabo mai girma

    [13] Ranar da munafikai maza da munafikai mata ke cewa waɗanda suka yi imani: "Ku dube mu, mu yi makamashi daga haskenku!" A ce (musu): "Ku koma a bayanku, domin ku nemo wani haske." Sai a danne a tsakaninsu da wani garu yana da wani ƙyaure, a cikinsa nan rahama take, kuma a bayansa daga wajensa azaba take

    [14] Suna kiran su, "Ashe, ba tare muke da ku ba?" Su ce: "I, amma ku, kun fitini kanku, kuma kun yi jiran wata masifa, kuma kunyi shakka, kuma waɗansu gurace-gurace sun ruɗe ku, har umurnin Allah ya je muku, kumamaruɗi ya ruɗe ku game da Allah

    [15] To, a yau ba za a karɓi fansa daga gare ku ba. Kuma ba za a karɓa daga waɗanda suka kafirta ba. Makomarku wuta ce, ita ce mai dacewa da ku, kuma makomarku ɗin nan ta munana

    [16] Shin, lokaci bai yi ba ga wa ɗanda suka yi imani zukatansu su yi tawalu'i ga ambaton Allah da abin da ya sauka daga gaskiya? Kada su kasance kamar waɗanda aka bai wa littafi a gabanin haka, sai zamani ya yi tsawo a kansu, saboda haka zukatansu suka ƙeƙashe, kuma masu yawa daga cikinsu fasiƙai ne

    [17] Ku sani cewa Allah Yana rayar da ƙasa a bayan mutuwarta. Lalle Mun bayyanamuku ayoyi da fatan za ku yi hankali

    [18] Lalle masu gaskatawa maza da masu gaskatawa mata, kuma suka ranta wa Allah rance mai kyau, ana riɓanya musu, kuma suna da wani sakamako na karimci

    [19] Kuma waɗanda suka yi imani da Allah da MazanninSa waɗannan su ne kamalar gaskatawa kuma su ne masu shahada awurin Ubangjinsu. suna da sakamakonsu da haskensu. waɗanda suka kafirta kuma suka ƙaryata game da ayoyinMu, waɗannan su ne'yan Jahim

    [20] Ku sani cewa rayuwar duniya wasa ɗai ce da shagala da ƙawa da alafahri a tsakaninku da gasar wadata ta dukiya da ɗiya, kamar misalin shuka wadda yabanyarta ta bayar da sha'awa ga manoma, sa'an nan ta ƙeƙashe, har ka ganta ta zama rawaya sa'an nan ta koma rauno. Kuma, alamra akwai azaba mai tsanani da gafara daga Allah da yarda. Kuma rayuwar duniya ba ta zama ba face ɗan jin daɗin ruɗi kawai

    [21] Ku yi tsere zuwa ga (neman) gafara daga Ubangjinku, da Aljanna faɗinta kamar faɗin sama da ƙasa ne, an yi tattalinta domin waɗanda suka yi imani da Allah da ManzanninSa. Wannan falalar Allah ce, Yana bayar da ita ga wanda Ya so. Kuma Allah Mai falala ne Mai girma

    [22] Wata masifa ba za ta auku ba a cikin ƙasa ko a cikin rayukanku face tana a cikin littafi a gabanin Mu halitta ta. Lalle wannan, ga Allah, mai sauƙi ne

    [23] Domin kada ku yi baƙin ciki a kan abin da ya kuɓuce muku, kuma kada ku yi mumar alfahari da abin da Ya ba ku. Kuma Allah ba Ya son dukkan mai taƙama, mai alfahari

    [24] Watau, waɗanda ke yin rowa, kuma suna umumin mutane da yin rowa. Kuma wanda ya juya baya, to, lalle Allah, Shi ne kaɗai Mawadaci, Godadde

    [25] Haƙiƙa, lalle Mun aiko ManzanninMu da hujjoji bayyanannu, kuma Muka saukar da Littafi da sikeli tare da su domin mutane su tsayu da adalci, kuma Mun saukar da baƙin ƙarfe, a cikinsa akwai cutarwa mai tsanani da amfani ga mutane, kuma domin Allah Ya san mai taimakonSa da ManzanninSa a fake. Lalle ne Allah Mai ƙarfi ne, Mabuwayi

    [26] Kuma haƙiƙa, lalle, Mun aiki Nuhu da Ibrahim, kuma Muka sanya Annabci da Littifi a cikin zuriyarsu; daga cikinsu akwai mai neman shiryuwa, kuma masu yawa daga cikinsu fasiƙai ne

    [27] Sa'an nan Muka biyar a bayansu da ManzanninMu; kuma Muka biyar da isa ɗan Maryama, kuma Muka ba shi Linjila kuma Muka sanya tausayi da rahama a cikin zukatan waɗanda suka bi shi, da ruhbananci wanda suka ƙaga, shi, ba Mu rubuta shi ba a kansu, face dai (Mun rubuta musu neman yardar Allah, sa'an nan ba su tsare shi haƙƙin tsarewarsa ba, saboda haka Muka bai wa waɗanda suka yi imani daga cikinsu sakamakonsu kuma masu yawa daga cikinsu fasiƙai ne)

    [28] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku bi Allah da taƙawa, ku yi imani da ManzonSa Ya ba ku rabo biyu daga rahamarSa, kuma Ya sanya muku wani haske wanda kuke yin tafiya da shi, kuma Ya gafarta muku. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai rahama

    [29] Domin kada mutanen Littafi su san cewa lalle ba su da ikon yi ga kome na falalar Allah, kuma ita falalar ga hannun Allah kawai take, Yana bayar da ita ga wanda Ya so (wannan jahilci ya hana su imani). Kuma Al1ah Mai falala ne mai girma

    Al-Mujadila

    Surah 58

    [1] Lalle Alla Ya ji maganar wadda ke yi maka jayayya game da mijinta, tana kai ƙara ga Allah, kuma Allah na jin muhawararku. Lalle Allah Mai ji ne, Mai gani

    [2] Waɗanda ke yin zihari daga cikinku game da matansu, sumatan nan ba uwayensu ba ne, babu uwayensu face waɗanda suka haife su. Lalle su, suna faɗar abin ƙyama na magana da ƙarya, kuma lalle Allah haƙiƙa Mai yafewa ne, Mai gafara

    [3] Waɗanda ke yin zihari game da matansu, sa'an nan su koma wa abin da suka faɗa, to, akwai 'yanta wuya a gabanin su shafi juna. Wannan ana yi muku wa'azi da shi. Kuma Allah Mai ƙididdigewa ne ga abin da kuke aikatawa

    [4] To, wanda bai samu ba, sai azumin wata biyu jere a gabanin su shafi juna, sa'an nan wanda bai sami ikon yi ba, to, sai ciyar da miskinai sittin. Wannan domin ku yi imani da Allah da Manzonsa. Kuma waɗannan hukunce-hukunce haddodin Allah ne. Kuma kafirai, suna da azaba mai raɗadi

    [5] Lalle waɗanda ke saɓa wa Allah da ManzonSa, an wulakanta su kamar yadda aka wulakantar da waɗanda ke a gabaninsu, kuma lalle Mun saukar da ayoyi bayyanannu, kuma kafirai na da azaba mai wulakantawa

    [6] Ranar da Allah zai tayar da su gaba ɗaya, sa'an nan Ya ba su labari game da abin da suka aikata, Allah Ya lissafa shi, alhali kuwa su, sun manta da shi, kuma a kan kome Allah Halartacce ne

    [7] Ashe, ba ka ga cewa lalle Allah Yana sane da abin da yake a cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa ba? Wata ganawa ta mutum uku ba za ta kasance ba face Allah Shi ne na huɗu ɗinta, kuma babu ta mutum biyar face Shi ne na shida ɗinta, kuma babu abin da ya kasa wannan kuma babu abin da yake mafi yawa face Shi Yana tare da su duk inda suka kasance, sa'an nan Ya ba su labari game da abin da suka aikata a Ranar ¡iyama. Lalle Allah Masani ne ga dukkan kome

    [8] Ashe, ba ka ga waɗanda aka hane su ba daga ganawar, sa'an nan suna koma wa abin da aka hane su daga gare shi, kuma suna ganawa game da zunubi da zalunci da saɓa wa Manzon Allah, kuma idan sun zo maka sai su gasihe ka da abin da Allah bai gaishe ka da shi ba, kuma suna cewa a cikin zukatansu: "Don me Allah ba Ya yi mana azaba saboda abin da muke faɗi?" Jahannama ita ce mai isarsu, za su shigeta. Saboda haka makomarsu ta munana

    [9] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan za ku yi ganawa, to, kada ku gana game da zunubi da zalunci da saɓa wa Manzon Allah, kuma ku yi ganawa game da alheri da taƙawa. Ku bi Allah da taƙawa wanda za a tattara ku zuwa gare, shi

    [10] Ganawar daga Shaiɗan take kawai domin ya munana wa waɗanda suka yi imani, alhali kuwa ba zai iya cutar su da kome ba face da iznin Allah. Kuma sai muminai su dogara ga Allah

    [11] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan an ce muka, "Ku yalwata a cikin majalisai," to, ku yalwata, sai Allah Ya yalwata muku, kuma idan an ce muku, "Ku tashi" to, ku tashi. Allah na ɗaukaka waɗanda suka yi imani daga cikinku da waɗanda aka bai wa ilim wasu darajoji masu yawa, kuma, Allah Mai ƙididdigewa ne ga dukan kome

    [12] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan za ku ganawa da Manzon Allah, to, ku gabatar da 'yar sadaka a gabanin ganawarku, wannan ne mafi alheri a gare ku, kuma mafi tsarki. Sai idan ba ku sami (abin sadakar ba), to, lalle, Allah, Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [13] Ashe, kun ji tsoron ku gabatar da sadakoki a gabanin ganawarku? To, idan ba ku aikata ba, kuma Allah Ya komo da ku zuwa ga sauƙi, sai ku tsai da salla, kuma ku bayar da zakka, kuma ku yi ɗa'a ga Allah da ManzonSa. Kuma Allah ne Mai ƙididdigewa ga abin da kuke aikatawa

    [14] Ashe, baka ga waɗanda suka jiɓinci waɗansu mutane da Allah Ya yi hushi a kansu ba, ba su cikinku, kuma ba su a cikinsu kuma suna rantsuwa a kan ƙarya, alhali kuwa suna sane

    [15] Allah Ya yi musu tattalin azaba mai tsanani. Lalle su abin da suka kasance suna aikatawa ya munana

    [16] Sun riƙi rantsuwowinsu garkuwa, saboda haka suka kange (muminai) daga jihadin ɗaukaka tafarkin Allah. To, suna da azaba mai wulakantawa

    [17] Dukiyoyinsu ba su wadatar musu kome ba daga Allah, haka kuma ɗiyansu. Waɗannan 'yan wuta ne. Su, masu dawwama ne a cikinta

    [18] Ranar da Allah ke tayar da su gaba ɗaya, sai su yi Masa rantsuwa kamar yadda suke yi muku rantsuwa (a nan duniya) kuma suna zaton cewa su a kan wani abu suke! To, lalle su, su ne maƙaryata

    [19] Shaiɗan ya rinjaya a kansu, sai ya mantar da su ambaton Allah, waɗannan ƙungiyar Shaiɗan ne. To, lalle ƙungiyar Shaiɗan, su ne masu hasara

    [20] Lalle, waɗanda ke saɓa wa Allah da ManzonSa waɗannan suna a cikin (mutane) mafi ƙasƙanci

    [21] Allah Ya rubuta cewa," Lalle zan rinjaya, Ni da ManzanniNa." Lalle Allah Mai ƙarfi ne, Mabuwayi

    [22] Ba za ka sami mutane masu yin imani da Allah da RanarLahira suna soyayya da wanda ya saɓa wa Allah da ManzonSa ba, ko da sun kasance ubanninsu ne, ko ɗiyansu ko 'yan'uwansu, ko danginsu. waɗannan Allah Ya rubuta imani a cikin zukatansu, kuma Ya ƙarfafa su da wani ruhi daga gare Shi, kuma zai shigar da su a gidajen Aljanna, ƙoramu na gudana ƙarƙashinsu suna masu dawwama a cikinsu. Allah Ya yarda da su, kuma sun yarda da Shi. Waɗannan ƙungiyar Allah ne. To, lalle ƙungiyar Allah su ne masu babban rabo

    Al-Hashr

    Surah 59

    [1] Abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa ya yi tasbihi ga Allah, alhali kuwa, Shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [2] Shi ne wanda Ya fitar da waɗanda suka kafirta daga Mazowa Littafi, daga gidajensu da kora ta farko. Ba ku yi zaton suna fita ba, kuma sun tabbata cewa ganuwowinsu masu tsare su ne daga Allah, sai Allah Ya je musu daga wajen da ba su yi zato ba, kuma Ya jefa tsoro a cikin zukatansu, suna rushe gidajensu da hannayensu da kuma hannayen muminai. To, ku lura fa, ya masu basirori

    [3] Kuma ba domin Allah Ya rubuta musu korar ba, da Ya azabta su a cikin duniya, kuma a Lahira suna da azabar wuta

    [4] Wannan domin lalle su, sun saɓa wa Allah, da ManzonSa alhali kuwa wanda ya saɓa wa Allah, to, lalle Allah, Mai tsananin uƙuba ne

    [5] Abin da kuka sare na dabiniya, ko kuka bar ta tsaye a kan asallanta, to da iznin Allah ne, kuma domin Ya wulakanta fasiƙai

    [6] Kuma abin da Allah Ya sanya ya zama ganima ga ManzonSa, daga gare su, to, ba ku yi hari a kansa da dawaki ko raƙuma ba amma Allah ne Ya rinjayar da ManzanninSa a kan wanda Yake so, kuma Allah Mai ikon yi ne a kan kome

    [7] Abin da Allah Ya sanya shi ganima ga ManzonSa dagamutanen ƙauyukan nan, to, na Allah ne, kuma na ManzonSa ne kuma na masu dangantaka da marayu da miskinai da ɗan hanya (matafiyi) ne domin kada ya kasance abin shawagi a tsakanin mawadata daga cikinku kuma abin da Manzo ya ba ku, to, ku kama shi, kuma abin da ya hane ku, to, ku bar shi. Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle, Allah, Mai tsananin uƙuba ne

    [8] (Ku yi mamaki) Ga matalauta masu hijira waɗanda aka fitar daga gidajensu da dukiyoyinsu, suna neman falala daga Allah da kuma yarda, kuma suna taimakon Allah da ManzonSa! Waɗannan su ne masu gaskiya

    [9] Da waɗanda suka zaunar da gidajensu (ga Musulunci) kuma (suka zaɓi) imani, a gabanin zuwansu, suna son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma ba su tunanin wata bukata a cikin ƙirazansu daga abin da aka bai wa muhajirina, kuma suna fifita waɗansu a kan kawunansu, kuma ko da suna da wata larura. Wanda ya saɓa wa rowar ransa, to, waɗannan su ne masu babban rabo

    [10] Kuma waɗanda suka zo daga bayansu, suna cewa, "Ya Ubangijinmu! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga 'yan'uwanmu, waɗanda da suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani ƙulli a cikin zukatanmu ga waɗanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jin ƙai

    [11] Ashe, ba ka ga waɗanda suka yi munafinci ba, suna cewa ga 'yan'uwansu, waɗanda suka kafirta daga Mazowa Littafi, "Lalle idan an fitar da ku, lalle za mu fita tare da ku, kuma ba za mu yi ɗa'a ga kowa ba game da ku, har abada, kuma lalle idan an yaƙe ku, lalle za mu taimake ku haƙiƙatan?" Alhali kuwa Allah na shaidar cewa lalle su tabbas, maƙaryata ne

    [12] Lalle idan an fitar da su, ba za su fita tare da su ba kuma lalle idan an yaƙe su ba za su taimake su ba, kuma lalle idan sun taimake su lalle ne, haƙiƙatan, za su juyar da bayansu domin gudu, sa'an nan kuma ba za a taimake su ba

    [13] Lalle ku ne kuka fi bayar da firgita a cikin zukatansu bisa ga Allah, wannan kuwa domin su lalle waɗansu irin mutane ne da ba su ganewa

    [14] Ba su iya yaƙar ku gaba ɗaya, face a cikin garuruwa masu ganuwa da garuna, ko kuma daga bayan katangu. Yakinsu a tsakaninsu mai tsanani ne, kana zaton su a haɗe, alhali kuwa zukatansu dabam- dabam suke. Wannan kuwa domin su, lalle wasu irin mutane ne da ba su hankalta

    [15] Kamar misalin waɗanda ke a gabaninsu, ba da daɗewa ba, sun ɗanɗani kuɗar al'amarinsu, kuma suna da wata azaba mai raRaɗi

    [16] Kamar misalin Shaiɗan a lokacin da yake ce wa mutum, "Ka kafirta," To, a lokacin da ya kafirta ɗin, ya ce (masa): "Lalle babu ruwana da kai. Lalle ni ina tsoron Allah Ubangijin halitta

    [17] Sai aƙibarsu ta kasance cewa su biyun duka suna a cikin wuta, suna masu dawwama a cikinta. "Kuma wannan shi ne sakamakon masu zalunci

    [18] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku bi Allah da taƙawa kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma ku bi Allah da taƙawa. lalle Allah, Mai ƙididdigewa ne ga abin da kuke aikatawa

    [19] Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka manta Allah shi kuma Ya mantar da su rayu, kansu. Waɗannan su ne fasiƙai

    [20] Yan Wuta da 'yan Aljanna ba su daidaita. 'Yan Aljanna, su ne masu babban rabo

    [21] Da Mun saukar da wannan Alƙur'ani a kan dutse, da lalle ka ga dutsen yana mai tawali'u, mai tsattsagewa saboda tsoron Allah, kuma waɗancan misalai Muna bayyana su ne ga mutane, da fatan za su yi tunani

    [22] (Wanda Ya saukar da Alƙur'ani) Shi ne Allah, wanda babu wani abin bautawa face Shi Masanin fake da bayyane, Shi ne Mai rahama, Mai jin ƙai

    [23] Shi ne Allah, wanda babu abin bautawa face shi, Mai mulki, Mai tsarki, Aminci, Mai amintarwa, Mai Tsarewa, Mabuwayi, Mai t஛astawa Mai nuna isa, tsarki ya tabbata a gare Shi daga abin da suke yi na shirki da Shi

    [24] Shi ne Allah, Mai halitta, Mai ginawa, Mai surantawa. Yana da sunaye masu kyau, abin da ke a cikin sammai da ƙasa suna tsarkake Shi, kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    Al-Mumtahana

    Surah 60

    [1] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku riƙi maƙiyiNa kuma maƙiyinku masoyi, 845. Kuna jefa soyayya zuwa gare su, alhali kuwa haƙiƙa sun kafirta da abin da ya zo muku, na gaskiya, suna fitar da Manzon Allah tare da ku (daga gidajenku) domin kun yi imani da Allah, Ubangijinku, idan kun fito domin jihadi saboda ɗaukaka kalmaTa da neman yardaTa, kuna asirta soyayya zuwa gare su alhali kuwa Ni ne Mafi sani ga abin da kuka ɓoye da abin da kuka bayyana, kuma duk wanda ya aikata shi daga cikinku, to, lalle ya ɓace daga tsakar hanya

    [2] Idan sun kama ku, za su kasance maƙiya a gare ku, kuma su shimfiɗa hannuwansu da harsunan gurin ku kafirta

    [3] Zumuntarku ba za ta amfane ku ba, haka kuma ɗiyanku, a Ranar Kiyama. (Allah) zai rarrabe tsakaninku, kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatawa

    [4] Lalle abin koyi mai kyau ya kasance a gare ku game da Ibrahim da waɗanda ke tare da shi a lokacin da suka ce wa mutnensu, "Lalle mu babu ruwanmu daku, kuma da abin da kuke bautawa, baicin Allah, mun fita batunku, kuma ƙiyayya da jiyewa juna sun bayyana a tsakaninmu, sai kun yi imani da Allah Shi kaɗai." Face maganar Ibrahim ga ubansa (da yace), "Lalle za ni nema maka gafara kuma ban mallaki kome ba daga Allah saboda kai." "Ya Ubangijinmu! A gare Ka muka dogara, kuma gare Ka muka mayar da al' amuranmu, kuma zuwa gare Ka makoma take

    [5] Ya Ubangijinmu! Kada Ka sanya mu fitina ga waɗanda suka kafirta, kuma Ka yi gafara gare Mu. Ya Ubangijinmu! Kai ne Mabuwayi, Mai hikima

    [6] Lalle, haƙiƙa, abin koyi mai kyau ya kasance a gare ku daga cikinsu, ga wanda ya kasance yana fatan (rahamar) Allah da Ranar Lahira, kuma wanda ya juya baya, to, lalle Allah, Shi ne wadatacce, Godadde

    [7] Ana tsammanin Allah Ya sanya, a tsakaninku da tsakanin waɗanda kuka yi ƙiyayya da su, wata soyaya daga gare su, kuma Allah Mai ikon yi ne, kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [8] Allah ba Ya hana ku, daga waɗanda ba su yaƙe ku ba saboda addini kuma ba su fitar da ku ba daga gidajenku, ga ku kyautata musu kuma ku yi musu adalci. Lalle Allah Yana son masu adalci

    [9] Allah Yana hana ku kawai daga waɗanda suka yake ku saboda addini kuma suka fitar da ku daga gidajenku, kuma suka taimaki juna ga fitar da ku, karku jiɓince su, kuma wanda ya jiɓince su, to waɗannan su ne azzalumai

    [10] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan mata muminai suka zo muku, suna masu hijira, to, ku jarraba su. Allah Shi ne mafi sani ga imaninsu. To, idan kun san su muminai ne, kada ku mayar da su zuwa ga kafirai. Su matan ba su halatta ga aurensu, su kuma kafiran ba su halatta ga auren matan. Ku ba su abin da suka ɓatar na dukiya. Kuma babu laifi a kanku ga ku aure su idan kun ba su sadakokinsu. Kuma kada ku riƙe auren mata kafirai, kuma ku tambayi abin da kuka ɓatar daga dukiya, su kuma kafirai su tambayi abin da suka ɓatar na dukiya. Wannan hukuncin Allah ne Yana hukunci a tsakaninku. kuma Allah, Masani ne, Mai hikima

    [11] Kuma idan wani abu ya kuɓuce muku daga matanku zuwa ga kafirai sa'an nan kuma kuka ɗauki fansa, to, sai ku bai wa waɗanda matansu suka tafi kwatankwacin abin da suka ɓatar na dukiya. Kuma ku yi biyayya da taƙawa ga Allah wanda kuke masu imani da Shi, Shi Kaɗai

    [12] Ya kai Annabi! Idan mata muminai suka zo maka suna yi maka mubaya'a a kan ba za su yi shirki da Allah ba ga kome, kuma ba su yin sata, kuma ba su yin zina, kuma ba su kashe, ya'yansu, kuma ba su zuwa da ƙarya da suke ƙirƙirawa a tsakanin hannuwansu da ƙafafunsu kuma ba su saɓa maka ga wani abu da aka sani na shari'a, to, ka karɓi mubaya'arsu, kuma ka nemi Allah Ya gafarta musu. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [13] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada ku jiɓinci waɗansu mutane da Allah Ya yi hushi a kansu. Lalle sun yanke tsammani daga (rahamar) Lahira, kamar yadda kafirai suka yanke tsammani daga mazowa kaburbura

    As-Saff

    Surah 61

    [1] Abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa ya yi tasbihi ga Allah alhali kuwa, Shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [2] Ya ku waɗanda suka yi imani! Don me kuke faɗin abin da ba ku aikatawa

    [3] Ya girma ga zama abin ƙyama awurin Allah, ku faɗi abin da ba ku aikatawa

    [4] Lalle Allah Yana son waɗanda ke yin yaƙi domin ɗaukaka KalmarSa, a cikin safu kamar su gini ne mai ɗamfarar juna

    [5] Kuma a lokacin da Musa ya ce wa mutanensa: "Ya mutanena! saboda me kuke cutar da ni, alhali kuwa lalle kun sani cewa lalle ni Manzon Al1ah ne zuwa gare ku?" To, a lokacin da suka karkace, Allah Ya karkatar da zukatansu. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane fasiƙai

    [6] Kuma a lokacin da Isa ɗan Maryayama ya ce: "Ya BaniIsra'ila! Lalle ni Manzon Allah ne zuwa gare ku, mai gaskata abin da ke gaba gare ni na Attaura, kuma mai bayar da bushara da wani Manzo da ke zuwa a bayana, SunasaAhmad (Mashayabo)." To, a lokacin da ya je musu da hujjoji, suka ce: "Wannan sihiri ne, bayyananne

    [7] Kuma wane ne mafi zalunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ya Jingina ta ga Allah, alhali kuwa shi, ana kiran sa zuwa ga Musulunci? Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [8] Suna nufin su bice hasken Allah da bakunansu alhali kuwa Allah Mai kammala haskenSa ne, kuma ko da kafirai sun ƙi

    [9] Shi ne wanda Ya aiko ManzonSa da shiriya da addinin gakiya, domin Ya ɗaukaka shi a kan wani addini dukansa kuma ko da mushirikai sun ƙi

    [10] Ya ku waɗanda suka yi imani! Shin, in nuna muku wani fatauci wanda zai tsarshe ku daga wata azaba mai raɗaɗi

    [11] Ku yi imani da Allah da ManzonSa, kuma ku yi jihadi ga ɗaukaka kalmar Allah game da dukiyoyinku da rayukanku. Wannan shi ne alheri a gare ku idan kun kasance kuna da sani

    [12] Sai Allah Ya gafarta muku zunubbanku, kuma Ya shigar da ku gidajen Aljanna, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu, da waɗansu ɗakuna masu daɗi a cikin gidajen Aljannar zama. Wannan shi ne babban rabo, mai girma

    [13] Da wata (falala) da yake kuna son ta; taimako daga Allah da cin nasara wanda yake kusa. Kuma ka yi bushara ga muminai

    [14] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku kasance mataimakan Allah kamar abin da Isa ɗanMaryama ya ce ga Hawariyawa, "Waɗanne ne mataimakana zuwa ga (aikin) Allah?" Sai wata ƙungiya daga Bani Isra'ila ta yi imani, kuma wata ƙungiya ta kafirta. Sai muka ƙarfafa waɗanda suka yi imani a kan maƙiyansu, saboda haka suka wayi gari marinjaya

    Al-Jumu'a

    Surah 62

    [1] Abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin kasa suna tasbihi ga Allah, Mamallaki, Mai tsarki' Mabuwayi, Mai hikima

    [2] Shi ne wanda Ya aika, a cikin mabiya al'adu, wani Manzo daga gare su yana karanta ayoyinSa a kansu, kuma yana tsarkake su, kuma yana sanar da su littafin da hikimarsa ko da yake sun kasance daga gabaninsa lalle suna a cikin ɓata bayyananna

    [3] Da waɗansu mutane daga gare su, ba su i da riskuwa da su ba, alhali kuwa shi ne Mabuwayi, Mai hikima

    [4] Waccan wata falalar Allah ce Yana bayar da ita ga wanda Yake so. Kuma Allah ne Ma'abucin dukan falala mai girma

    [5] Misalin waɗanda aka ɗora wa ɗaukar Attaura sa'an nan ba su ɗauke ta ba, kamar misalin jaki ne Yana ɗaukar littattafai. Tir da misalin mutanen nan da suka ƙaryata game da ayoyin Allah! Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai

    [6] Ka ce: "Ya ku waɗandasuka tuba (Yahudu)! Idan kun riya cewa ku ne zaɓaɓɓun Allah ba sauran mutane ba, sai ku yi gurin mutuwa idan kun kasance masu gaskiya

    [7] Kuma ba za su yi gurinta ba har abada saboda abin da hannayen su suka gabatar. Kuma Allah ne masani ga azzalumai

    [8] Ka ce "Lalle mutuwar nan da kuke gudu daga gareta, to, lalle ita mai haɗuwa da ku ce sa'an nan kuma ana mayar da ku zuwa ga masanin fake da bayyane, domin Ya baku labari game da abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [9] Ya ku waɗanda suka yi imani! Idan anyi kira zuwa ga salla a ranar Jumu'a, sai ku yi aiki zuwa ga ambaton Allah, kuma ku bar ciniki. Wancan ɗinku ne mafi alheri a gare ku idan kun kasance kuna sani

    [10] Sa'an nan idan an ƙare salla, Sai ku watsu a cikin ƙasa kuma ku nema daga falalar Allah, kuma ku ambaci sunan Allah da yawa ɗammaninku, ku sami babban rabo

    [11] Kuma idan suka ga wani fatauci ko kuma wani wasan shagala, sai su yi ruguguwar fita zuwa gare su, kuma su bar ka kana tsaye. Ka ce: "Abin da yake a wurin Allah ne mafi alheri daga fataucin, alhali kuwa Allah ne Mafi alherinmasu arzutawa

    Al-Munafiqun

    Surah 63

    [1] Idan munafukai suka je maka suka ce: "Mune shaidar lalle kai haƙiƙa Manzon Allah ne," Kuma Allah Yana sane da lalle Kai, haƙiƙa ManzonSa ne, kuma Allah Yana shaida lalle munafukan haƙiƙa, maƙaryata ne

    [2] Sun riƙi rantsuwowinsu garkuwa, sai suka taushe daga tafarkin Allah. Lalle su abin da suka kasance suna aikatawa ya munana

    [3] Wancan, domin lalle su, sun yi imani, sa'an nan kuma suka kafirta, sai aka yunƙe a kan zukatansu. Saboda su, ba su fahimta

    [4] Kuma idan ka gan su, sai jikunansu su ba ka sha'awa kuma idan sun faɗa, za ka saurara ga maganarsu. Kamar dai su ƙyami ne wanda aka jingine. Suna zaton kowace tsawa a kansu take. Su ne maƙiyan, sai ka yi saunarsu. Allah Ya la'ane su. Yaya ake karkatar da su

    [5] Kuma idan aka ce musu "Ku zo Manzon Allah ya nema maku gafara," Sai su gyaɗa kawunansu, kuma ka gan su suna kangewa, alhali kuwa suna masu girman kai

    [6] Daidai ne a kansu, ka nema musu gafara ko ba ka nemamusu ba. faufau Allah ba zai gafarta musu ba. Lalle Allah, ba zai shiryar da mutane fasiƙai ba

    [7] Su ne waɗanda ke cewa "Kada ku ciyar a kan wanda ke wurin Manzon Allah har su watse," alhali kuwa taskokin sammai da ƙasa ga Allah suke kuma amma munafukai ba su fahimta

    [8] Suna cewa "Lalle ne idan mun koma zuwa Madinar, haƙiƙa mafi rinjaya zai fitar da mafi ƙasƙanta daga gare ta, alhali kuwa rinjayar ga Allah take kuma da ManzonSa, kuma da muminai, kuma amma munafikai ba su sani ba

    [9] Ya ku waɗanda suka yi imani! Kada dukiyoyinku da ɗiyanku su shagaltar da ku daga ambaton Allah. Kuma wanda ya yi haka, to, waɗannan su ne masu hasara

    [10] Kuma ku ciyar daga abin da Muka azurta ku daga gabanin mutuwa ta je wa ɗayanku har ya ce: "Ya Ubangijina! Don me ba Ka yi mini jinkiri ba zuwa ga wani ajali makusanci domin in gaskata kuma in kasance daga salihai

    [11] Kuma Allah ba zai jinkirta wa wani rai ba idan ajalinsa ya je. Kuma Allah Masani ne ga abin da suke aikatawa

    At-Taghabun

    Surah 64

    [1] Abin da yake a cikin sammai da wanda yake a cikin ƙasa suna tasbihi ga Allah. Gare Shi mulki yake, kuma gare Shi godiya take. Kuma Shi, a kan kome, Mai ikon yi ne

    [2] Shi ne wanda Ya halitta ku. Sa'an nan daga gare ku akwai kafiri kuma daga gare ku akwai mumini. Kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatawa

    [3] Ya halitta sammai da ƙasa da abin da yake hakkinSa. Kuma Ya suranta ku, sa'an nan Ya kyautata surorinku. Kuma zuwa gare Shi makoma take

    [4] Yana sanin abin da ke a cikin sammai da ƙasa. Kuma Yana sanin abin da kuke boyewa da abin da kuke bayyanawa. Kuma Allah Masani ne ga abin da ke cikin ƙiraza

    [5] Shin, babban labari bai je muku ba na waɗanda suka kafirta daga gabani, sai suka ɗanɗani uƙubar al'amarinsu kuma suna da wata azaba mai raɗaɗi

    [6] Wancan saboda lalle su Manzanninsu sun kasance suna je musu da hujjoji bayyanannu, sai suka ce: "Ashe, wasu mutane za su shiryar da mu?" Sai suka kafirta kuma suka juya baya, kuma Allah Ya wadatu (daga gare su). Kuma Allah wadatacce ne, Godadde

    [7] Waɗanda suka kafirta sun riya cewa ba za a tayar da su ba. Ka ce: "Ni, ina rantsuwa da Ubangijina. Lalle za a tayar da ku haƙiƙatan, sa'an nan kuma lalle ana ba ku labari game da abin da kuka aikata. Kuma wannan ga Allah mai sauƙi ne

    [8] Saboda haka ku yi imani da Allah da ManzonSa da hasken nan da Muka saukar. Kuma Allah, ga abin da kuke aikatawa, Mai labartawa ne

    [9] A ranar da Yake tattara ku domin ranar taruwa. Wancan ne ranar kamunga. Kuma wanda ya yi imani da Allah, kuma ya aikata aikin ƙwarai, zai kankare masa munanan ayyukansa, kuma Yashigar da shi gidajen Aljanna, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu har abada. Wannan ne babban rabo mai girma

    [10] Kuma waɗanda suka kafirta, kuma suka ƙaryata game da ayoyinMu, waɗannan sune'yan wuta, suna madawwama a cikinta. Kuma tir da makoma, ita

    [11] Wata masifa ba za ta samu ba face da iznin Allah. Kuma wanda ya yi imani da Allah, Allah zai shiryar da zuciyarsa. Kuma Allah, ga dukan kome, Masani ne

    [12] Kuma ku yi ɗa'a ga Allah, kuma ku yi ɗa'a ga Manzo. Sa'an nan idan kun juya baya, to, abin sani kawai, akwai iyarwa bayyananna a kan ManzonMu

    [13] Allah babu wani abin bauta wa face Shi. Kuma ga Allah, sai muminai su dogara

    [14] Ya ku waɗanda suka yi imani! Lalle ne daga matanku da ɗiyanku akwai wani maƙiyi a gare ku, sai ku yi saunarsu. Kuma idan kuka yafe, kuma kuka kau da kai, kuma kuka gafarta, to, lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [15] Dukiyoyinku da ɗiyanku fitina ɗai ne. Kuma Allah, a wurinSa akwai wani sakamako mai girma

    [16] Sai ku bi Allah da taƙawa gwargwadon abin da kuka sami iko. Kuma ku saurara kuma ku yi ɗa'a, kuma ku ciyar, ya fi zama alheri gare ku. Kuma wandaya saɓa wa rowar ransa, to, waɗannan su ne masu babban rabo

    [17] Idan kun bai wa Allah rance, rance mai kyau, (Allah) zai ninka shi a gare ku kuma Ya gafarta muku. Kuma Allah Mai yawan godiya ne, Mai haƙuri

    [18] Shi ne Masanin fake da bayyane, Mabuwayi, Mai hikima

    At-Talaq

    Surah 65

    [1] Ya kai Annabi! Idan kun saki mata, sai ku sake su ga iddarsu, kuma ku ƙididdige iddar. Kuma ku bi Allah Ubangijinku da taƙawa. Kada ku fitar da su daga gidajensu, kuma kada su fita face idan suna zuwa da wata alfasha bayyananna. Kuma waɗancan iyakokin Allah ne. Kuma wanda ya ƙetare iyakokin Allah, to, lalle ya zalunci kansa. Ba ka sani ba ɗammanin Allah zai fitar da wani al'amari a bayan haka

    [2] Sa'an nan idan sun isa ga ajalinsu (na idda) sai ku riƙe su da abin da aka sani ko ku rabu da su da abin da aka sani kuma ku shaidar da masu adalci biyu daga gare ku. Kuma ku tsayar da shaidar domin Allah. Wancan ɗinku ana yin wa'azi da shi ga wanda ya kasance yana yin imani da Allah da Ranar Lahira. Kuma wanda ya bi Allah da taƙawa, Allah zai sanya masa mafita

    [3] Kuma Ya arzuta shi daga inda ba ya zato. Kuma wanda ya dogara ga Allah, to, Allah ne Ma'ishinsa. Lalle Allah Mai iyar da umurninSa ne. Haƙiƙa Allah Ya sanyama'auni ga dukan kome

    [4] Kuma waɗanda suka yanke ɗammani daga haila daga matanku, idan kun yi shakka, to, iddarsu wata uku ce da waɗanda ba su yi haila ba. Kuma ma'abuta cikinna ajalinsu, (shi ne) cewa su haifi cikinnansu. Kuma wanda ya bi Allah da taƙawa, (Allah) zai sanya masa wani sauƙi daga al'amarinsa

    [5] Wancan umurnin Allah ne, Ya saukar da shi zuwa gare ku. Kuma wanda ya bi Allah da taƙawa, Allah zai kankare masa munanan ayyukansa, kuma Ya girmama masa sakamako

    [6] Ku zaunar da su daga inda kuka zaunar daga gwargwadon samunku. Kuma kada ku cuce su domin ku ƙuntata a kansu. Kuma idan sun kasance ma'abuta ciki, sai ku ciyar da su har su haifi cikinsu. Sa'an nan idan sun shayar da mama saboda ku, sai ku ba su tsadodinsu. Kuma ku yi shawara a tsakaninku bisa abin da aka sani. Kuma idan kun nuna talauci to wata mace za ta shayar da mama saboda shi (mijin)

    [7] Sai mawadaci ya ciyar daga wadatarsa kuma wanda aka ƙuntata masa arzikinsa, to, sai ya ciyar daga abin da Allah Ya ba shi. Allah ba Ya kallafa wa wani rai face abin da Ya ba shi. Allah zai sanya sauƙi a bayan tsanani

    [8] Kuma da yawa daga alƙarya wadda ta yi tsaurin kai daga barin umurnin Ubangijinta da ManzanninSa, sai Muka yi mata hisabi, hisabi mai tsanani, kuma Muka, azabtar da ita azaba abar ƙyama

    [9] Sa'an nan ta ɗanɗana masifar al'amarinta. kuma ƙarshen al'amarinta ya kasance hasara

    [10] Allah Ya yi musu tattalin wata azaba mai tsanani. Saboda haka ku bi Allah da taƙawa, ya ma'abuta hankula, waɗanda suka yi imani! Haƙiƙa Allah Ya saukar da wata tunatarwa zuwa gare ku

    [11] Manzo, yana karatun ayoyin Allah bayyananu a kanku domin Ya fitar da waɗanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan ƙwarai daga duffai zuwa ga haske. Kuma wanda ya yi imani da Allah ya aikata aikin ƙwarai Allah zai shigar da shi gidajen Aljanna ƙoramu na gudana daga ƙarƙashnsu suna masu dawwama a cikinsu har abada. Haƙiƙa Allah Ya kyautata masa arziki

    [12] Allah, wanda Ya halitta bakwai ɗin sammai kuma daga ƙasa kwatankwacinsu, umuruinSa yana ta sauka a tsakaninsu domin ku san lalle Allah Mai ikon yi ne akan dukan kome, kuma lalle Allah, haƙiƙa Ya kewaye ga dukan kome da sani

    At-Tahrim

    Surah 66

    [1] Ya kai Annabi! Don me kake haramta abin da Allah Ya halatta maka, kana neman yardar matanka, alhali kuwa Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    [2] Haƙiƙa Allah ya faralta muku warware rantsuwoyinku, kuma Allah ne Mataimakinku kuma shi ne Masani, Mai hikima

    [3] Kuma a sa'ilin da Annabi ya asirta wani labari zuwa ga sashen matansa, to, a lokacin da ta ba da labari da shi. Kuma Allah Ya bayyana shi a gare shi, ya sanar da sashensa kuma ya kau da kai daga wani sashe. To, a lokacin da ya ba ta labari da shi, ta ce: "Wane ne ya gaya maka wannan?" Ya ce: "Masani, Mai labartawa, Ya gaya mini

    [4] Idan ku biyu kuka tuba zuwa ga Allah, to, haƙiƙa zukatanku sun karkata. Kuma idan kun taimaki juna a kansa to, lalle Allah Shi ne Mataimakinsa, da Jibrilu da salihan muminai. Kuma mala'iku a bayan wancan, mataimaka ne

    [5] Mai yiwuwa ne Ubangijinsa, idan ya sake ku, Ya musanya masa waɗansu matan aure mafiya alheri daga gare ku, Musulmai muminai masu tawali'u, masu tuba, masu ibada, masu, azumi, zawarori da 'yammata

    [6] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku kare wa kanku (da iyalinku wata wuta makamashinta mutane da duwatsu ne. A kanta akwai waɗansu mala'iku masu kauri, masu ƙarfi. Ba su saɓa wa Allah ga abin da Ya umurce su, kuma suna aikata abin da ake umunin su)

    [7] Ya ku waɗanda suka kafirta! Kada ku kawo wani uzuri a yau. Ana yi muku sakamakon abin da kuka kasance kuna aikatawa kawai ne

    [8] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku koma zuwa ga Allah komawar gaskiya. Mai yiwuwa Ubangjinku Ya kankare muku miyagun ayyukanku kuma Ya shigar da ku a gidajen Aljanna, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu a ranar da Allah ba Ya kunyatar da Annabi da wadanda suka yi imani tare da shi. Haskensu yana tafiya a gaba gare su da jihohin damansu, suna cewa, "Ya Ubangijiumu! Ka cika mana haskenmu, kuma Ka yi mana gafara. Lalle Kai, a kan dukkan kome, Ya kai Mai ikon yi ne

    [9] Ya kai Annabi! Ka yaki kafirai da munafwkai. Kuma ka tsananta a kansu. Kuma matattararsu Jahannama ce, kuma tir da makoma, ita

    [10] Allah Ya buga wani misali domin waɗanda suka kafirta: matar Nuhu da matar Luɗu, sun kasance a ƙarƙashin wasu bayi biyu daga bayinMu salihai, saisuka yaudare su, saboda haka ba su wadatar musu da kome daga Allah ba. Kuma aka ce: "Ku shiga, ku biyu, wuta tare da masu shiga

    [11] Kuma Allah Ya buga wani misali domin waɗanda suka yi imani; matar Fir'auna, sa'ad da ta ce "Ya Ubangiji! Ka gina mini wani gida a wurinKa a cikin Aljanna. Kuma Ka tsirar da ni daga Fir'auna da aikinsa. Kuma Ka tsirar da ni daga mutanen nan azzalumai

    [12] Da Maryama ɗiyar Imrana wadda ta tsare farjinta, sai Muka hura a cikinsa daga ruhinMu. Kuma ta gaskata game da ayoyin Ubangijinta da LittattafanSa alhali kuwa ta kasance daga masu tawali'u

    Al-Mulk

    Surah 67

    [1] (Allah), Wanda gudanar da mulki yake ga hannunSa, Ya tsarkaka, kuma Shi Mai iko ne a kan kome

    [2] Shi ne Wanda Ya halitta mutuwa da rayuwa domin Ya jarraba ku, Ya nuna waye daga cikinku ya fi kyawon aiki, Shi ne Mabuwayi, Mai gafara

    [3] Shi ne wanda Ya halitta sammai bakawi, ɗabaƙoƙi a kan juna, ba za ka ga goggociya ba a cikin halittar (Allah) Mai rahama. Ka sake dubawa, ko za ka ga wata ɓaraka

    [4] Sa'an nan ka sake maimaita, dubawa, ganinka zai komo maka, gajiyayye, ba da ganin wata naƙasa ba

    [5] Kuma lalle Mun ƙawata samar farko da fitillu, kuma Muka sanya su abin jifa ga shaiɗanu, kuma Muka yi musu tattalin azabar Sa'ir

    [6] Kuma waɗanda suka kafirce wa Ubangjinsu na da azabar Jahannama, ta munana ga zamanta makomarsu

    [7] Idan an jefa su a cikinta, sai su ji daga gare ta wata ƙara, tana tafasa

    [8] Tana kusa ta tsage domin hushi, ko da yaushe aka jefa wani ɓangaren jama'a a cikinta, matsaranta na tambayar su da cewa, "Wani mai gargaɗi bai je muku ba

    [9] Sai su ce: "I, lalle wani mai gargaɗi ya je mana, sai muka ƙaryata shi, muka ce, 'Allah bai saukar da kome ba, ba ku cikin kome sai ɓata babba

    [10] Kuma suka ce: "Da mun zamo muna saurare, ko muna da hankali, da ba mu kasance a cikin 'yan sa'ir ba

    [11] Wato su yi iƙrari da laifinsu. Allah Ya la'ani'yan sa'ir

    [12] Lalle waɗanda ke tsoron Ubangjinsu, a ɓoye, suna da wata gafara da wani sakamako mai girma

    [13] Kuma ku asirta maganarku ko ku bayyana ta, lalle shi, (Allah), Masani ne ga abin da ke cikin ƙiraza

    [14] Ashe, wanda Ya yi halitta ba zai iya saninta ba, alhali kuwa shi Mai tausasawa ne, kuma Mai labartawa

    [15] Shi, (Allah), Ya sanya muku ƙasa horarriya, sai ku tafi cikin sasanninta, kuma ku ci daga arzikinSa, kuma zuwa gare shi ne tashin yake

    [16] Shin ko kun amince cewa wanda ke cikin sama, ba zai iya shafe ƙasa tare da ku ba, sai ga ta tana mai girgiza

    [17] Ko kun amince cewa wanda ke cikin sama ba zai iya sako muku iskar guguwa ba? To, za ku san yadda (aƙibar) gargaɗiNa take

    [18] Lalle, waɗanda ke gabansu sun ƙaryata (manzanni). To, yaya (aƙibar) gargaɗiNa ta kasance

    [19] Ba za su yi dubi ba zuwa ga tsuntsaye a kansu, masu sanwa, kuma suna fiffikawa, babu mai riƙe da su sai (Allah), Mairahama? Lalle shi Mai gani ne ga dukan kome

    [20] Wane ne wanda zai zame muku mayaƙin da zai taimake ku, wanda ba (Allah) ba, Mai rahama? Kafirai ba su a cikin kome face ruɗu

    [21] Wane ne wanda zai ciyar da ku, idan (Allah) Ya riƙe arzikinSa? A'aha, sun yi zurfi cikin girman kai da tashin hankali

    [22] Shin, wanda ke tafiya a kife a kan fuskarsa ya fi zama a kan shiryuwa, ko kuwa wanda ke tafiya miƙe a kan hanya madaidaiciya

    [23] Ka ce: "(Allah) Shine Wanda Ya ƙaga halittarku, Ya sanya muku ji da gani da tunani, amman kaɗan ce ƙwarai godiyarku

    [24] Kuma kace "Shi ne Ya halitta ku daga ƙasa, kuma zuwa gareShi ne ake tashin ku

    [25] Kuma suna cewa, "Yaushe ne wannan alkawarin zai tabbata in dai kun kasance masu gaskiya ne ku

    [26] Ka ce: "Ilmin a wurin Allah kawai yake, kuma ni mai gargaɗi kawai ne, mai bayyana (gargaɗin)

    [27] To, lokacin da suka gan ta (azabar) a kusa, fuskokin waɗanda suka kafirta suka munana, kuma aka ce (musu) wannan shi ne abin da kuka zamo kuna ƙaryatawa

    [28] Ka ce musu "Idan Allah Ya halaka ni ni da wanda ke tare da ni, ko kuma, Ya yi mana rahama, to, wane ne zai tserar da kafirai daga wata azaba mai raɗaɗi

    [29] Ka ce: "Shi ne Mai rahama mun yi imani da Shi, gare Shi muka dogara, saboda haka za ku san wanda yake a cikin ɓata bayyananniya

    [30] Ka ce: "Ko kun gani, idan ruwanku ya wayi gari faƙaƙƙe, to, wane ne zai zo muku da ruwa wani mai ɓuɓɓuga

    Al-Qalam

    Surah 68

    [1] N. Na rantse da alƙalami da abin da (marubuta) suke rubutawa

    [2] Kai, saboda ni'imar Ubangijinka, ba mahaukaci kake ba

    [3] Kuma, lalle, haƙiƙa kana da ladar da ba ta yankewa

    [4] Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan halayen kirki, manya

    [5] Don haka, za ka gani, su kuma za su gani

    [6] Ga wanenku hauka take

    [7] Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga masu shiryuwa

    [8] Saboda haka kada ka bi masu ƙaryatawa

    [9] Suna fatar ka sassauta, su kuma su sassauta

    [10] Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walakantacce

    [11] Mai zunɗe, mai yawo da gulma

    [12] Mai hana alheri mai zalunci, mai zunubi

    [13] Mai girman kai, bayan haka kuma la'imi (ba ya son alheri)

    [14] Saboda ya kasance mai dukiya da ɗiya

    [15] Idan ana karanta masa ayoyinMu, sai ya ce: "Tatsuniyoyin mutanen farko ne

    [16] Za Mu yi masa alama a kan hanci

    [17] Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi masu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle za su girbe amfaninta, suna masu asubanci

    [18] Kuma (suka yi niyya), ba su ko togewa

    [19] Wani mai kewayawa daga Ubangijinka ya kewaya a kanta, (ya ƙone ta,) alhali suna barci

    [20] Sai ta wayi gari (baƙa ƙirin) kamar dare

    [21] Sai suka kirayi juna, suna masu yin asubanci

    [22] Cewa ku yi sammako ga amfanin gonarku, idan kun kasance masu girbewa

    [23] Sai suka tafi suna shawara a ɓoye (suna cewa)

    [24] Lalle kada wani miskini ya shigar muku ita a yau

    [25] Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rowa, matuƙar iyawarsu

    [26] Lokacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)

    [27] Ba haka ba, mu dai, an hana mu ne

    [28] Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, ya kamata ku tsarkake Allah

    [29] Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzalumai

    [30] Sai suka fuskanci juna, suna zargin kansu

    [31] Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mu ne muka kasance masu ƙetare iyaka

    [32] Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da ya fi ta. Lalle, mu (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, masu kwaɗayi ne

    [33] Haka dai azabar take, kuma lalle ne azabar Lahira ta fi girma, in da sun kasance za su iya ganewa

    [34] Lalle ne masu taƙawa na da a wurin Ubangijinsu, gidajen Aljanna na ni'ima

    [35] Shin ko za Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar masu laifi

    [36] Me ya same ku, yaya kuke yin hukunci (da haka)

    [37] Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantawa

    [38] Cewa kuna da, a cikinsa lalle (duk) abin da rayukanku suka zaɓa

    [39] Ko kuna (riƙe) da wasu rantsuwoyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Ranar ¡iyama, cewa lalle ne kuna da abin da kuke hukunta wa kanku

    [40] Ka tambaye su, wane, a cikinsu, ke lamuncewa ga samun wannan (hukuncin)

    [41] Ko suna da abokan tarewa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kawo abokan tarayyarsu, idan sun kasance masu gaskiya

    [42] Ranar da za a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujuda, sai ba za su iyawa ba

    [43] Su fito da idanu ƙasƙantattu, wulakanci yana rufe su. Lalle ne a da sun kasance ana kiran su zuwa, yin sujudar, alhali kuwa suna lafiya lau, (suka ƙi yi)

    [44] Saboda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna labari (Alƙur'ani). Za Mu yi musu istidraji daga inda ba su sani ba

    [45] Ina jinkirta musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne

    [46] Ko kana tambayar su wata la'ada ne, saboda haka su, daga wannan tarar, suke jin an nauyaya musu

    [47] Ko kuma suna da ilmin gaibu ne, wato suna yin rubutun (abin da suke faɗa daga gare shi) ne

    [48] Saboda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abucin kifi, alokacin da ya yi kira, alhali yana cike da hushi

    [49] Ba domin ni'ima daga wajen Ubangijinsa ta riske shi ba, lalle ne da an jefa shi a cikin wofintacciyar ƙasa, alhali yana abin zargi

    [50] Sai Ubangijinsa Ya zaɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutanen kirki

    [51] Kuma lalle, ne waɗanda suka kafirta suna yin kamar su kayar da kai sabo da kallonsu (kallon mamaki), a lokacin da suke jin karatun Alƙur'ani, kuma suna cewa, "Lalle ne shi mahaukaci ne

    [52] Shi (Alƙur'ani) bai kasance ba, face abin tunatarwa ne ga duka duniya

    Al-Haqqa

    Surah 69

    [1] Kiran gaskiya

    [2] Mene ne kiran gaskiya

    [3] Kuma me ya sanar da kai abin da ake cewa kiran gaskiya

    [4] Samudawa da Adawa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dukar zuciya

    [5] To, amma Samudawa to, an halakasu da tsawa mai tsanani

    [6] Kuma amma Adawa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙetare haddi

    [7] (Allah) Ya hore ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da juna, saboda haka, kana ganin mutane a cikinta kwance. Kamar su ƙiraruwan dabino ne, waɗanda suka faɗi

    [8] To, ko kana ganin abin da ya yi saura daga cikinsu

    [9] Kuma Fir'auna ya zo da waɗanda ke gabaninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, saboda laifi

    [10] Domin sun saɓa wa manzon Ubangijinsu, saboda haka ya kama su da wani irin kamu mai ƙaruwar (tsanani)

    [11] Lalle ne, Mu, a lokacin da ruwa ya ƙetare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan

    [12] Domin Mu sanya shi, gare ku abin tunawa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi)

    [13] To, idan an yi busa a cikin ƙaho, busa ɗaya

    [14] Kuma aka ɗauki ƙasa da duwatsu, kuma aka niƙa su niƙawa ɗaya

    [15] A ran nan, mai aukuwa za ta auku

    [16] Kuma sama za ta tsage, domin ita a ran nan, mai rauni ce

    [17] Kuma mala'iku (su bayyana) a kan sasanninta, kuma wasu (mala'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan ranar

    [18] A ranar nan za a bijira ku (domin hisabi), babu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓoyewa

    [19] To, amma wanda aka bai wa littafinsa a damansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina

    [20] Lalle ne ni, na tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisabina ne

    [21] Saboda haka, shi yana cikin wata rayuwa yardadda

    [22] A cikin Aljanna maɗaukakiya

    [23] Nunannun 'ya'yan itacenta makusanta ne (ga mai son ɗiba)

    [24] (Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, saboda abin da kuka gabatar a cikin kwanukan da suka shige

    [25] Kuma wanda aka bai wa littafinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kawo mini littafina ba

    [26] Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisabina ba

    [27] In da dai ita, ta kasance mai halaka ni gaba ɗaya ce

    [28] Dukiyata ba ta wadatar da ni ba

    [29] Ikona ya ɓace mini

    [30] (Sai a ce wa mala'iku) "Ku kama shi, sa'an nan ku sanya shi a cikin ƙuƙumi

    [31] Sa'an nan, a cikin Jahim, ku ƙona shi

    [32] Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zira'i saba'in, sai ku sanya shi

    [33] Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin imani da Allah, Mai girma

    [34] Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bayar da) abincin matalauci

    [35] Saboda haka, a yau, a nan, ba ya da masoyi

    [36] Kuma babu wani abinci, sai daga (itacen) gislin

    [37] Babu mai cin sa sai masu ganganci

    [38] To, ba sai Na yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba

    [39] Da abin da ba ku iya gani

    [40] Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne

    [41] Kuma shi ba maganar wani mawaƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai za ku gaskata

    [42] Kuma ba maganar boka ba ne. Kaɗan ƙwarai za ku iya tunawa

    [43] Abin saukarwa ne daga Ubangijin halitta duka

    [44] Kuma da (Muhammadu) ya faɗi wata magana, ya jingina ta gare Mu

    [45] Da Mun kama shi da dama

    [46] sa'an nan, lalle ne, da Mun katse masa laka

    [47] Kuma daga cikinku babu wasu masu iya kare (azabarMu) daga gare shi

    [48] Kuma lalle ne shi (Alƙur'ani) tanatarwa ce ga masu taƙawa

    [49] Kuma lalle, ne Mu, wallahi Muna sane da cewa daga cikinku alwwai masu ƙaryatawa

    [50] Kuma lalle ne shi (Alƙarani) wallahi baƙin ciki ne ga kafirai

    [51] Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙsheni

    [52] Saboda haka, ka tsarkake sunan Ubangjinka, mai girma

    Al-Ma'arij

    Surah 70

    [1] Wani mai tambaya ya yi tambaya game da azaba, mai aukuwa

    [2] Ga kafirai, ba ta da mai tunkuɗewa

    [3] Daga Allah Mai matakala

    [4] Mala'iku da Ruhi (Jibrila) suna takawa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shekara dubu hamsin ne

    [5] Saboda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyawo

    [6] Lalle ne su, suna ganin ta mai nisa

    [7] Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa

    [8] Ranar da sama za ta kasance kamar narkakkar azurfa

    [9] Kuma duwatsu su zama kamar saɓin sufi

    [10] Kuma aboki ba ya tambayar inda wani aboki yake

    [11] Ana sanya su, su gajuna, mai laifi na gurin da zai iya yin fansa, daga azabar ranar nan, da ɗiyansa

    [12] Da matarsa da ɗan'uwansa

    [13] Da danginsa, masu tattara shi

    [14] Da wanda ke a cikin duniya duka gaba ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsirar da shi

    [15] A'aha! Lalle ne fa, ita ce Laza

    [16] Mai twale fatar goshi

    [17] Tana kiran wanda ya juya baya (daga addini) kuma ya kau da kai

    [18] Ya tara (dukiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka

    [19] Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi

    [20] Idan sharri ya shafe shi, ya kasa haƙuri

    [21] Kuma idan alheri ya shafe shi, ya yi rowa

    [22] Sai masu yin salla

    [23] Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, masu dawwama ne

    [24] Kuma waɗanda a cikin dukiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne

    [25] Ga (matalauci) mai roƙo da wanda aka hana wa roƙon

    [26] Da waɗannan da ke gaskata ranar sakamako

    [27] Da waɗannan saboda azabar Ubangijinsu, suna jin tsoro

    [28] Lalle ne, azabar Ubangijinsu ba wadda ake iya amincewaba ce

    [29] Da waɗanda suke, ga farjojinsu, masu tsarewa ne

    [30] Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dama suka mallaka. To lalle ne sukam ba waɗanda ake zargi ba ne

    [31] To, duk wanda ya nemi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan su ne masu ƙetare iyaka

    [32] Kuma da waɗannan da suke ga amanoninsu da alkawarinsu masu tsarewa ne

    [33] Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, masu dagewa ne

    [34] Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, masu tsarewa ne

    [35] Waɗannan, a cikin gidajen Aljanna, waɗanda ake girmamawa ne

    [36] Me ya sami waɗanda suka kafirta, a wajenka, suna gaugawar (gudu)

    [37] Daga jihar dama, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a

    [38] Shin kowane mutum daga cikinsu yana neman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)

    [39] A'aha! Lalle Mu, Mun halitta su, daga abin da suka sani

    [40] Saboda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wuraren ɓullowar rana da wuraren faɗuwarta ba, lalle Mu, Masu iyawa ne

    [41] Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alheri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjaya ba

    [42] Saboda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wasa, har su haɗu da ranarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita)

    [43] Ranar da suke fitowa daga kaburbura da gaugawa, kamar su, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugawa

    [44] Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa)

    Nuhu

    Surah 71

    [1] Lalle ne Mun aiki Nuhu zuwa ga mutanensa, cewa ka yi gargaɗi ga mutanenka gabanin wata azaba mai raɗaɗi ta zo musu

    [2] Ya ce: "Ya mutanena ni, a gare ku, mai gargaɗi ne, mai bayyanawa

    [3] Cewa ku bauta wa Allah, ku ji tsoronSa, kuma ku bi ni

    [4] Allah zai gafarta muku daga zunubanku kuma Ya jinkirta muku zuwa ga ajalin da aka ambata. Lalle ne ajalin Allah idan ya zo, ba za a jinkirta Shi ba, da kun kasance masana (ga abin da nake faɗa da, kun bar kafirci)

    [5] (Nuhu) ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne, na kirayi mutanena, a cikin dare da yini

    [6] To, amma kirana bai ƙare su ba sai da, gudu (daga gare ni)

    [7] Kuma lalle ne ni, ko da yaushe na kiraye su domin Ka gafarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufafinsu, su doge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyakar girman kai

    [8] Sa'an nan lalle ne ni, na kira su, a bayyane

    [9] Sa'an nan lalle ne, na yi yekuwa saboda su, kuma na gana da su a cikin asiri

    [10] Shi na ce, 'Ku nemi gafara daga Ubangijinku, lalle ne shi Ya kasance Mai gafara ne

    [11] Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga

    [12] Kuma ya yalwata muku game da dukiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gonaki, kuma Ya sanya muku koguna

    [13] Me ya same ku, ba ku fatar samun natsuwa daga Allah

    [14] Alhali kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin halaye

    [15] Ba ku ga yadda Allah Ya halitta wasu sammai bakwai ɗabaƙoƙi a kan juna ba

    [16] Ya sanya wata a cikinsu, yana mai haske, Ya sanya rana babbar fitila

    [17] Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa

    [18] Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa

    [19] Kuma Allah Ya sanya muku ƙasa shimfidaɗɗiya

    [20] Domin ku shiga a cikinta, hanyoyi masu faɗi

    [21] Nuhu ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne su sun saɓa mini sun bi wanda dukiyarsa da ɗiyansa ba su ƙare shi da kome ba sai da hasara

    [22] Kuma sun yi wani makirci, makirci babba

    [23] Kuma suka ce: Faufau kada ku bar gumakanku, kuma faufau, kada ku bar wadda, kuma kada ku bar suwa kuma kada ku bar Yagusa da Ya'uƙa da Nasra

    [24] Kuma lalle ne sun ɓatar da (mutane) masu yawa, kuma kada Ka ƙara wa azzalumai (kome) sai ɓata

    [25] Saboda laifukansu na ganganci aka nutsar da su, sa'an nan aka sanya su a wuta. Saboda haka ba su sama wa kansu wani mataimaki wanin Allah ba

    [26] Kuma Nuhu ya ce: "Ya Ublngijina! Kada Ka bari, a kan ƙasa, daga cikin kafirai, wanda ke zama a cikin gida

    [27] Lalle ne, Kai idan Ka bar su, za su ɓatar da bayinKa, kuma ba za su haifi kowa ba face fajiri mai yawan kafirci

    [28] Ya Ubanginjina! Ka yi mini gafara (ni) da mahaifana biyu, da wanda ya shiga gidana, yana mai imani, da muminai maza da muminai mata, kuma kada Ka ƙara wa azzalumai kome sai halaka

    Al-Jinn

    Surah 72

    [1] Ka ce: "An yi wahayi zuwa gare ni cewa wasu jama'a na aljannu sun saururi (karatuna), sai suka ce: Lalle ne mu mun ji wani abin karantawa (Alƙui'ani), mai ban mamaki

    [2] Yana nuni zuwa ga hanyar ƙwarai, saboda haka mun yi imani da shi ba za mu koma bauta wa Ubangijinmu tare da kowa ba

    [3] Kuma lalle ne shi girman Ubangijinmu, Ya ɗaukaka, bai riƙi mata ba, kuma bai riƙi ɗa ba

    [4] Kuma lalle ne shi, wawanmu ya kasance yana faɗar abin da ya ƙetare haddi ga Allah

    [5] Kuma lalle ne mu, mun yi zaton mutum da aljani ba za su iya faɗar ƙarya ba ga Allah

    [6] Kuma lalle ne shi wasu maza daga cikin mutane, sun kasance suna neman tsari da wasu maza daga cikin aljannu, saboda haka suka ƙara musu girman kai

    [7] Kuma lalle ne su, sun yi zato, kamar yadda kuka yi zato, cewa Allah ba zai aiko kowa ba

    [8] Kuma lalle ne mu mun nemi (hawan) sama, sai muka, same ta an cika ta da tsaro mai tsanani da kuma yulaye

    [9] Kuma lalle ne mu, mun kasance muna zama daga gareta, a wuraren zama domin saurare. To wanda ya yi saurare a yanzu, zai sami yula, mai dako dominsa

    [10] Kuma lalle ne mu ba mu sani ba, shin, sharri ne aka yi nufi ga waɗanda ke cikin ƙasa, ko Ubangijinsu Ya yi nufin shiriya a gare su ne

    [11] Kuma lalle ne mu, akwai salaihai a cikinmu, kuma akwai a cikinmu waɗanda ba haka ba mun kasance ƙungiyoyi dabam-dabam

    [12] Kuma lalle ne mu mun tabbata ba za mu buwayi Allah ba, a cikin ƙasa, kuma ba za mu buwaye Shi da gudu ba

    [13] Kuma lalle ne mu, a lokacin da muka ji shiriya, mun yi imani da ita. To wanda ya yi iimani da Uhangijinsa, ba zai ji tsoron nakkasa ba, kuma ba zai ji tsoron zalunci ba

    [14] Kuma lalle ne mu akwai a cikinmu, waɗanda suka miƙa wuya, kuma akwai a cikinmu karkatattu. to, wanda ya miƙa wuya waɗancan kam sun nufi shiryuwa

    [15] Kuma amma karkatattu sai suka kasance makamashi ga Jahannama

    [16] Kuma da sun tsayu sosai a kan hanya, da lalle Mun shayar da su ruwa mai yawa

    [17] Domin Mu jarraba su a ciki, kuma wanda ya kau da kai daga tuna Ubangijinsa, Ubangijinsa zai shigar da shi azaba mai hauhawa

    [18] Kuma lalle ne wuraren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kowa tare da Allah (da su, a cikinsu)

    [19] Kuma, lalle ne shi, a lokacin da bawan Allah ke kiran Sa sun yi kusa su zama kamar shirgi a kansa

    [20] Ka ce: "lna kiran Ubangijina ne kawai, kuma ba zan tara kowa da Shi ba

    [21] Ka ce: "Lalle ne, ni ba ni mallakar wata cuta gare ku, kuma ba ni mallakar wani alheri

    [22] Ka ce: "Lalle ne, ni kowa ba ya iya cetona daga Allah, kuma ba zan iya samun mafaka ba daga gare Shi

    [23] Face iyarwa, daga Allah, da manzancinsa. To, wanda ya saɓa wa Allah da ManzonSa, to, lalle yana da wutar Jahannama suna masu dawwama a cikinta, har abada

    [24] Har idan sun ga abin da ake yi musu gargaɗi da shi, to, za su san wanda ya zama mafi raunin mataimaki da mafi ƙarancin adadi

    [25] Ka ce: "Ban sani ba a kusa ne abin da ake yi muku gargaɗi da shi, ko Ubangijina Ya sanya maSa dogon ajali

    [26] Shi ɗai ne Masanin fake saboda haka, ba Ya bayyana gaibinSa ga kowa

    [27] Face ga wanda Ya yarda da shi, wato wani manzo sa'an nan lalle ne, zai sanya gadi a gaba gare shi da baya gare shi

    [28] Domin Ya san lalle, sun iyar da saƙonnin Ubangijinsu, kuma (Shi Ubangijin) Ya kewaye su da sani, kuma Ya lissafe dukan kome da ƙididdiga

    Al-Muzzammil

    Surah 73

    [1] Ya wanda ya lulluɓe

    [2] Ka tsayu domin yin salla a cikin dare (duka) face kaɗan

    [3] Rabinsa, ko ka rage abu kaɗan daga gare shi

    [4] Ko ka ƙara kansa kuma ka kyautata karanta Alƙu'ani, daki daki

    [5] Lalle ne, Mu, za Mu jefa maka magana mai nauyi

    [6] Lalle ne, tashin dare shi ne mafi tsananin natsuwa, kuma mafi daidaituwa ga magana

    [7] Lalle ne, kana da, a cikin yini, wani tasihi mai tsawo

    [8] Kuma ka ambaci sunan Ubangijinka, kuma ka yanke (ƙauna daga kowa ka koma) zuwa gare Shi, yankewa

    [9] Shi ne Ubangijin mafitar rana da mafaɗarta, babu abin bautawa face Shi. Saboda haka ka riƙe Shi wakili

    [10] Kuma ka yi haƙuri ga abin da suke faɗa, kuma ka ƙaurace musu, ƙauracewa mai kyawo

    [11] Kuma ka bar Ni da masu ƙaryatawa, mawadata, kuma ka jinkirta musu kaɗan

    [12] Lalle ne, a wurinMu, akwai wasu maruruwa masu nauyi da Jahim

    [13] Da wani abinci mai maƙara da azaba mai raɗaɗi

    [14] Ranar da ƙasa ke raurawa, da duwatsu kuma duwatsu su kasance tudun rairayi mai malala

    [15] Lalle ne, Mu. Mun aika zuwa gare ku, wani Manzo mai shaida a kanku, kamar yadda Muka aika wani Manzo zuwaga Fir'auna

    [16] Sai Fir'auna ya saɓa wa Manzon, saboda haka Muka kama shi kamu mai tsanani

    [17] To, yaya, idan kun kafirta, za ku kare (azabar) wani yini mai mayar da yara (tsofaffi) masu hurhura

    [18] Sama za ta tsage a cikinsa, wa'adinsa ya kasance mai aukuwa

    [19] Lalle ne, wannan wata tunatarwa ce, sai dai wanda ya so, ya kama hanyar ƙwarai zuwa ga Ubangijinsa

    [20] Lalle ne, Ubangijinka Ya sani cewa, kai kana tsayuwa a kusan kashi biyu daga uku na dare, da rabinsa, da sulusinsa, tare da wani ɓangare na waɗanda ke tare da kai. Allah Yake iya ƙaddara dare da yini, Ya san ba za ku iya lissafa shi ba, saboda haka Ya karɓi tubarku sai, ku karanta abin da ya sauƙaƙa na Alƙur'ani. Ya san wasu daga cikinku, za su yi ciwo, kuma wasu za su yi tafiya cikin ƙasa suna neman falalar Allah da fatauci, kuma wasu za su yi yaƙi a cikin banyar Allah. Saboda haka ku karanta abin da ya sauƙaƙa daga gare shi, kuma ku tsai da salla kuma ku bayar da zakka, kumaa ku bai wa Allah rance, rance mai kyawo. Kuma abin da kuka gabatar domin kanku, na alheri, za ku same shi a wurin Allah zai kasance mafifici (daga wanda kuka ajiye) kuma zai fi girma ga sakamako, kuma ku roƙi Allah gafara; lalle ne Allah Mai gafara ne, Mai jin ƙai

    Al-Muddaththir

    Surah 74

    [1] Ya wanda ya lulluɓa da mayafi

    [2] Ka tashi domin ka yi gargaɗi

    [3] Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi

    [4] Kuma tutafinka, sai ka tsarkake su

    [5] Kuma gumaka, sai ka ƙaurace musu

    [6] Kada ka yi kyauta kana neman ƙari

    [7] Kuma saboda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure

    [8] To, idan aka yi busa a cikin ƙaho

    [9] To, wannan, a ranar nan, yini ne mai wuya

    [10] A kan kafirai, ba mai sauƙi ba ne

    [11] Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai

    [12] Kuma Na sanya masa dukiya shimfiɗaɗɗiya

    [13] Da ɗiya halartattu

    [14] Kuma Na shimfiɗa? masa kome shimfiɗawa

    [15] Sa'an nan, yana kwaɗayin in yi masa ƙari

    [16] Faufau! Lalle ne, shi ya kasance, ga ayoyinMu, mai tsaurin kai

    [17] Za Ni kallafa masa wahala mai hauhawa

    [18] Lalle ne, Shi, ya yi tunani, kuma ya ƙaddara (abin da zai faɗa game da Alƙur'ani)

    [19] Saboda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara

    [20] Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara

    [21] Sa'an nan, ya yi tunani

    [22] Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk

    [23] Sa'an nan, ya juya baya, kuma ya bunƙasa

    [24] Sai ya ce: "Wannan abu dai ba kome ba ne face wani sihiri, wanda aka ruwaito

    [25] Wannan maganar mutum dai ce

    [26] Za Ni ƙona shi da Saƙar

    [27] Kuma me ya sanar da kai abin da ake cewa Saƙar

    [28] Ba ta ragewa, kuma ba ta bari

    [29] Mai nacewa ga jiki ce (da (ƙuna)

    [30] A kanta akwai (matsara) goma sha tara

    [31] Kuma ba Mu sanya ma'abuta wuta (wato matsaranta) ba, face mala'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (goma sha tara) ba, face domin fitina ga waɗanda suka kafirta domin waɗanda aka bai wa littafi su sami yaƙini kuma waɗanda suka yi imani su ƙara imani, kuma waɗanda aka bai wa littafi da muminai ba za su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kafirai su ce: "Me Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misali?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma babu wanda ya san mayaƙan Ubangijinka face Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba face wata tunatarwa ce ga mutum

    [32] A'aha! Ina rantsuwa da wata

    [33] Da dare a lokacin da ya juyar da baya

    [34] Da safiya idan ta waye

    [35] Ita (wutar) ɗayan manyan masifu? ce

    [36] Mai gargaɗi ce ga mutum

    [37] Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabata ko ya jinkirta

    [38] Kowane rai ga abin da ya aikata jingina ce

    [39] Face mutanen dama

    [40] A cikin Aljanna suna tambayar juna

    [41] Game da masu laifi

    [42] (Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar

    [43] Suka ce: "Ba mu kasance muna a cikin masu salla ba

    [44] Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalauta ba

    [45] Kuma mun kasance muna kutsawa tare da masu kutsawa

    [46] Mun kasance muna ƙaryata ranar sakamako

    [47] Har gaskiya (wato mutuwa) ta zo mana

    [48] Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba

    [49] Haba! Me ya same su, suka zama masu bijirewa daga wa'azin gaskiya

    [50] Kamar dai su, jakuna firgitattu ne

    [51] Sun gudu daga zaki

    [52] A'aha! Kowane mutum daga cikinsu yana son a zo masa da takardu (da sunansa) ana watsawa

    [53] A'aha! Kai dai, ba su jin tsoron Lahira

    [54] A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tunatarwa ce

    [55] Domin wanda ya so, ya tuna

    [56] Kuma ba za su tuna ba face idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gafara

    Al-Qiyamma

    Surah 75

    [1] Ba sai Na yi rantsuwa da Ranar ¡iyama ba

    [2] Ba sai Na yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba

    [3] Sin, mutum yana zaton cewa ba za Mu tara ƙasusuwansa ba

    [4] Na'am! Masu ikon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓoɓin yatsunsa

    [5] Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fajirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa

    [6] Yana tambaya: "Yaushe ne Ranar ¡iyama

    [7] To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli)

    [8] Kuma, wata ya yi husufi (haskensa ya dushe)

    [9] Aka tara rana da wata

    [10] Mutum zai ce a ran nan "Ina wurin gudu

    [11] A'aha! babu mafaka

    [12] zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a ranar nan, yake

    [13] Ana gaya wa mutum, a ranar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar

    [14] Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne

    [15] Kuma ko da ya jefa uzurorinsa (ba za a saurare shi ba)

    [16] Kada ka motsar da harshenka game da shi domin ka yi gaugawar riƙe shi (Alƙur'ani)

    [17] Lalle ne, wajibi ne a gare Mu, Mu tara shi. Mu (tsare maka) karatunsa

    [18] To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa

    [19] sa'an nan, lalle wajibi ne a gare Mu, bayaninsa

    [20] A'aha! Ba haka ba kuna son mai gaugawar nan (duniya) ne

    [21] Kuna barin ta ƙarshen (Lahira)

    [22] Wasu huskoki, a ranar nan, masu annuri ne

    [23] Zuwa ga Ubangijinsu masu kallo ne

    [24] Wasu huskoki, a ranar nan, masu gintsewa ne

    [25] Suna zaton a sako musu masifa mai karya tsatso

    [26] A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai

    [27] kuma aka ce: "Wane ne mai tawada

    [28] Kuma ya tabbata cewa rabuwa dai ce

    [29] Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri

    [30] Zuwa ga Ubangijinka, a ranar nan, magargaɗa take

    [31] To, bai gaskata ba, kuma bai yi salla ba

    [32] Amma dai ya ƙaryata, kuma ya juya baya

    [33] Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutanensa, yana taƙama

    [34] Halaka ta tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dacewa

    [35] Sa'an nan, wata halaka ta tabbata a gare ka domin ta fi dace wa

    [36] Shin, mutum na zaton a bar shi sagaga (wato babu nufin kome game da shi)

    [37] Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

    [38] Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓoɓinsa

    [39] Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace

    [40] Ashe wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rayar da matattu

    Ad-Dahr

    Surah 76

    [1] Lalle ne, wata mudda ta zamani ta zo a kan mutum, bai kasance kome ba wanda ake ambata

    [2] Lalle ne, Mu Mun halitta mutum daga ɗigon ruwa garwayayye, Muna jarraba shi, saboda haka Muka sanya shi mai ji mai gani

    [3] Lalle ne, Mu, Mun shiryar da shi ga hanyar ƙwarai, ko ya zama mai godiya, kuma ko ya zama mai kafirci

    [4] Lalle ne, Mu, Mun yi tattali, domin kafirai, sarƙoƙi da ƙuƙumma da sa'ir

    [5] Lalle ne, mutanen kirki za su sha daga finjalin giya abin gaurayarta ya kasance kafur ne

    [6] Wani marmaro ne, daga gare shi bayin Allah suke sha, suna ɓuɓɓugar da shi ɓuɓɓugarwa

    [7] Suna cikawa da alwashin (da suka bakanta), kuma suna tsoron wani yini wanda sharrinsa ya kasance mai tartsatsi ne

    [8] Kuma suna ciyar da abinci, a kan suna bukatarsa, ga matalauci da maraya da kamamme

    [9] (Suna cewa): "Muna ciyar da ku ne domin neman yardar Allah kawai, ba mu nufin samun wani sakamako daga gare ku, kuma ba mu nufin godiya

    [10] Lalle ne, mu muna tsoro daga Ubangijinmu, wani yini mai gintsewa, mai murtukewa

    [11] Saboda haka Allah Ya tsare musu sharrin wannan yini, kuma Ya hlɗa su da annurin huska da farin ciki

    [12] Kuma Ya saka musu saboda haƙurin da suka yi, da Aljanna da tufafin alharini

    [13] Suna masu zaman ginciri, a cikinta, a kan karagu, ba su ganin rana a cikinta, kuma ba su ganin jaura

    [14] Kuma, inuwoyinta suna kusa, a kansu, an hore nunannun 'ya'yan itacenta, horewa

    [15] Kuma ana kewayawa a kansu da finjalai na azurfa da kofuna waɗanda suka kasance na ƙarau

    [16] ¡arau na azurfa, sun ƙaddara su ƙaddarawa, daidai bukata

    [17] Ana shayarwa da su, a cikinta, finjalan giya, wadda abin gaurayarta ya kasance zanjabil ne

    [18] Wani marmaro ne, a cikinta, ana kiran sa salsabil

    [19] Kuma wasu yara samarin dindindin na kewayawa, a kansu, idan ka gan su, za ka zaci su lu'ulu'u ne wanda aka watsa

    [20] Kuma idan ka ga wannan wurin, to, ka ga wata irin ni'ima da mulki babba

    [21] Tufafinsu na sama na alhari ni ne, kore da mai walƙiya, kuma an ƙawace su da mundaye na wata curin azurfa kuma Ubangijinsu, Ya shayar da su abin sha mai tsarkakewar (ciki)

    [22] (A ce musu) "Lalle ne, wannan ya kasance, a gare ku sakamako, kuma aikink. ya kasance abin godewa

    [23] Lalle, Mu ne Muka saukar da Alƙur'ani a gare ka, saukarwa

    [24] Saboda haka ka yi haƙuri ga hukuncin Ubangijinka, kuma kada ka bi, daga cikinsu, mai zunubi ko mai kafirci

    [25] Kuma ka ambaci sunan Ubangijinka, safe da maraice

    [26] Daga dare, sai ka yi sujuda gare Shi, kuma ka tsarkake Shi dare mai tsawo

    [27] Lalle ne, waɗannan suna son mai gaugawa (duniya) kuma suna bari, a bayansu, wani yini mai nauyi

    [28] Mu ne Muka halitta su kuma Muka, ƙarfafa halittarsu, kuma idan Mun so, za Mu musanya su da wasu mutane kwatankwacinsu, musanyawa

    [29] Lalle ne, wannan wata tunatarwa ce, saboda wanda ya so ya riƙa hanyar kirki zuwa ga Ubangijinsa

    [30] Kuma, ba za ku so ba, sai Allah Ya so, lalle ne Allah Ya kasance Masani' Mai hikima

    [31] Yana shigar da wanda Ya so a cikin rahamarsa, kuma azzalumai, Ya yi musu tattalin wata azaba mai raɗaɗi

    Al-Mursalat

    Surah 77

    [1] Ina rantsuwa da iskokin da ake sakowa jere, suna bin juna

    [2] Sa'an nan, su zama iskoki masu ƙarfi suna kaɗawa da ƙarfi

    [3] Kuma, masu watsa rahama watsawa

    [4] sa'an nan, da ayoyi masu rarrabe gaskiya da ƙarya rarrabewa

    [5] Sa'an nan da mala'iku masu jefa tunatarwa ga Manzanni

    [6] Domin yanke hamzari ko domin gargadi

    [7] Lalle ne, abin da ake yi muku wa'adi da shi tabbas mai aukuwa ne

    [8] To, idan taurari aka shafe haskensu

    [9] Kuma, idan sama aka tsage ta

    [10] Kuma, idan duwatsu aka nike su

    [11] Kuma, idan manzanni aka ƙayyade lokacin tara su

    [12] Domin babbar ranar da aka yi wa ajali

    [13] Domin ranar rarrabewa

    [14] Kuma, me ya sanar da kai ranar rarrabewa

    [15] Bone ya tabbata a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [16] Ashe, ba Mu halakar da (masu ƙaryataw) na farko ba

    [17] Sa'an nan, kuma za Mu biyar musu da na ƙarshe

    [18] Haka nan, Muke aikatawa da masu yin laifi

    [19] Bone ya tabbata a ranar nan ga masu ƙaryatawa

    [20] Ashe, ba Mu halitta ku daga wani ruwa wulakantacce ba

    [21] Sa'an nan Muka sanya shi a cikin wani wurin natsuwa amintacce

    [22] Zuwa ga wani gwargwadon mudda sananna

    [23] Sa'an nan, Muka nuna iyawarMu? Madalla da Mu, Masu nuna iyawa

    [24] Bone ya tabbata a ranar nan ga masu ƙaryatawa

    [25] Ashe, ba Mu sanya ƙasa matattara ba

    [26] Ga rayayyu da matattu

    [27] Kuma, Muka sanya, a cikinta, kafaffun duwatsu maɗaukaka, kuma Muka shayar da ku ruwa mai daɗi

    [28] Bone ya tabbata, a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [29] Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna ƙaryatawa game da shi

    [30] Ku tafi zuwa ga wata inuwa mai rassa uku

    [31] Ita ba inuwar ba, kuma ba ta wadatarwa daga harshen wuta

    [32] Lalle ne, ita, tana jifa da tartsatsi kamar soraye

    [33] Kamar dai su raƙumma ne baƙaƙe

    [34] Bone ya tabbata, a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [35] Wannan, yini ne da ba za su iya yin magana ba

    [36] Ba za a yi musu izni ba, balle su kawo hanzari

    [37] Bone ya tabbata, a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [38] Wannan ranar rarrabewa ce, Mun tattara ku tare da mutanen farko

    [39] To, idan akwai wata dabara gare ku, sai ku yi ma Ni ita

    [40] Bone ya tabbata, a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [41] Lalle ne, masu taƙawa suna a cikin inuwowi da maremari

    [42] Da wasu 'ya'yan itace irin waɗanda suke marmari

    [43] (A ce musu) "Ku ci ku sha cikin ni'ima saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa

    [44] Lalle ne, Mu haka Muke saka wa masu kyautatawa

    [45] Bone ya tabbata, a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [46] (Ana ce musu) "Ku ci ku ji ɗan dadi kaɗan, lalle ne dai ku masu laifi ne

    [47] Bone ya tabbata, a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [48] Kuma, idan an ce musu: "Ku yi ruku'i; ba za su yi ruku'in (salla) ba

    [49] Bone ya tabbata, a ranar nan, ga masu ƙaryatawa

    [50] To, da wane labari (Littafi), waninsa (Alƙur'ani) za su yi imani

    An-Naba'

    Surah 78

    [1] A kan me suke tambayar juna

    [2] A kan muhimmin labari mai girma (Alƙur'ani)

    [3] Wanda suke saɓa wa juna a cikinsa

    [4] A'aha! Za su sani

    [5] Kuma, a'aha! Za su sani

    [6] Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba

    [7] Da duwatsu turaku (ga riƙe ƙasa)

    [8] Kuma, Mun halitta ku maza da mata

    [9] Kuma, Muka sanya barcinku hutawa

    [10] Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura

    [11] Kuma, Muka sanya yini (yazama) lokacin neman abinci

    [12] Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai masu ƙarfi

    [13] Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rana)

    [14] Kuma, Muka saukar daga cikakkun giragizai, ruwa mai yawan zuba

    [15] Domin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi

    [16] Da itacen lambuna masu lillibniya

    [17] Lalle ne, ranar rarrabewa ta kasance abin ƙayyade wa lokaci

    [18] Ranar da za a yi busa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a

    [19] Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙofofi

    [20] Kuma, aka tafiyar da duwatsu, sai suka kasance ƙura

    [21] Lalle ne, Jahannama ta kasance madakata

    [22] Ga masu ƙetare iyakoki, ta zama makoma

    [23] Suna, masu zama a cikinta, zamunna

    [24] Ba su ɗanɗanawar wani sanyi a cikinta, kuma ba su ɗanɗana abin sha

    [25] Face tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini

    [26] Sakamako mai dacewa

    [27] Lalle ne, su, sun kasance ba su fatar sauƙin wani hisabi

    [28] Kuma, suka ƙaryata game da ayoyinMu, ƙaryatawa

    [29] Alhali, kowane abu Mun ƙididdige shi, a rubuce

    [30] Saboda haka, ku ɗanɗana domin haka, ba za Mu ƙara muku kome ba face azaba

    [31] Lalle ne, masu taƙawa na da wani wurin samun babban rabo

    [32] Lambuna da inabobi

    [33] Da cikakkun 'yammata, tsarar juna

    [34] Da hinjalan giya cikakku

    [35] Ba su jin yasassar magana, a cikinta, kuma ba su jin ƙaryatawa

    [36] Domin sakamako daga Ubangijinka, kyauta mai yawa

    [37] Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakaninsu, Mai rahama, ba su da ikon yin wata magana daga gare Shi

    [38] Ranar da Ruhi da mala'iku za su tsaya a cikin safu, ba su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai

    [39] Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makoma zuwa ga Ubangijinsa

    [40] Lalle ne, Mu, Mun yi muku gargaɗin azaba makusanciya, ranar da mutum ke dubi zuwa ga abin da hannayensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, da dai na zama turɓaya

    An-Nazi'at

    Surah 79

    [1] Ina rantsuwa da mala'iku masu fisgar rayuka (na kafirai) da ƙarfi

    [2] Da masu ɗibar rayuka (na muminai) da sauƙi a cikin nishaɗi

    [3] Da masu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo

    [4] Sa'an nan, su zama masu gaugawa (da umurnin Allah) kamar suna tsere

    [5] Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni

    [6] Ranar da mai girgiza abubuwa (busar farko) za ta kaɗa

    [7] Mai biyar ta (busa ta biyu) na biye

    [8] Wasu zukata, a ranar nan, masu jin tsoro ne

    [9] Alhali idanunsu na ƙasƙantattu

    [10] Suna cewa "Ashe lalle za a iya mayar da mu a kan sawunmu

    [11] Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu

    [12] Suka ce: "Waccan kam komawa ce, taɓaɓɓiya

    [13] To, ita kam, tsawa guda kawai ce

    [14] Sai kawai ga su a bayan ƙasa

    [15] Shin, labarin Musa ya zo maka

    [16] A lokacin da Ubangijinsa Ya kiraye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwa

    [17] Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙetare haddi

    [18] Sai ka ce masa, Ko za ka so ka tsarkaka

    [19] Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa

    [20] Sai ya nuna masa ayar nan mafi girma

    [21] Sai ya ƙaryata, kuma ya saɓa (umurni)

    [22] Sa'an nan ya juya baya, yana tafiya da sauri

    [23] Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira

    [24] Sai ya ce: "Ni ne Ubangijinku mafi ɗaudaka

    [25] Saboda haka Allah Ya kama shi, domin azabar maganar ƙarshe da ta farko

    [26] Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsoron Allah

    [27] Shin, ku ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta

    [28] Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta

    [29] Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta

    [30] Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta

    [31] Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyayarta

    [32] Da duwatsu, Ya kafe ta

    [33] Domin jiyarwa daɗi a gare ku, kuma ga dabbobinku

    [34] To, idan uwar masifu, mafi girma, ta zo

    [35] Ranar da mutum zai yi tunanin abin da ya aikata

    [36] Kuma, a bayyana Jahim ga mai gani

    [37] To, amma wanda ya yi girman kai

    [38] Kuma, ya zaɓi rayuwa ta kusa, (wato duniya)

    [39] To, lalle ne Jahim, ita ce makoma

    [40] Kuma, amma wanda ya ji tsoron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai

    [41] To, lalle ne Aljanna ita ce makoma

    [42] Suna tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta

    [43] Me ya haɗa ka da ambatonta

    [44] Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake

    [45] Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsoron ta

    [46] Kamar su a ranar da za su gan ta, ba su zauna ba face a lokacin marece ko hantsinsa

    Abasa

    Surah 80

    [1] Ya game huska kuma ya juya baya

    [2] Saboda makaho ya je masa

    [3] To, me ya sanar da kai cewa watakila shi ne zai tsarkaka

    [4] Ko ya tuna, domin tunawar ta amfane shi

    [5] Amma wanda ya wadatu da dukiya

    [6] Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi

    [7] To, me zai cuce ka idan bai tsarkaka ba

    [8] Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugawa

    [9] Alhali shi yana jin tsoron Allah

    [10] Kai kuma ka shagala ga barinsa

    [11] A'aha! Lalle ne, wannan tunatarwa ce

    [12] Saboda wanda ya so ya tunaShi (Allah)

    [13] (Tunatarwa ce) ta cikin littafai ababan girmamawa

    [14] Ababan ɗaukakawa, ababan tsarkakewa

    [15] A cikin hannayen mala'iku marubuta

    [16] Masu daraja, masu ɗa'a ga Allah

    [17] An la'ani mutum (kafiri). Me ya yi kafircinsa

    [18] Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi

    [19] Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddara shi (ga halaye)

    [20] Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa

    [21] Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari

    [22] Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tayar da shi

    [23] Haƙiƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lokacin sanya shi a cikin kabari)

    [24] To, mutum ya duba zuwa ga abincinsa

    [25] Lalle ne Mu, Mun zuo ruwa, zubowa

    [26] Sa'an nan, Muka tsattsage ƙasa tsattsagewa

    [27] Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta

    [28] Da inabi da ciyawa

    [29] Da zaituni da itacen dabino

    [30] Da lambuna, masu yawan itace

    [31] Da 'ya'yan itacen marmari, da makiyaya ta dabbobi

    [32] Domin jin daɗi a gare ku, ku da dabbobinku

    [33] To, idan mai tsawa (busa ta biyu) ta zo

    [34] Ranar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa

    [35] Da uwarsa da ubansa

    [36] Da matarsa da ɗiyansa

    [37] Ga kowane mutum daga cikinsu, a ranar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi

    [38] Wasu huskoki, a ranar nan, masu haske ne

    [39] Masu dariya ne, masu bushara

    [40] Wasu huskoki, a ranar nan, akwai ƙura a kansu

    [41] Baƙi zai rufe su

    [42] Waɗannan su ne kafirai fajirai (ga ayyukansu)

    At-Takwir

    Surah 81

    [1] Idan rana aka shafe haskenta

    [2] Kuma idan taurari suka gurɓace (wani ya shiga a cikin wani)

    [3] Kuma idan duwatsu aka tafiyar da su

    [4] Kuma idan raƙuma masu cikunna aka sake su wawai, ba ga kowa ba

    [5] Kuma idan dabbobin daji aka tattara su

    [6] Kuma idan tekuna aka mayar da su wuta

    [7] Kuma idan rayuka aka haɗa su da jikunkunansu

    [8] Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta

    [9] Saboda wane laifi ne aka kashe ta

    [10] Idan takardun ayyuka aka watsa su (ga masu su)

    [11] Kuma idan sama aka feɗe ta

    [12] Kuma idan Jahim aka hura ta

    [13] Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita

    [14] Rai ya san abin da ya halartar (a ranar nan)

    [15] To, ba sai Na yi rantsuwa da taurari matafa ba

    [16] Masu gudu suna ɓuya

    [17] Da dare idan ya bayar da baya

    [18] Da safiya idan ta yi lumfashi

    [19] Lalle ne shi (Alƙur'ani) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah

    [20] Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi

    [21] Wanda ake yi wa ɗa'a (wato shugaban mala'iku) ne a can, amintacce

    [22] Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne

    [23] Kuma lalle ne, ya gan shi a cikin sararin sama mabayyani

    [24] Kuma shi, ga gaibi ba mai rowa ba ne

    [25] Kuma shi (Alƙur'ani) ba maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce

    [26] Shin, a ina za ku tafi

    [27] Lalle ne shi (Alƙur'ani), ba kome ba ne face gargaɗi ga talikai

    [28] Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu

    [29] Kuma ba za ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Ya yarda

    Al-Infitar

    Surah 82

    [1] Idan sama ta tsage

    [2] Kuma idan taurari suka watse

    [3] Kuma idan tekuna aka facce su

    [4] Kuma idan kaburbura aka tone su

    [5] Rai ya san abin da ya gabatar, da abin da ya jinkirtar

    [6] Ya kai mutum! Me ya ruɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci

    [7] Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaita ka, Ya kuma tsakaita ka

    [8] A cikin kowace irin sura Ya so Ya gina ka a kanta

    [9] A'aha, ba haka ba, kuna ƙaryatawa game da sakamako

    [10] Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara

    [11] Masu daraja, marubuta

    [12] Suna sanin abin da kuke aikatawa

    [13] Lalle ne, masu ɗa'a ga Allah, dahir, suna cikin ni'ima

    [14] Kuma lalle ne, fajirai, dahir, suna cikin Jahim

    [15] Za su shige ta a ranar sakamako

    [16] Ba za su faku daga gare ta ba

    [17] Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa renar sakamako

    [18] Sa'an nan, me ya sanar da kai abin da ake ce wa ranar sakamako

    [19] Rana ce da wani rai ba ya iya mallakar kome domin wani rai al'amari, a ranar nan, ga Allah (ɗai) yake

    Al-Mutaffifin

    Surah 83

    [1] Bone ya tabbata ga masu naƙƙasawa

    [2] Waɗanda suke idan suka auna daga mutane suna cika mudu

    [3] Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikeli, suna ragewa

    [4] Ashe! Waɗancan ba su tabbata cewa lalle su, ana tayar da su ba

    [5] Domin yini mai girma

    [6] Yinin da mutane ke tashi zuwa ga Ubangijin halitta

    [7] Haƙiƙa lalle ne littafin fajirai dahir, yana a cikin Sijjin

    [8] Kuma, me ya sanar da kai abin da ake ce wa Sijjin

    [9] Wani 1ittafi ne rubutacce

    [10] Bone ya tabbata a ranar nan ga masu ƙaryatawa

    [11] Waɗanda suke ƙaryatawa game da ranar sakamako

    [12] Babu mai ƙaryatawa gare shi face dukan mai ƙetare haddi mai yawan zunubi

    [13] Idan ana karatun ayoyinmu, a kansa, sai ya ce: tatsuniyoyin mutanen farko ne

    [14] A'aha! Ba haka ba, abin da suka kasance suna aikatawa dai, ya yi tsatsa a cikin zukatansu

    [15] A'aha! Haƙiƙa, lalle ne su daga Ubangijinsu, ranar nan, waɗanda ake shamakancewa ne

    [16] Sa'an nan, lalle ne, su masu shiga cikin Jahim ne

    [17] Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatawa game da shi

    [18] A'aha! Haƙiƙa lalle ne littafin masu ɗa'a yana a cikin Illiyyina

    [19] Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cewa Illiyyuna

    [20] Wani littafi ne rubutacce

    [21] Muƙarrabai suke halarta shi

    [22] Lalle ne, masu ɗa'a ga Allah tabbas suna cikin ni'ima

    [23] A kan karagu, suna ta kallo

    [24] Kana sani a cikin huskokinsu, akwai kwarjinin ni'ima

    [25] Ana shayar da su daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta

    [26] ¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, masu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nema

    [27] Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnim yake

    [28] (Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi

    [29] Lalle ne, waɗanda suka kafirta sun kasance (a duniya) suna yi wa waɗanda suka yi imani dariya

    [30] Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe

    [31] Kuma idan suka juya zuwa ga iyalansu, sai su tafi suna kakaci

    [32] Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne

    [33] Alhali kuwa, ba a aike su ba domin su zama masu tsaro a kansu

    [34] To, yau fa (a Lahira] waɗanda suka yi imani, su ke yi wa kafirai dariya

    [35] A kan karagu, suna ta kallo

    [36] Shin an saka ma kafirai abin da suka kasance suna aikatawa

    Al-Inshiqaq

    Surah 84

    [1] Idan sama ta kece

    [2] Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin sauraron

    [3] Kuma idan ƙasa aka miƙe ta

    [4] Kuma ta jefar da abin da yake a cikinta, ta wofinta daga kome

    [5] Kuma ta saurari Ubangijinta, aka wajabta mata yin sauraren

    [6] Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne

    [7] To, amma wanda aka bai wa littafinsa da damansa

    [8] To, za a yi masa hisabi, hisabi mai sauƙi

    [9] Kuma ya juya zuwa ga iyalinsa (a cikin Aljanna), yana mai raha

    [10] Kuma amma wanda aka bai wa littafinsa, daga wajen bayansa

    [11] To, za shi dinga kiran halaka

    [12] Kuma ya shiga sa'ir

    [13] Lal1e ne shi, ya kasance (a duniya) cikin iyalinsa yana mai raha

    [14] Lalle ne ya yi zaton ba zai komo ba

    [15] Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi

    [16] To, ba sai Na rantse da shafaƙi ba

    [17] Da dare, da abin da ya ƙunsa

    [18] Da wata idan (haskensa) ya cika

    [19] Lalle ne kuna hawan wani hali daga wani hali

    [20] To, me ya same su, ba su yin imani

    [21] Kuma idan an karanta Alkur'ani a kansu, ba su yin tawali'u

    [22] Ba haka ba! waɗanda suka kafirta, sai ƙaryatawa suke yi

    [23] Alhali Allah Shi ne Mafi sani ga abin a suke tarawa

    [24] Saboda haka, ka yi musu bushara da azaba mai raɗaɗi

    [25] Face waɗanda suka yi imani, suka aikata ayyukan ƙwarai, suna da wani sakamako wanda ba ya yankewa

    Al-Buruj

    Surah 85

    [1] Ina rantsuwa da sama mai taurarin lissafin shekara

    [2] Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa

    [3] Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa

    [4] An la'ani mutanen rami

    [5] Wato wuta wadda aka hura

    [6] A lokacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune

    [7] Alhali su, bisa ga abin da suke aikatawa ga muminai, suna halarce

    [8] Kuma ba su tuhumce su ba, face kawai domin sun yi imani da Allah Mabuwayi, wanda ake godewa

    [9] Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kome halarce Yake

    [10] Lalle ne waɗanda suka fitini muminai maza da muminai mata, sa'an nan ba su tuba ba to, suna da azabar Jahannama, kuma suna da azabar gobara

    [11] Lalle ne waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, suna da gidajen Aljanna, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashin gidajen. Wancan abu fa shi ne rabo babba

    [12] Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai

    [13] Lalle ne Shi, Shi ne Mai ƙaga halitta, kuma Ya mayar da ita (bayan mutuwa)

    [14] Kuma Shi ne Mai gafara, Mai bayyana soyayya

    [15] Mai Al'arshi mai girma

    [16] Mai aikatawa ga abin da Yake nufi

    [17] Ko labarin rundanoni ya zo maka

    [18] Fir'auna da samudawa

    [19] A'aha! waɗanda suka kafirta suna cikin ƙaryatawa

    [20] Alhali, Allah daga bayansu, Mai kewaye su ne (da saninSa)

    [21] A'aha! Shi Alƙur'ani ne mai girma

    [22] A cikin Allo tsararre

    At-Tariq

    Surah 86

    [1] Ina rantsuwa da sama da mai aukowa da dare

    [2] To, me ya sanar da kai abin da ake cewa mai aukowa da dare

    [3] Shi ne tauraron nan mai tsananin haske

    [4] Babu wani rai face a kansa akwai wani mai tsaro

    [5] To, mutum ya duba, daga me aka halitta shi

    [6] An halitta shi daga wani ruwa mai tunkuɗar juna

    [7] Yana fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji

    [8] Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyawa ne

    [9] Ranar da ake jarrabawar asirai

    [10] Saboda haka, ba shi da wani ƙarfi, kuma ba shi da wani mai taimako (da zai iya kare shi daga azabar Allah)

    [11] Ina rantsuwa da sama ma'abuciyar ruwa mai komawa yana yankewa

    [12] Da ƙasa ma'abuciyar tsagewa

    [13] Lalle ne shi (Alƙur'ani), haƙiƙa magana ce daki-daki

    [14] Kuma shi ba bananci bane

    [15] Lalle ne su, suna ƙulla kaidi na sosai

    [16] Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi

    [17] Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu

    Al-A'la

    Surah 87

    [1] Ka tsarkake sunan Ubangijinka Mafi ɗaukaka

    [2] Wanda Ya yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar

    [3] Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alheri da ta sharri)

    [4] Kuma Wanda Ya fitar da makiyaya

    [5] Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa

    [6] Za mu karantar da kai (Alƙur'ani) saboda haka ba za ka manta (shi) ba

    [7] Face abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake boye

    [8] Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi

    [9] Saboda baka, ka tunatar, idan tunatarwa za ta yi amfani

    [10] Wanda yake tsoron (Allah) Zai tuna

    [11] Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta

    [12] Wanda zai shiga wutar da ta fi girma

    [13] Sa'an nan ba zai mutu ba a cikinta, kuma ba zai rayu ba

    [14] Lalle ne wanda ya tsarkaka (da imani) ya samu babban rabo

    [15] Kuma ya ambaci sunan Ubangijinsa, sa'an nan ya yi salla

    [16] Ba haka ba! Kuna zaɓin rayuwa ta kusa duniya

    [17] Alhali Lahira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa

    [18] Lalle ne, wannan yana a cikin littafan farko

    [19] Littaffan Ibrahim da Musa

    Al-Ghashiya

    Surah 88

    [1] Lalle ne labarin (¡iyama) mai rufe mutane da tsoronta ya zo maka

    [2] Wasu huskoki a ranar nan ƙasƙantattu ne

    [3] Masu aikin wahala ne, masu gajiya

    [4] Za su shiga wata wuta mai zafi

    [5] Ana shayar da su daga wani marmaro mai zafin ruwa

    [6] Ba su da wani abinci face dai daga danyi

    [7] Ba ya sanya ƙiba, kuma ba zai wadatar daga yunwa ba

    [8] Wasu huskoki a ranar nan masu ni'ima ne

    [9] Game da aikinsu, masu yarda ne

    [10] (Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya

    [11] Ba za su ji yasassar magana ba, a cikinta

    [12] A cikinta akwai marmaro mai gudana

    [13] A cikinta akwai gadaje maɗaukaka

    [14] Da kofuna ar'aje

    [15] Da filoli jere

    [16] Da katifu shimfiɗe

    [17] Ashe to ba za su dubawa ba ga raƙuma yadda aka halitta su

    [18] Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta

    [19] Da zuwa ga duwatsu yadda aka kafa su

    [20] Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗa ta

    [21] saboda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai

    [22] Ba ka zama mai ikon tanƙwasawa a kansu ba

    [23] Face dai duk wanda ya juya baya, kuma ya kafirta

    [24] To, Allah zai yi masa azaba, azabar nan da take mafi girma

    [25] Lalle ne, zuwa gare Mu komowarsu take

    [26] Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisabi

    Al-Fajr

    Surah 89

    [1] Ina rantsuwa da alfijiri

    [2] Da daruruwa goma

    [3] Da (adadi na) cika da (na) mara

    [4] Da dare idan yana shuɗewa

    [5] Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)

    [6] Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Adawa ba

    [7] Iramawa masu sakon ƙirar jiki

    [8] Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garuruwa (na duniya)

    [9] Da samudawa waɗanda suka fasa duwatsu a cikin Wadi suka yi gidaje

    [10] Da Fir'auna mai turaku

    [11] Waɗanda suka ƙetare iyakarsu, a cikin garuruwa

    [12] Saboda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu

    [13] Saboda haka Ubangijinka Ya zuba musu bulalar azaba

    [14] Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka

    [15] To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wato Ya girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni

    [16] Kuma idan Ya jarraba shi, wato Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walakanta ni

    [17] A'aha! Bari wannan, ai ba ku girmama maraya

    [18] Ba ku kwaɗaita wa junanku ga (tattalin) abincin matalauci

    [19] Kuma kuna cin dukiyar gado, ci na tarawa

    [20] Kuma kuna son dukiya, so mai yawa

    [21] A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai

    [22] Kuma Ubangijinka Ya zo, alhali mala'iku na jere, safu- safu

    [23] Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunani. To, ina fa tunani yake a gare shi

    [24] Yana dinga cewa, "Kaitona, da na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rayuwata

    [25] To, a ranar nan babu wani mai yin azaba irin azabar Allah

    [26] Kuma babu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa

    [27] Ya kai rai mai natsuwa

    [28] Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhali kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a duniya) abar yardarwa (da sakamakon da za a ba ka a Lahira)

    [29] Sabobda haka, ka shiga cikin bayiNa (masu bin umurui a duniya)

    [30] Kuma ka shiga AljannaTa (a Lahira)

    Al-Balad

    Surah 90

    [1] Ba sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba

    [2] Alhali kai kana mai sauka a cikin wannan gari

    [3] Da mahaifi da abin da ya haifa

    [4] Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala

    [5] Ko yana zaton babu wani mai iya samun iko, a kansa

    [6] Yana cewa "Na halakarda dukiya mai yawa

    [7] Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba

    [8] Shin, ba Mu sanya masa idanu biyu ba

    [9] Da harshe, da leɓɓa biyu

    [10] Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyoyi biyu ba

    [11] To, don mene ne bai shiga Aƙaba ba

    [12] Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake ce wa Aƙaba

    [13] Ita ce fansar wuyan bawa

    [14] Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abucin yunwa

    [15] Ga maraya ma'abucin zumunta

    [16] Ko kuwa wani matalauci ma'abucin turɓaya

    [17] Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi imani, kuma suka yi wa juna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayi

    [18] Waɗannan ne ma'abuta albarka

    [19] Kuma waɗanda suka kafirta da ayoyinMu, su ne ma'abuta shu'umci

    [20] A kansu akwai wata wuta abar kullewa

    Ash-Shams

    Surah 91

    [1] Ina rantsuwa da rana da hantsinta

    [2] Kuma da wata idan ya bi ta

    [3] Da yini a lokacin da ya bayyana ta

    [4] Da dare a lokacin da ya ke rufe ta

    [5] Da sama da abin da ya gina ta

    [6] Da ƙasa da abin da ya shimfiɗa ta

    [7] Da rai da abin da ya daidaita shi

    [8] Sa'an nan ya sanar da shi fajircinsa da shiryuwarsa

    [9] Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sami babban rabo

    [10] Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya taɓe

    [11] Samudawa sun ƙaryata (Annabinsu), domin girman kansu

    [12] A lokacin da mafi shaƙawarsu ya tafi (wurin soke rakumar salihu)

    [13] Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsoratar da ku ga raƙumar Allah da ruwan shanta

    [14] Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka soke ta. Saboda haka Ubangijinsu Ya darkake su, saboda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azabar ga mai laifi da maras laifi)

    [15] Kuma ba ya tsoron aƙibarta (ita halakawar)

    Al-Layl

    Surah 92

    [1] Ina rantsuwa da dare a lokacin da yake rufewa

    [2] Da yini a lokacin da yake kuranyewa

    [3] Da abin da ya halitta namiji da mace

    [4] Lalle ne ayyukanku, dabam-dabam suke

    [5] To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa

    [6] Kuma ya gaskata kalma mai kyawo

    [7] To, za Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi

    [8] Kuma amma wanda ya yi rowa, kuma ya wadatu da kansa

    [9] Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyawo

    [10] To, za Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani

    [11] Kuma dukiyarsa ba ta wadatar masa da kome ba, a lokacin da ya gangara (a wuta)

    [12] Lalle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya

    [13] Kuma lalle ne Lahira da duniya Namu ne

    [14] Saboda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka

    [15] Babu mai shigarta sai mafi shaƙawa

    [16] Wanda ya ƙaryata, kuma ya juya baya

    [17] Kuma mafi taƙawa zai nisance ta

    [18] Wanda yake bayar da dukiyarsa, alhali yana tsarkaka

    [19] Alhali babu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake neman sakamakonta

    [20] Face dai neman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka

    [21] To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da za a ba shi)

    Ad-Duha

    Surah 93

    [1] Ina rantsuwa da hantsi

    [2] Da dare a lokacin da ya rufe (da duhunsa)

    [3] Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙi kaba

    [4] Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko

    [5] Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta ba ka kyauta sai ka yarda

    [6] Ashe, bai same ka maraya ba, sa'an nan Ya yi maka makoma

    [7] Kuma Ya same ka ba ka da shari'a, sai Ya shiryar da kai

    [8] Kuma Ya same ka matalauci, sai Ya wadata ka

    [9] Saboda haka, amma maraya, to, kada ka rinjaye shi

    [10] Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsawa

    [11] Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (domin godiya)

    Ash-Sharh

    Surah 94

    [1] Ba Mu buɗa maka zuciyarka ba (domin ɗaukar haƙuri da fahimta)

    [2] Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe

    [3] Wanda ya nauyayi bayanka

    [4] Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka

    [5] To, lalle ne tare da tsananin nan akwai wani sauƙi

    [6] Lalle ne tare da tsananin nan akwai wani sauƙi

    [7] Saboda haka idan ka ƙare (ibada) sai ka kafu (kana roƙon Allah)

    [8] Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi

    At-Tin

    Surah 95

    [1] Ina rantsuwa da Attinu da Azzaitun

    [2] Da Dur Sinina

    [3] Da wannan gari amintacce

    [4] Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa

    [5] Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni

    [6] Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda ba ya yankewa

    [7] To, bayan haka me ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bayan Tashin ¡iyama)

    [8] Ashe Allah ba Shi ne Mafi masu hukunci kyawon hukunci ba

    Al-'Alaq

    Surah 96

    [1] Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta

    [2] Ya hahitta mutum daga gudan jini

    [3] Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci

    [4] Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami

    [5] Ya sanar da mutum abin da bai sani ba

    [6] A'aha! Lalle, ne mutum haƙiƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu)

    [7] Domin ya ga kansa, ya wadata

    [8] Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take

    [9] Shin, ka ga wanda ke hana

    [10] Bawa idan ya yi salla

    [11] Ashe, ka gani, idan (shi bawan) ya kasance a kan shiriya

    [12] Ko ya yi umurni da taƙawa

    [13] Ashe, ka gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya juya baya

    [14] Ashe, bai sani ba cewa Allah Yana gani

    [15] A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne za Mu ja gashin makwarkwaɗa

    [16] Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi

    [17] Sai ya kirayi ƙungiyarsa

    [18] Za Mu kirayi zabaniyawa (mala'iku masu girma)

    [19] A'aha kada ka bi shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka)

    Al-Qadr

    Surah 97

    [1] Lalle ne Mu, Mun saukar da shi (Alƙur'ani) a cikin Lailatul ƙadari (daren daraja)

    [2] To, me ya sanar da kai abin da ake cewa Lailatul ¡adari

    [3] Lailatul ¡adari mafi alheri ne daga wasu watanni dubu

    [4] Mala'iku da Ruhi suna sauka a cikinsa da iznin Ubangijinsu saboda kowane umurni

    [5] Sallama ne shi daren, har fitar alfijiri

    Al-Bayyina

    Surah 98

    [1] Waɗanda suka kafirta daga mutanen Littafi, da mushirikai, ba su kasance masu gushewa daga gaskiya ba har hujja ta je musu

    [2] Wani Manzo daga Allah, yana karatun wasu takardu masu tsarki

    [3] A cikinsu akwai wasu littafai masu ƙima da daraja

    [4] Kuma waɗanda aka bai wa Littafi ba su saɓa wa juna ba face bayan hujjar ta je musu

    [5] Kuma ba a umarce su da kome ba face bauta wa Allah suna masu tsarkake addinin gare Shi, masu karkata zuwa ga addinin gaskiya, kuma su tsai da salla kuma su bayar da zakka, kuma wannan shi ne addinin waɗanda suke a kan hanyar ƙwarai

    [6] Lalle ne waɗanda suka kafirta daga mutanen Littafi da mushirikai sana cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta. Waɗannan su ne mafi ashararancin talikai

    [7] Lalle ne waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, waɗannan su ne mafifita alherin halitta

    [8] Sakamakonsu, a wurin Ubangijinsu, shi ne gidajen Aljannar zama, ƙoramu na gudana daga ƙarƙashinsu suna madawwama a cikinta har abada. Allah Ya yarda da su, kuma su, sun yarda da Shi. wannan sakamako ne ga wanda ya ji tsoron Ubangijinsa

    Az-Zalzala

    Surah 99

    [1] Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta

    [2] Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi

    [3] Kuma mutum ya ce "Me neya same ta

    [4] A ranar nan, za ta faɗi labarinta

    [5] cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta

    [6] A ranar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu

    [7] To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi

    [8] Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi

    Al-'Adiyat

    Surah 100

    [1] Ina rantsuwa da dawaki masu gudu suna fitar da kukan ciki

    [2] Masu ƙyasta wuta (da kofatansu a kan duwatsu) ƙyastawa

    [3] Sa'an nan masu yin hari a lokacin asuba

    [4] Sai su motsar da ƙura game da shi

    [5] Sai su shiga, game da ita (ƙurar), a tsakanin jama'ar maƙiya

    [6] Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa

    [7] Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa dl haka

    [8] Kuma 1alle ne ga dukiya shi mai tsananin so ne

    [9] Shin, ba ya da sanin lokacin da aka tone abin da yake cikin kaburbura

    [10] Aka bayyana abin da ke cikin zukata

    [11] Lalle ne Ubangijinsu, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne

    Al-Qari'a

    Surah 101

    [1] Mai ƙwanƙwasar (zukata da tsoro)

    [2] Mene ne mai ƙwanƙwasa

    [3] Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa mai ƙwanƙwasa

    [4] Ranar da mutane za su kasance kamar 'ya'yan fari masu watsuwa

    [5] Kuma duwatsu su kasance kamar gashin sufin da aka saɓe

    [6] To, amma wanda ma'aunansa suka yi nauyi

    [7] To, shi yana a cikin wata rayuwa yardadda

    [8] Kuma amma wanda ma'aunansa suka yi sauƙi (babu nauyi)

    [9] To, uwarsa Hawiya ce

    [10] Kuma me ya sanar da kai mece ce ita

    [11] Wata wuta ce mai zafi

    At-Takathur

    Surah 102

    [1] Alfahari da yawan dukiya da dangi ya shagaltar da ku (dagaibada mai amfaninku)

    [2] Har kuka ziyarci kaburbura

    [3] A'aha! (Nan gaba) za ku sani

    [4] Sa'an nan, tabbas, za ku sani

    [5] Haƙiƙa, da kuna da sani sani na yaƙini

    [6] Lalle ne da kuna ganin Jahim

    [7] Sa'an nan lalle ne za ku gan ta, da idanu, bayyane

    [8] Sa'an nan lalle ne za a tambaye ku, a ranar nan labarin ni'imar (da aka yi muku)

    Al-'Asr

    Surah 103

    [1] Ina rantsuwa da zamani

    [2] Lalle ne mutum yana a cikin hasara

    [3] Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka yi wa juna wasiyya da bin gaskiya, kuma suka yi wa juna wasiyya da yin haƙuri (su kam, basu cikin hasara)

    Al-Humaza

    Surah 104

    [1] Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa)

    [2] Wanda ya tara dukiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa

    [3] Yana zaton cewa dukiyarsa za ta dawwamar da shi

    [4] A'aha! Lalle ne za a jefa shi a cikin Huɗama

    [5] Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa Huɗama

    [6] Wutar Allah ce wadda ake hurawa

    [7] Wadda take leƙawa a kan zukata

    [8] Lalle ne ita abar kullewa cea kansu

    [9] A cikin wasu ginshiƙai miƙaƙƙu

    Al-Fil

    Surah 105

    [1] Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba

    [2] Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba

    [3] Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsaye, jama'a-jama'a

    [4] Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta

    [5] Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye

    Quraish

    Surah 106

    [1] Saboda sabon ¡uraishawa

    [2] Sabonsu na tafiyar hunturu da ta bazara

    [3] Saboda haka sai su bauta wa Ubangijin wannan Gida (Ka'abah)

    [4] wanda Ya ciyar da su (Ya hana su) daga yunwa, kuma Ya amintar da su daga wani tsoro

    Al-Ma'un

    Surah 107

    [1] Shin, ka ga wanda ke ƙaryatawa game da sakamako

    [2] To, wannan shi ne ke tunkue maraya (daga haƙƙinsa)

    [3] Kuma ba ya kwaaitarwa bisa bayar da abinci ga matalauci

    [4] To, bone ya tabbata ga masallata

    [5] Waɗanda suke masu shagala daga sallarsu

    [6] Waɗanda suke yin riya (ga ayyukansu)

    [7] Kuma suna hana taimako

    Al-Kauthar

    Surah 108

    [1] Lalle ne Mu, Mun yi maka kyauta mai yawa

    [2] Saboda haka, ka yi salla domin Ubangijinka, kuma ka soke (baiko, wato sukar raƙumi)

    [3] Lalle mai aibanta ka shi ne mai yankakkiyar albarka

    Al-Kafirun

    Surah 109

    [1] Ka ce: "Ya ku kafirai

    [2] Ba zan bauta wa abin da kuke bauta wa ba

    [3] Kuma ku, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bauta wa ba

    [4] Kuma ni ban zama mai bauta wa abin da kuka bauta wa ba

    [5] Kuma ku, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bauta wa ba

    [6] Addininku na gare ku, kuma addinina yana gare ni

    An-Nasr

    Surah 110

    [1] Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara

    [2] Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya-ƙungiya

    [3] To, ka yi tasbihi game da gode wa Ubangijinka, kuma ka neme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tuba ne

    Al-Masad

    Surah 111

    [1] Hannaye biyu na Abulahabi sun halaka, kuma ya halaka

    [2] Dukiyarsa ba ta tsare masa kome ba, da abin da ya tara

    [3] Za ya shiga wuta mai huruwa

    [4] Tare da matarsa mai ɗaukar itacen (wuta)

    [5] A cikin kyakkyawan wuyanta akwai igiya ta kaba (Ranar ¡iyama)

    Al-Ikhlas

    Surah 112

    [1] Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaici

    [2] Allah wanda ake nufin Sa da buƙata

    [3] Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba

    [4] Kuma babu ɗaya da ya kasance tamka a gare Shi

    Al-Falaq

    Surah 113

    [1] Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya

    [2] Daga sharrin abin da Ya halitta

    [3] Da sharrin dare, idan ya yi duhu

    [4] Da sharrin mata masu tofi a cikin ƙulle-ƙulle

    [5] Da sharrin mai hasada idan ya yi hasada

    An-Nas

    Surah 114

    [1] Ka ce "Ina neman tsari ga Ubangijin mutane

    [2] Mamallakin mutane

    [3] Abin bautawar mutane

    [4] Daga sharrin mai sanya wasuwasi, mai ɓoyewa

    [5] Wanda ke sanya wasuwasi a cikin ƙirazan mutane

    [6] Daga aljannu da mutane